Hausa Novels

Auren Gado Complete Hausa Novel

Sponsored Links

 

*AUREN GADO*

 

*Matar s

 

 

 

Daga marubuciyar

KUKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO, ……

 

 

 

*ASLM MAKARANTA, INA YIWA KOWA FATAN ALKHAIRI, GODIYA MARA IYAKA ZUWA GA MASOYA RUBUTU NA A DUK INDA KUKE, JINJINA TA BANGIRMA GAREKU, SOYAYYAR KU ABIN ALFAHARI CE AGARENI, GOYON BAYANKU SHINE SILAR CIGABA NA ALLAH YA BARMIN KU A DUK INDA KUKE CIKIN AMINCI, TUNDAGA MASOYANA NA NIGERIA DA KUMA NA KETARE INA WA KOWA FATAN ALKHAIRI, NAFA DAWO BATAREDA NA SHIRYA BA DOMIN KU MASU BIYONI SUNA ROKONA, MATAR SOJA KIFARA MANA AUREN GADO MUN MATSU, TOH GASHI NAN SAI NEMAN GOYON BAYAN KU KAMAR KODA YAUSHE,*

 

*with ur help wnn lbrn zaitafi AUNTY  deeja domin bantaba tsallaka koda airport ba don haka keep guiding me akan komai, and please make sure kin turomin na jirgi nasameki a bangkok din nan just once please, tunda corona ta hanani zuwa makka bana, but don’t worry kudin na gona just pray muyi harvesting buhu dari na soya beans, bana zamuje vocation a duk fadin bangkok, ayi kokari a biya don Allah zansiya takin gona 😉*

 

BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM

 

 

 

 

🆓 page

 

 

 

1⃣&2⃣

 

A kwance yake abakin wani tafkeken beach , yana kallon duk matan dake kaida kawowa a wurin cikin fitinannun bikini da kuma lafta laftan sun glasses, wani irin ya mutse fuskar shi yakeyi domin kamar kashi haka yake ganin su, ba Abinda ya dameshi, bayajin mace zata iya burgeshi just like that saboda shigar banza,

Kallon shi nayi dakyau, gayen ba laifi chocolate ne shi duk da banga idanun shi ba saboda suna boye a cikin sun glass, Amma nasan zasu kasance masu kyau da tsari, lips dinshi kuwa I can clearly see them suna sheki very soft and shinny, he is behaving like jinin sarauta Amma I don’t know yet who is he? Gefen shi system dinshi ne tareda wayoyin shi guda biyu, daya tayi kara ya dauka cikin sauri domin ganin sunan dake jikin screen din wayar, “heartbeat, Hmmm no wonder mata basa burgeshi duk da yawon da sukeyi a gabanshi necked, sai dai me, yanda yake zuba shagwaba tareda maganar da yakeyi yasa mamaki ya cikani domin daga gani bada mace yake magana ba, is he a gay???

 

“Yaya please, wai kai are you really serious you are getting married??,

Banajin maganar dayan side d’in saidai Amsar shi, “of cos yaya dole inzo Auren ka nine fa best friend best brother and ur best partner in life, am coming insha Allahu, but kasan halin momy kuma I don’t want problem shiyasa nake zama na a bangkok, is alright am on my way don’t worry heartbeat, just for you.

Datse call din yayi ya mike, a lokacin na kalleshi da tsarin jikinshi daba riga sai guntun wando kawai ga six packs dinshi da suka fito gwanin burgewa alamar yana gyming, tareda kulada lafiyar jikinshi sosai, zare sunglass din yayi, na kalle sexy eyes da lashes dinshi kamar na mace zaro zaro, he is really handsome, one look zakiyi mai ki afka soyayyar shi indai zaki kalli wa’innan killer eyes dinshi, gashi ya iya juyasu, kamar wani karuwar namiji, cikin takun kasaita ya zura beautiful sleepers dinshi na maza ya kwashi kayanshi tareda key ya nufi can gefe inda ya parker open jeep dinshi, ya zube su tareda zama yajata a guje yabar wurin,.

 

Wani D’an madai daicin gidane a cikin jerin gidajen dake cikin unguwannin dake shahararriyar Unguwar ta

Phetchaburi Road, Makkasan,

Ratchathevi, Bangkok 10400 Thailand. unguwa ce ta wanda ya tada Kafada da Abubuwan duniya, duk da gidan da ya shiga ba wani kato bane amma kana ganin shi kasan ya gaji da haduwa, maid dinshi ne yayi saurin taron shi da gorar ruwa tareda towel, karba kawai yayi ya nufi bathroom, ya dauki Kusan hour guda kafin yafito kamar zai canjo fata,

Yana fitowa daure da guntun towel ya tsaya Turus tareda zubawa dakin ido yana mamakin ta, tayi mai dai dai tareda kashe shi da idanu, he just hate that character a wurin mace, shi so yake rana daya Allah ya hadashi da mace mai kunya, that is, tagama siyemai zuciya, but this kind of girls dake rayuwa a irin wannan garin wai in the name of study, Ahh he really hate them, karuwai kawai,

Ganin kallon rainin wayau Dayake watsa mata yasa ta zaburo tareda matsowa cikin rangwada, doguwar riga ce har kasa she cover all her body but akwai gyara a al’ amarin ta, duk da kyakykyawa ce gata a dire, kuma fara tas bai hana kagano idanun ta sun bude,.

“Hey dear tafada cikin kashe murya, wani irin kallon don’t touch me ya mata tayi saurin daga hannun ta sama tareda cewa “is ok I won’t dear, but please  just once give me chance to prove myself.

“Dont even try to suffer ur self, nafada miki fauzy am not interested, just back up. ” am ready to follow you I promise zanyi duk y’anda kakeso am ready to change for you, nafada ma dady na kai nakeso zamu koma kano tare dakai please na horu ka soni don Allah, “Look don’t even try, bazan Auri sauran wasu ba  infact am not ready for marriage now shiyasa dana gama school naki komawa gida saboda nasan Abinda zai faru, don haka kifita a rayuwa ta banason naci. Kuka tasa mai tareda  dukawa kasa, “I swear bantaba bari wani yasanni ba kawai romance ne kuma kasan is a normal thing ai, kana ganin saboda kai nakasa komawa gida kullum cikin karya nake musu please  karka tarwatsa min Rayuwa kaine cikon numfashi na, tausayin ta yaji sosai domin ta dade tana wahala a kanshi tun baya kulata har yafara D’an sauraran ta, “Oh come on, kinsan natsani kuka ko, ki shirya am going tomorrow mutafi nija am going for good, if you are ready….. “Of cos dear am ready, tafada tana dariya mai hade da tausayin kanta, goge hawaye tayi tafita cikin sauri domin ganin ta tattara duk Abinda zata bukata.

“Ahhh yafada tareda dafe kai, this girl is headache I swear,

Shiryawa yayi cikin guntun wando da black singlet yafito gwanin burgewa  sai tsadadden agogon shi da kuma dankwalelen zoben dake karawa hannun shi tsari da kyau wa’inda baya taba rabuwa dasu, infact ko shopping zaiyi agogo ne first a tsarin shi he just love watches saboda suna karamai tsari da kwarjini,

 

Abincin shi ya zauna yafaraci wa’inda duk ganye ne sai crabs roasted ones, saida ya dauki lokaci kafin ya kammala ya sanya tissue ya goge bakinshi ya mike, duk al’adar Chinese ta gama ratsa shi abincin su harshen su al adunsu, wainda zasuyi matukar wahalar dashi a nija,.

Saida yayi clearing komai a daren, about visa da sauransu, karfe uku na Asuba jirgin su ya daga wanda zai kasance long journey duk da a jirgine, tafiyace ta Kusan awoyi,  tana zaune a gefen shi ta zuba mai ido sai faman danna system dinshi yakeyi like ba wata halittar dake existing a kusa dashi,

 

She don’t bloody care tunda yace su koma nija tasan komai zaizo cikin sauki,

Saida  ya dauki lokaci kafin ya rufe ya saka headphones ya rufe idanun shi yana farin cikin zaije wurin yayan shi wanda yafi kowa daraja a duniya a wurin shi yana mashi so mai girma yana kaunar shi fiyeda kanshi,

Duk da su marayu ne ubansu ya mutu tun yana D’an karami, baiyi lacking komai ba, domin baban su gawurtaccen D’an siyasa ne kuma D’an kasuwa wanda yanada share a manyan campanonin dake ciki da wajen kasar mu harma da ketare, subiyu ne kacal wurin mahaifiyar su, yayan shi Ahmed sai shi Ibrahim khalel wanda khalel din  ne yafi amfani dashi,

Gatan da yake dashi baya faduwa haka kudi ba matsala bane a rayuwar su domin mahaifiyar su itama ba azaune takeba tana aiki da first bank tareda matsayi mai girma,

Akwai banbancin hali a tareda shi da d’an uwanshi, domin shi mai zuciya ne, shikuma Ahmed yanada sanyin hali da hakuri,  shakuwa ce mai girma da tausayi a tsakanin Y’an Uwan biyu sukan iyawa juna sadaukarwa ta kowacce hanya, tun suna yara balle kuma yanzu, kowa yasan how they love each other, don haka ko ginin su a hade yake basu taba raba gida ba duk da sunfi karfin hakan, katoton gidan mahaifin su suka kara fadadawa tareda buga plat biyu nasu tangama tangama sai na mahaifiyar su wanda a ciki ma akwai part part dinsu, domin bataso suyi mata nisa, mace ce mai tsananin zafi da kuma rashin hakuri gashi bata son sunan talaka bare kuma talauci batason rashin Aji a rayuwar ta don haka kullum burinta ta fantama, bakaramin shiri takeyi a Auren ya’yan taba tunkafin su tashiyi ma, saidai kash ansamu akasi domin Ahmed ya kaucewa tsarin ta ta hanyar dakko Y’ar talaka tulus, wanda bakaramin daga akasha ba kafin ta Amince da zancen Auren bayan dogayen sharuddan data gindaya bayan Amincewar ta. To muje dai zuwa yanzu zamu fara,.

 

 

 

Karfe goma jirgin nasu ya sauka a babban filin jirgin na Aminu kano, wanda sukaci karo da motoci birjik a jere na taron su, tuni fauzy ta matso “you see kamar jira akeyi indawo kaga irin motocin da sukazo daukana please ka yarda muje gidanku after two days sai intafi gida. “Hmm yafada tareda watsa mata kallon you lost ur mind, kafin ya ce “al adar Chinese ce wannan ba ta bahaushe ba don haka go home zanyi inviting dinki to my brother wedding ok,. “Ok tafada cikin farin ciki, ta nufi masu taron ta wainda kana ganin motocin kasan itama Y’ar gidan wani kwallon barawon kasar muce,.

 

Hango yayan shi da yayi yasa ya tafi da sauri cikin farin ciki ya rungume shi, Ahmed din ma kyakkywa ne suna matukar Kama saidai shi fari ne while Khaleel chocolate ne, “my yaya kai kadai kazo were is mommy?

“Long story muje ko, yafada yana karbar jakarshi karama tareda bawa driver umarnin kwaso kayan da yazo dasu yakai boot, saida suka zauna yace “Am sorry yaya sai jiya nayi placing odar na kayan matar ka zasuzo tunda by air ne kafin bikin insha Allahu nasan zakaso su.

Rungume shi yayi cikeda farin ciki tareda cewa “tank you my kani,  but please karka bari momy tasani kawai zamu Ajiye mata ne a dakina har akawo ta. “Why?  Cos momy batason ta infact bakaramin yaki akayi ba kafin ta Amince ayi komai. “Mommy mommy bazata canja ba, so why she hate her? “Because she is poor. Saurin kallon shi yayi “so brother is your foult kasan momy tunfarko ai why ka dakko poor girl uhm?

“Because I love her so much I love Naziya a lot khaleel, she is innocent and young she is very cute I can’t help it, bazan iya Auren wata ba in har aka hanani zama da ita. Rungume shi yayi cikeda so da kuma tausayin D’an Uwan nashi yace “is ok am here you know I will support you, don’t mind mommy, but her name is unique. “Yeah she is also unique brother, yafada yana lumshe idanun shi tareda jin soyayyar ta mai zafi har wasu irin madarar ruwan hawaye ne suka taru a idanun shi,.

 

A cikin fitacciyar unguwar ta sulaiman crescent suka yada Zango cikin wani tafkeken gini na kece raini, tsarin gidan kamar a turai, ya fito tareda shakar iskar kayan marmarin dake   zagaye da ginin gidan,

Harabar gidan shake yake da motoci different product da kuma runfuna na Alfarma dake karkashin bishiyoyin kwakwa ta ko ina irin na gargajiya da masu kudi keyi,.

 

Kallon shi Ahmed yayi tundaga kasa har sama “bazaka canja character dinka bako yawo daguntayen kaya imagine tundaga bangkok kazo da three quarter da t shirt baka ko jin sanyi? “Kamar ka mantani ko yaya nifa I hate heat wallahi shiyasa nake wuni a beach., zaka hadu da momy muje ciki,.

 

 

A tafkeken katon falon an tsara shi fiyeda tunanin mai karatu kujeru Kusan set uku ya mamaye amma da sauran fili kowane set da center carpet dinshi masu laushi da nutse kafafu, standing art tangama tangama ta koina bayan na jikin gini wainda suka zama kamar decoration a falon,

A tsaye take tanata kai da kawo kamar Y’ar sintiri tana jiran fevourite son d’inta, ya iso, ta hana masu aiki sukuni sun kalkale but parts dinshi yafi sau uku da safen nan,  dishes kuwa kamar a hotel saboda d’oki,

Macece hakima kamar  Aisha D’an kano margayiya taci Abuja style cikin tsadadden leshin ta wanda yafi karfin dari a jikin ta, da glashin ta na kara karfin idanu, wanda yakara fito da haiba da hutun ta harma da masu gidan ranar data tada Kafada a ciki,

 

Sallamar su yasa tamike cikeda fara’a tana “Oyoyo my happiness welcome back dear tafada tana rungume shi tareda bubbuga bayan shi, “tank you mommy munsame ku lafiya?  “Alhmdulillah tafada tareda dagowa tana “ai dai tunda kadawo yanzu zanji saukin lamura na at least inada inda zancika burina, ka huta ka dage ka dakko min Y’ar gidan bayero ko buhari, ka huce min takaici. Tafada tana watsawa Ahmed harara, dukar da kanshi yayi tareda daukar Karamar jakar D’an Uwan nashi yayi ciki da ita, zama tayi a set daya tareda janyoshi tana faman korafi tun bai hutaba, ” hope zaka dakko Y’ar gidan mutanen arziki kai ba Y’ar matsiyata ba?  “Mommy mommy mommy please meyasa kike hakane?  Nifa am here because of my brother, kinsan banason korafi kibarshi ya Auri choice dinshi koda cripple ce tunda shi zai zauna da ita please allow him to be happy I beg of you. “Shikenan tunda kaima kabi bayan shi, amma promise me zaka share min hawaye kaji? “Ok I promise bari inje in huta am tired, fresh up akawo maka abinci a ciki ko? “Yes please kinsan me nakeso ai ko? “Sosai karka damu na shirya maka komai.

A zaune yasamu brother dinshi yana dafe da kanshi ya zauna tareda dafashi cikeda tausayi “relaxed bro am here komai zaiyi normal kaji, Aunty what ma sunan ta? “Naziya, yafada fuskar shi na washewa domin sunan ta kawai nabashi farin ciki, “get ready zamuje unguwar su anjima kaganta kaji. “Ok my heartbeat. “Stop that name kafin my Naziya taji tayi kishi fa. “Oh no yaya zata shiga tsakanin mu ne, to nima zanbi bayan mommy fa. Rungume shi yayi tareda cewa “no no no tasan da zaman ka, tundaga lokacin da muka fara haduwa, da ita, ka huta zanfada maka komai game da ita kafin muje gidan,.

 

 

Karfe biyu ya farka daga baccin gajiyar da yayi yaga Ahmed zaune ya na baza kamshi cikin D’an datsesiyar getzner  tana maiko, tashi yayi “yaya har kayi wanka?  What is the time now? Agogon shi ya nuna mai ya zabura yana holy shit, ya diro a lumtsumemiyar katifar shi, yayi bathroom domin baiyi Azahar ba, cikin sauri sauri ya zura jallabiya ya tada sallah, domin duk abinda yake yi baya son wasa da ibadar shi amma idan ka kalleshi zaka dauka rayuwar duniya tafi komai ratsa shi amma yarone mai   riko da Addini bisa ga  goyon yayan kwarai da yazamo mai tamkar uba.

Saida ya idar ya bude jakar shi tareda ciro kananan kaya.

“Wait gidan kawu zamuje a mandawari  kasan halin shi ka sa manyan kaya nasa an shirya maka new ones a wardrp dinka na nan dana can side d’in.

“What?  Kasan nifa banason zafi ga garin nan da zafin tsiya kuma insa kayan da zasu hanani sakewa, “wait yaya ba an gama zuba komai ba a part dinmu why muke nan har yanzu? “Bisaga umarni na khaleel bazan yarda a saka Y’ar talakawa cikin ginin da na narkarda dukiyar mijina datawa ba, a kawo min gayyar  k’uma da kudin cizoba ta zo nan ya isheta zama tunda bazata iya zama  a katon giniba, domin ko dakin generator dinmu yafi gidan ubanta girma,. Saurin kaucewa khaleel yayi domin inda sabo sun saba,  ya nufi katon wardrp din yaga kaya shake saida yayi murmushi saboda yasan aikin yayan nashi ne,

Fito da Kala daya yayi irin na jikin shi ya nufi hanyar bathroom domin ya canja saboda mommy dake dakin,

Tana zazzaga complain, fitowa yayi tareda rungume ta yana baza kamshi shima kanshi da yasha askin matasan zamani ya na sheki ya sha gyara ya ce” mommy please enough of your complains kibar yayana yasamu farin cikin shi mana,. “Oh wato kuna tunanin bansan what is best for him ba ko?  Bayan na kawo mai yammata Kala Kala Yaran kawaye na masu ilimi amma ya nace sai Y’ar talakawa mtsww, ka kara Abinci kafin kutafi gidan kawun naku kafin yazo yana baza min fitinar shi shima yace na hanaku zuwa ku gaidashi, ta fita tana kasaita, “Hmmmm Sorry brother kariga kasan halin momy. “Is ok eat muje ko?

 

Hour guda ta kaisu gidan na kawun nasu Alhaji modu mai gwal wanda D’an kasuwa ne sosai a harkar gwalagwalai, mutum ne a tsaye akan zumuncin shi domin baida wasa yanada mata biyu da yara sunkai goma, shikadai Hajiya balkisu ke shakka domin yafita fitina kuma shima yanada kudi shiyasa take ragamishi domin sau tari yakan yimata Abu tace yaci Arzikin Aljihun shi.

Sunada kanni biyu mata bayan mahaifin su khaleel  shine babba sai Alhaji modu din, su Y’an Asalin garin maiduguri ne iyayen su ne suka kawosu babban birnin na kano, sunginu suma duka domin ba talaka a cikin su har matan ma domin suna gidajen kusoshin kasar mu,

 

 

Y’an mata ne birjik a gidan wainda kowaccen su nada burin samun daya daga cikin wa’innan zaratan mazan saidai sam su Hankalin su baya kan kannin nasu infact basa burin Auren zumunci ma, itama Hajiya balkisu bata ra’ayi domin batason ya’yan ta suyi Aure inda bazata iya juya Suruka ba,,

Domin tasan Y’an Uwan mijinta duk ba wai mutunci sukeda shiba wanketa zasuyi akan ya’yan su,

Sun samu tar bar bangirma daga uwar gidan Kawu modun kafin ya dawo,

Sundauki lokaci a gidan har kawun nasu yazo, wanda yayi farin ciki sosai ya musu nasiha tareda basu shawarori, “yanzu tunda kadawo khaleel saika tallafawa D’an Uwan ka domin yayi matukar kokari wajen tafiya da campanoni da kuma masana’antun ku, sai kuci gaba da tafiyar da kasuwancin ku cikin tsari, Sannan naje munyi magana da uban Naziya, Auren naku nan da sati biyu aka tsayar don haka ka je ka karasa shirin ka  “na kammala komai kawu ni ta wajena. “Toh masha Allah, sai mu jira lokaci Allah ya tabbatar da Alkhairi, Amma dattijon nata mutumin Arziki ne baidamu da Abin duniya ba gaskiya karka damu da shirmen mata wannan gidan irin shi ya kamaci namiji ya nemi Aure. Wani irin dad’i yaji tareda sauke Ajiyar zuciya, saida suka yi magrib kafin su bar gidan, suna hanya yana bashi labarin Naziya,…….. 🖊

 

 

*watch out, domin salon zai tafiyar daku masoya muje zuwa*

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻 *AUREN GADO* 🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

 

🆓 page

 

 

3⃣&4⃣

 

 

………….. D’an karamin gidane mai zaure a cikin tsohuwar unguwar ta jakara, almajirai ne birjik a zauren da Alama malami ne a gidan  mai Y’ar Karamar tsangayar Almajirai,  ko tsakar gidan ma akwai wasu dakuna dake dauke da Almajirai, rayuwar gidan sun dauki Almajiran kamar Yaran gida ba kyama ba wulakanci, matar gidan inna kulu mace mai hakuri, tanada ya’ya  mata guda hudu manya biyu sunyi Aure sai Naziya da kanwar ta Shukrah, Yanzu Naziya nada shekara goma shatakwas sai shukrah mai shabiyar, ta kammala secondary dinta Bana a makarantar gwamnati, a tsugune take tana wanke kwanonin da suka bata Y’ar Karamar wayarta ce a kunne a gefen ta tana sauraron karatun Al’qur’ani mai  girma tana bi a hankali cikin kwarewa,

Kare mata kallo nayi domin yarinyar batayi Kama da kalar talaka ba  domin dai dai da duddugen kafarta farare ne tas kyakkywa ce sosai kamar wata Y’ar larabawa tana sanye da guntun hijabi akan al adar ta da kuma koyarwar inna kulu domin gidan su akwai mazajen Almajirai akoda yaushe,   fitowa dattijuwar tsohuwar tayi tareda cewa “inkin kammala ki dora mana Abincin rana Naziya, shukrah ta kai mana markade tunda duk babu  Almijirai yau, “toh Inna. Tafada tana wanke wurin data bata, she is really cool and beautiful ga tarbiya dake tattare da ita jikinta ba rama kuma bakiba duk da tana cikin hijabin ta nagano hakan jikinta D’an dai dai bazaka taba yimata kallon talauci ba duk da Abinci baifi karfin tukunyar suba, mahaifin su yana koyarwa yana sana’oin shi wanda yake daukar gidanshi da kuma hidimomin iyalin shi,

Haduwar  ta da Ahmed wata rana ce tadawo makaranta a gajiye shikuma yazo unguwar su gidan wani yaron shi dabaida lafiya, tafiya takeyi cikin gajiya a kuma natse ta gefen titi, y’anda ya kwaso motar tashi yasa ya watsa mata ruwan datti kasancewar gari ne na damuna ga kuma yanayin unguwar da yatara guraben ruwa ta ko Ina,  saurin jatayi ta tsaya domin gaba daya uniform d’inta ya baci Har fuskar ta ma ruwan ya fallatso mata, saurin fakawa yayi ya fito da sauri yana so yabata hakuri,

Dago kyawawan idanun ta tayi tareda goge fuskar ta da gefen hijabin ta inda jan ruwan bai bata ba, ta kuma kallon y’anda ya saki baki yana kare mata kallo batareda ya iya cewa komai ba, yarinyar ta gama tafiya dashi, juyawa tayi ganin baida niyyar cewa komai tayi gaba, saurin shan gaban ta yayi “Am sorry please ki tsaya muyi magana, ya zaki wuce batareda kince komai ba bayan nayi miki laifi?

Saurin Tsayawa tayi tareda dago idanun ta masu narkar da zuciya tace “nice zanbaka hakuri domin hanyar bata Y’ar talaka bace Nazo kuma na tsaya, sannan don Allah ka matsa in wuce kafin ayi wani tunani akaina a cikin unguwa ba mutuncin gidan mu bane tsayuwa da bako a kan titi. Tafada tana rabewa tayi gaba.

“Wow wow wow what a magic voice, yafada yana binta a hankali tana sauri har ta fada gidan su da gudu domin tana jin takun shi a bayan ta   a mugun tsorace take dashi domin yayi Kama da Aljani a wurinta domin he is very handsome kana ganin shi kaga D’an hutu,.

 

Gefen Ahmed tunda yasa Naziya a ido yakasa sukuni saida yabi ta gefen yaron shi yaji komai akanta, tuni yagano Y’ar babban gidace wato gidan dattijan kwarai,  baiyi kasa a guiwa ba ya dawo yasamu mahaifinta tareda neman izinin neman ta, Malam garba yaso ya hana domin ganin D’an gidan wani ne Bayason ya saka Y’ar shi cikin matsala, ya nuna mai mahaifin shi ya rasu kuma shike rikeda kanshi ba wata matsala, bai Amince ba saida ya turo kawun shi yazo suka tattauna ya Amince yabada izinin neman ta,.

 

Allah yagani bawai Ahmed baiyi mata bane, ita batada burin shiga gidan da yafi karfin ta wanda bata ma riga taga dukiyar ba tukun kawai shitake gani   kudin su na bata tsoro, ganin irin k’a’i dar mahaifin ta,  baya ko sake mata kudi infact tuni ya daina zuwa da shigar da zata hanata sakewa dashi domin ya lura da yanayin ta dana gidan su tsab, yasamu kanta ta hanyar nuna mata akarkashin wani yake shima yana hustling ne,. Shiyasa yasamu kanta har ta Amince suka Gina soyayya mai karfi a tsakanin su she really loves him domin he is very simple baida fushi baida girman kai saurayi ne mai natsuwa wanda ko yatsanta bai taba kokarin kamawa ba soyayya yake mata mai tsafta, har kawo yanzu da Al amarin yakai ga zancen Aure, zaman ta dashi tagano Abu biyu sune masu matukar muhimmanci a rayuwar shi, mommy and khaleel wanda basa hira sutashi bai kira sunan shi ba tagano irin tsantsar soyayyar da yakewa kanin nashi ta hanyar bata labarin shi a kullum zaice “in munyi Aure zaki rika dafa mai Abincin da yakeso baya son irin namu na nija zansa akoya miki irin dishes din da yakeso.  Abun na bata mamaki ace mutum Abincin mu na nija mai shegen test baya burgeshi sai mara magi? she almost know everything about him by now saboda labarin shi, tasan yana karatu a waje kamar yadda Ahmed yafada mata kawun su ya kaishi waje karatu, Ita kanta so take taga wannan khaleel din da labarin shi baya karewa a bakin Ahmed,. Tana son Ahmed sosai halin shi, yanayin natsuwar shi ya banbanta da na samarin zamani masu burin cakumar mace da sunfara soyayya……..

Wannan shine D’an takaitaccen labarin Naziya da Ahmed.

 

 

A hanyar su ta dawo wa daga sabon titi yake bashi labarin komai na su Naziya tareda fadamai boye mata kudin da yayi saboda batason mai kudi y’anda ta nuna mai. Khaleel yasamu kanshi da yin dariya, ” she is funny wace mace ce  batason hutu da kudi in this era? ” my Naziya wants a simple life ba a ginata akan greedness ba, all this kyale kyalen duniya basa burgeta do you know nasha siya mata gifts in ajiye domin gudun matsala ko fushin ta, do you know tun zaman mu bata taba demanding tana bukatar wani Abu a wurina ba, “she is such a diamond in the rocks, she is different khaleel my Naziya is perfect I told you. “Hmmm Allah yasa tana sonka like you love her? “She do Insha Allahu, koda baikai wanda nake mata ba nasan tana sona,

Karar wayar khaleel yasa yace “my God this witch. Yafada yana cutting call din. “Fauzy right?  “Yes yaya ta cika naci bana son mace mai naci. “Hhhhh you are lucky khaleel fauzy batada laifi and secondly irinta mommy keso Y’ar gidan wasu kaga babanta ne minister na kudi, don haka bakada matsalar mommy kabada kai musha biki bayan nawa.   “Yaya why ake Aure? “Hhhh khaleel saboda Aure sunnah ce mai karfi, sannan ba Abinda ke karawa namiji mutunci irin Aure, ga kuma samun natsuwa da soyayya idan kayi dace. “Yaya I don’t need any natsuwa a wurin mace ni. “Ah bakada lafiya ne?  “Kalau nake kawai bana jin akwai macen da zatasa inji ni a namiji sai kawai in lafiyata ta motsa,. “You are wrong khaleel, kana samun macen da kakeso manhood dinka yadaina  kwanciya cikin sauki, domin the moment you fall in love, zaka ji duk duniya ba Abinda kakeso sai kasamu kwanciyar hankali da farin cikin zuciyar ka, you are my younger brother but bazan boye maka ba na matsu ba a daura min Aure da Naziya ba am eager to have her ban taba jin lafiya ta tana aiki ba saida na hadu da ita, don haka kaima duk ranarda ka afka soyayyar wata zaka gano komai. Dariya kawai yayi domin shi yasan lokacin da kawai yake samun erection sai inya tashi a bacci yake sanin he is healthy ba wata Y’ar macen dake daga mai hankali   domin bai sawa ranshi ba ma bare Abun duniya ya dame shi.

 

Cikin unguwar suka nufa wadda tuni yaji wani iri musamman irin kofar gidan dayaga sun tsaya  Almajirai birjik sunata karatu ga hasken farin wata daya dallare KO Ina fiyeda hasken lantarkin dake wurin,   wayar shi ya daga tareda danna number ta, ba bata lokaci ta daga hade da yin sallama, “Gimbiya kifito ku gaisa da heartbeat tare muke dashi.

Cikin murna ta mike tace “gani nan zuwa yanzu inga wannan kanin namu.

Yana kishingide ko motsi baiyi ba impact bayajin zai iya fitoda takalmin shi wajen wannan unguwar, dole momy tayi spark ai, don ma batazo tagani ba ma da in sama da kasa zata hade ba Yarda zatayi ba  yasani.

Fitowa tayi cikin natsuwar ta sanye da hijabin ta, ta karaso jikin motar dayake tsaye nad’e da hannu, ya zubawa kofar gidan idanu har ta karaso kusa ta d’an tsaya nesa kadan kanta akasa ta gaida shi, “Ina wuni. “Lafiya kalau gimbiya ya kike? “Alhamdulillah, cikin  muryar ta mai cikeda natsuwa, kwankwasa glass din motar yayi, ya sauke a natse tareda gyara zaman da yayi kamar wani sarki,  kamshin shi mai matukar tsada ya huro tareda muryar shi mai cikeda wasu irin sirrika suka sakata dago kai cikin  sauri,

A cikin kyawawan idanun shi nata yasauka domin hasken motar na haskashi dakyau, wani irin sanyi jikin ta yayi Mata domin Sam baiyi Kama da sunan kanin Ahmed ba a wurin ta saidai Yaya, irin cika motar da yayi da kwarjinin shi tareda kamshi da cikar haibar shi, kallo daya ta sauke idanun ta akanshi Wanda tsab da ita gwanace ya isa ta Zane hoton shi, daga ganin shi bazaiyi yawan magana ba, kuma zaiyi miskilanci sosai. Tunanin ta ya katse ne lokacin da taji saukar muryar shi a cikin kunnen ta “Yayana naga Auntyn zamu iya tafiya ko?  Shine kalmar data fito kawai batareda gaisuwa ko wani dogon zance ba. Ta shirya sakewa dashi domin karo dankon soyayyar ta a zuciyar Ahmed,  amma is impossible yanzu don taki jinin girman kai da nuna isa just because yaje waje karatu, tuni taji yafita a ranta takuma daura damarar Kama kanta da Al amarin shi koda ta shiga gidan nasu,.  Saida Ahmed ya leka kanshi tareda zuba mai ido “come on brother kafito mana ku gaisa da kyau, “no mungaisa daga nan ka sallameta mutafi nagaji kasan bangama hutawa ba, yafada a mugun kagare yake subar wurin yanajin warin Almajirai daga inda yake Idan yakara more minutes a wurin he will surely vomit,. Ya lura da yanayin shi don haka a gurguje ya sallameta ta tafi tana mai jin takaicin wannan khaleel din,.

Yana tada motar yace “Yaya wannan Y’ar yarinyar zaka Aura?  Why?? she is too young for you please, fuskar shi a kwabe, “hhhhh she is perfect banason Auren katuwar mace ko over twenty nafison irinta mutum ya mori kuruciyar ta yafi Amma Idan ka Auri wayayyun mata bazaka mori komai ba, nafison innocent girl da zankoya wa komai,. “Hmmm zakasha aiki wallahi ai wahala zakayi kafin wannan ta iya daukar ka, kuma Yaya iyayen ta suka yarda suyi mata Aure? “Yes saboda mu anan takai Aure tunda ta kammala secondary,.

“What?  Yaya this is too much, da Ina nan bazan bari kafara sonta sosai ba gaskiya. “You are too late now, domin inaji a jikina Idan ban Auri Naziya ba zaku iya rasani  so ku tayani Addu’a kawai Ina son ta fiyeda tunanin ka nasan you will always support my back. “Of cos brother Insha Allah.

 

 

Karfe goma suka isa unguwar su, Wanda mommy Saida taci gaba da fada “kunje ghetto Area ko nasani saiya jamun kai, ka wuce kayi wanka kazo kuci Abinci kaima wuce ka watsa wainnan kayan dustbin kafin ka dawo falon nan kajini ko?  Wucewa yayi cikin sanyin jiki ya tafi dakin shi Yana mai jin bakin cikin halin na momyn shi, kasa fitowa yayi saboda rashin jin dadin Abun, shima khaleel kasa cin komai yayi ya kalli momyn dake kan korafi “mommy why please?  Ki yi hakuri Ki daina fada akan abunda dole za ayi. “Yes za ayi Amma ni Balkisu bazan bari ya cakuda min iri da na talakawa ba mu zuba tunda dangin ubanku sun nuna sunfini iko akan shi  ni kuma zan nuna musu sai naso komai ketafiya mu zuba nida su.

“Momy ji nake kamar in koma bangkok kawai domin bazan iya tsayawa inga d’an uwa na a damuwa ba, please Ki barshi ya samu natsuwa mana. “Khaleel, kana ganin uwa zataki d’an tane?  Ina son Ahmed kamar yanda nake sonka saidai bazan iya  kawar da idona akan kwashi kwaram din da zai debo min ba.

Mikewa yayi kawai cikin fushi yabar mata Abincin yayi dakin yayan nashi,  a kwance yake Yana tunani, dafashi yayi, dagowa yayi tareda rungume Khaleel din, “brother am worried, bansan irin zaman da zamuyi da Naziya a gidan nan ba, bana so injefa Y’ar mutane a damuwa bayan an bani amanar ta. Bubbuga bayan shi yayi “karka damu Ina nan zan taimaka maka ba Abunda zai samu baby doll dinka. Yafada cikeda dariyar tsokana domin ya kwantar da hankalin d’an uwan nashi,

Shigowa tayi dauke da tray tana fara’a domin taga Alamar Idan tayi sake yaran  nata zasu juya mata baya akan zancen Auren nan, Wanda bazata taba Yarda da hakan ba,

 

 

“Toh yaran momy ga Abincin nakawo muku ni na damu kuci, kashin awaki, ta ajiye a tsakiyar gadon tareda jansu da hira kamar zata mayarda su ciki, tuni suka ware suka kwashi deshes din, tana cewa “bayan rasuwar mahaifin ku nayi iya bakin kokari na ganin bakuyi maraici ba, Alhamdulillahi yau dukan ku kunkai matasa Abun Alfahari a wurina,  forgive your mother Ahmed na dauki buri mai girma akan ku naso nice zanyi maku zabin matan da suka dace daku Amma ka watsa mun duk shirina Ahmed. “Am sorry momy, kuma nayi miki Alkwarin zaki samu Naziya a duk yanda kikeso bazakiyi dakin sani ba yarinyace mai tarbiya da kin Amince da tuni nakawo miki ita ma kingan ta. “Aa tunda ansa rana ai lokacin zaizo don haka basai ka kawo taba, bakomai zan cika burina akan khaleel. “No mommy khaleel ma yanada tashi zabin ai, yafada Yana kashe mai ido, “no no no bana sonta Yaya please meye haka she is my mate fa tare muka kammala karatu why zaka ce Ina sonta ita keso na ni banga Y’ar da zanso ba har yanzu’

Wani irin dadi mommy taji ganin khaleel bazai juyuba a wurin mace tunda ita keso shi bayaso ai irinta takeso, “wow Auta na wacece wannan yarinyar? “Mommy Y’ar gidan minister kudin Nigeria ce, “what?  Tafada tana dafe kirji, “Y’ar gidan mai nasara kake fada? Oh my god khaleel, ta rungume shi, that’s my son, ka kawomin ita kaji kace tazo inganta Amma ka gama wanke min zuciya d’an nan. Tafada tana mikewa bari inkira Auntyn ku infada mata tafara shirya mana babbar harka ta Fita tana danna kiran kanwar tata mai ra’ayi irin nata. Binta sukayi da kallo suna mugun mamakin halin na mommy, sai kace wadda bata jiku da kudi ba, kullum she is hungry for more, kallon Ahmed yayi da fuskar tausayi yace “why zaka fada mata Yaya kasan am not ready, kuma yanzu tunda taji bazata taba bari insha ruwa in Ajiye cup ba. “Is OK fauzy love you a lot kuma meye laifinta nasan tun lokacin da kuke tare, ya isa haka ka Amince bayan nawa kawai a daure min kai, do you know, Ina mafarkin ganin Auren ka?  Ina so inyi witnessing Auren ka inga jinin ka. “Hhh oh come on Yaya kamar wani tsoho na barin wasiyya please tare zamu cika gidan nan da yara, “who know Khaleel? Allah kadai yasan me zai faru gobe, kasan cewa nan gaba kaine zaka rike gidan nan?  “Why Yaya?  Indai har kana nan bazan taba daukar girma ba saidai in tafiya zakayi dole in rike kana dawowa zanbaka komai domin ka shagwaba ni tuntasowa ta Abu daya nasani shine in saka master card dina inciri duk Abunda nake so ba tareda antanbaye ni me nayi dasu ba, Yaya nasan kudin da daddy yabari bawai haihuwa sukeyi da kansu ba kaine kakara habaka su har suka kai haka kaine jigon gidan nan bazan taba iya Abinda kakeyi ba…… “Shhhhhh zakayi Idan bana nan fiye ma da Wanda zanyi saboda I believe kai jarumi ne kafini iya tafiyar da Rayuwa. “Enough of this discussion kana sani a damuwa. “OK now kakira fauzy kafara bata kulawa domin tunda zancen yaje kunnen mommy ba fashi, yafada Yana dariya,.

 

Fita yayi daga dakin yayan nashi yanajin wani iri “Aure?  Gaskiya bai shirya ba infact zaiyi ne saboda yayanshi ya insisting kuma koda baison Abu Idan yayan shi na sonshi dole shima ya soshi, Allah kadai yasan iyakar soyayyar da yake wa d’an uwan nashi, kwanciya yayi a kujera a dakin nashi Yana mai runtse idanun shi, so yake ya tuna komai na fauzy da quality’s dinta just for Ahmed, Amma first thing da yafado mai a rai yasa ya zabura  tareda  girgiza kai, “no no no why her?

Cikin Sauri ya dauki wayar shi domin ya k’aryata  tunanin shi, fauzy ya Kira, kamar mai gadin wayar ta ta dauka jikin ta na rawa “oh my goodness darling you call me?  Tafada tareda Sanya kukan farin ciki, tundazu take kiranshi yaki dagawa har wani zazzabi takeji saboda damuwa tana yimai wani irin so mara misali. Tun isowar ta ake tarairayar ta Amma duk natsuwar ta bata tare da ita,

“Yes I call. Yafada Yana gyara zaman shi domin baisan ma mai zaice ba kuma. “Tank you darling for calling, please Ina so inganka kasan is hard for me kwana daya bansaka a idoba  I can’t. “Is OK zaki iya zuwa gidan mu gobe yanzu dare yayi. “OK am coming tomorrow tank you darling. Tafada tana buga tsalle tareda rungume filo, tasan yafara damuwa da ita tunda har yake so taje gidan su yanzu, hakurin ta ya fara aiki yanzu. Kwanciya tayi tareda Addu’ar gari yawaye ta ganta agidan su.

 

 

 

Gefen Naziya ta shiga gida da takaicin khaleel, domin yaron mugun d’an wulakanci ne, inba wai gizo idanun ta ke mata ba kamar kallon kyama yake mata, bayan duk unguwar su an shaida tsabtar su, duk da suna fama da Almajirai Inna kulu nada kokarin ganin ta tsabtace gidanta sosai,. Kwance take tana juyi shukrah ta matso gefen ta akan Y’ar madai daiciyar katifar tasu, tace “Aunty lafiya? “Hmm bakomai. “Aa Ina kallon yanda kike ta juyi tundazu kinkasa bacci, meke faruwa ne? “Kawai Ina tunanin yanda zan zauna da Ahmed ne tareda kanin shi shukrah dazu sunzo, baida k’irki irin Ahmed ya cika girman kai  da nuna shiyayi karatu a kasar waje. “Ni kuwa Aunty kallon Arziki sosai nakeyiwa Yaya Ahmed fa. “No yafada min Yana da ubangida mai kirkine watarana motocin yake zuwa dasu, “nidai Aunty Ina tantama domin ko tsarin jikinshi ya isa ya nuna Yana cikin hutu. “Ni kuma me zakice dani?  Tunda kowa kallon Y’ar masu kudi yakemin a school ko in munfita, halitta ce kawai. “Hmm tom kiyi bacci Ki kyale wani kanin shi Bashi zaki Aura ba.

 

 

 

Washe gari Karfe goma tayi mata a gidan su khaleel cikin tangamemiyar motar ta ta yayi, da kanta ta tuko kanta, da taimakon shi ta zo gidan domin unguwar su ba boyayya bace,  momy ta zage sai rawar kafa takeyi an shirya mata tarba Kala Kala, cikin adon jan material doguwar Riga dinkin yayi na yayan masu daula,  taci gwala gwalai wuya da hannayen ta tana zabga sheki da kamshi. Ta hadu ba sauki domin ta iya caba ado. Tasamu tarba gefen momy, Wanda koda tazo gidan bai tashi baccin safe ba,

Momy sai Ina ta saka Ina ta Ajiye takeyi da ita, sai zare idanun ta takeyi taga inda zai bullo. “Huh khaleel na bacci haryanzu bai tashi ba,   kinsan da gajiya a jikin shi.

Shigowar Ahmed ne yasa Momy tace “ka duba d’an uwan ka ko ya tashi ga bakuwar ta iso. Gaisawa sukayi Yana Kara ganin wayewar ta da kudi Wanda yasan ba yanda za ayi Naziya tazo gidan nan saboda shi, banbancin yayan talaka kuma y’an gidan mutunci kenan da kuma ya’yan masu kudi. Yanzu meye Abun burgewa a nan mace ta nuna rawar kafa akan namiji, idanun fauzy ya gama budewa gaskiya and zasuyi kusan sa’a da Khaleel like he said, wucewa yayi Yana daya sanin bashi goyon baya akanta,.

A kwance ya sameshi Yana kallon saman pop, “oh you wake up? So kazo fauzy is here. “You see tunda Asuba mayyar ta tanbayeni address nafada mata don uwar ta a gidan mu zata karya?  Dariya Ahmed yayi, “Auzubillahi yada zagi?  “That’s why Yaya bana sonta wallahi batada kamun kai  Sam ace Karfe goma ta zo wurin saurayi saikace ba iyayen ta a gidan. “Yanzu dai katashi kayi fresh up kafito tana jira mother in law dinta ta bata big welcome. Tashi yayi ya shige bathroom, like Always Saida ya kwashe hour guda kafin ya fito Wanda shirin nashi ma Saida ya kwashi rabin hour cikin guntayen kayan nashi kamar yanda ya saba.

Cikin takun kasaita da shan kamshi ya fito falon,   fuskar shi Sam ba fara’a, “ga shinan yaron kirki ya fito. Mommy Tafada tana mikewa tareda taroshi kamar wani kwai jitake kamar ta goyashi saboda so, jikin fauzy na rawa tace “hy darling kamar ta ruga ta rungume shi takeji. “Tashi kuje dakin shi zakufi sakewa bari insa a hado muku breakfast akawo ciki. Cikin sakewa tace “Saidai baby ni ai mommy kin cika min ciki tun zuwana kike duramin ciye ciye, Tafada tana Dariya, “Allah Y’ar nan, to bakomai ai gidan kune nan.

Zama yayi a falon fuskar shi a cakude yace “ke iyayen Ki basa gidane kika fito early morning? Kallon fuskar shi tayi tareda yin murmushi duk da tasan maganar banza yafada mata ranta bai baci ba, “mommy na nan dady na nan kuma sun san inda naje. “Really?  Kuma basuyi kokarin hanaki ba? “Why zasu Hanani?  Bayan su masu goyon baya na ne akan duk Abinda nakeso kasan cewa sun san komai akan ka dady na a shirye yake da katuro neman Aure na, please khaleel ka cika mun burina I promise zaka sameni yanda kakeso zan share maka damuwar ka duka zanbaka gatan da mata basa iya bawa mazajen su just give me chance.

“OK zanturo tunda mommy ta Amince dake and my brother too yanzu kije gida zanturo. Tsalle ta buga tareda Dane shi ta rungume shi kam” don Allah da gaske zaka tura?  Oh my god khaleel zanyi suman dadi yau. Tafada tana share hawaye, ban bare ta yayi a jikin shi ya ce “oh come on a gidan surukai kike fa behave yourself.

“Farin ciki ne yamun yawa baby muje mota indakko wa momy tsarabar ta please, Tafada tana riko hannun shi, jinta takeyi kamar anyi mata bushara da gidan Aljannah……. 🖊

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻 *AUREN GADO* 🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

 

🆓 page

 

 

 

5⃣&6⃣

 

 

..,………. Kaya na kece raini ta kawowa momy tsaraba Wanda tayi ta godiya kamar zata goyata, bayan tafiyar ta bata da wani zance sai na “Ibrahim khaleel bikin ka zamu gwan gwaje  ba karya kaga Abun Arzikin da ta kawomin tun ba ayi Aure ba? Wucewa yayi cikin dakin shi domin shi yanzu daya sani yake mara iyaka daya Amince mata tazo gidan su har Mommy ta ganta, yanzu ya boni shikam………

Wasa wasa Saida aka kwashe kusan sati daya bai kuma daukar wayar taba ta Kira ta turo msg yafi hamsin Yana shareta, momy tayi nacin zancen turawa gaisuwa Yana ja baya, domin shidai bai shirya ba infact baya ra’ayin zama da fauzy she is not his choice zai cutar da itane kawai, bazata taba samun kanshi yanda take soba. Bikin Ahmed da Naziya ya matso gefen gidan su shikadai ke shirin shi da Abokan shi Yana cikin tsananin farin ciki, momy tace bazata wahala akan Y’ar talaka ba, yan uwan tane dai suka fara cika gidan, musamman Aunty zarah, Wanda itace kanwar ta da sukazo hali daya, komai na Aunty zarah sai a hankali  tana son gayu da babbar harka.

Duk akwatunan da Ahmed ya hada momy ta sa anrage duk wani gold tasa ancire ansa passion  wai basu san darajar su ba talakawa ne. Baida yanda zaiyi saidai farin cikin shi daya Khaleel ya hadomai Nagani na fada a bangkok, don haka sunkai sun boye sai in ta tare, duk wani event mommy ta soke wai yarinyar da ba wayayya ba yaja musu Abun fada bada itaba, don haka ya hakura domin Albarkar Aure yake nema in Allah ya mallaka mai ita burin shi ya gama cika, sannan farin cikin shi daya itama tace bata son wani bidi’a walima ta isheta da za ayi a gidan su,.

Khaleel yana gefe baya cewa komai he just feel boring baiga Abun burgewa a yin Auren ba ba wani Abu da ya bashi sha’awa da har zaiji yanason yayi Auren ma,  fauzy sarkin naci tazo tun Ana jibi Bikin ta tare duk inda Aunty zarah ta shiga suna tare gaba daya yabi d’an uwan nashi sun kauracewa gidan suna part din Ahmed saboda jama’ar da suka cika na momy, yaki ko Yarda su hadu da ita, ta d’an ji sanyi ganin tana cikin gidan su kuma no matter what sai sun hadu kafin ta koma gida, ita da ta samu daurin gindi a wurin uwar miji ma, ita kanta tasan mommy batason Auren Ahmed domin ta gama bata labarin ta tas.

 

Rana bata karya inji bahaushe, Alkawari ya cika, inda Aka daura Auren Ahmed da Naziya akan sadaki mafi daraja, sai muyi fatan Allah ya kade fitina, tunda aka daura Auren ya baro taron ya dawo gidan tareda kulle kanshi cikin dakin su, zazzabi yakeji mara dalili tareda jin wani irin bakon Al amari a tattare dashi, Ahmed nata neman  shi, Saida ya kirashi ya dauka yafada mai cewa yana gida, dawowa yayi shima tareda barin Abokan shi ya same shi a dukun kune cikin bargo,

 

Cire babbar rigar shi yayi ya zauna gefen gadon tareda cewa “bakada lafiya ne? “Fever ke son kamani, “sorry namiji, kasan me?  Yafada yana gyara zama, tashi Khaleel yayi ya jingina a jikin gadon yace what my brother? “Burina yacika khaleel, today Naziya is legally mine, but am worried me zata fuskanta a cikin gidan nan, how is she going to react after she find out about everything? “Like what brother?  Like our wealth, this big mansion, and mommy. Yafada yana rage murya cikeda tausaya wa kanshi, kamar yarone yaga alawa Ana mai kwalelenta haka yakeji yanzu, yasamu farin cikin shi Amma baya cikin farin ciki.

 

Matsowa yayi sosai kusa da d’an uwan shi yace “Yaya this is the time da zakayi fighting back, ka tsaya akan ra’ayin ka, you have to talk brother, fight for your love, and Aunty Naziya will be happy  bazaka samu Matsala da itaba, in tace zata sama yayana hawan jini bazan raga mata ba cos batasan irin fighting da kakeyi akan soyayyar taba. “Hmmm you known, nafison momy ta barni in  zauna a gefen mu,  bana son Naziya ta shiga cikin damuwa nasan zata sha wahala Idan akace zata zauna cikin gidan, she can’t handle it, bata saba da irin wannan rayuwar ba. And mommy is our mother dole mubi Abinda takeso Auren Naziya da A hannu na yake Dana hakura for mommy happiness, but Allah kadai yasan mai ya boye a cikin Al’ amarin,

Yafada cikeda damuwa, Dariya khaleel yayi mai d’an sauti wadda ta Kara bayyana kyanshi sosai, “Yaya this my Aunty is very lucky, tasamu miji mai sonta sosai Anya zaka kuma Aure nan gaba like the way mommy is planning? ” no Khaleel bana son Naziyata ta zauna da kishiya Ina so tayi rayuwar y’anci ne, Ina son inganta cikin hutu da walwala, khaleel na gama tsara irin yanda nakeso rayuwar Naziya ta kasance, I love her beyond your imagination, ka tayani son Naziya kaima kamar yanda nake sonta.

Sundauki dogon lokaci yana daukewa yayan nashi damuwa ta hanyar k’arfa famai guiwa,  Saida friends suka fara kiranshi ya Fita tareda barin khaleel cikin damuwa, Alwashi ya dauka mai girma akan zai taya yayan shi fighting akan duk Abinda zai daga mai hankali bazai so yaganshi cikin damuwa ba,.

 

Bai kuma Fita a gidan ba ko sallah a part din yakeyi ya koma ya kwanta, yarasa abunda duk ya Cire mai walwala da natsuwa bayajin dadin jiki da zuciyar shi baki daya,  he just fee like going back to bangkok,  baisan mai ke hana shi sukuni ba.  Sai Karfe Tara Ahmed ya kuma shigowa dakin ya tsaya a kan shi tareda cewa “brother what is wrong?  You look very dull. “I don’t know Yaya kawai bana jina cikin natsuwa. “relax  nima haka nakeji tundazu but now am fine, your Aunty is here khaleel, finally Naziya is here. Zama yayi tareda rungume Khaleel din yana fitarda hawayen da yarasa na menene ke fitowa daga idanun shi.

Saida ya d’an natsu yace let go and welcome your sister in law. Mikewa yayi ba musu, ya bishi sanye cikin kana nan guntayen kayan da ya canja tundazu.

 

Gefen Naziya kuwa   tunda suka sako kai cikin wannan tafkeken gidan gaban ta ke faduwa gashi gwaggonnin tane suka rakota su uku bisa ga umarnin malam domin baison gayyar tsegumi, kanta a duke yake tunda motar da ta dakko su ta shigo, cikin Y’ar rakiyar ta daya tace “t’irk’ashi  wannan gidan mutum daya ne ko dai gidan y’an yankan kai? Sauran  suka fara salati, shikenan malam saida Y’ar nan yayi, irin wannan gidan saikace wata unguwar? Saurin daga kanta tayi ta saki baki tareda dafe kirjin ta tana karanto Addu’ar tsari a cikin zuciyar ta, jikin ta shegen rawa yafarayi. Har motar ta tsaya Abokin da ya dakko su yace “Hajiya kufito mu shiga ciki ko?  Kamar way’enda kwai ya fashewa a ciki haka suka fito ji sukeyi kamar ace ar su ruga, shi ya musu jagora kowaccen su Addu’ar da duk tazo bakin ta takeyi, rike take da tsintsiyar hannu irin wainda ake rikewa na share dattin daki a wurin sabuwar Amarya bisa ga Al Ada, nasan wasu sun san wannan Al Ada akan ce ta share duk fitinar d’akin kafin ta zauna cikin dakin ta.

 

Daya cikin gwaggon nin nata tace “kawo Abar nan inrike da ita zankoma Y’ar nan domin ko takarda bazaki shara ba a gidan nan, “Toh ai gidan da waje ma babu ko Alamar d’aud’a  bare ciki, ai wajen ma ni yafi dakina tsafta, haka suketa sambatu tsakanin su. Ita kuwa jitakeyi kamar ta ruga da gudu saboda tsoro, wasu irin zafafan hawaye ne ke zubowa akan kyakkyawar innocent face dinta. She is regretting today, wayace ta Amince mai? wayace ta yarda da Auren shi? gashi yayi mata karya yakawo ta gidan da bata taba zuwa kusa da irin shiba.

 

 

A falon mommy ce hakimce itada y’an uwan ta, Zarah ce ke gefen ta da kuma uwar y’an kanzagi fauzy, sunayin Sallama mommy tace Zarah kusa katuwar tabar mar nan akan carpet din Idan sun tafi a fita a Y’ar da ita a waje kar k’uma ta  shigo mana gida.

Sunji komai a kunnen su jikin su na rawa suka karaso akan tabarmar suka zauna tareda gaida su cikin girma mawa, cikin su daya tayi karfin hali tace “Hajiya toh ga Amanar Y’ar ki nan Allah ya tayaki riko.

“Ni Amanar me zaku bani saikace wata kishiya ta, to kuji infada muku tun mijina nada rai ko zance bai taba zuwa ba bare ayi zancen yimin kishiya, don haka karma ku fara ku jira Wanda ya Auro ta yazo kubashi…… Yauwa ga shi nan ma, Tafada tana nuna shi domin yana fitowa yaji zancen momyn wani irin zafi tareda damuwa zuciyar shi ta shiga. Khaleel ma yaji komai kuma he is not happy da irin yanda mommy takeyi ga su fauzy dake musu wata irin Dariya kamar sunga kashi  itada zarah, wani irin baci ran khaleel yayi da Sauri ya matso tareda kallon Fauzy, ” ke wace iri ce uban me  kikeyi a gidan mu haryanzu baki tafi ba?

 

“Aa banson shirme Ibrahim, ya yarinya tazo maka k’ara zaka hauta da fada? “Mommy angama Bikin tazo ta wuce gidan ubanta tom. Jikin ta na rawa ta zabura ta nufoshi kamar zata fada jikin shi “no please na dauki permission wurin mommy na ta yarda inyi kwana biyu baby just for you….. “Oh come on, ke meyasa bakisan….. Saurin dafashi Ahmed yayi domin bayason more humiliation agaban y’an uwan Matar shi Dama  ita kanta, yanzu yana tunanin how he is going to face her ne ma.

Shiru yayi tareda juyawa da Sauri ya yi cikin dakin shi dake part din momy,  ranshi yayi mugun baci dole ya koyawa wannan fauziyar hankali gobe.

Fadin zuciyar Naziya da tunanin ta bata lokacine ma, daya daga cikin y’an uwan mommy ne tace “ku muje in nuna muku part d’in ta, Tafada tana mikewa kafin ya yar ta ta kuma kwab’a, sanyi Ahmed yaji domin yama d’askare yakasa ko motsi.

Suna shiga suka ware idanu domin basuga ko tsinken da sukasa aka kawoba, wadda ta rakosu ce tace  “wannan dakin mijinta ne gidan su na waje a can akasa da kayan ta, kamar tasan me suke tunani,

Domin sunga gadajene na kasar waje ba irin nasu d’an wambai ba.

 

Cikin sauri sukace “tunda munrako ki Naziya mu zamu koma dare nayi, Allah yabada zaman lafiya da hakuri kinji ki rike tarbiya da mutuncin malam Dana kulu domin kinsamu tarbiya dai dai gwargwado kinsha nonon hakuri da kuma mutunci, Allah ya kade fitina. Suka juya cikeda sanyin jiki, riko daya daga cikin su tayi tasa kuka “Don Allah gwaggo karku tafi kubarni ni kumayar dani gida wurin Inna bana son nan gidan. Tafada tana kuka mai cikeda tausayin kanta da Rayuwar ta, daga shigowar ta harta karanto irin Rayuwar da zatayi a cikin wannan gidan.

Shigowar Ahmed ne yasa takara rike ta gam tana gunji.  “Ahmed ka rike Amana ga Matar ka mu zamu tafi kaji. Babbar Tafada cikeda tausayin Y’ar tasu, hannu yasa zai rikota tayi tsalle ta koma gefe tareda sakin su tana gyara hijabin ta dogo.

Fita sukayi ta koma gefen dakin ta zauna tareda saka kuka mai zafi da kuma k’ara,

Rakasu yayi a gurguje yadawo domin kukan da takeyi bakaramin daga mai hankali yakeyi ba.

A zaune take ta hada kai da guiwa tana kuka mai ciwo. Zama yayi dabas a gaban ta cikin sanyin jiki, tanajin kamshin jikinshi daya cika ko Ina, takasa dagowa. Hannun shi ya dora saman kanta, da yasa tayi Saurin dagowa tareda ja baya tana Kara hade jikinta wuri daya,

“Am sorry bazan kuma tabaki ba tunda bakyaso, Amma please kiyi shiru haka kukan ki na tabamin zuciya sosai.

Yafada yana kallon yatsun Hannun ta farare tas da sukasha jan lalle Hannun ya mugun burgeshi, ji yake kamar ya riko ya tsotsa, bai taba ganin lalle ya burgeshi ba sai a Hannun ta. Jin shirun shi yasa ta dago tareda zubamai lashes d’in ta masu kyau da kuma fararen idanun ta da suka cabe da ruwan  hawaye, taga Inda yake kallo da ya shagalar dashi sosai. Saurin cusa Hannun ta tati cikin hijabin ta da yabashi damar kallon na fararen kafafun ta, wani irin gauron numfashi yaja tareda d’an matsawa kusa da ita, ta kuma ja baya again. “Why Naziya? Please karki horani a haka zuciya ta zata buga, ki horani ta kowacce hanya but karkiyi min iyaka da zuwa gareki, am dreaming about it always, nasan ni mai laifine a wurinki, Amma kisani ni mai sonki ne shiyasa na boye miki gaskiyar rayuwata Naziya banason in rasaki I love you so much my wife. Yafada yanajin  wani irin shauk’i da yanayi mara misali, kallon shi takeyi wani iri kamar zataga wani Abu daban, batajin zata iya Rayuwa a cikin wannan gidan tareda kuma mahaifiyar shi da itace farkon matsalar data Kara girgiza ta.

 

“Am sorry Naziya, nasan i’m wrong domin bakiyi planing zama a irin gidan nan ba, yafada yana murmurshi, domin itace mace ta farko dayaga wai batason daula. How silly? Maganar mommy tasa yayi Saurin ja baya tareda tashi tsaye ya kalleta “kazo ka zauna gaban jaririyar yarinya a daren farko to kazo ka wuce dakin d’an uwan ka kowa yasan ango baya shiga dakin Amarya sai anyi budar kai don haka wuce kabani wuri tun ban sab’amaka ba.

Daukar babbar rigarshi yayi yafita jikinshi a sanyaye. “Ke kuma ki tashi kidaina wannan kukan munafuncin kije kisha Ac anzo inda yafi gidan tsoho  ga katifa mai numfashi aje a more, kin  zo kina kukan munafurci. Tafada tana fita dakin cikin fada.  Zubewa tayi nan kasan dakin tasa kuka, “Ahmed yasa ankawo ta inda bazata taba yin mutunci ba,har wani irin ciwo taji gefen kanta nayi saboda kukan da takeyi.

 

A kwance ya samu khaleel idanun shi a bude yana kallon saman dakin wani irin zazzabi yakeji har yanzu Wanda yarasa dalilin faruwar shi,  jin takun d’an uwan nashi yasa yayi Saurin juyawa ya kalle shi, “Yaya ango me kakeyi a nan yau? Yanda yaga hawaye tareda ganin damuwa kwance a fuskar d’an uwan nashi yasa yaji tuni zazzabin shi ya tafi, tashi yayi cikeda damuwa yace “Yaya taki kulaka ne?  Zan bata mata rai Idan ta nemi jefamin kai cikin cikin damuwa. Yafada jikinshi na rawa domin yaune karo na farko dayaga hawaye a idanun jarumin yayan nashi mai hakuri.

“Mommy. Yafada yana Rungume d’an kanin nashi domin yasamu sauki. “Me tayi kuma?  Fadamai yayi yana jan numfashi, “oh Mommy, Bari inje inyi mata magana. Yafada yana kokarin tashi tsaye, rikeshi yayi tareda girgiza kai, “karkaje tace Al Ada ce sai gobe zan shiga wurin Matata.

“What kind of Al Ada? “Budar kai. Zabura yayi cikin haushi “let me talk to her. “No leave it, just do one thing please go and check on  her please she was  crying.

 

“No kabarta zatayi shiru ka kwanta yau ne kawai tunda ka hanani inyi mata magana.

“Please go Ina so inji ko tadaina kuka, inaji a jikina tana can tana kuka.

Bayason musu, especially da yayan nashi don haka mikewa yayi kawai ya fita.

Ba kowa a falon yanzu duk Suna cikin part din mommy Suna hira da shewa, girgiza kai yayi yana tunanin Abinda zai aikata gobe a gidan halin shi dasuka sani bai canja ba bayason rubbish.  Tundaga falon yakejin kukan ta kasa kasa. Wani irin zafi yaji a zuciyar shi, da sauri ya shiga dakin, a kwance take a kasan kamar yanda take tundazu saidai yanzu Ana iya ganin kayan jikinta domin duk hijabin ya tattare ya koma wurin cikinta, zaka iya ganin perfect figure dinta, Wanda ko Ahmed bai taba samun damar ganin ta haka ba, kullum tana cikin hijabi,  akan kafarta idanun shi yafara sauka.

Wanda wani irin attraction ya rika jansa ya kasa Cire idanun shi, “first time da henna designs ya Bashi sha’awa, ga kafafun ta kamar na turawa a mulmule farare tas dasu, “Wow she is Unique, zuciyar shi ta furta. Domin tsarin jikinta da yake gani,  bai taba ganin small body with a perfect shape ba like her.

Motsinta yasa yadawo hayyacin shi cikin Saurin tareda tsorata ta zuba mai ido, tana zarewa, domin ita bata taba ganin katon namiji irin shi da guntun wando da singlet a gaban ta hakaba, wane irin gida Ahmed ya kawota, da Sam ba tsari ba wani sanin ya kamata.  Saurin jan hijabin ta tayi kasa tana mikewa kukan nata ya dauke dif,  fuskar shi mai natsar da yaro mai kukan banza, tuni ta hadiyi wani irin miyau, she knows he’s khaleel domin ganin farkon da tayimai bazai taba bacewa a idanun taba. Gaba daya jitakeyi ya cika mata dakin da girman shi, ga fuskar shi mara walwala, idanun shi masu dauke da wani irin sinadari Wanda batasan ma ma’anar shiba.  Juyawa tayi ta Bashi baya ganin ya dauke kanshi batareda ya iya cewa komai ba. Saida ya dauki lokaci kafin yagama tunanin yanda zaifara yimata magana, cikin karfin hali yace “good tunda ba kuka kikeyi ba, Yaya na is worried sosai shiyace inzo in dubaki, tunda kinyi shiru shikenan, yafada yana tafiya batareda ya kuma kallon gefen taba,  a falon yaci karo da ledar da yayan shi ya Ajiye Wanda kowane ango ke shigarwa Amarya da ita, dauka yayi ya koma, dai dai  ta kuma juyowa, idanun ta suka kuma cin karo dashi, wani irin Saurin juyawa ta kumayi   ledar ya Ajiye “you have to eat karki kwanta da yunwa Yaya na zai damu.  Yafada yana fita Hannun shi cikin pocket din guntun wandon nashi.

Cikin sauri bayan ya fita ta dannawa kofar key domin Allah yagani batason ganin shi again,…………. 🖊

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

 

Ga masu son su biya ga account details dina, *NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB*

 

 

 

 

🆓 page

 

 

 

7⃣&8⃣

 

 

…………… A tsaye ya samu  Ahmed yanata sintiri, yana ganin shi ya rikoshi “kuka takeyi ko brother? Yatanbaya cikeda damuwa. “No Yaya tayi shiru nabata ledar da ka Ajiye a falon relax am sure zataci ta kwanta. Yana gama fada ya haye gadon ya kwanta tareda juyawa yayan nashi baya. “Tank God, and tanks to you brother. Yafada yana d’an samun natsuwa, bathroom ya shige yabarshi idanun shi kur, baya kojin bacci, saida yaji fitowar Ahmed ya rufe idanun shi kamar maiyin bacci.  Saida ya shimfida dadduma ya fara jero sallolin nafila tareda Addu’oi masu zafin akan Rayuwar shi data Matar shi, ba Abinda yake nema sai farin cikin Naziya a wurin Ubangiji tareda neman zaman lafiya a tsakanin su.

Ganin har Karfe biyu shima yakasa baccin ya diro tareda dauro Alwalar ya tada sallah shima, haka gefen Naziya bayan ta kulle bathroom tafara nema saida tayi da gaske ta gano inda zata latsa ruwan yafito kafin tayi Alwala tafito, dadduma tagani a gefe da Qur’ani ta tada sallah, saida tayi raka’a biyu ta zauna tana jan k’ira’a a zuciyar ta. Domin fadar manzon mune aduk halin da mutum ya shiga to ya koma ga Allah,

 

:(Fadhkuroonee adhkurkum washkuroo lee wa laa

takfuroon

“So remember Me; I will remember you. And be

grateful to Me and do not deny Me.) :

Wanda duk ya tuna da ubangiji shima bazai manta da shiba a duk halin da yashiga.

Sai  Asuba ta tada sallah saida tayi nafila raka’a biyu kafin farillah, taci gaba da karatun ta,  sai Karfe shida ta kwanta a kan daddumar, wani irin bacci mai cikeda salama ya dauke ta domin Qur’ani maganin damuwa ne Idan har kayi Imani da Allah.

 

Haka gefen Ahmed da Khaleel basu runtsaba saida sukaje Mosque suka dawo, saida Ahmed ya duba kofar dakin nashi yajita a rufe,  bai bugaba domin kar momy taji, dakin khaleel suka koma, kwanciya yayi yana murmurshi “daga yau bazan kuma kwana nikadai ba, ko tareda kai “am going to sleep on my wife shoulder, yafada with so much excitement, Runtse idanun shi yayi tareda yin shiru yarasa abunda yakeji a Ranshi,  a haka dai sukayi bacci har zuwa Karfe Tara na safe, Wanda Ahmed din ne yafara tashi domin ya matsu ya fita yaga halin da Naziya ke ciki.

Saida yayi wanka ya tashi Khaleel “get up sleeping beauty muje muga momy inaso in duba Naziya Yafada yana goge fuskar shi da towel, tashi yayi yana salati tareda wucewa batareda ya furta komai ba,

 

Saida yayi wanka ya fito, yasamu har Ahmed ya shirya sai kyalkyale jikin shi yakeyi domin so yake ya burgeta, Idan ta ganshi tasan bata zabi mijin banza ba. Shiryawa yayi shima khaleel cikin shigar tashi ta fama, kallon shi Ahmed yayi “yakamata kasa manyan Kaya zamuje gidan malam later gaisuwa tareda godiya inaso muje tare dakai. “no please banason zuwa wannan unguwar Yaya.”For me please. “OK for you. Amma bazan sa kayan zafi ba sai zamu tafi. “No problem muje”.

 

Naziya saida mai aiki ta tasheta ta tashi cikin sauri ta bude kofar tace “Hajiya tace kifito kitayamu aikin breakfast. Tace tom tareda gyara zaman hijabin ta ta fito, tareda taimakon mai aikin suka shirya irin Abincin da sukeci wainda idan aka barta bazata iya ko kunna gas din ba bare sauran kayan wutar. Wurin gasa crabs din khaleel ne tasha mamaki,  domin ita tsawon Rayuwar ta bata taba ganin ta ido da idoba sai a text book, da kuma manyan d’anyun crayfish da Sam basuda kyan gani a idonta tana kallo aka gasa su a oven aka yanka mai salad da kuma tumatur manya aka jera su crayfish din da crabs din akan ganyen, so takeyi taga wazaici wannan Abun, sai kwai da ko kadashi ba ayiba ansaka mishi kayan kashe k’arni, kawai fasashi akayi a frying pan aka d’an barbada chilli powder asama kadan.

Tana gefe tana kallon ikon Allah sai d’an abinda zata iya yi kawai take tabawa kamar fere dankali da yanka kayan miyan da za’ayi source dasu,  Karfe Tara da Rabi suka shirya komai a dining table, dai dai lokacin momy ta fito cikin shigar Alfarma da gwala gwalai, ta kalleta cikin fada, ” Ina fatan bada wainna kayan kika shiga kitchen ba?  Kanta tayi Saurin dukarwa tareda gaida momyn Ina kwana. Tace “mu nan wanka akeyi sau goma in antashi domin akwai ruwa basai anje tuka tuka ba ko rijiya ba don haka karki kuma shigar min kitchen da datti, yanzu ma Allah yasa khaleel ya iya cin abincin nan kin shiga kina yimai kakkabi da wannan katon hijabi kamar wadda keda nakasa, ke Kodai wannan kyan naki a fuska ne rufa rufa akayiwa Dana a cikin hijabi?  Oya Cire shi yanzu ingani wallahi inkinada ko kuna guda dayane yau sai kunbiya mu sadakin mu. Tafada dai dai y’an kanzagin ta na fitowa tareda kuma su khaleel da suka sawo kai cikin falon.

Dariya Fauzy tayi tace “may be akwai inda keda illah Mommy, Tafada tana tafawa da Aunty zarah dake biyeda ita, “kwarai kuwa a Cire kar a cuci dana,.

Cikin sauri ta Cire hijabin kanta bako d’an kwali sumarta mai tsananin tsawo da kyau kamar buzuwa na nade cikin sabon ribbon, gashine kwance har gaban goshin ta Wanda ke sanarda kai akwai sumar. Kayan jikinta kuwa atamface dai dai talaka wadda malam ya dunka mata tafitar biki akalla zatakai dubu goma, domin kawai ya fitarda Y’ar tashi ranar Aure ya dunka mata su kusan guda uku,

Atamfar mai golden ce blue, dinkin nata nazamani mai kyau na Amare Riga da sket ya mata cif mai d’an shoki ta baya perfect figure dinta ya fito fiyeda tunanin masu sa idon dake wurin, duk sun gama yarda cewa Naziya mace ce kuma  kyakkyawa ajin farko ba kamar na Y’ar talaka ba. D’askarewa Ahmed yayi domin yau ne yasan ya tsinci dami akala, yau yake ganin wacece Naziya, wani irin yanayi yakeji, burin shi bai wuce ya ganshi daga shi sai itaba a kebe ya samu ya rage damuwa da wahalar da yasha kafin yasameta.

Gefen Khaleel kuwa bazaka taba gano komai ba sai tsantsar bacin rai da bakin ciki Wanda yarasa dalilin shi, cikin zafin zuciya ya kalli fauzy ” you come and get lost from my house, angama biki ki koma gidan ubanki right now. Yafada cikin karaji da fitinar da ba Wanda yataba jin yayi irin ta. “Aunty zarah I thought Aure kikeyi kema kije gidanki mungode da zumunci we need privacy that’s enough.

Fadan da yakeyi ba Wanda za a iya tsaya wa ayi musu dashi bane, mommy ma mamaki takeyi tareda kallon shi saida ya kuma cewa “I said get lost. Tace “khaleel ” cikin tsawa, “ka kiyaye ni ba inda zasuje, kuma don iskanci ka manta Zarah kanwa tace uwa daya uba daya, don’t forget your manners and Fauzy, karka manta she is your bride to be. “Momy tell them to stay within their limit, ita Aunty zarah ba girman mu tayi ba I can talk to her any how, and   Fauzy Auren ta kikeso inyi zan iya fasawa anytime idan naso, don haka before I change my mind leave”.  Yafada yana nuna mata hanya.

 

“Innalillahi, ni Balkisu daga zuwan ki kinfara hada mana gida” Tafada tana nuna Naziya, lallai kuwa yarinya kintabo tsuliyar dodo, Ahmed kaga Abun da ka debo, yarinya mai farar kafa bad luck to our family. Wani irin zafi yakeji tareda kallon momy yana girgiza kai, “no mommy me tayi, Ina bin duk Abinda kikeso momy saboda ingama lafiya please na rokeki kibarmu mu koma gefen mu zamufi samun kwanciyar hankali.

“Naga takaina ni Balkisu kaga ni ko yarinya ta shigo da mugun Asiri, toh wallahi kunyi kadan keda iyayen ki zan nu na muku ni Balkisu in kun kwana akan buzu ni akan dadduma nake kwana mu zuba, daga shigowar ki Dana yafara musu dani. “Momy please stop” this drama is enough. Khaleel yafada yana matsawa kusa da ita tareda riko Hannun ta Alamar lallashi domin yaga Alamar nuna fushin su b’ata Al amarin zai karayi, domin kwanciyar hankalin d’an uwan nashi yace “Fauzy kuzo muyi breakfast Aunty zarah please komai ya wuce OK. “Dama Ibrahim kai raini ne dakai tun kana yaro shiyasa Ahmed yafika Abun kirki.

“Oh am sorry my Aunty yafada yana Dariya kadan, zama sukayi, ita kuma ta wuce dakin da ta kwana tana share hawaye masu ciwo da dumi, domin all her life bata taba tsayawa gaban mutane ba hijabi ba, yau gashi an wulakanta ta saboda me?  Saboda tana Y’ar talaka, shiyasa batason tasa Rayuwar ta inda tafi karfin ta.

 

Ahmed kokarin bin ta yakeyi mommy tace “zonan d’an anace shiryawa zatayi tafito kuma kiyi sauri don bazamu tsaya jiranki ba hamshakiya. Komawa yayi ya zauna tareda zubawa bayanta ido har ta shige, ga koshi ga kwanan yunwa shine wannan.

Gudun fada yasa tayi wanka cikin sauri bayan ta gano inda zata Tara ruwan, domin ko bakomai tanajin labarai tareda gani a TV  sometimes duk da ita ba ma’abociyar kallo bace, bisaga Al’adar gidansu na riko da Addini tareda kaucewa duk wata Rayuwa ta nasara, sai gata a yau tana Rayuwa cikin nasara baki daya domin a ganin ta gidan baki daya ma  Rayuwar nasara sukeyi.

 

Ganin bataga kayan taba yasa ta mayarda na jikin ta, tareda daura d’an kwalinta ko mai bata shafa ba ta fito cikin sauri. Suna zaune yanda ta barsu,  sai Ahmed da ya rike Haba yana kallon ta inda zata bullo, Ajiyar zuciya yayi ganin fitowar ta, yanzu ya samu damar karewa gabanta kallo da take tahowa toward him, Ajiyar zuciya ya jera tafi goma, domin shidai yana ganin samu da rashi ga mace Allah ya Bashi ta huce takaici Amma mommy taja layi,  “bazamuga tsiya ba mudai ki kwana da Kaya ki tashi dasu ki shiga kitchen kifito yanzu kuma kizo ki zauna cikin mu kina tsami, maza ki koma ki canja Kaya, Ahmed kaga illar Auren irin wannan yaran ko? yanzu da akwai bakon ido da munsha kunya. Shiru tayi takasa cewa komai. Cikin sauri Ahmed yace “mommy kayanta na part din mu ne shiyasa duk can aka kaisu, “oh kace kagama planing din tarewa acan to kaje ka kwaso mata kayan zuwa nan ban Amince maka zama da wannan ignorant din ba a cikin wannan gidan ba sai in kashirya yin wani Aure kwa tare da Amaryar Arziki ba wannan ba, Tafada tana nunata sama da kasa, da Alama kalaman mommy nayiwa khaleel zafi fiyema da Ahmed domin yasan d’an uwan nashi hakuri ne kawai yasa yakasa cewa komai shikuwa hakurin shi yafara karewa. “Mommy please am hungry ko intafi ne waje inci yau bazamuci breakfast din ba? “Kizo ki zubawa kowa yarona najin yunwa kinja kin tokare. Matsowa tayi jikin ta NA rawa,  ” gefen da Khaleel yake ta fara nufowa kanta akasa bata ma iya kallon idanun mutanen, infact haryanzu bazata iya tantance kamannin fuskokin su ba. Wani irin kamshin turaren wuta d’an mai duguri mai sanyin kamshi, Wanda ya Kama jikinta ya daki hancin shi, Hmmm yana matukar son kamshi a Rayuwar shi, ga wannan da yake shaka mai wani sirri na daban.

Plate ta dauka ta fara zuba musu chips din dankali da source, Ahmed so yake ta kalleshi, just once ko zaiji sauki domin Allah kadai yasan Abinda ke cikin zukiyar shi, damuwar da yake ciki bata faduwa.

Saida ta zubawa kowa tazo kan Khaleel, ya daga mata hannu tareda janyo tarkacen shi gabsnshi domin shi cimar shi daban take a gidan, zuba mai ido tayi tana kallon shi zaici wannan Abun? “Naziya “. Ahmed ya Kira sunan ta cikin wani irin kashe murya tareda tsareta da idanu, batada choice dole tadaga idanun ta takalle shi, nuna mata kujerar gefen shi yayi tareda mata Alamar tazo ta zauna. Ba musu ta nufi gefen shi, mommy nata hararar ta kasa kasa, Su fauzy kuwa kallon village girl suke mata, zama tayi a takure da kanshi ya zuba mata Abincin tareda hada mata tea very thick, “toh shanyayye ita batada hannu ko?  Inji mommy shidai shiru yayi, saboda jin ta a zaune kawai a kusa dashi yaji ya d’an natsu kadan.

 

Tsit kakeji  sai karan cokula, ganin hankalin kowa nakan plate ya sauke left hand dinshi tareda dafe Hannun ta daya dake Kan laps d’in ta, gam gam, wani irin zabura tayi, Wanda khaleel ne kawai idanun shi yagani, idanun ta a gefe take kallon Ahmed din tareda kokarin kwace wa ta kasa , wani irin bakon Al amari takeji domin zata iya cewa wannan ne karon farko da namiji ya rike mata hannu, gashi ba rikewar  kawai yayiba wani irin murzawa yakewa Hannun kamar kwadayin shi akan Hannun yake,

Har wani irin zafi takeji, shi kuwa laushi da santsin Hannun ne ke rikitashi domin tuni yama daina cin Abincin, jiyake kamar ya dauketa suyi tsuntsuwa subar wurin, he really need privacy with his wife.

A haka kowa ya kammala batareda taci ko cokali daya ba, kuma yunwa takeji ta fitar hankali,  domin tunjiya batasa komai a cikin taba, domin ko kallon ledar  da khaleel ya Ajiye mata batayi ba.

Shiyafara mikewa tareda barin wurin, saida yaga hankalin mommy zai dawo kanshi ya saki Hannun tareda gyara natsuwar shi da ta dade da zuwa bulaguro sanadin jin shi cikin wani irin yanayi mara misali, bai taba jin kanshi in needs kamar yanzu ba, Hannun ta ya rike duk ya rikice idan ya Rungume ta fa?  Ai suma kila zaiyi kai tsaye,

 

Saurin tashi tayi jin ya saki hanun tayi daki cikin sauri, dakyar ya karasa breakfast yana bawa kanshi laifi domin yaga ko tea bata shaba, mommy ta kalli plate din ta tace “Ahmed aiki ya sameka saikaje ka siyo mata kosai da koko kasan ba asaba da shan shayi ba bare kuma chips,  ta fada tana barin dining din zuwa tsakiyar falon ta hakimce tareda su fauzy,

Shigowar y’an matan kawu modu ne yasa ya saki fuskar shi tareda tasowa, yana murmurshi “sai yanzu zakuzo ganin Amaryar? “Yaya Ahmed ai jiya ma muna gidan nan saboda kana hidima ne yasa baka sani ba. “OK kun fita. “Ina Amaryar mu?  Tana ciki, and please muje kutayani kwaso kayanta zuwa nan. Yafada yanayin gaba,  binshi sukayi,Suna hira a tsakanin. Akwatunan da yayi mata ne kawai ya kwaso mata yabar na Khaleel a can, gudun fitinar mommy, domin ko wainda yayi hanawa tayi akai wai kar su kwaso musu kudin cizo da k’uma,  inda Allah ya taimake shi malam yace bayason bidi’ar kawo akwatin abarta a dakin ta idan ta tare, Wanda hakan ya mugun sanyaya mai rai.  shigowa yayi da katuwar akwatin zai shige tareda kanin nashi, “Ahmed Ajiye a nan zasu shiga da ita ciki. “Momy bazasu iyaba tanada nauyi sosai. Zabura tayi tace “Zarah kuzo ku kamamin, yana gani haka suka dauka tiki- tiki saboda dai kar Abarshi ya kebe da Matar shi, yadawo tsakiyar falon ya zauna tareda dafe kanshi, Allah yagani angama shiga Rayuwar shi, Mutum yayi Aure Amma jin dadin Aure ya gagare shi.

Fitowa tayi tana sababi tareda zama gefen shi, “na fada maka miji baya zuwa wurin mace ba ayi budar kai ba, don haka karka sake inga kafarka cikin dakin nan bada izini na ba.

Saurin kallon ta yayi “mommy ai yaune kuma shike nan ko?  “Nadai na fada maka kar inga kafar ka ciki inba haka ba zan daga maka nono.  Tashi kawai yayi yabar gidan cikeda tsantsar damuwa da kuma bacin rai.

Uwa uwace shiyasa kawai baida yanda zaiyi saidai ido.

Dakin Naziya kuwa ta saki jiki sosai da y’an matan wainda sun Cire mata damuwa da kadaici tareda kewar gida, su suka ware suka shirya mata komai na kayan ta a wardrp, da kayan shafan ta wa inda tasan sunja kudi sosai, kayan akwatin sunyi matukar girgiza ta domin saiti biyu ne, wai don ma mommy ta hana shi yayi yanda yaso kenan. Su suka sata ta caba Ado tareda ciro mata wani tsadadden less baki, Abunka da farar fata tuni ta haska ga dinkin kamar angwada ta, suka murza mata dauri,  tafito gwanin burgewa, Karfe daya gidan ya cika da y’an uwan ta masu kawo gara Wanda sun kure kokarin su sunyi dai dai gwargwado, inji bahaushe yace  ka fada wa mai zuciya biki ba mai dukiya ba.

Mommy ma tasan sunyi kokari saidai hassada da idan bakason mutum ko tsarki da madara kake mai bazai taba kaunar kaba…………. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

Masu son su biya ga account details dina ,

*NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB* Sai Ku min magana ta wannan number 09069200154

 

 

 

 

 

🆓 page

 

9⃣&🔟

 

 

………… Khaleel yabar gidan bayan ya gama breakfast shima domin shikadai yasan damuwar shi, bayajin zai Amince da wannan Auren tareda ci gaba da zama a Nija yana ganin irin wainnan Abubuwan, he can’t take it. Saida Ahmed ya nemeshi a waya yafada mai inda yake a can suka hadu, dafashi yayi “why kafita bayan nafada maka zamuje gaisuwar surukai? “Yaya tunda na duba naga baka gidan I know you’re hurt shiyasa nafita, and please Yaya don’t just sit down  and watch things ka dauki Action mana. Yafada yana kallon shi cikin damuwa, murmurshi Ahmed din yayi tareda cewa “my brother, a wurin wa zandauki Action?  Don’t forget she is our mother dole mubi ta duk yanda takeso.   “Its unfair”, haka zakaci gaba da kallon Abubuwa nafaruwa till when? “Ko zuwa yaushe ne Am ready inyi mata biyayya khaleel am ready to obey what ever she said, can’t you do that for your mother?  I can’t Yaya gaskiya am seeing everything you need privacy with your wife amma an tauye ka, yakamata tunda ka rabota da y’an uwan ta ka bata kulawa, itama tanada right akan ka fiyeda mommy don haka dole ka kula da yarinyar nan, kasan yanda kukayi and you disappoint her daka boye mata gaskiya I know she is in pain, please Yaya she needs your comfort.

 

 

“Hmmm my brother has grown up, yafada yana rungume shi gam gam tareda jin dadi, “khaleel kasan how hard am trying?  Banda zabi ne, Amma Inna fada maka bana damuwa k’arya  nayi, “I needs my wife like any other man da yayi sabon Aure I want her very badly, yazanyi in iya Cire idanuna akan matata bayan she is closer to me, this is the hardest time for me. Yafada yana tunano yanda yaganta dazu without hijab, her shape her chest her hair, oh God! he has the most beautiful girl as  his wife.

 

Rungume shi khaleel yayi tareda cewa “I will help you through this brother. “Thank you”. Daga nan suka wuce gidan kawun su tareda godiya akan hidimomin shi, ya musu Allah yasanya Alkhairi,  tareda nasiha mai zafi akan zaman Aure, kafin ya dawo kan Khaleel, “kai balkisu Tafada min komai akan Y’ar gidan mai Nasara, and am happy da zakayi Aure kaima, kuma ni bazan hanaka Auren zabin kaba, zankuma shige maka gaba har kaima Allah ya cika maka naka burin, Amma Ahmed kayi sa’ar surukai nagari Allah ya kad’e fitina, kunje kun gaida su? ” yanzu zamuje kawu friends dina ma na jirana daga nan can zamuje. “To to to, kuje Allah ya muku Albarka, zan Dauki Abokina mu samu ganin mai nasara, idan komai yayi dai dai zanfada muku. “Mungode sukafada baki daya, Wanda itace kalmar farko da ta fito daga bakin shi bayan gaisuwa domin Allah yagani Fauzy saidai idan Allah yayi baida ta cewa, fuskar shi kawai zaka kalla kasan baya farin ciki. “Relax brother, bakasan me zai faru gobe ba, kayi hakuri may be haka Allah ya tsara dole zaka yi Rayuwa da fauzy, don haka ka nemi zabin Allah, inba Alkhairi bace sai ya baka wata. “Mata biyu Yaya? “Yes kaiba namiji bane? ” no please kai kace bakason biyu nida nake kanin ka inyi biyu, ni mace daya is OK for me. “You can handle two wife’s nasan kanina, I believe in you. Yafada yana Dariya, haduwa sukayi suka tafi jakara tareda Abokan Ahmed din. Wanda khaleel ya daure har cikin gidan da Akwai Sauran mutane suka shiga suka kwashi gaisuwa cikin mutunci da girma. Wanda idanun shi nakan Inna kulu wadda yasani ba tantama kyanta Naziya ta dakko, haka yabi Shukrah da kallo yana ganin tsantsar kamar su tareda yayyin ta masu Aure duk Suna Kama, Amma no one like Naziya she is more beautiful a cikin su.

 

“Shiru yayi kawai yana nazari har suka gama gaishe gaishe suka fita waje domin gaida Malam dake dakin zauren tareda manyan Almajiran shi, a nan khaleel ya Amince yes yayan shi yayi Aure inda ya dace, dattijo na gari mai mutunci, nasihar farko itace “sai kayi hakuri da duk wani shiririta ta mata zakaci ribar zama a duniya ka rike gaskiya kabi maganar mahaifiyar ka kagama lafiya, Allah ya kade fitina ya kuma baku zuri’a tagari. Wani irin girman tsohon khaleel yagani tareda tsantsar mutuncin shi, tabe bakin shi yayi tareda kada kai kawai Wanda shikadai yasan meke zuciyar shi.

 

Saida sukabar gidan sukaje harabar katon gidan nasu ya dafashi “Yaya I don’t know much about Al Ada, Amma nagani Ina yaro idan Ana Aure a familyn mu idan ankai Amarya the next day y’an uwan ta nazuwa, why your bride basu zoba kuma sun san zata bukace su? “Hhh Khaleel mutunci kenan da gudun Abin duniya na gidan su Naziya bakaga komai ba ma Indai zuri’ar malam Abubakar ce,  “but Yaya naga younger sister d’in ta ko ita batazo wurin Y’ar uwar taba. “Kasan Abinda momy tayi musu jiya shima zai iya sawa su hana wani zuwa gidan nan. Yafada fuskar shi na canzawa,

“Is OK muje ciki yau dai zaka tare dakin ka enough of the budan kan. “Hmm Allah yasa. Anyi la’asar koda suka shiga gidan, Wanda tana takaiwa da dawowa daga kitchen zuwa falo domin shirya Abincin Dare, duk Abokan hirar nata suntafi, gashi momy tace tayi tuwo miyar kubewa da kuma farfesun kan rago.

Tana cikin Adon ta sosai haryanzu tareda baza kamshi kamar Amarya. Har zata fito cikin kitchen din taji muryar su Suna Dariya ta koma, wani irin zafi takeji a kirjin ta she thinks kamar da gangan ma Ahmed ya Aurota ya kawo cikin gidan su domin ta wulakan ta, toh yayi kuskure,  kuma  zata nuna mai Abinda Aka koyar da ita daga gidan su, zai gani tarbiyar Inna bazata taba faduwa kasa banza ba, she cried yerstaday, kuma bazata kuma zubar musu da hawaye ba, aiki kuma Alhamdulillah, bazai gagare taba domin ta horu girki ma zatayi Amfani da nata salon domin gujewa damuwa, da izinin Allah zata basu mamaki.

Da taimakon mai Aikin take Amfani da kayan wutar, tsab tuwon shinkafa ta dora Wanda tasa mai ruwa wadatacce da zai dahu lugub, sai kan ragon data wanke tas ta zuba a wuta tareda neman kayan kamshi na gargajiya ta daka ta  watsa, tuni kamshi ya cika ko Ina.

Tayi dai dai kuma hankalin ta kwance tana aikin ta, ya shigo ciki, turus yayi yana kallon ta cikeda mamaki domin dai bai kamata ta shiga kitchen ba, tana Amarya kuma kwana daya a gidan miji a ce tafara aiki bayan ga maids cike da gida,  wucewa yayi wajen firij saida ya bude taji motsi tareda Saurin juyowa tagan shi ya daga gorar ruwa sama yana sha, Saurin juyawa tayi tana cigaba da aikin ta, domin ta lura ya cika girman kai, and she promise zata kiyaye shi tunda baice Mata ba itama bazata taba yimai magana ba.

Har ya Ajiye gorar ya juya Abun shi yana mamakin halin ta, ko kallo bai ishe taba Wato? Hmmm”.

 

Karfe shida ta kammala tuwon tareda miyar kubewa lafiyayya da taji namomi a ciki, maid tace”Aunty Saura Abincin master karami. Kallon ta tayi “da daren ma bayacin Abincin mutane? “Yes saidai Ana dafamai ruwan tea ya hada ko coffee. Shiru tayi kafin tace ta kwaso shrimp   d’in da su crabs, da kanta ta gyara ta wanke tas tasa ta gyara Mata Y’ar citta dasu garlic tace ta daka mata su da Albasa da tarugu saida suka daku ta d’an sa ruwa ta shafe su tsab harda spices, ta saka a oven, ta saka lowest yanda bazai kone ba kafin tayi wanka, maid din ta yanka mai salat ta wanke su tumatur.

Dakin ta ta koma ta tube tareda shiga wanka, cikin Sauri Sauri, ta dauro Alwala domin ankira magrib, bata tsaya yin dogon Azkar ba ta mike cikin Sauri ta canja zuwa wata doguwar rigar Atamfa mai flay cikin dinkin  da malam ya Mata, tayi kyau sosai,

ta daura dankwali ta fito. Yanzu duk sunfito Suna falon momy dasu Ahmed harma da Khaleel, yana Rungume da katuwar tab yana dannawa, Suna hira kasa kasa su duka. “Toh hamshakiya abamu Abinci yunwa mukeji. Mommy ta fada. Muryar ta a kwance tace na gama momy zan shirya ne kawai a dining. “Noo ki sa maid ta shinfida mana dadduma anan bazamu hau saman ba,.

Bakomai yasa tace hakan ba saidan kar su zauna kusa itada Ahmed. Domin sa idawan ta dazu sun tsegunta Mata kamar yana rike Mata hannu ta kasan table, Wanda bazaka taba gane munafukan sungan suba.

Tunda ta fito Ahmed ya zuba Mata ido wani irin numfashi yakeja a ciki, domin Allah yagani shiba dutse bane, idanun shi ko kyaftawa basayi akan kirjin ta da yake gani, tareda Ayyana irin cika mai Hannun da zasuyi, har wani irin Aunawa yakeyi, he know dai dai Hannun shi ne. Kallo ta yakeyi sosai har mommy ta lura. Tareda Ayyanawa a ranta “Ahmed Indai ni Balkisu ce na haifeka bazaka taba hadamin iri da yar matsiyata ba muje zuwa.

Tayi k’wafa, Saida ta jera komai tareda turawa khaleel nashi  cimar ta koma gefe ta zauna itama, gaba daya kamshi ya gama cikasu, ita kanta mommy miyon ta ya tsunke,  wani irin murmurshi Ahmed keyi na jin dadi, domin yana ganin yanayin Abincin yasan zaiyi dadi sosai.

Khaleel ma kallon Abincin shi yakeyi, domin ba ataba hadamai shi da komai ba yana ganin yanda yayi wani irin kyau ga Aroma na tashi.  Momy kallon yanda yake kallon Abincin tayi tace “idan bazaka iyaci ba ayi maka wani? “No is OK, yafada yana daukar fork yafara ci. Wani irin test yaji tareda dadin da baitaba jin yayi ba, domin ta yimai hadin da kowama zai iya ci. Kallon shi Ahmed yayi “yadai brother its good? “Of cos Yaya she is a wonderful cook. Batareda ya kalli side d’in ta ba.

Shiru kakeji a wurin kowa na zuri, saida taga kowa baiyi complain ba itama ta debi kadan tafaraci, Ahmed sai aika Mata da sakonni yakeyi ta gefen ido, ta dukar da kanta dama suna facing juna itada shi.

Saida mommy tayi nak tace “next time idan zaki tuka tuwo ki tabbatar yayi sulbi sosai. To kawai tace domin idan dai ba tuwon masara takeso    ya koma ba,  tasan ko hasidin iza hasada yasan tuwon nan ya tuku. Maid din ce ta tayata suka kwashe komai zuwa kitchen, tayi daki domin yin sallah. Suma fita sukayi masallaci.

 

Mommy ce zaune a falon tana waya da Zarah “So nakeyi Auren khaleel ayishi cikin Sauri, don haka zanturo miki kudi kifara yomin odar Kaya na gani nafada, domin bikine zamuyi shi na kece raini.

Shigowa sukayi tayi Saurin Sallama, ta Ajiye wayar, zama sukayi tareda gaidata, tace tom dare yayi ku wuce ku kwanta Allah ya tashemu lafiya. Taci gaba da latsa wayar ta, “mommy in tafi dakina? “Ahmed yafada cikin sanyin murya mai hade da lallashi. “Saurin uban me kakeyi?  Da da bakayi Auren ba uban me ya sameka?  Kaga Ahmed ka fita idona in rufe, saboda aji dadin Asirce ka shiyasa kake kokarin shige Mata, to kabari sai nan da sati daya idan  Agumun da aka kullo Mata ya sirace ehem. Saurin kallon ta khaleel yayi tareda cewa “Haba momy haka ake Aure fisabilillahi? Ai da kin hana kawai yayi Auren wannan irin kwalelen ya isa Haba. “Toh ubana ai kai nasani zaka iya dukana ma, to dak’ar ni kaji, ku tashi ku wuce kubani wuri kafin in canja shawara.

Khaleel ya fara mikewa fuuu ya wuce saboda takaici, Ahmed ya tsaya tareda zamewa kasa ya dafa kafarta “don Allah momy in laifi nayi miki ki yafemin don Allah, kibarni in sauke hakkin Y’ar mutane ko lekata inyi infito minti biyar ya isa don Allah. Yafada yana zubo da kwalla, tace “minti biyar idan ka wuce hakan zan shigo kuma wallahi bazakaji da kyau ba.

Tashi yayi da sauri yana share kwalla “na gode mommy, ya nufi dakin yana Ajiyar zuciya, a zaune take tana waya da Shukrah a wayar Inna, tanajin motsi ta kashe tareda mikewa tana jan hijabin data Cire ta Ajiye a gefen gadon nashi. Rufe jikinta tayi a cukurkude tareda daburcewa ta rasa Ina zata shige ma, “Hmmm yayi doguwar  Ajiyar zuciya. Ya fara takowa cikin natsuwa tareda zuwa gaban ta. Hannayen ta ya riko. “Naziya”Am sorry please kinji komai zai wuce please don’t be angry with me I love you, hannu yasa ya zame hijabin dake kafadar ta ya fadi kasa ya zuba Mata ido tundaga sama har kasa.

“I don’t know you baby, yanzu nake sanin God gift da nasamu batareda sani na ba, you are beautiful baby, yafada idanun shi na kadawa kamar zaiyi kuka, cikin natsuwa ya bude hannayen ta yajata saman kirjin shi, jikinta na wani irin rawa domin wannan ne karon farko da namiji ya rungume ta, shikuwa jin kirjinta a nashi tuni yajishi a sama, Abunka da pure man da bai saba da cakuduwa da mata ba, Saura kiris su zube kasa, yana fesar da iska bakinshi domin samun sauki ya dago fuskar ta tareda dora lips dinshi kan kyakkyawan bakinta yaji kiran momy, ” Ahmed karka Bari inshigo ciki ranka zai baci nafada maka. Saurin janyewa tayi domin a tsorace take dashi tanajin yanda yake murza jikinshi a laps dinta she can feel his hardness, da bata kawo komeye ba ma. Muryar shi a shake yaja baya “please kibiyoni Anjima Kinga mommy tace infita anan   please wife kifito ko kitchen ne muyi magana. Yafada yana fita cikin hanzari da Sauri, wasu irin kwalla ne suka taru a idanun shi.

Zamewa tayi kasa ta zauna tanajin wani irin yam yam a jikin ta, Allah yagani tana son Ahmed, Abinda ya boye mata Wannan ta fahimci dalilin shi domin ita ta nunamai batason namiji mai hali, Sannan yanzu ta Kara fahimtar shi Waye daga jiya zuwa yau, yana matukar son familyn shi yana bin umarnin mahaifiyar shi mai cikeda matsaloli Wanda ta daura damarar zata yi mata biyayya muddin ranta domin Ahmed, wani irin tausayi yabata yanzu, hawayen data hango akan kyakkywar fuskar shi kawai ya karya mata zuciya, me zatayi da zai sanyaya mai rai?

Daukar wayarta tayi ta Kira yayar ta bayan ta kulle kofar ta, Aunty Raliya, itace babbar yayar su ita ma tana Auren mai d’an hali saidai kamar yanda Al Adar su take suba masu yawon gidajen y’an uwa bane, “Aunty Raliya Ina wuni. “Amarya yadai kina kirana Karfe goma lafiya ko? “Lafiya kalau Aunty yasu Abba?  Duk sunyi bacci, Ina fatan ba Matsala ko?  “Um um, “Ina mijinki kike Kira na by this time? ” baya nan yana dakin su. “What bangane ba, kodai kinki yarda dashi ne?  “Aa. “Naziya, ki fadamin damuwar ki Kinga ke ba kawaye gareki ba da zaki fadamusu ni yayar kice bazan so ki cutu ba,  bakomai Aunty. “OK listing to me  kije ki dafamai ruwan tea  mai kayan hadi ki shirya ki kaimai dakin nashi, kinsan wasu maza basa son shiga dakin mata saidai mata su bisu, “Aunty sai inje? “Karkije kinji, ki tsaya shirme wawuya kawai. Ta datse kiran kit, domin tanada zafi, tasan duk Abinda ke faruwa kuma sunada labarin uwar mijin Naziya domin Zarah kusa da ita take kuma haryau batasan Naziya kanwar tabace don haka ko dazu tashigo tana bata labarin Hajiya bilkisu da yanda take  juya Ahmed, tana dariya da jin dadi,

 

 

Shiru Naziya tayi tarasa ta Ina zata fara, tashi tayi cikin Sauri, saida ta leka falon taga bakowa domin mommy nada nauyin bacci tana shiga dakin ta ta bingire, kitchen ta shiga ta dafamai ruwan tea harda na’a na’a, yana tashin kamshi, ta samu tea jug da cup ta zuba ta fita tana tunanin Ina zata ganshi harta bashi tea din takoma dakinta, jitayi anriko Hannun ta, tayi Saurin juyawa zata Sa ihu yace “Shhhhhh, nine, ware idanu tayi, jikin ta na rawa tace “ga tea Dama shi zankai……… Rikota kawai yayi ya nufi hanyar dakin khaleel da ita, yana kan computer yana duba   harkokin company dinsu da Ahmed ke gabatar mai yanzu, ganin su yayi  kawai ya sauke kanshi. Saida ya zaunar da ita ya koma gefen Khaleel yace “brother please excuse us. Dago kai yayi tareda kallon yayan nashi cikin idanun shi kuma yasan sarai me yake nufi yace “Ina zanje Yaya nida dakina? “Go to my room please, “zan tsaya a falo idan kungama magana indawo but I can’t go to your room yanzu na Matar ka ne, “OK tanks ten minutes kafin mommy ta farka,.tashi yayi tareda daukar wayar shi ya fita yana “quick brother kaga Ina aiki na ka tsayar dani,

Kulle kofar yayi tareda nufar inda take tsaye cikin hijabin ta,……. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

Ga masu son su biya ga account details dina, *NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB* sai ku min magana ta wannan number 09069200154

 

 

 

 

 

🆓 page

 

 

1⃣1⃣&1⃣2⃣

 

 

 

 

…………….rikota yayi zuwa jikin shi tana zamewa yace “wait Naziya please magana zamuyi kawai. zama yayi agefen gadon, ya dorata akan kafarshi, “Kiyi hakuri da duk Abinda yake faruwa that’s our destiny, komai zaizo karshe, nasan kinada tarbiya kinada hakuri please keep it up, zamuci ribar Abun, idan kikaci gaba da tafiya a haka banida wata damuwa, yakamata ace yanzu mun zama daya, yakamata ace muna cikin bargo daya, yakamata mu zauna muyi hira in kula dake kamar kowane miji, but don’t worry komai zai wuce, yafada yana zagaye west dinta da hannayen shi, tareda kwantar da kanta cikin kirjin shi, wani irin Abu takeji yana mata yawo a cikin jiki duk lokacin da ya tabata, kodon bata taba experiencing irin haka a Rayuwar ta bane. Jin yanda yake cusa kanshi a wuyan ta yasa take d’an zamewa domin tanajin yanda yake kokarin daga hijabin jikinta tareda nufar kirjinta yana so yaji how they are. Tayi Saurin riko Hannun shi tareda Saurin juyawa tana girgiza mai kai cikeda marai raicewa. Kallon ta yayi cikeda roko yanaso tabarshi yayi yanda yakeso ko zai rage zafi domin yasan bazai yuwu ya nemeta a dakin khaleel ba, kuma yana falo zai iya jinsu domin yasan bakaramin aiki zaiyi ba, kuma yasan zata iya mai kuka tunda ko kirjinta bai fara tabawa ba . “Naziya ” yakirata cikin wata irin murya, “inaso intaba inji, nonon ki nada kyau dazu kamar inyi tsalle in cafka nakeji Dana ganki ba hijab, kibani Dama ingansu inyi wasa dasu ko kadan ne. Wani irin tsalle tayi tareda zamewa ta rufe fuskar ta saboda kunya da maganar shi ta bata, kai namiji baida ta ido, saikace ba Ahmed innocent man ba yafada har yana dariya, “is OK tashi in rakaki wata rana da kanki zaki bani insha. Saurin mikewa tayi ya dafata “da munkwana tare da tuni sunzama toy dina, Amma lokaci ne. Kunya kamar ta nutse kasa, shikuwa ko ajikin shi,

Fitowa sukayi yana tsaye a falon rikeda ruwa mai sanyi yana kwankwada idanun shi cikin nata karab, idan ba gizo idanun ta suke mata ba tana ganin irin kallon rainin hankalin da yake mata, hartayi Saurin kwace Hannun ta ta wuce da Sauri, yana “baby ba Sallama, ita kuwa bazata iya tsayuwa kusa da d’an rainin hankalin nan bane Sam, mai halin yahudawa, ace mutum kullum cikin guntayen kaya kamar wani nakan dutse, mtsww.

 

Saurin wucewa dakin yayi yana karewa gadon nashi kallo yaga yanda zanin ya zame gaba daya, saboda zaman da sukayi a gefen shi, kuma bakaramin jujjuyawa Ahmed yarikayi ba saboda mugun feelings din da yakeji, shigowa yayi yace “Sorry Bari in gyara mana gadon, shiru yayi har yagama ya wuce bathroom, yana kallon yayan nashi bai ce tak ba, ganin yayo wanka yafito yaganshi a tsayen yace “yadai ko wankan kaima zakayi? “No ba munyi wanka ba kaima naga weather din is OK why you bath again? “Hhhh oh come on brother ko bakaga ma tata ta shigo ba kaima kasan dole inyi wanka ai.  “in ten minutes?  Ya fada batareda ya san maganar ta fito ba, “of cos is enough for me. Ya bashi Amsa tareda hayewa gadon ya kwanta cikeda farin ciki, kafin ya tuno da tea ya diro ya tsiyaya  ya farasha yana lumshe idanun shi.

Komawa yayi kan kujera ya zauna yana danna waya har Ahmed yagama ya haye gadon yana cewa “ga coffee idan zakasha narage maka. “Uhm. Kawai ya Amsa, ganin Sam bazai iya bacci ba ya mike ya shiga bathroom wanka yayi tareda Alwala yadawo dakin yatada sallah.

 

 

 

Gefen Naziya kuwa, tayi bacci cikin kwanciyar hankali tareda farin ciki, tasan Allah yabata miji mai halin kwarai kuma da yardar Allah zata tayashi yiwa mahaifiyar shi biyayya.

Sabo da tashi da wuri Karfe hudu ta tashi, saida ta yi sallar nafila kafin biyar tayi farillah, ta zauna Azkar zuwa Karfe shida ta fito cikin karamin hijabi zuwa kitchen, ta shirya musu breakfast mai lafiya. Kafin bakwai da rabi ta kammala ta gyara ko Ina takoma tayi wanka, shiryawa tayi cikin Riga da zani, tafito tsab,  tana kamshi.

Kiran mommy yasa ta fito da gudu tana amsawa ta ganta hakimce, dukawa tayi ta gaida ita, “ke bakisan kiyi pleasing uwar miji ba ta hanyar shiga dakina ki gyaramin da kuma dakin khaleel, toh daga yau gyaran dakunan mu na Hannun ki idan kin tashi. “Toh mommy. “Oya a shirya mana breakfast anan yau ma.

Fitowa  Ahmed yayi idanun shi kur akanta yana aika Mata da sako tareda murmurshi mai cikeda sirrika. Itama tayimai tareda dukar da kanta tafara aikin ta,

“Ina Ibrahim din?  Bacci yakeyi jiya baiyi bacci da wuri ba yace sai ya tashi. “Aa nifa banason wasa da ciki, ke Naziya yi Sauri ki kaiwa dana Abinci a daki karya kwanta da yunwa. “Mommy da kin Bari ya tashi. “Wuce maza ki kaimai.  tafada, tana cewa “jeki zanyi serving din mu maza ki tabbatar yaci kafin ya kwanta. Jim tayi kamar bazataje ba tace “me kike jira?  Cikin tsawa, da Sauri ta dakko tray ta shirya mai komai nashi ta wuce jiki a sanyaye “Allah yagani itadai jinin ta bai hadu dana gayen nan ba, baiyi mata ba Sam, da Sallama ta shiga dakin,  yana kwance a tree seater a kudun dune,  fuskar shi ce kawai a bude. Idanun shi biyu yana kallon sama, Sallamar ta yasa ya d’an juyo cikeda yanga, ta tsaya daga nesa muryar ta na rawa ga shi inji Mommy, ta dora akan karamin table zata juya, “Serve me. Yafada cikin isa, tayi Saurin juyowa “wannan mugun d’an rainin wayau ne, batason musu don haka cikin Sauri ta juyo batareda ta kalle shiba ta hada mai komai tafita cikin Sauri.

“Hmmm kawai yace yafara cin Abincin shi. Yana lumshe idanun shi.

Komawa tayi falon tace tabashi. Kafin ta zauna tafara nata Karin.

 

 

Toh haka dai kwanaki keta tafiya yau Naziya ta kai wata daya cur Agidan komai na gidan tundaga gyaran dakunan su zuwa kitchen ya koma Hannun ta, complain din momy ya riga ya shiga jikinta, Ahmed kuwa yanzu ganin shima gagarar ta yakeyi domin dokar mommy tayi nisa yanzu, tun yana rokonta harya hakura ya zura ido, sai rama yakeyi a tsaye saboda damuwa baya ko son haduwa da Naziya saidai suyi chart da wayar da ya siya mata katuwa wadda ta boyeta a dakin ta bata Bari mommy tagani ba, by now ta fuskanci muguwar kiyayyar da mommy ke mata. Idan ya fita aiki kuwa yana kiranta kullum bata hakuri yakeyi,. Tana kwantar mai da hankali domin ta saki jiki dashi sosai, yanzu har marmarin ganin shi takeyi akusa da ita she is missing his touch, rabon da ya rungume ta tun a dakin Khaleel, kullum Aunty Raliya shawarwari take bata wainda Sam basuda Amfani a wurin ta tunda an hanata sakewa da mijin ta. Iyakar ta dashi sai ban hakuri tareda Sanya mata Albarka a kullum “Naziya ke Y’ar Aljannah ce, watara na zakiyi farin ciki, ki Kara hakuri komai mai wucewa ne.

 

 

Bikin khaleel Ansa rana wata daya mommy sai shiri akeyi An shirya event Kala Kala, khaleel ko a jikin shi domin Amaryar ma ko wayar ta baya dauka, Wanda ta watsa shi a kwandon shara tunda dai uwar miji na sonta ai zata wataya kuma dole ya sota.

Zaune suke a office din yayan nashi ya kalle shi “brother sai ramewa kakeyi are you Alright? “Am not khaleel, yama zan zama cikin kwanciyar hankali bayan kana ganin me yake faruwa?  “Am sorry Yaya bansan yanda zantaimake kaba. “Is OK yanzu kaga maganar shigo da kaya zai zo dai dai da lokacin Auran ka naso kaje da kanka,  ko zaka Bari kaje honey moon gaba daya? Yafada yana d’an murmurshin karfin hali. “Noo wane irin honey moon?  Zantafi kawai idan nadawo ai ba guduwa zatayi ba. OK kafadawa mommy ba ruwana.

 

Karfe biyu suka shigo gidan, an baje akwatunan sunkai saiti bakwai an narka dukiya kamar za asiyo mutum, suna shigowa tace “Yauwa khaleel zoku gani komai yaji?  Tafada cikeda farin ciki, ya zauna yana kallon kayan tareda mamaki ” mommy kayan Waye duka? “Ga rainin wayau, na Matar ka ne mana. “Duka?  Yes gaskiya aa a raba biyu abawa Naziya rabi. “Why zan bata rabi?  Saboda am sure ba ayi mata irin haka ba. Yafada cikin zafin rai, “bazan  bayar ba domin batasan darajar suba, fitar kunya nakeson inyi dasu gidan minister guda dole akai Abinda baza a raina muba, Kuma ka nemo motar da za a hada mai tsada ta mata. Ahmed ne ya katse maganar  “Zamuyi placing oder momy na kayan mu sai kasa a turo motar da kakeso kafin katafi.

Saurin kallon shi tayi tareda cewa “Ina zaije? “China zai shigo mana da wasu kaya. “Yaushe?  Nan da sati uku. “Saboda mugunta?  yaro zaiyi Aure ya Amarce shine zaka  turashi wajen kwaso kaya? “Mommy, ni nace zanje ba Yaya ya sani ba, I want to go. “You are not going don haka ya shirya shi yaje, tunda nashi Auren baida Amfani, idan kanaso kaji dadi Ahmed sai ka Auro zabin zuciya ta Amma Indai Inada rai bazan hada iri da yar masu zama akan buzuba a mallake min da’.

Kallon momyn yakeyi wani iri, sometimes sai yaji kamar ba ita ta haifeshi ba, domin duk uwa tana son farin cikin d’an ta. Tashi yayi kawai yayi dakin shi dai dai tana fitowa ya ganta Amma saboda ciwon da kirjin shi ke mai yakasa ko tsayawa yayi mata magana. Kallon shi tayi sosai, taga ramar shi a yau tareda yanda yayi sanyi sosai, duk da ba mai hayaniya bane,

Jikin ta yayi sanyi, Allah yagani yanzu ba Abinda takeso irin su zauna suyi hira ido da ido ita dashi domin kullum soyayyar shi karuwa takeyi a zuciyar ta.

Kallon momyn  khaleel yayi “mommy me kike nufi da d’an uwana?  “Kamar ya?  “Momy ki barshi ya samu natsuwa mommy don’t you see how sad he is? Bakya ganin yanda yake ramewa? Mommy Yayana na cikin damuwa sosai, I beg of you kibarshi ya huta haka. Wani irin kallon zanci ubanka tayi mai kafin ta mike cikin fada tayi dakin Khaleel din, “zanje inji dalilin da zai rika hadani  da kai kana titsiyeni kamar ubana.

Binta yayi yana yi mata magana tayi banza tayi dashi. Zaune yake yana dafe kirjin shi, ta shigo “toh kanin uwata Wato da kun hadu saika rika zugo d’an uwan ka yana titsiyeni kamar ubana ko, toh ka fita I dona kuma ka saurare ni, nayiwa Kawata magana Hajiya sa’ade maganar Y’ar ta Salifa idan ka shirya zama da Matar son taka toh ka yarda ka Auri zabin rai na lokacin zanbaka damar da zaka zauna da Matar son taka.

Kallon mahaifiyar tashi yakeyi tareda yin tagumi saida ta ci gaba da fada yace “am sorry momy bazan iya musu dakeba kiyi duk Abinda ya dace insha Allahu zanyi miki biyayya. “What Yaya?  Me kake fada?  This is too much gaskiya Haba momy p…… “Quit Khaleel Yafada cikin dakamai tsawa, tareda nuna shi da yatsa “not a word again, why are you challenging our mother? Kar in kuma jin kalma daya daga bakin ka. Fita tayi kawai tana amsa wayar fauzy tana dariya “Y’ar Albarka wane irin product kike Amfani dashi na kayan kwalliya?

Wani irin bakin ciki khaleel yaji tareda kallon Ahmed din ya wuce domin shima ya batamai rai. kwanciyar shi yayi kawai yana kallon sama. Dawowa yayi ya tsaya akan shi “Yaya what ever is happening is  not right. why zaka zuba ido kana over looking komai, how could you accept the second marriage?  Ka manta me kafadamin, kaman ta kafadamin bazaka taba hada Naziya da wata mace ba?  She didn’t deserve All this life Yaya, she deserve to be happy. “Hmmm ya kakeso inyi Khaleel?  Inyi disobeying mommy oh what?  “She is my mother Ina so mu rabu lafiya, and Naziya yes I love her more than my life, yazanyi dole inbi mommy in inaso inga dakyau, ba wata mace da zata samu matsuguni a zuciya ta, ita kadai nakeso ita kadaice zabina, if Auren da mommy zatayi min shine zaisa tabarni da matata in zauna lafiya then be it, am ready to obey what ever she said that’s final. Yafada yana mikewa cikin fushi yayi bathroom.

 

 

“She didn’t deserve it. Yafada yana naushin iska, he feels as kamar shi yafi kowa jin ciwon Abinda akeyi mata, ita kanta nuna wa take ba Abinda ke damun ta, tun ranar da tazo gidan nan yaganta tana kuka bai kuma ganin ta cikin bacin rai ba, sai kace bata da zuciya?

Fita yayi fuu dai dai tana shiga kitchen, cikin zafin zuciya ya bi bayan ta, kafin ta ankara jin hucin mutum kawai tayi yana fesa mata numfashi cikin zafi a bayan wuyan ta, kurawa kwantacciyar Sumar dake wurin idon ta yayi, idanun shi sun kada, he don’t really know why zuciyar shi ke tafasa, he is trying to control his Anger da baisan dalilin taba.

“Auzubillahi. Tafada tana ja baya da Sauri domin tsayuwar da yayi a bayan ta ya kaucewa tsarin Addini, kuma shi ba muharramin ta bane, wani irin kallon bakada tarbiya take watsa mai tareda nisan ta kanta daga kusa dashi, he can clearly read her reactions, don haka tuni zuciyar shi ta Kara hawa, “what?  Why are you looking at me like  that? Yafada yana describing da hannun shi,  A haka zaki karasa zaman Rayuwar Auren naki you don’t care about your husband, kawai kiyi bacci ki tashi ki dafa Abinci, shine damuwar ki, you are pretending as if you don’t care about All this wealth, you are such a jocks,  kin zauna kin baje ba Abinda ya dameki sai kici kiyi bacci you forget All your responsibilities, look if anything happen to my brother because of you, I won’t forgive you.

Tunda ya fara magana kallon shi takeyi, kuma irin kallon you won’t get away with this, yanayin shiru ta gyara tsayuwar ta tareda daga gira daya, and she look very cute, “oh really?  So nice bansan responsibility dina ba?  Saboda nayi shiru Ina kallon komai, waya fada maka Ina farin ciki da duk Abinda yake faruwa da zaman Aure na?  Nice nakeda complain ba yayan kaba because I know my right, and da kake cewa duk Abinda ya samu yayan ka bazaka yafemin ba, ni kuma in wani Abu ya same ni fa? Kana tunanin iyaye na zasu yafe muku? “And don’t forget he is my husband, kuma munyi Aure saboda Ina son shi ba kiyayya ba, this house Hmm who told you am happy in this house? hakuri nakeyi bisa ga irin tarbiyar da aka dorani akai, iyaye nagari suka daga rayuwata, yawo da shigar da bata dace ba duk iyayen mu sun hane mu, shiga hurumin da bana muba duk iyayen mu sun hane mu, Saboda sudin iyaye ne nagari……… “Nice ba uwar kwarai ba kenan?  Mommy tafada cikin tsananin bala’i

Jikin Naziya na rawa tayi Saurin kame bakin ta, tareda dana sanin biyewa zuciyar ta ta tsaya kula khaleel bayan hakan ma bai dace ba, yanzu tun ba aje ko inaba she is regretting……. 🖊

 

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

 

Ga masu son su biya ga account details dina, *NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB* sai Ku min magana ta wannan number 09069200154

 

 

 

 

🆓 page

 

1⃣3⃣&1⃣4⃣

 

 

 

………….. “Mommy,  magana mukeyi please don’t interfere please. “Karya ne wallahi duk naji Abinda ke faruwa tundaga farko, Wato munafuka sai ki rika nuna halin kirki Wato mugun halin ki na can cikin zuciyar ki ko, “toh kin fada son ranki yanzu ki saurare ni mai miji, yau nawa ga wata? Aure zanyi wa mijin naki rana daya da Khaleel, zan Auro mai Matar kwarai Matar nunawa sa’a ba Y’ar gidan masu kwana kan buzu ba, munafuka kinayi kamar tagari Ashe bakin hali na nan a gefen zani,  kin tsaya kina musayar miyau da kanin mijin ki sai kace sa’an ki. Dafe kanshi kawai yayi, you mess up things kawai, Naziya durkushewa tayi for the second time ta saki kuka mai ciwo “kishiya Aure?  Bayan ita ko dama ba abata ba ta mori Auren shine ake wani zancen za ayi mata kishiya?.

Tashi tayi da gudu tawuce zuwa daki tabar aikin domin wani irin zafi zuciyar ta keyi mata.

Kukan ta ya taba mishi zuciya fiyeda tunanin mutum wani irin sarawa kanshi keyi kamar  zai tsage biyu.

“Kai kuma ka tsaya yarinya karama na zuba maka rashin kunya kana kallon ta, bazaka watsa mata Mari ba, kauce ni in wuce ka batamin rai. Tafada tana fita, sintiri yakeyi a kitchen din yarasa Ina zai sa kanshi, kallon da ta watsa mai ne yafi komai daga mai hankali, she really hate him. Fita yayi da sauri ya Kira maid yace ta karasa aikin girkin yayi dakin shi,

“Ahmed yasamu akan dadduma yana lazimi, yace “Yaya please go to your wife she is crying please. Saurin mikewa yayi me yake faruwa?  Wa ya sata kuka?  “Is you Yaya kaine sanadi, mommy Tafada mata zakayi Aure please go to her. Yafada zuciyar shi na wani irin rawa, komawa Ahmed yayi gefen gadon ya zauna dabas, “I can’t go khaleel. “Why? Yaya Matar kace, she needs your comfort please. “Mommy tayi min iyaka da ita. “Iyaka?  What iyaka?  “Yaya hakkin yarinyar nan bazai barka ba karka manta ba mommy ce kawai keda  hakki akanka ba, why ka Auro ta idan bazaka iya ba?

 

Kukan da yaga Ahmed din nayi yasa yayi Saurin zama gefen shi ya rungume shi yana Ajiyar zuciya, “am sorry Yaya please nasan komai, amma kaine kabada kofar komai dake faruwa. Bai iya cewa komai ba sai shesheka yakeyi “am sorry khaleel banda karfin zuciya irin taka am weak.

Saida ya fitar da kwallar tausayin d’an uwan nashi.

 

Naziya kuwa tana shiga ta kulle kofar ta fada bathroom ta shako kukan ta son ranta, Karar wayar ta tasa ta fita ta dauka ganin number Ahmed dince yasa ta datse kiran kit tareda kiran Aunty Raliya.

Tana dauka tasaki kuka mai ciwo. “Aunty wallahi nagaji ni zankoma gida nagaji bazan iya ba, zan mutu a rasa dalilin mutuwa ta Aunty please kizo ki tafi dani.

Saida tayi ma ishinta ta yi shiru tana jinta, “Naziya’, ta kirata, bata iya amsawa ba sai sheshsheka tace ” kin taba ganin ko kwana muntaba yi agida tunda mukayi Aure, bare kuma yaji? Dagani har Aisha ba wadda ta taba kai Karar mijin ta cikin gida ko gaban malam, muna hakuri tareda bawa junan mu shawara in Matsala ta taso, infada miki gaskiya?  Ba macen da batada kalar tata Matsalar Aure, please Naziya ki dauki halin  Inna, kina gani kullum malam yabon ta yakeyi domin yasan mace ce tagari, nasan duk Abinda yake faruwa a gidan Auren ki, ba kanki farau ba, ki jajirce kici gaba da hakuri, yanzu fa aka fara Naziya, ni nafada miki tun farko kibi mijin ki tunda shi an hanashi binki, biyayyar Aure kikeyi bauta kikeyi, ki rungumi taki kaddarar Allah zai kawo miki mafita.

“Aunty banki ta taki ba, Amma inayin iya bakin kokari na, kinaji fa wai Aure zai karayi. “Toh sai me?  Baki yarda da kanki bane?  Ke ba mace bace?  Look ki nuna musu Auren ba komai bane idan bakida hakki zakiga saka mako, nasan kinada hakuri ki Kara akai kar taurin kanki ya motsa Wanda bakya juyuwa.

“Hmmm nagode Aunty, insha Allahu zanyi hakuri. “That’s my sister, kuma insha Allahu zamuzo karshen satin nan nida Aisha. Dadi taji sosai domin Y’ar uwarta ta bata shawara mai kyau, tareda sanyaya mata zuciya.

 

Sharewa tayi da komai cikin ikon Allah, ta Kara rungumar hakuri tareda daura damarar share komai, tana ganin yanda aketa shirin biki kamar da gayya itama Amarya anyo mata kayan fitar kunya, Aljihu tasa Ahmed ya bude yana bata kudi ta zabgi kaya, ciwo yakeyi a tsaye batareda ya fadawa kowa ba shikadai yasan damuwar shi, Naziya tuni ya  nesanta kanshi da ita domin ya rage mata damuwa, itama ta Ajiyeshi a kwandon shara, badon bata damuwa ba, biki nata matsowa shikuma yana shirin tafiyar shi.

Khaleel yayi yayi yabarshi ya tafi yace no shi zaije Ana gama biki Washe gari zai wuce. Mommy ma basu fada mata shirin su ba.

Khaleel ma tuni ya kiyayi Naziya domin ya lura tsanar tashi ta Kara yawa fiyeda da, yana ganin yanda take hada girar sama data kasa in sun hadu, shi yasan halinta Wanda Ahmed bai san shiba ma yanzu, daga gani macece kaifi daya inbata yinka shikenan, ga taurin kai.

Tana lura da Al amarin shi yanzu sama sama in sun hadu ta lura yanzu baya fitowa da kana nan kaya ko falo, tun ranar da tayi mai gori.

 

Biki fa yazo Amare nata rawar kafa, angwaye kuwa ko motsi basayi, ko Khaleel Yafada mata karta sake ta sakashi cikin shirmen party d’in su. Momy ta tattara su duka ta watsar tana hidimar ta, itadai tasan burin ta zai cika ya’yan ta zasu Auri irin zabin ranta,  don haka ta zage ta bude bakin Jakarta.

Lafiyayyan mothers day suka shirya a tafkeken hall  da yaji kudi, ta gayyaci manyan mata masu kudi da Aji, da kanta tayowa Naziya dunkuna Kala goma wai na dannar kirji tasa na fitar biki.

 

Lokacin da malam yaji labari, waya yasa aka hadashi da ita ya mata nasiha tareda Sanya mata Albarka, Wanda ta Kara mata kwarin guiwa, bawai Abun baya taba ta bane a’a “ya za’ayi bazai zafeta ba, kawai dai ta rungumi hakuri da kuma waraka,  Wato Alqur’ani mai girma. Wanda shine maganin duk wata damuwa da yayewar bakin ciki.

Ana Saura kwana uku biki tasa Shukrah tazo domin ta yi mata lalle, Wanda saida tayi da gaske Malam yabari, tazo suka baje a dakin suna hira tana yimata lalle, “Aunty Kinga magana ta ko, nafada miki Yaya Ahmed mai kudi ne, gaskiya kin more irin wannan katon gidan. “Hmmm. Kawai tace, “Amma Aunty kin d’an rame kadan sai haske kawai da kika Kara, Ina Yaya Ahmed din? “Yana nan, kuma ki rage surutu kiyi sauri kafin lokacin da Malam yabamu yayi, Amma Aunty da gaske Aure zai Kara wai?  “Eh. “Auren ku wata daya da y’an satika shine zai Kara? “Ya isa maganar shukrah, tafada domin batason zancen,

Maid ta kawo musu kayan ciye ciye a dakin, domin mommy tafita, har suka gama ta rakota tareda bata kyautar kayan shafa, domin batada kudi a hannun ta, suna fitowa su Ahmed sukayi Sallama, tayi Saurin dauke kanta. Shukrah baki har kunne domin tayi mugun sabo dashi tace “lah Yaya Ashe zangan ka kafin intafi? “A a shukrah kece a gidan namu?  “Eh  Yaya Ahmed har nagama wa Amaryar taka lalle zantafi,  Saurin kallon hannun nata sukayi dukan su, khaleel yayi Saurin dauke kanshi, “kai Amma mungode shukrah da wannan zuwan Yafada yana matsawa kusa da Naziya ya riko hannun ta, shukrah tayi Saurin rufe idanun ta saboda kunya ta ruga hanyar waje tana ni na gudu gida Aunty bye, Dariya Ahmed yayi yace “please Brother ka kaita gida. Amsawa yayi kawai ya fita, motar shi ya fada dalleliya yabi bayan ta, tareda yimata horn, ta tsaya don har tafita wajen gate d’in, “muje ko’ Yafada ba wani walwala, “nagode zansamu adai daita ma. “Come on ki shigo Yaya Ahmed yace inkai ki.

Budewa tayi kawai saboda batason musu, gashi ya cika mata ido, maganar gaskiya zaiyi wulakanci domin fuskar tashi Sam ba fara’a ko walwala, don haka batayi yunkurin cemai komai ba har ya  Kama hanya yana driving slowly, sai kamshin shi da kwarjini da ya cika motar, “me yasa bakya zuwa kina ganin Y’ar uwar ki?  Yafada batareda yako kalli gefen taba, itama Abun yazo mata a bazata  duk ta diririce, saida ya mai maita, tace “ba a barin mu  fita zuwa yawo. Tabe bakin shi yayi kawai bai kuma cewa komai ba har ya kaita kofar gidan  tace ta gode, ya ciro kudi a gaban motar shi ya mika mata masu yawa, Saurin kallon hannun shi tayi ta koma gefe tana girgiza kai, domin kudin zai kai dubu Ashirin, “nagode bama karbar kudi a waje. Mayar wa yayi kawai yaja motar shi tareda bade ta da kura yayi gaba, “tab Aunty Naziya wannan ai yafi Yaya Ahmed girma da cika ido ga girman kai kamar d’an gidan Sarki,. Tafada tana bin bayan motar shi da kallo har ya bace.

 

 

 

Su khaleel na fita ta fisgi hannun ta tayi dakin ta da gudu, yanzu ne wani irin bakin ciki yake rufe mata zuciya, bin bayan ta yayi batareda ya shirya ba, zubewa tayi agadon ta kife tareda sakin kuka mai taba zuciya,   dafata yayi tayi Saurin zabura fuskar ta shabe shabe da hawaye “don’t touch me. Tafada kai tsaye tana mai kallon kai ne sanadi, “Ina dana sani, nayi hakuri tunda ga ranar farko da Nazo gidanku, bawai nace mommy bata isa tayi min fada bane, a’a kaine Matsala ta, kai kakawo ni gidan nan, Amma sai dai in hadu dakai a hanya, duk na daure nayi hakuri, yanzu kishiya…… Takarasa tana kife kanta a cinyar ta, shiru yayi tareda dafe kanshi yazame gefen gadon ya Rungumo ta baki daya zuwa jikin shi tana kokarin Sauka. “Nasani Naziya, ki yafemin don Allah, nasan sai Allah ya tanbayeni hakkin ki, domin banyi miki Adalci ba, yazanyi Naziya Ina gudun bakin uwa, yanzu ma na kaucewa tsarin ta da dokar ta, don Allah kiyi shiru ki yafemin kar Kisa ni a cikin damuwa, kinsan cewa ganin kwanciyar hankalin ki ke kwantar min da nawa, Amma yanzu idan kina wannan kukan zuciya ta zata iya bugawa kowa yarasa ni. Saurin yin shiru tayi tareda share hawaye da bayan hannun ta “meye laifi na?  Saboda Ina Y’ar talaka? Meye illar talauci tunda bamu nema a wurin wani ba,  Alhamdulillah da gidan da na fito bama raina Abin da Allah ya bamu. “I know” Naziya please forgive me, kuma Kisa a ranki wata rana komai zai wuce, zakiyi farin ciki insha Allahu, ni nasan banda wata kalma da zanyi Amfani da ita domin baki hakuri Amma nasani na zalunce ki, ki yafemin. Naziya na gaza akanki ban sauke nauyin ki dake wuyana ba. Yafada yana dora fuskar shi akan wuyan ta, wasu irin hawayen shi taji suna bin wuyan nata, da sauri ta dora hannun ta saman kanshi tareda cewa “don Allah kayi shiru nima kaga na hakura nayi shiru, kaga bakyau babba na kuka. Tashi yayi tareda ita ya zauna gefen gadon, tareda fuskantar ta yana share idanun nashi yana mai murmushi kadan, “wayace miki ni babba ne a wurin ki? “Kai babba ne ai ka girme ni sosai. “No ni jaririne a wurinki domin wata rana shayar dani zakiyi,,, wani irin saurin rufe fuskar ta tayi saboda kunya, “Hhhhhh ko za a bani ne yanzu, Yafada yana riko west dinta cikin tsokana, ta zame cike da kunya,  dadin moment din sukeji sosai, ta kalle shi cikeda tausayin shi tace, “bakada lafiya ne?  Murmurshi yayi, “yes. “Meke damun ka?  “Soyayyar matata, you know banason in rasaki Naziya  idan nayi tunanin zaki iya gajiya ki gujeni hankalina natashi,  bazan iya ganin ki kina Rayuwa ba agidana ba, banason inganki tareda wani Naziya saboda Ina sonki Ina kishin ki, ganin ki a inuwar Aurena yana sani inji farin ciki, yana rage min damuwa, please stay with me, my wife komai zaizo karshe wata rana zamu kasance a cikin inuwa daya zanganki da jini na atare dake a wannan shafaffen marar. Yafada yana shafo cikin ta, d’an zamewa tayi kadan domin yanasa ta jin wani iri a jikin ta. A wannan lokacin ya bata farin ciki mai yawa Wanda zata sakashi a tarihin Rayuwar ta domin yamata Alkawura da yawa akan yanda zaman su zai kasance, anan yake fada mata bayan bikin Khaleel da kwana biyu zaiyi tafiya, Kinga da momy zata Amince tare zamu tafi dake, muje musha soyayyar mu a can har in zagaya dake kasashe da dama.

Maganar mommy ce tasa ya mike tareda cewa mommy is here bari inje. Ya fita da sauri, tana tsaye tareda Khaleel Wanda shigowar shi kenan, tare suka zuba mai ido suna kallon shi, Wani irin mugun kallo ta watsa mai, “uban me kakeyi a ciki?  Shiru yayi ya kasa Amsata, “Ahmed idan ka ketare iyakar da nayi maka banyafe maka nono na da kasha ba. Tafada tana nuna shi da yatsa, saurin daga kanshi yayi tareda girgiza kai kawai ya wuce domin bazai iya magana ba,

Khaleel ne yakalleta “why mommy? d’an  ubanka, wallahi kaima kaji ko a mafarki naji ka fada soyayyar Y’ar talaka bazamu kare lafiya dakai ba. “Saboda me?  Talaka ba mutum bane mommy?  “Me ake da sunan talauci ma?  Ni wuce bani wuri kuma kaji Abinda nace maka ko ku nemi Amaren ku sallame su banason harkar tsiya tunda dai Allah ya Azurta mu, idan bazaka iya cirewa a jikin ka ba kazo inbaka kabasu. “Wallahi mommy ba shegiyar da zanbawa kudina saboda tayi taron banza ai sunada kudi kowacce Aljihun ta yayi kuka, yafada yanayi gaba batareda ya tsaya saurarar taba, “kaga d’an banza, ai da Ahmed ne yanzu zaiyi Abinda nace Amma wannan mai taurin kan tsiyan sai mun sha fama.

 

Biki fa yazo, Amare nata shan even, momy yau ne take nata taron gidan makil da mutane ta gama cika gida da manyan mata y’an karya unguwar kawai daka shigo zakasan biki akeyi na kece raini, Naziya tun da gari ya Waye take jinta wani iri, mugun sanyi da zazzabi ke rufeta ma saboda damuwa, yau dai ba aiki domin komai odar momy tayo har Abinci,

Don haka tana kwance tana lazumi da carbinta na yatsa,  Shigowa tayi cikin fada, “ke banason bakin ciki da kishi ki tashi ki shirya ki fito, kinzo kin kunshe a cikin daki kamar tsohuwar munafuka, Aure dai gobe insha Allahu sai an daura shi ko zaki mutu, in banda Abunki keda ko dadin Auren baki sani ba meye na kishi, don haka fito maza yanzu mutane natanbaya Ina uwar gidan Ahmed.

 

 

Tashi tayi cikin Sauri, tace “toh mommy, ta wuce bathroom ta sheko wanka, cikin kayan da momy ta bata ta ciro wani lafiyayyen leshi riga da sket kamar dinkin Amare ta saka, tana taje sumar ta taji Sallamar y’an uwan ta, Aunty Raliya da Aisha harma da Shukrah, wani irin tsallen dadi tayi domin Wannan ne karon su na farko a gidan nata, ta karbi d’an karamin goyon Aisha tace “Aunty my kalefa ya Kara wayau. Kallon ta sukeyi kawai domin sunga Alamar rama atareda ita ga kuma damuwa, basuce komai ba saida suka natsu shukrah ta tayata kwalliya ta murza dauri,  sukace muje ki rakamu mugaida uwar mijin ki. “Toh tace suka fita, tana can kuryar dakinta da kawaye sai shewa sukeyi ita tafara Sallama  wasu suka Amsa wasu suka zuba mata ido,  suga Ina wannan kyakkywar ta fito, “mommy ga yayyina sunzo su gaisheki. “Toh sannun ku da zuwa, tafada tana gyatsina, kije dasu can dakin ki kisa Abasu komai domin akwai wadatar shi anan kuje. Tafada batareda tajira ko gaisawa suyi ba. Aisha dayake tanada fushi, har ta juya, Raliya ce ta tsaya tace “Allah yasa ayi a sa’a yakuma kade fitina, wasu sukace Amin. Ta juya Naziya tabi bayan ta,

 

Suna shiga dakin Aisha tafara sababi “wallahi Aunty Raliya wannan Matar batada mutunci yanzu dama Abunda ake fada gaskiya ne, gaskiya ni da malam zaiji magana ya raba Auren nan kawai. “Kinsan me zakiyi?  Dakin bar nan saikije ki same shi kuyi magana kinji Aisha. Raliya tafada cikin haushi, wane irin Abu ne zaki  tadawa yarinya hankali da mugayen kalaman ki, to sai me akanta farau da irin wannan uwar mijin?  Don Allah kirika tausasa zuciyar ki. “Kiyi hakuri Aunty Abun ne yabata mun zuciya kalli yanda yarinya ta koma saboda fitinar wannan Matar, yanzu yarinya ko wata biyu kwarara batayi ba za azabgo mata kishiya wallahi ba adalci.  “Ya isa bashi yakawo muba munzo ne mu debe mata kewa  don haka don Allah ki daina mitar haka. Shigo musu da Abubuwan ciye ciye tayi ta baje musu tareda daukar kaleefa tana mai wasa,

Domin su dauke mata damuwa suka saki jikin su sosai tareda yimata hira tareda shawar wari, ta saki jiki a ranar, lokacin da aka fara taron ma tare suka shirya suka fito wanda tun shigowar ta gidan wannan ne karon farko data tako kofar gidan a yanzu ne take sanin Aljannar duniyar da take ciki,  Suna fitowa khaleel na shigowa  rikeda key cikin manyan kayan da ta lura yanzu yana kokarin sakawa, kallon ta yayi ya dauke kai tareda matsowa ya gaida su Aunty cikin girma yace kuzo muje inkai ku. Taso tace bazata shiga motar tashi ba Amma ba hali domin sun Ansa har suna godiya, Aunty Raliya tace munko gode domin bamu san wurin ba, shukrah ce agaba ita dasu Aunty a baya fuskar ta turbune domin Allah dai yagani tamafi kaunar mommy akan khaleel, a harabar wurin ya Ajiyesu dai dai ana kawo Amaryar tashi fauzy wadda tasha ado kamar zataje gasa cikin tsaddun bridal dress, Washe baki tayi tayi saurin nufoshi “baby “kazo. “No banzo ba mutane nakawo am going back, yafada yana shigewa cikin motar ya datse, su Aunty sukayi mai godiya  yace bakomai batareda ya ko kalli gefen Naziya ba, gaba daya kawayen ta sukayo mata cah, “angon kenan Fauxy gaskiya gayen nan yaje, Amma akwai wulakanci. “Ba ruwanku I love him like that. Tafada tana juyi tareda cewa suje, suka take mata baya tana yiwa su Naziya kallon banza,

An barar da kudi a wannan taron na gagaruman mata da hamshakai, to suma dai ba laifi domin sunyi kwalliyar su cikin mutunci ba wadda tasaka gyale dukan su hijabine, Wanda ya janyo suke musu kallon rashin wayewa da tsantsar kauyanci,  su momy an barar da rawa da kudi itada sauran iyayen Amaren, su Naziya na gefe itada y’an uwan ta har akaci aka sude, fitar tata tasata cikin farin ciki at least  tafito a cikin wannan gidan dayake kamar kurkuku a wurin ta.

aka yi komai suka yi gidajen su, tayi farin cikin kasancewa tare dasu domin sun Cire mata kadaici da damuwa,  Wanda sukayi mata Alkawarin dawowa Washe gari yinin bikin, throughout ranar har dare batasa Ahmed a idoba, an zubawa Amaren kayan su a sababbin ginin nasu dake gidan, kowacce an narka mata dukiya fiyeda tunani, dama haka Hajiya bilkisu takeso.

Kayan Naziya da ko a ido bata taba ganin suba tuni antattare an zuba su a store an zuba na Amarya…….. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

And now AUREN GADO,

 

Ga masu son su biya ga account details dina, *NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB* sai Ku min magana ta wannan number 09069200154

 

 

 

 

 

🆓 page

 

 

 

1⃣5⃣&1⃣6⃣

 

 

 

……………… Ta kwana da matukar tunani a wannan daren, Rayuwar ta da Ahmed, distance relationship, hatred tsakanin ta da  y’an uwan shi, musamman Khaleel, she don’t really know why, bata kaunar ganin shi, idan akwai Wanda zata nunawa tsana itace mommy wadda ta hanata sakewa a Rayuwar Auren ta, but why him?  So take ta nemo Amsar takasa, juyi takeyi cikeda mutuwar jiki, idan tace bata cikin damuwa tayi karya, Ace Auren ta wata cikin na biyu ba kwanciyar hankali,  batasan dadin miji ba batasan dadin zaman Aure ba infact ba Abinda ta karu dashi sai girki da gyaran gidan, Wanda anayi ne domin a kuntata mata, basusan ta horu da aiyuka agidan ubanta ba, ba aikin da zai gagare ta, tsoranta daya a rayuwa kar  a rabata da mijin ta, domin duk Abinda ke faruwa soyayyar shi bata ragu a zuciyar ta ba, sai ma karuwa da tayi duk wani moment ita da Ahmed idan ta kadaici cikin farin ciki take kasan cewa, idan tana tuno su, tasani duk ranarda ta samu freedom da mijin ta zaman su zai yi d’ad’in gaske.  Bata cire tunanin wata rana zatayi farin ciki ba, Wanda tana fatan tayi nasara insha Allahu. Tashi tayi tareda yin sallah ta roki Allah akan ya cire idanun ta akan duk Abinda zai faru da kuma Wanda ya faru a baya, tareda neman juriya da nasara a rayuwar ta ta yanzu da kuma nan gaba.

 

Washe gari aka tashi da shagalin biki, Wanda tun da safe jikin ta yagaza dauka daka kalleta kasan tana cikin tsananin damuwa da kadaici, Ahmed ya boyewa ganin ta baki daya, Wanda batada masaniyar baida lafiya ne, Saida khaleel ya kawo mai likita batareda sanin kowa ba.

Yana tareda d’an uwan shi har safe bai runtsa ba Abu biyu ke damun shi a zuciya, why yayan shi keda mugun hakuri?  And wani gefe kuwa kanshi yake tuhuma, why why why?  Domin shi karan kanshi da baida karfin zuciya cikin wata biyun nan da ya ga likitan zuciya, he is in big trouble, big mess Wanda yasani shi karan kanshi, he is a fighter domin duk Wanda ke yaki da zuciyar shi shine babban jarumi, Wanda kowa yasan yaki da zuciya Abune mai matukar wahala.

Dafashi da akayi yasa ya dawo cikin hayyacin shi tareda kallon yayan nashi, daya tashi zaune yana murmurshi kadan, kana ganin shi kasan cikin jinya yake. “All night bakayi bacci ba khaleel, why kuma kasan yau ranar Auren kane dole ka raya wannan daren. “Yaya ya jikin naka?  “Alhamdulillah inajin sauki a jikina, ya Naziya kagan ta? how is she? ” Yaya all you worried about is her? Why bayan ita bata damu da neman kaba if tasan Abinda ya dace me zai hana ta nemeka? “Kafada mata banda lafiya? “Nop Yaya. “Kaga batada masaniya, and please Khaleel take care of her, that girl deserve to be happy. “How Yaya bayan kaine zaka kula da ita she needs you more than me, kaine mijin ta. “I know khaleel. Ya Rungumo shi a jikin shi, yace “you have alot of responsibility, mommy, Fauziya and our company, I know you are stronger than me. “Yaya please stop All this you know  you’re breaking my heart, Yaya I have something in mind, Wanda bai kamaci in sakashi a zuciya ta ba I hate myself please forgive me. “What is that khaleel, me kakeso I promise to give it to you koda rayuwa tace saboda kaine farin ciki na. Wasu irin hawaye masu zafi suka gangaro a kwayar idanun shi for the first time, yaji he need them, saboda sometimes tears heal some wounds.

“Noo Yaya bana son destiny din da zai zamo musayar rayuwar ka, I don’t want that destiny, but Yaya is really painful, bansan yanda zanfada maka ba and please don’t ask me too much question bazan iya amsaka ba. “Is OK bazan tanbaye ka komai ba, but dole inji dalilin zubar hawayen jarumin kani na, what is that, meye ya taba zuciyar the stone heart Ibrahim khaleel? “Yaya. “No am not asking the new ango but am sure kana kukan farin ciki ne yau zakayi Aure and you will last on bed more than me. Yafada yana daga gira daya, ya tuno da irin question din da yamai ranar da sukayi hira a dakin shi da Naziya. Dafe kanshi kawai yayi tareda sakin yayan nashi, “Hmmm yaja dogon Ajiyar zuciya, “I know kani na sai yafi thirty minutes. Mikewa yayi cikin sauri, am coming Yaya bari inje cikin gida. Yafita fuuu dagashi sai guntun wando yau ko singlet babu a jikin shi yama manta da taron matan dake gidan, burin shi ya ganshi a cikin gidan.

Dayake kowa na sha’anin gaban shi sannan kuma an Waye ba wani Abu bane don haka no one care, har ya shiga main palo, dai dai taci kukan ta tayi nak har wani zazzabi takeji ta fito jikinta kamar ba ruwa ba Wanda ya damu da ciwon zuciyar ta. Taga shigiwar khaleel fuuu ya wuce dakin shi, bayan shi ta hanga yana shigewa Wanda dole ta bishi taji inda zataga Ahmed domin ta gaza zuciyar ta tayi rauni,  ta leka dakin khaleel din yafi sau goma tun jiya dukan su basa ciki, infact ko gyaran datayi bai baci ba.

Shiga yayi ya kalli gadon cike da wani irin zafi zuciyar shi keyi Wanda bai taba jin irin shi ba, ya fisge zanin gadon ya jefar tareda zubewa kasa yasaki wani irin kuka mai karfi kadan Wanda ba Wanda zai jishi,

 

Tayi matukar tsorata da kuma jin mamakin kukan namiji, tun dosowar ta kofar dakin kuma tanada yakinin a cikin dakin khaleel yake fitowa, wake kuka haka?  Bude kofar tayi cikin Sauri, ya dago fuskarshi karab cikin idanun ta, tayi matukar girgiza, bata taba kawo zata ganshi yana kuka ba, meye yasa shi kuka haka ?  The great mai girman kai, this is serious, kokarin juyawa tayi kawai domin a tunanin  ta koma meye ba hurumin ta bane. “Wait. Yafada cikin sanyi tareda mikewa yana share hawayen shi, tsayawa tayi cak har ya iso wurin, hijabin dake jikin ta tarike gefen shi gam tana jiran taji me zaice, saida ya matsa ya tura kofar ya datse, ta zaro idanun ta, “meye na rufeni a dakin ka, bana son rainin wayau ka bude min kofa intafi. Tafada bakin ta na rawa  kamar zatayi kuka, “Hmmm, me kike nema? “Mijina. Tafada kai tsaye batareda ta kalli y’an da ma yake ba, “bakida lafiya ne?  Saurin dago kanta tayi ta kalle shi akaron farko  tun shigowar ta, da gudu ta datse makullin idanun ta, “Auzubillahi. Tayi saurin ja baya, Wanda Abun yayi mugun batamai rai fiyeda tunani,

Bata taba ganin bear chest din namiji ra’ayil aini ba sai yau ga kirjin nashi da shegen fadi da wata irin suma mai tada tsigar jikin mace,

Fisgo hijabin ta  da yayi cikin zafin rai yasa tafara istigifari tareda bude idanun ta tana mai kallon that’s why I hate you, “you are behaving like baki taba ganin namiji ba kaya ba, kina Abu kamar wata saliha, look karki daukeni jahili ko mara sanin iyakar shi,  I know my limit shiyasa kike tsaye agaba na batareda wani Abu yafaru dake ba, ni kikeyiwa a’u’ziya? kamar Kinga shedan. Cikin tsiwa da zafin zuciya tace “meye banbancin ku da shi, kana ratsa mata tsirara bayan kasan haramcin Abun sannan wuce limit! yes you cross All the limit da ka rikemin hijabi now let me go. Tafada cikin karaji, saurin sakin hijabin yayi tareda sai daita  kanshi yana shafo sumar kanshi tareda d’an naushin iska.

“Am sorry, kiyi hakuri am worried ne because my brother is sick tun jiya. Saurin natsuwa tayi tareda sakin jiki tace “Ina yake?  Jikin ta na rawa, yana part d’in mu na waj… Ko gama sauraran shi batayi ba ta bude kofar ta fice da sauri,

She knows it shiyasa itama batada lafiya, saboda Ahmed d’in ta is sick,

Tana fita ya datse kofar tareda zubewa kasa ya hade kai da guiwa, “khaleel you are so dead. Ya furta yana sakin Kara.

Da taimakon mai aiki tasan inda Ahmed din yake Wanda shine karon farko data shiga wannan part din Wanda ya kamata ta kasance a ciki, tundaga falon take zuba ido domin tasan dukiyar dake ciki bata malam bace, infact ko kudin labulen dake cikin falon zai siya kaf kayan dakin ta, wani irin karyewa zuciyar ta tayi takasa daga kafarta daga nan ta zube, shikenan tata takare za ashiga tsakanin ta da mijin ta domin  tasan  burin mommy ya cika ta Auro mai burin ranta,

 

Jin kukan ne yasa yafito daga bedroom ya ganta a wurin da gudu ya karaso gaban ta, “Naziya Naziya, ya zube tareda rikota zuwa jikinshi, “Am sorry please, Allah yagani kukan ki yafi komai daga min hankali please kiyi hakuri komai nada dalili believe me, dago kanta tayi ta ce”harda guduna kadawo dakin Amaryar ka tun bata tareba, Ahmed meye ribar zama na a karkashin inuwar Aurenka? “Soyayya ta Naziya, soyayyar kice Ribar Auren mu, Wanda nayi miki Alkawari muddin baki tare cikin gidan nan ba bazan taba samun farin cikina ba kece walwala ta kece farin cikina, am sick Naziya saboda damuwa datayi min yawa zuciya ta na ciwo. , Hawayen ta tayi saurin sharewa, “Ahmed Ina son zama dakai, ka koyamin sonka duk da bamu zauna tare ba, halin ka hakurin ka tarbiyar ka, Ina son halayen ka, kaddarar rayuwar mu, nadauka am not blaming you for that shine kaddarar mu, please karkayi ciwo zan shiga damuwa kaji, tafada tana shigewa cikin jikin shi da kanta kuma a karon farko, taji ta iya sakin jiki dashi batareda kunya ko nuku nuku ba, Ajiyar zuciya ya sauke ya gyara zaman shi dakyau tareda rungume ta gam a jikin shi shima, “Wow Naziya sarkin kunya yau ta rungume ni haka?  What a lucky day, kice intashi ingirgice kawai mu shige daga cikin dakin mu yau. Sunne kanta tayi cikin kirjin shi tana jin kunya, tareda kokarin tashi ta gudu, “no karya ne yarinya kinkawo kanki don haka let go inside ki bani Abinci inci domin rabona da Abinci tun shekaran jiya, “why?  Tafada cikin damuwa, “because am worried about you kullum Ina tunanin Ina shiga hakkin ki idan namutu ubangiji zai tanbayeni hakkin ki Naziya, kiyafemin kinji. “No bakayi min komai ba, muje in hada maka Abincin kaci, akwai komai a ciki ne? “Yes let go, yafada yana Rungumo kugunta. Ya dade a tsaye yakasa shigowa falon yana ganin yanda take shigewa jikin Ahmed, komawa yayi kan kujera ya zauna tareda runtse idanun shi gam only God knows what is going on in his mind,

 

 

Dagewa tayi ta shirya mai girki lafiyayya domin takara zama expert yanzu saboda shine kawai aikin ta a gidan, yana biyeda ita har cikin kitchen din, yana shige Mata harta gama yace  suje falon domin yaji muryar khaleel na waya,  kuma shima tunjiya baici komai ba saboda yaga yayan shi baici ba, tayi mugun jin haushin shi domin ya katse musu lokacin mai dadi ta hanyar zuwa musu gida,

Fitoda komai yana tayata, yana zaune a wurin batareda ya motsa ba, idanun shi a rufe har suka jera Abincin, tana gefen Ahmed yasa hannu ya cire hijabin jikinta batareda ta shirya ba, doguwar riga ce a jikinta mai kyau ta kanti,  wadda ta d’an kamata shiyasa take yawo da hijabin, saurin kallon shi tayi tareda narke fuskar ta “kana so ingudu ne?  “No wife inaso inyi kallon matata ne, Kinga yanda kikayi kyau, and,,ya matsa daidai kunnen ta ya rada mata “this your chest baby please agama abani hakkina I need them very badly.

Hannu tasa ta datse fuskar ta tana girgiza kai, “Allah zantafi fa. Cikeda wata irin murya mai daukeda tsantsar shagwaba mai burge y’an maza, Wanda saida khaleel ya daure ya kalleta, a yau yake ganin dariyar ta da kyau hade da farin cikin ta, he feels a little happy one side, ga dimple d’in ta wow,. “Yaya Am hungry yafada domin katse moment din, “let eat brother, ta zuba musu tareda cewa “wannan Abincin ai wasu basu san dadin irin shiba, oh zaka iya cin Abincin mu na Nigeria ba kyankyasai ba. “For the first time a lokacin yaji wata irin dariya tazomai, shima  Ahmed Saida ya dara, “ke Waye yafada miki sunan su kyankyaso? ” oho nidai ai mutum ba Abinci yakeci ba sai tarkace, daga kunama sai k’wari.

“Hmm, kawai yace yafaracin Abincin shi batareda yace tak ba yaci sosai saida ya kusa cinyewa  tace “little brother inkara maka ne? Dago kanshi yayi ya kalleta wani iri kafin yace “am OK Aunty babba tanks. Ya mike, “Wow Wato kasan Aunty karama na zuwa ko? Harara ta watsawa Ahmed d’in tareda daukar hijabin ta ta Mayar, zata wuce. “Wait my Hajiya ai muje a yimin wanka ki karasa ladanki tukuna.

Kokarin tafiya takeso tayi, khaleel yace “Yaya please let her go kafin mommy ta ankare. “Muje intayaka tafada kai tsaye,  domin batasan meye matsalar shi na yimusu karan tsaye ba yanaso ya hanata sakewa a lokacin da ta samu damar ta,

 

“Toh munafuka Y’ar gidan masu kwana kan buzu, zoki fita shashasha, ko kunya an narkawa yarinya dukiya kinzo kin shige, zo ki wuce, kai kuma Ahmed idan ka wuce iyakata banyafe ba, kaima khaleel dakai ake haduwa anamin bita da kulli,  kuzo ku shirya ku tafi daurin Aure, in mace ce matsalar ka Ahmed na zabo maka ta kece raini ba wannan Y’ar shilar ba, koma daka nayi baki.  Da gudu ta fita while khaleel ya wuce Abinshi batareda ya tanka ba Ahmed ma haka ta karaci sababi tareda turo masu aiki su Kara gyara duk Abinda aka bata a turare shi.

Saida ta shaki kukanta ta tashi tayi wanka ta caba Ado wayar ta ta dakko taga sakonnin shi da basa taba rabuwa da wayar ta, “Am sorry matata idan muka dawo zankira ki mu fita shakatawa kinji. Dariya tayi kamar dagske yanzu mommy nace wa Ahmed zai sunne kai, “my gentle man. Tafada cikin nishadi, so hana ganin laifi,

 

 

Biki yayi biki ko Ina ba masaka tsinke a cikin babban birnin na kano a yau Auren yaran manyan mutane guda hudu at once, ga kuma Y’ar masu kasa Wato fauziya,

Daurin Aure ne Wanda ya jirkita garin ba kadan ba manyan baki ta ko Ina, kawu wakilin Angwaye Wanda baisan da zancen Auren Salifa ba sai ranar Auren, ya fara fada kamar zai Ari baki, har cikin gidan yazo ya kirata “Hajiya bilkisu halina na nan, yanzu saboda Allah yaro Aure wata biyu kisa ya karo Aure?  Hajiya bilkisu kiji tsoron Allah. “Toh  nidai bani nasa yaron nan Karin Aure ba ka kirashi ka tanbayeshi. “Koda bani na haifeshi ba jini nane nasan halin Ahmed nasan tirsasashi kikayi kuma Ina gargadinki da kibi a hankali. Shigowa Khaleel yayi ya zauna tareda gaida kawun yace “don Allah kasa baki ta bar yarinyar ta tare a part d’in ta kafin wata tazo kuma kawu ai itace uwar gida yakamata ace ita tafara shiga wancan gidan. “Yanzu kokarin kai karata kakeyi Ibrahim, Wato ya turoka kazo kasa kawunku ya yanke ni toh ka koma ka fadamai wallahi sai Salifa ta shiga Wannan gidan kafin Wannan Y’ar gidan malaman ehem. Tayi fuuu ta shige, ya so ya cire son zuciya ya agaji yayan shi amma mommy, Hmmm. “Khaleel ku shirya mu wuce ka Kira d’an uwan ka, mu ake jira,. Yafada domin lokaci natafiya kuma suntara manyan Kasa harda mai kano baki daya, kuma zai dawo mata idan komai ya natsa.

 

Andaura Auren fauziya da Khaleel sai kuma Salifa da Ahmed, Wanda akan sadaki mai matukar tsada akan miliyoyin kudi, domin gadarar mommy, Wanda Ana gama daurin Aure angwayen suka dawo dakunan su kowa kajishi shiru, ba wani motsi, lokacin da aka Kira mommy andaura ta rangada guda tareda kawayen ta, kannin mijinta ne suka iso suna Allah Sanya Alkhairi badon sun soba,  babbar tace Ina uwar gidan Ahmed d’in?  Tana nan zuwa anjima za akawo ta. Mommy tafada da gadara, “Hmmm Allah ya shiryeki bilkisu Wato harda yayan mu bai duniya baki canja bakin hali ba ko?, to wallahi sai Kinga sakamako idan kika cutarda Y’ar mutane. “Toh ku dama wayake taku dama ai duk kannin miji y’an bakin ciki ne don haka ni yau banda lokacin ku nayiwa ya’ya na AUREN GATA.

Taci gaba da guda, dakin Ahmed suka nema inda suka sameta zaune yan uwan ta sunzo tana ta walwalar ta ta fauwala wa Allah, Wanda ta mugun burgesu zama sukayi a dakin suka sake sosai sukasha hira anan suke fada mata su gwaggwnin mijinta ne, ta saki jiki ta kula dasu itama dasu Aunty Raliya sai hira sukeyi.

Damuwar ta kadan ce zuciyar ta na wurin Ahmed batasan halin da yake cikiba Wanda saida yakira likita ya dubashi yace “gaskiya Ahmed idan zuwa gobe bakaji sauki ba kazo Asibiti ayima xray saboda ciwo a kirji yanada matukar Matsala.

Godiya yayi yasha maganin shi ya kwanta yayi bacci sosai har magrib.

 

 

Taro ya ragu zuwa Karfe bakwai duk taron Naziya sun watse sai ita kadai, yau ta yabawa d’an gin Ahmed harda y’an gidan kawu gefenta suka tare sun share mommy da gayyar ta, yanzu bakajin komai sai kai da kawon su Aunty zarah iyayen ango,

Takwas aka kawo Amare Wanda kafin Wannan lokacin ba Wanda yasan inda angwayen suke.

Main house aka shigo dasu cikeda guda Wanda tanaji,  a take wani kuka yazo mata, shikenan rayuwar da tafara mafarki watace zatayi da mijin ta, shikenan sun samu third party tunkafin su mori Auren su.

Saida suka gama feshe feshe kafin kai Amaren gefen su wainda kowacce cike take da tata salon rashin kunyar hade da rawar kai………. 🖊

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

Y’AY’AN GATA

And now AUREN GADO,

 

 

Ga masu son su biya ga account details dina, * NAFISA HASSAN SANI 7304736012 @ FCMB* sai Ku min magana ta wannan number 09069200154

 

 

 

 

 

 

🆓 page

 

1⃣7⃣&1⃣8⃣

 

 

……….. Sai Karfe goma sha daya suka shigo main house, mommy na zaune sai faman jiran su takeyi,ta gwada numbobin su ba Wanda yake shiga, tanata sababi Su zarah na tausar ta, da sallamar shi ya shigo cikin falon while khaleel na biyeda shi cikin shigar shadda bugaggiya Y’ar gaske fara dal, “ko kin ga y’an rainin hankalin ko sai yanzu zasu shigo gida kusan Karfe goma sha daya. “Ahmed ne ya matso gefen ta tareda zama yana gaida Aunties dinsu, tareda cewa sorry mommy muna tareda Abokai ne. “Which abokai?  Kai inkanada Abokai shi Wannan miskilin nadasu ne?  Kun bar ya’yan mutane sukadai suna jiranku kamar masu gadi.

Carab ya bude baki a karon farko yace “jiran me sukeyi mana?  Bayan ba ayi budar kai ba, sai su jira nan da sati daya idan an yi budar kai sai muje wurin su ni bacci nakeji, Yaya good night. Yafada batareda ya jira Amsar suba ya wuce Abinshi, ido kawai Ahmed yabishi da shi, bakin mommy a sake tace “Allah ya hadani da yaron banza, kai kuma bazaka tashi ka wuce dakin Amaryar taka ba? “Mommy gaskiya ne ita baza ayi mata budar kan ba? ” ubanka kaji tashi ka wuce ko ranka ya baci yanzun nan,  shima zanje in same shi. Mikewa yayi domin baijin dadi sosai dauriya yakeyi kuma Allah yagani bayason kowa yasan halin da yake ciki  yanzu.

Yana kallon kofar dakin shi kamar yashiga yakeji yasan halin da take ciki, Amma ba hali mommy ta kasa ta tsare. “Za abiyoka da kazar Amarci nasa anyi muku gashi mai kyau. Ko amsawa baiyi ba ya fita, a zaune Amaryar tashi take tayi dai dai cikin wasu irin fitinannun nighties duk jikinta a bayyane gata ba wani shahararren kyau ba, sai faman tauna chewing gum takeyi tana kas kas kamar wata tsohuwar karuwa.

 

Tundaga falon ya hango ta kafa daya kan daya tana jijjiga, zai iya cewa yaune karo na biyu ganin shi da ita Wanda baima san ta Ina zai fara yimata magana ba, domin ko ganin farko bai wani mata kallon arziki ba,  don haka ko yanzu yana shigowa ya dauke kanshi ya wuce ta gaban ta. “Kai, tace cikin zafi. “Kashi ka wuce? ace ankawoni tun Karfe takwas kowa ya watse ya barni baka shigo ba sai yanzu? kuma ka ganni kamar wata Kashi ka gani. “Oh sorry ya fada batareda ya kalle taba domin bai sha’awar hakan, murmurshi tayi tareda matsowa tana karkada jikin ta da shirin rungume shi, yayi saurin ja baya tareda cewa “please bacci nakeji sosai kuma kaina naciwo, am very tired please let me go. Ya wuce da sauri yabarta tana cizon yatsa, batasan da yanajin lafiya yau sai ya nemo Matar sonshi yaci Amarci kota halin Yaya, Amma bayajin dadi shikadai yasan me yakeji a jikin shi. Yana shiga dakin shi ya datse gam batareda ya  jira wani Abu ba, idanun ta sun nuna mai zata iya mai fyade inyayi wasa ta karasa shi, saida ya kwabe ya zube kan gado domin yayi sallolin shi a waje,  ya janyo wayar shi yafara neman ta, tana kan dadduma tana lazumi taji Karar wayar, tasan shine don haka cikin Sauri ta mike ta dauka, Ajiyar zuciya yasauke yace “Y’ar Aljannah.” Ina wuni, ta gaidashi cikeda tausayin kansu domin yama fita zama Abin tausayi, “ba lfy my wife, ko in zo ne? ” aa. “Why?” mommy na falo suna hira. Hmm! zaki tayani hira har safe? eh, Amma hakkin Amarya fa? “Don’t say that again sai kisa inji guiltiness akan ki” naki hakkin fa? ” ni na yafe. “Nikuma fa?  Ni Ina bukatar hakkina Naziya, kinsan cewa ba Abu bane mai sauki namiji yayi ido biyu da Mace kamar ke ya kawar da ido ba, mommy ce ta tsaya min akan layi da tuni munfara lissafin wata biyu cikina. Rufe idanun ta tayi gam saboda kunya kamar yana ganin, “shy girl, nasan kin rufe ido.

Hira sukasha sosai yana yi yana bata hakuri tareda alkawura masu yawa.

 

Gefen Amarya ta cika ta batse momyn ta ta Kira tana kuka tafada mata angon yaki ko shigowa dakin ta, a daren Karfe biyu ta Kira mommy tana sababi, “nifa ba dutse nakai muku ba yarinya ce shakaf mai jini a jika don haka kari nji kar ingani, zancen wulakan ta min ya’. Tayi ta bata hakuri kafin ta gwada kiranshi yana busy, ta hakura ta barwa safiya,  banzar kuwa kazarta ta yaga  iya son ranta ta sha baccin ta nak, domin tasan dai dole yagama gudun shi yadawo mata domin a shirye take tsab.

Fauzy ma tasan halin kayan ta batasa akaba tasani tunda dai ta shigo, a juri zuwa rafi wata rana tulu zai fashe, Amma zama daram itada Khaleel tunda buri ya cika.

 

Gefen shi ma baccin shi yasha har safe batareda tunanin wata kaya fauzy ba,sai Asuba ya fito da shirin zuwa masallaci, ya samu mommy zaune itada bata tashi da wuri, tace  Yauwa ku nake jira kuyi sallah kuzo kaida d’an uwan ka Ina jiran ku yanzu, fita yayi  kawai Abun shi yasan tatsuniyar gizo bata wuce ta k’oki.

A masallaci suka hadu, saida suka idar yace “her excellency is calling. “Who?  “Your mom. “Oh ba MAMAN ka bace kai?  Shiru yayi kawai, domin shikam baisan me zaiyi mommy ta canja ba, ciki suka shiga yana mai nasihohi masu ratsa jiki da taba zuciya, suna saka kafa tafara sababi “nikam yau zanyi maganin ku duka sai kunfada min inkunada wata uwar bayan ni, Ina muku gata yara kuna watsa min kasa a ido, toh yau dukan ku Ina bukatar ku dakin matayen ku banason jin rashin kunyar ka Ibrahim. Sannan kai tunjiya Ina kiranka kaida ubanwa kake waya? Da ka kwashe tsawon dare kana busy? “Mommy kiyi hakuri, nida Naziya ne. “Innalillahi, Wato tanan ka bullo Ahmed kuna hadewa ta waya, ita kuma munafuka kamar salaha, mayya ta lashe min kurwar yaro to wallahi zanyi maganin Abun, karyar buzu tsohon ta yakeyi, mu munsha tabara mun sha yaseen , ta rangada mata Kira, Wanda duk tanajin komai.

Da sauri ta fito da hijabin sallar ta tace “gani momy. “Ni ba uwar ki bace ta cikin bukka munafuka, ke kin kaini bango hakurina ya kare akan ki inba zuciyar kare kikeda ba kizo ki koma gidan ubanki, ace mace don rashin zuciya miji bai neman ki baidamu dakeba saboda kin rab’i Ac kin like kin manne kamar kaska, ke wa ya iya da bakin nacin talaka? zo don Allah kibarmin gida Ahmed dai yayi Aure aje aci gaba da cin tuwon dawa da gero.

Tafada tana nuna mata hanya.

Kuka takeyi tunda momy tafara magana Wanda Wanda duk sauran bakinta sun taso, fauzy ma data bugo sammako ciki taji komai, tana dariyar mugunta tareda komawa ta Kira Salifa tazo kar ayi bata, domin tasan da zaman Naziya kuma tasan komai akai don haka tasan zatayi farin ciki yau idan taga Abinda mommy tayi,

 

Dafe kirjin shi yayi yana mai wani irin zafi tuni numfashin shi yafara seizing batareda kowa ya luraba, domin kan Khaleel na kasa idanun shi kamar wuta saboda bakin cikin halin mommy, da kuma irin cin zarafin da takeyiwa Naziya.

Zubewar da yayi Tim yasa khaleel ya zabura yayi kanshi, Wanda yabawa sauran damar ganin Abunda ke faruwa, har mommy tuni tayi dif kamar ruwa ya cinyeta,

“Yaya” khaleel yafada cikin tashin hankali, ya tarai rayoshi, saidai tuni jini yafara bin hanci da bakin shi, wani irin zubewa Naziya tayi jikin ta na rawa kukan da take ya tsaya ba Abinda take kallo sai jinin dake fita a fuskar Ahmed, cikin tsananin jarumta da mazantaka khaleel ya cirashi da gudu yayi waje yana mai kwalawa driver Kira yakawo mai key,  yasaka shi cikin motar tareda rungume shi cikin tashin hankali driver yaja suka fita a guje domin gari yayi haske,

Mommy daskarewa tayi tana jin numfashin ta kamar zaifita saboda tashin hankali, Ba Abinda takeso duniya sama da ya’yan ta da kuma dukiyar ta, batasaon rasa kodaya a cikin biyun nan, don haka ganin yanayin Ahmed yasa tajita kamar ana zarar ranta. Saida zarah ta jijjigata ta dawo dai dai, “zarah muje wurin dana ingan shi, kar yarona ya mutu muje inga halin da yake ciki.

Ita ta dakko mata key da hijabi suka fito, su fauzy na tsaye turus basuda niyyar motsi, sanin halin khaleel yasa suka Kira driver yafada musu inda suke, Naziya kuwa kuka takeyi kamar zata mutu, idan ta kalli jinin dake kwance inda aka dagashi, hijabin jikinta ta zare cikin rudu ta goge kasan tiles din tsab tana kuka, Aunty Raliya ta Kira tana kuka tafara fada mata, ta lallashe ta tareda cewa “kiyimai Addu’a Allah yabashi lafiya ba kuka ba, banason shirme. Toh Aunty. Ta datse kiran tana mai dauro Alwala ta koma kan dadduma hannayen ta a Asama domin neman sauki wurin mai duka.

 

 

Gefen mommy koda suka isa Asibiti daidai da zuwan kawu modu domin Khaleel ya kirashi, hawaye yake sharewa tareda sintiri, kawun na zuwa yace ” Meya same shi khaleel? ” d’an uwana Kawu yana Aman jini hanci da baki suna ciki har yanzu basuce komai ba, ya mugun fita hayyacin shi, matsowa Mommy tayi jikinta na rawa “Ibrahim me yasamu d’ana?. Dago idanun shi yayi ya kalle ta cikin kallon kece sanadi mommy. “Look at it mommy kinga irin ta ko, d’an uwana na cikin Wannan halin because of you, mommy don dai ke uwata ce Amma in wani ne bazan taba yafe mai ba, now just pray d’an uwana ya tashi lafiya I promise dole abashi farin cikin shi that’s enough! hakurin shi yayi yawa. “Ibrahim ‘ kawu ya daka mai tsawa, “me yasa kake fadawa mahaifiyar ka magana haka, me yafaru?  Matsawa yayi cikin karyewar zuciya, ya fada jikin kawun ya saki kuka mai zafi Wanda ba Wanda zaice jarumin namijin ne ke irin Wannan kukan.

Bubbuga bayan shi kawu yayi ” ya isa insha Allahu zai tashi lafiya, Kayi shiru haka. Fitowar likita ne yasa ya yi saurin share hawayen yace “lafiya doctor yaya na fa? “Please kaine Khaleel?.  “Yes”. Come your brother is calling you.

Bin likita yayi da Sauri kawu ya bishi shima, mommy zata shiga likita yace su tsaya waje mutane zasuyi yawa a emergency.

Jinin ya tsaya kadan sai Wanda ke bin hancin shi kadan kadan, yana isa yaja gefen rigar shi ya goge mai, “yaya please ka cire damuwa zaka tare da Matar ka I promise you kaji. Wani irin numfashi yaja mai wuya tareda fitarda murmurshin dole.

Yace “kawu”, tareda mika hannu yace ga Amanar d’an uwana, kawu don Allah ka kula dashi ka tsaya mai akan komai, inason yayi farin ciki, kawu don Allah make him happy kar ya shiga damuwa idan bana nan, Khaleel take care of Naziya, where is she?  Please call her, ka kawo min ita Ina so in roketa gafara please go and bring her. Ja da baya yayi tareda girgiza kai, ” no no no stop that yaya nothing is going to happen to you, bari inkawo ta please yaya kadaina magana haka ciwo ai ba shine mutuwa ba, I don’t like this, stop it. Am sorry Khaleel. Yafada yana mai kallo mai cikeda sakonni, fita yayi da sauri yana yi kamar zai tashi sama, riko hannun kawu ya kuma yi, “kawu don Allah kar Kabari Naziya ta fita agidana ko bani, kawu kabawa Khaleel ita ya Aura nasan zai bata kulawa saboda soyayyar da yake min please kawu”. Mugun sanyi jikin kawun yayi domin Abun ya tsorata shi, a’a Ahmed kadaina irin Wannan maganar, haka d’an uwana yatafi yabarmin Amanar ku, bangama saukewa ba zaka bani wata, Insha Allahu zaka tashi kaji, likita kuyi aikin ku mana,. Yafada cikin tsawa, “Alhaji muna bakin kokarin mu Amma zuciyar shi tariga tagama kunbura shiyasa yake Aman jini, tunfarko yasan yanada ciwon zuciyar yabari tunani yashige shi Wanda yafi karfin zuciyar.

“Karka kawo min hauka nawa zanbiya ayi mai aiki, inba zaku iya ba infita dashi waje. Mommy ce ta shigo tana kuka tareda matsowa kusa da gadon da yake” Ahmed meke damun ka?  Me yafaru dakai?  Don Allah katashi.

Rikota kawai yayi dakyar ma yanzu yake fitarda numfashi, “ki  ya fe min mommy na. Ya fada daya bayan daya yana riko hannun ta gam Wanda tanajin rikon cikin jijiyoyin ta rikone mai matukar karfi irin na fitar rai, koda takalle shi kafin tace wani Abu sai dai ganin jinin tayi yana Kara fitowa tareda kafewar idanun shi sama, kafin ya saki Hannun ta. Suman zaune tayi na wucin gadi kafin likita da kawu su gama magana su juyo, zarah ma tashigo, wani irin tsinkewa jinin ta yayi domin ba tantama Ahmed dai rai yayi halin shi,

“Innalillahi wa Inna ilaihirrajiun. Kullu nafsin za’ikatul maut. Kowane rai tabbas ne zai daddani zafin mutuwa don haka sai muyi fatan cikawa da imani, Ahmed dai yatafi yabar Wannan duniya mai cikeda rudani.

“Aunty Ahmed yatafi” Zarah tafada tana dora hannun ta saman kai, kawu wani irin zuface ta karyo mai tuni ya ciro hular kanshi yana fifita, “ya Allah” Kawai ya iya fada saboda sarkewar kalmomin bakin shi, saida zarah ta jijjiga mommy, kafin ta fasa kuka”wayyo Allah na ni balkisu Ahmed tafiya Kayi kabarni, why Ahmed why?

Rufeshi likita yasa Akayi da farin zanin gadon, yace Alhaji sai hakuri Ahmed lokaci yayi. Dakyar kawu ya iya saita natsuwar shi yana goge gumi kamar ya hadiyi kunama, ya ciro wayar shi a Aljihu ya yakira Khaleel, ” kana Ina?  “Yanzu na  shiga gida kawu zan dakko Matar yaya. “Stay there muna zuwa. “Why yaya yac…. “Just do as I said, yafada cikin fada kafin ya katse kiran.

Shi ya hada komai yayi clearing aka basu Ambulance Abunka da kudi cikin minti kadan suka tafi da gawar su,

Mommy kamar ta haukace ji take kamar a mafarki wai Ahmed dinta ne ya mutu. Aunty zarah ido yayi Hulu Hulu.

 

Naziya tun fitar su take kan dadduma, zuciyar ta bugawa takeyi da karfi takasa ko motsawa, su kuwa Amare suna hakimce kowacce taci Ado kamar masu gasar gwal. Sun hakimce a falon,

A harabar kuwa Khaleel ya kasa gaba ya kasa baya saboda tashin hankali, ga umarnin kawu, yana daskare jikin motar yaji kukan Ambulance, wani irin kallo yake wa motocin su mommy, ganin yanda Aunty zarah ta riko mommy sannan kawu shima ya fito kai ba hula, ya maida idanun  shi akan Ambulance yana kallon nurses din suna bude motar, ganin sunfito da mutum rufe da farin kyalle ya zube kasa war was, domin baya bukatar Karin bayani akai. Masu aikin ne suka ruga  wajen shi domin jin faduwar tashi Tim.

Mommy ta tafi luuu itama tana shirin zubewa, shima ya mutu ko zarah?  In ya mutu shima ni tawa ai takare kenan. Tafara sambatu, zarah ta riketa tana jijigata a’a Aunty bai mutuba, kai ku shiga dashi ciki, kawu dai nata gawa yasa aka shige dashi ciki, hakama Khaleel anyi ciki dashi,

Wanda tuni hankalin kowa ya kawo kan abinda yake faruwa banda Naziya, domin Amarya Salifa ita kanta jikin ta yayi mugun sanyi, wane irin Abu ne haka Auren ta jiya miji ya mutu yau,

Kukan da mommy ta fasa yasa Naziya fitowa jiki na tsuma da carbi, ganin mutum kwance akasa ga kawun su zaune agaba ya dafe kai yasa tafito jikin ta a mace tana sand’a kamar barauniya.

Kukan dasu Aunty zarah dasu Salifa keyi yasa ta gano duk Abinda yake faruwa. Dabas ta baje akasa kamar kurma, kafin kace me, tuni ji da ganin ta sun dauke.

 

Koda ta farko, taga dakin ta makil da mutane harda su gwaggon nin ta dasu Aunty Raliya da kuma matan kawu.

Zabura tayi tana kallon jikewar da jikin ta yayi da ruwan da aka rika kelaya mata,

Ganin ta zaburo Aunty Raliya ta riketa, “Naziya bi a hankali ruwa ne a hannun ki. Kallon hannun tayi, tareda kallon mutanen tace mafarki nakeyi ba mutuwa yayi ba ko?  Aunty bai mutuba ko?  Ku fadamin Ina yake?

Dafata kanwar malam tayi tace “ki yawaita Inna lillahi Wa Inna Ilaihir Raji’una Naziya. Tafiya takuma yi luuu. Suka kwantar da ita, kowa na share kwalla,

Khaleel kuwa saida akayi da gaske ya farfado, lokacin angama hada gawar Ahmed, zabura yayi kawai, ko digon hawaye yakasa fitowa a idanun shi.

Kannen shi ne yaran kawu maza suka rikeshi “yaya Khaleel bi a hankali karka fadi. “Let me go. Yafada cikin  fada. Kafin ya fisge ruwan yafice cikin Sauri lokacin za adauki gawar zuwa makwanci, harda malam yazo gidan yau.

Cikin sauri yace “kawu kubari inyi mai Addu’a, fuskar shi ba ko Alamar hawaye domin ance kuka wuri yake samu watarana zuciyar shi ta cushe ta inda bako digon hawaye dake shirin zubowa.

Kowa yasan na zuci yakeyi Wanda ke cin zuciya, don haka malam yace “Ibrahima, ka saki zuciya Kayi kuka bakyau hadiye Abu yana illata mutum cikin sauri.

“Malam muje akai yayana makwancin shi. Yafada yanasa hannu ya daga makarar gefe daya domin yasan idan shine yayan shi zaiyi mai har wankan karshe, Amma tunda bai samu yimai ba shine zai sakashi cikin Kabari tareda samai kasa da binshi da Addu’oi.

 

Yabawa kowa mamaki yanda ya sakawa kanshi jarumta, har zuwa makabarta, inda da hannayen shi yasakashi cikin Kabari, tareda yimai kallon karshe, Wanda anan zuciyar shi ta karye ya fara fitoda hawaye, shikenan yayan shi yatafi, gatan shi Wanda saboda shi yadawo Nija, da ana dawo da hannun ago go baya da ya canja tsarin rayuwar Dan uwan shi , da ya hanashi shiga bakin ciki, Amma me komai mukaddari ne baida Wannan damar komai, yanda Allah yatsara haka zai kasance.

Lallabo shi akayi dakyar zuwa gida malam da sauran y’an uwan su, harma da mutane gari Wanda kowa mutuwar Ahmed din ta girgiza shi, Wanda sai ka mutu ake sanin halayen ka, wasu nacewa dazufa sun gaisa a masallaci, Wanda ita rayuwa haka take yanzu kana nan Anjima baka sai wani kuma, rai bakon duniya, Allah yasa mucika dakyau da imani………. 🖊

 

 

 

 

“Kai jama’a bantaba k’isa ba a littafina irin Wannan don haka nikaina na koka na girgiza Wanda nasan watarana saidai labarina nima zantafi, ya Allah Kayi mana kyakkywan karshe kasa mucika dakyau da imani don darajar ma aiki, S. A. W�

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA,

BARIKI AUREN SOJA,

MUK’ADDARI,

WANAKE AURE,

ZANYI BIYAYYA, Y’AY’AN GATA, And now AUREN GADO,

 

 

 

 

Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y’an 🇳🇪 Niger  ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,

 

*my fans masu maganar Ahmed yabar k’wanshi, ai mommy zataji dadi gwara tayi nadama ta har Abada tasan Allah yabata yaro mai yi mata biyayya har bayan idon ta, kuma shine zai zamar mata tabo har karshen Rayuwar ta don haka muje zuwa dama bahaushe yace in kana mugunta bakayi wa kanka ba to baka cika mugu ba*

 

Last 🆓 page

 

 

1⃣9⃣&2⃣0⃣

 

 

 

 

………….. Naziya kuwa Abin kamar a mafarki haka take ganin shi, koda ta farfado manya suka natsar da ita sunayi mata nasiha, sai Ajiyar zuciya takeyi takasa koda fitarda hawaye, Saida Akace mata har an sallace shi an dangana shi da makwancin shi ne ta fasa kuka, shikenan yanzu bazata kuma ganin shi ba, haka rayuwar su tazama tarihi Auren ta dashi yazama tarihi, Wannan wace irin kaddara ce ta bullo a cikin Rayuwar ta? Istigifari ta farayi domin kar Imanin ta yayi rauni, Amma kowa yasan bakaramin ciwone a zuciyar taba rashin mijin da kukayi Aure wata biyu yatafi yabarka, kowa ya tausaya mata, har kanin Baban su Ahmed din na gidan sunzo, mommy kuka take tana birgima, cikin masifa Aunty Fatima tace “Wallahi bilkisu kukan ki baida Amfani ai saiki tashi kiyi farin ciki, Ahmed yatafi yabar miki duniyar, ba Auren kece raini ba! yau gashi yabar miki matan duka, kiyi Addu’a ma ko jika ace yabar miki jikin Y’ar talakar da bakyaso, kin hana yara sakat ai munsan komai kallon ki mukeyi kawai kijira Abinda zai biyo baya, wallahi sakamako na zuwa. Matar kawu ce uwar gidan tace “Aa Fatima kubarta haka rashin d’a tayi kuma kuzo ana zama kuna tada fitina. “Nayi shiru Matar yaya”.

Kuka Momy ta fasa, yanzu take data sani mara Amfani Ina ma Ina ma, Allah yasa Naziya tanada ciki, Allah yasa zata ga Abinda zai cire mata kewar d’an ta mai hakuri, Kuka takeyi mara Amfani domin batada damar maida hannun agogo baya.

Khaleel kuwa zazzabi mai karfi ya rufeshi Saida likita yazo ya kuma dubashi, su Malam na tausar shi tareda mai nasiha mai ratsa zuciya, kabi d’an uwan ka da Addu’a shine kawai soyayyar da zaka nuna mai yanzu.

Gefen Amare Fauziya tafi d’an  natsuwa domin mutuwar ta taba zuciyar ta don duk shashancin mutum yau ace Wanda kasani yafadi ya mutu, dole kaji jikin ka yayi sanyi idan akwai Imani a tareda kai.

Gefen Amaryar Ahmed mommyn ta da y’an uwan ta nafama akan ta shirya takaba tace atafau bazata yimai takaba ba tunda ko kwana basuyi ba tare, maganar har taje kunnen mommy, bata iya cewa komai ba domin ta shiga rayuwar kurame na wucin gadi,  Naziya kam bazata iya bude baki tace wai mijinta bai kusance taba, domin akwai Alkunya kuma ko saboda soyayyar datake mai tareda hakkin igiyoyin nan uku dake wuyan ta dole tayi mai takaba, in akwai Abinda yafi haka ma zatayi mai domin ita tasan tayi rashi babba Wanda maida irin shi zaiyi wuya, ita ai jitake ma ta rufe shafin Aure a rayuwar ta.

A cikin kwanakin uku zuwa bakwai bamasu sauki bane ga duk makusantan mamacin, tun daga kan mommy, Naziya, Khaleel da duk wasu masoyan Ahmed,

A dakinta take tanayi mai takaba mai tsabta tareda binshi da Addu’oi dare da rana, kuka kuwa kullum dare sai tayishi rayuwar da sukayi dashi batada tsawo Amma yabar mata memories da zasu rika tuno mata dashi har karshen Rayuwar ta.

 

Seven days

 

Khaleel Ko part d’in shi bai zuwa tun ranar da fauzy ta shigo ko kallon ta baiyi ba, Abinci ma baya iya ci ya rame a fuskar shi sosai daka kalle shi,  Aunty zarah ce ta shiga dakin shi yana zaune rikeda waya karatun Alqur’ani mai girma natashi, idanun shi a rufe, sanye yake cikin jallabiya fara,  “Ibrahim” kazo Alhaji na Kira ta fada tareda juyawa, tashi yayi yana sa stop tareda rike gefen jallabiyar shi ya fita, a katon falon ya samesu dukan su har Naziya tana nade cikin hijabin ta, gefe daya Maman Salifa ce da ta Fauziya duk suna hakimce sai kuma Amaren a gefe, Wanda shi tun ranar da aka kawo su bai sasu a idoba, Kawu da malam ne zaune a kujera sai kannin kawun mata biyu gefe, mommy ce tayi shiru kamar ruwa ya cinyeta, kana ganin ta kasan mutuwar ta tabata. Kawun ne yace “Malam Abubakar na taraku ne anan saboda Abubuwa uku na farko dai Ina Kara mika ta’aziya ta gareka Ibrahim domin kai Kayi rashi, Allah ya Kara maka dangana tareda ikon daukar nauyin da aka dora a wuyanka,  na biyu akan maganar Matar Ahmed, sun kirani akan zasu tafi da ita gida domin bazata iya yimai takaba ba, don haka ga Malam muji shima idan zai tafi da Ita uwar gidan ne gida. Saurin dago kanshi yayi ya kalli gefen ta, sai yanzu yaga yanda ta rame tareda yin zuru zuru, gwanin tausayi, ya ce Kawu duk yanda kukayi daidai ne. Abinda ya iyacewa kenan,

Addu’a malam yayi kafin yabisu da nasihohi ya karayi musu ta’aziya, ya dora dacewa Idan so samune Naziya ta zauna a dakin ta, Amma a yanzu saboda dalilai masu yawa zan mayarda ita gida tayi takabarta, Allah ya gafartawa Ahmed.

Wani irin daci Khaleel keji a zuciyar shi, yarasa wane irin tunani zaiyi baida kalma daya da zai iya furtawa a halin yanzu,

Kukan mommy ne yasa suka kalle ta, ba Wanda yaji tausayin ta har Khaleel din ma, domin tsawon kwana bakwai din nan baya ko kallon gefen ta.

 

Toh Hajiya bilkisu Ahmed ya tafi, Amaryar da kika buga kirji kukayi mai yau tace bazata iya zama dashi ba, sannan Inada yakinin mugun halin ki ne yasa itama Matar tashi za a tafi da ita, domin ni Nafi  kowa sanin halin ki bazaki taba canzawa ba, da zaki canza da mutuwar yaya na zata fara canzaki, mundade muna daukar mugun halin ki yau kinga ni, Allah yasa ki dauki darasin idan har akwai sauran  kwakwal akan ki.

 

“Ya isheka Modu karka manta d’ana na rasa babban dana duk Wanda yayi kukan mutuwar nan Kara yayi min, sannan maganar bakin hali, naji abarni da kayana duk ko wacce tafi ruwa gudu cikin su, ni Abarni da zafin rashin d’ana kawai, tafada tana mikewa cikin zafi tayi daki tana kuka mara madafa.

Ko dago kai Naziya batayi ba Saida malam yace “su shukrah na nan zasu hada miki kayan ki su taho dake, ni zantafi dalibai na jirana a gida.  Ya musu sallama yatafi. Saura y’an uwan kawai da iyayen matan, Maman Fauzy tace toh Saura mu yaza’ayi da yarinya tun da tashigo ace bata samu kwanciyar hankali ba.

Cikin zafi yace “Zaku iya tafiya da ita in kun so I don’t need her.

Yafada cikin fada da kuma iyakar gaskiyar shi, “dama momy ta Aurota idan kunga bazaku iya zama ba ga hanya.

Cikin rawar jiki tace ” no mommy please kuje ni Ina nan. Tafada domin tana matukar kaunar Khaleel, bayan ta aureshi da kyar ta yaya zatayi sake ta fita, don haka tuni ta kashe bakin uwar, salifa ce taja uwar ta gefe, “mommy nidai kinga kisa  kawun su yasa Khaleel ya Aureni tunda anayin Auren gado, kinga yafi ma  Ahmed din haduwa mommy wallahi zan zauna in ya Yarda. “Y’ar gari nima tunani na kenan ai kinga yaron ya Tara dukiya kan dukiya gatashi gata uwar shi gata d’an uwan shi yanzu, ke fa uwar shi duk cikin mu tafimu kudi shegiyar, bari mukoma inyi magana.

 

Jiki na rawa suka koma falon lokacin Naziya ta mike tayi daki inda su Aunty Raliya ke hada mata kayan ta, daga Khaleel sai kawu sai gwaggon nin shi, mommy dasu zarah na daki,

Zama Maman Salifa tayi tana Washe baki “Alhaji Inada magana. Suka zuba mata ido kafin yace “munajin ki. “Yauwa nace ba, tunda dai ga d’an uwan shi mezai hana ayi tunani mai kyau a bashi Salifa sai a hada Auren gado. Wani irin saurin dago kanshi yayi tareda watsa musu kallon kun haukace ya ce “kuna hauka wallahi kun haukace, toh kusani kune sanadin duk Abinda ya faru a rayuwar d’an uwana, koda ace mata sunkare a duniya bazan taba Auren Y’ar kiba, don haka kawu ni natafi Inka gama domin one more minutes a nan zanyi Abinda bashi bane. Yafada yana wucewa a zuciye,

“Toh kunji sai ku tashi kubamu wuri, inji daya daga cikin matan, shigewa dakin mommy sukayi jiki a sanyaye,

 

Dayar tace “yaya  dakasa baki ya Auri Wannan Y’ar mai Hankali, itace Matar Aure ba wa’innan y’an barikin ba. “Zamuyi Wannan maganar ba yanzu ba kubari mu gama war ware rashin da mukayi sannan shima Khaleel baya cikin natsuwar shi yana bukatar natsuwa, company su ma manager din ne ke kulada komai tunda ba Ahmed.

Dakin mommy su zarah ke lallashin ta domin sunsan koma meye ita tafi kowa rashi, har suka samu tayi shiru tana Ajiyar zuciyar, Shigowar kawar tata yasa tace kuna nan Hajiya? Eh kawata ai na canja shawara, nace ai basai na dauketa ba kawai tunda zumunci mukayi niyyar hadawa tun farko ko yanzu bata baci ba tunda kanin shi na nan sai a hadasu Auren gado kawai.

Kallon su tayi kawai domin tasan Waye Khaleel kuma yanzu bata isa ta tunkare shiba sai bayan komai ya natsa, amma Ajiye mata biyu irin Salifa da fauzy Abun Alfaharin tane a matsayin surukai.

Zarah ce tace, “ai yanzu saidai abari komai yanatsa kafin Wannan maganar ta taso, kuma Karku manta yanada wata Matar fauzy kuma kinsan Y’ar waye. “Badamuwa nidai inzai Aure ni zan zauna da ko mata goma ne Salifa tafada, domin itafa kawai tasa rai.

“Oh Allah kasa mu zamo iyaye nagari ga ya’yan mu Amen.

 

 

Kwana ki natafiya Naziya yanzu tana gidan su duk kayanta dake gidan ankwashe har wainda bata moraba, tafara warware wa Amma kusan kullum cikin yiwa Ahmed Addu’a take da sadaka idan tasamu hali, har Azumi takeyi litinin da Al hamis domin Allah yakai ladan kabarin shi. Khaleel kuwa haryanzu bai dawo dai dai ba, fauzy tayi binshi har tagaji bai komawa kanta, ko fuskar shi bata gani. Yau yana kwance a katon falon mommy ta shigo ciki ita kanta ta rame, “Ibrahim, wai kai wane irin yaro ne, yazaka sawa yarinya ido tun kawo ta gidan ku bayan kasan akwai hakkin ta akan ka, kai bazakayi koyi da halin d’an uwan ka ba, Ahmed dina ba haka yake ba, idan har kaunar da kakewa d’an uwan ka gaskiya ne Kayi koyi da halin shi.

Dagowa yayi tareda cewa ” koyi nakeso inyi da Rayuwar da kika dora shi akai mommy, Ina ganin yadda yayi Rayuwa batareda Matar shiba, kuma kece kika sashi, ke kika hana yaya na ya sauke hakkin da ya dakko har yabar duniya, mommy kina tunanin Allah bazai tanbayi d’an uwana Wannan hakkin ba?  Ta dalilin tsanar da kike yimata har tabar gidan nan bataji dadin rayuwa da mijinta ba why Mommy? Don haka itama Matar son taki tayi biyayya irin nata tagani.

Ibrahim banson rashin kunyar ka haka kaga Ahmed…. “Mommy enough, kidaina kwatance da yaya, ribar me yaci, kinga Amfanin Abinda duk yakeyi?  See to avoid you and your wife, am going back to bangkok, zanje in kulada duk wani aiki da yayana yakeyi, bana ra’ayin zama anan, I don’t need her  idan tagaji tasan hanyar gidan Uban ta.

 

“Ibrahim, zan hadaka da kawun ku inni bazakaji magana taba. Wucewa kawai yayi, dama so yake kawai ayi fourty days ya yi gaba Amma yanzu baijin zai iya Kara ko kwana daya a garin kano gwara yatafi ko zai dawo dai dai.

Duk gurmin da Akeyi Fauziya ta shigo tana kallo, yana wucewa a zuciye ta nufo mommy cikin kallon tsana da kece sanadi, tace Wallahi bantaba sanin Abinda kikayi zai shafi farin cikina ba dana taka miki burki, kuma zanje in shirya inbi mijina. Ta buga mugun tsaki, “Fauziya karfa ki manta ni uwar mijin ki ce kike fadamin maganar da kikaga dama. uwar miji uwata ce ko uwar ubana ce? I beg give me a break. Ta yi gaba zuwa dakin shi dake part d’in .

 

Yana hada kayan shi, tayi sallama yayi wurgi da Abinda ke hannun shi saboda haushin takurar ta, ya juyo cikeda haushi, “can’t you learn from Naziya, kintaba ganin tana bin yaya the way you are following me? Please have some shame.

“Oh baby yazaka hanani bin mijina, you are my husband Inada right akan ka, and ka daina hadani da Wannan village and stupid girl……. Wani irin kukan kura yayi a wuyan ta, tareda shake ta ya hada da gini idanun shi kamar na bakin kumurci, “what did you said?  Cikin karaji, don’t repeat that again if not kin gama numfashi a duniya, I promise you, kin ce  hakki ko kinada hakkina?  gani ki diba in kinada karfi, hakkin na karfi ne kizo ki kwata,  useless, now get lost. Ya saketa tareda hankada ta waje,

 

Da mugun kuka tafita falon Wanda mommy naji tayi Saurin tarar ta, Fauziya lafiya Me Khaleel din ya miki? karki tabani kuma wallahi sai na fadawa daddy na ke kikaja Wannan aikin da kike taka ma dashi sai kin barshi. Tafita tana kuka, hannu ta dora aka, kunga yaro zaimin salalar tsiya, Allah sarki Ahmed da kana nan kaine kadai mai iya takawa yaron nan  birki, Allah ya jikan ka yaron kirki Allah yakai haske kabarin ka.

Ta share kwalla tabi bayan shi,

Lokacin yagama shirya jakar shi, kallon kayan tayi tareda zubamai ido, yanzu Khaleel bangama war warewa a rashin d’an uwanka ba zaka tafi kabarni  bayan kasan banda kowa sai ku biyu kacal, yanzu shi yatafi kai kuma zaka tafi kabarni.

 

Baice mata komai ba yayi hanyar bathroom, fita tayi tana fitar da hawaye, wayar ta ta dakko tafara kiran number wayar kawun nasu, yana dauka tasa mai kuka  tareda fadamai komai akan zaman shi da Fauziya, da kuma tafiyar da zaiyi. Yace mata Yana zuwa kawai ya katse kiran.

Bayan hour biyu kawun ya iso  lokacin yaci Ado cikin manyan kaya Wanda rabon shi dasu tun kafin mutuwar yayan nashi,

Lekowa mai aiki tayi tace Ana kiran shi a falon, ya ce tace yana zuwa, fitowa yayi, yasamu mommy gwanin tausayi gefen kawu akasa yau tunda tana neman taimakon shi. Sallama yayi yagaida shi, zama yayi a kasa kanshi akasa, fuskar shi ba annuri ko kadan, kawu yayi gyaran murya yace “Khaleel tafiya zakayi batareda sani na ba?  “Aa kawu yanzu ma gidan naku nake shirin zuwa infada maka.Toh Amma me zakaje yi kabar nauyin da yake wuyan ka anan, nafarko Matar ka, na biyu mahaifiyar ka na uku company, sannan wasiyar d’an uwan ka, ko bazaka cika mai burin shi bane, domin yafadamin tun ranar da zai rasu saboda rashin natsuwa banyi maganar da kowa ba, sai Malam, dago kanshi yayi domin jin wane magana akayi harda malam zai shiga ciki, “Ya bar maka Amanar Auren Naziya, kuma munyi magana da malam tunda zance ne na wasiyya ya Amince sai dai muyi Addu’a ta fita takaba lafiya sai a daura muku Aure da ita.

 

Wani irin zufa Kebin ta kowane kofa ta jikin shi, yakasa koda motsi baya iya koda daga yatsar hannun shi balle ta kafar shi,

Kukan mommy ne yasa yadawo hayyacin shi , wallahi bazai yuwu ba, yaza ayi yaya ya Aura ya mutu kanin shi ya Aura, kuma dole ne ni sai nayi Rayuwa da Wannan yarinya mai kamar mayya, nidai ban Amince ba gaskiya bada yawuna ba.

Kallon banza kawun yayi mata kafin yace ” ni nasan bazaki canja ba balkisu, kuma nasan ilimi yayi miki karanci da kin koma islamiyya, tunda bakisan Ibrahim zai iya Auren Naziya ba, kuma Ina so insani me yarinyar tayi miki, ko ince meye laifin ta?  Ni tanada laifi A wurina kana ganin saboda soyayyar ta dana ya hadiyi zuciya ya mutu, banason ta kuma lashemin zuciyar Khaleel din da ya ragemin nidai bada yawuna ba.

 

“Yawun ki basuda Amfani a wurin mu don haka Khaleel gareka idan ka Amince kafin ka wuce kaje kaga malam Allah ya taimaka ya kuma tsareka, sannan zancen Matar ka Wannan kaidai ba jahili bane kasan hakkin Aure to don haka Kayi kokari Kayi Abinda ya dace ni natafi.

Yafada yana mikewa, tashi yayi jikin shi a sanyaye yabi kawun Saida ya shiga motar shi yadawo gidan, tana nan ta cika tayi tab. Kana jina Ibrahim, wallahi kar kasake inji kadawo min da Wannan yarinya mai farar kafa gida, karka sake ka Amince da Wannan Auren nafada maka.

Wucewa kawai yayi cikin dakin shi, ya datse key tareda zubewa akasa, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka zubo mai, wainda baisamu yinsu ba tuntuni, Ashe maganar da Ahmed kullum yake fadamai zata kasance gaskiya, Wato akwai Abinda Allah ya boye shiyasa ya cusa mai muguwar soyayyar Naziya wadda bai taba yarda da itaba domin yasan is prohibited,

Yasha wahala yana kuma kan shan wahalar, zai iya rantsuwa da Al’qur ani yafi yayan shi son ta, Wanda baisan ya akayi soyayyar ta ta shiga zuciyar shi ba, how? when? Wani irin kuka yakeyi Am sorry yaya am sorry my brother da nasan zaka tafi kabarmin ita da na roki Allah ya cire min soyayyar ta ya barmin kai a rayuwa, Am sorry for loving your wife more than you brother, am sorry for feeling jealous idan kuna tare baka sani ba yaya, Inada kishin ta sosai yaya I use to cry behind door saboda zafin kishin ta, you are my brother but Ina kishin ganin ku tare, bansan ya akayi soyayyar ta ta shigeni ba, I love her more than the way you love her, I hate myself for that I swear to you, I control my feelings because of you.

You’re dead because of hidden destiny, hawayen shi ya share tareda  hadiye kukan, “I will make her happy yaya zancika maka burin ka, zanbata farin ciki fiyeda yanda Kayi mafarkin bata, zansata dariya fiyeda yanda take dariya idan kuna tare. Mikewa yayi ya zari key din hadaddiyar motar shi tareda goge fuskar shi da kyau ya fita cikin hanzari a falon da yabar mommy a nan ya same ta tana waya tana fadawa y’an uwan ta bakin labari, Modu ya rantse sai ya cakuda jinin ta da talaka…….. . 🖊

 

 

 

 

“Comment share the free pages please and Wannan ne last free page ku biya ku karanta cigaban yanda zata kasance, ya za ayi da rayuwar Naziya shin zata Amince, shin zataso Khaleel, ya rayuwar su zata kasance da Fauziya, idan Naziya ta Amince da Auren Khaleel wace wainar mommy zata toya?????  Muje zuwa yanzu za afara wasan this is just the beginning, let’s go my fans 💃, ga masu bukatar biya kofa a bude take chart me up 09011251444

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA Y’AY’AN GATA

And now AUREN GADO,

 

 

 

 

Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y’an 🇳🇪 Niger  ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,

 

 

2⃣1⃣&2⃣2⃣

 

 

……………. Tuki yakeyi cikin kwarewa tareda bin k’aidar  hanya, ya riga yasan hanyar gidan nasu Naziya, tunda yazo sau biyu, har kofar gidan ya isa, lokacin yana mak’il da Almajirai, da Alama Malam na gida, fitowa yayi yana wani irin sheki da haske duk da ya rame saboda mutuwar d’an uwan shi, wani Almajiri ya Kira yace yamai iso wurin Malam yace mai Ibrahim ne kanin Ahmed, ko minti biyu ba ayi ba saiga Malam cikin fararen manyan kaya, tsohon akwai tsafta da kwarjini, yayi saurin dukawa zai gaida shi, a’a Ibrahima tashi shigo daga ciki,

Har tsakar gidan yajashi domin zauren akwai mutane, yanayi yana kallon tsarin wurin Wanda zuciyar shi ke ayyana mai komai, tsakar gidan akwai inuwar bishiya wadda a karkashin ta aka samai kujera ya zauna Malam ma ya zauna suka gaisa kafin Matar k’irki ta fito, d’an dukar da kanshi yayi ya gaidata ta Amsa tareda yi mai gaisuwa, kafin Malam yace Hauwa Kira min Naziya, kafin nan shukrah ta kawowa bako ko sobo ne mai sanyi. Wani irin lugude yaji zuciyar shi tayi jin ankira sunan ta, ta’ aziya Malam yakuma yi mai tareda fatan Samun Rahamar ubangiji, yabishi da nasihohin da duk in zakazo wurin shi sai ya maka su. Shukrah ce ta kawo zobo mai sanyi a tsaftataccen sabon jug cikin na Naziya, ta Ajiye tareda gaida shi tayi gaba,

Fitowa naziya tayi cikin katon hijabin ta, kana ganin ta kasan ta rame sosai,

Sallama tayi,  ya dago kanshi suka hada ido, Wanda tunda akayi rasuwar daga ita harshi basu hadu ba.

Allah ya gani bata son shan inuwa daya da gayen nan don kawai yaci Albarkacin Ahmed ne batada yadda zatayi dashi, Amma tunda yanzu mai rabawa ta raba shikenan ta huta,

Gaida Malam tayi batada niyyar gaida shi, saida Malam yace ga kanin mijin ki naziya, dama Ina so in samu lokaci muyi magana daku dukan ku, akan wasiyar da mijinki yabari, wani irin faduwa gaban su yayi duka shi tsoron reaction dinta yakeyi ita kuma batasan wace wasiyya bace.

“Ibrahim Alhaji Amadu yazo min da maganar kuma ni bazanyi jayayya da wasiyyar mamaci ba” don haka yanzu magana na wurin ku, Naziya mijinki yabar wasiyya d’an uwan shi ya Aureki, don haka idan kinfita takaba sai adaura muku Aure.

Wani irin kukan tasa tareda zama gaban Malam d’in. Kallon lafiya Malam ke yi mata, shikuwa wani irin tsalle  zuciyar shi keyi saboda fargaba, “Malam don Allah karka Yarda nidai bazan koma gidan su ba, ni bazan yi Aure ba ni bana ma son shi kawai abarni haka, ni karatu nakeso inyi don Allah Malam karka hadani dashi.

 

 

Tashi kibani wuri Naziya banson shiririta, yaushe kika canja hali haka? tashi kafin ranki ya baci, wucewa tayi da gudu dakin Inna, Malam ya kalle shi, Kayi hakuri kaima bansan naka ra’ayin ba, Amma tunda kaine namiji in har ka Amince Naziya ita ba Matsala bace, kaje Allah ya maka Albarka yajikan d’an uwan ka, Ameen yace kawai zuciyar shi na wani suya, maganar ta ta bata son shi really touch his heart, wani irin zafi yakeji a kirjin shi, cikin dauriya yace Malam Wannan filin nakusa daku yaya Ahmed ya siye shi da sunan zai gina maka dakunan Almajirai batareda sanin kowa ba, bayan rasuwar shi Nagani a rubuce ya gama biyan contract din komai Allah bai nufa ya yi ba, inaso Inturo su, su duba yadda zasu tsara komai zanbar komai kafin intafi, zanje domin shigo da wasu kaya,

 

“Allahu Akbar Allah ya jikan shi yasa mutuwa hutuce a gareshi” Allah ya Albarkace ku baki daya. Ya Amsa da Amin, ya tashi yana farin cikin zai fara cikawa d’an uwan shi burin shi, duk da yatafi da ciwon maganar Naziya.

Bayan tafiyar shi ya kira Inna kulu da Naziya, ranshi a bace yace “Hauwa bansan cewa zan haifi yaron da zai yi musu dani ba, yau Naziya ke da nake yabonki kike kokarin watsamin kasa a ido, a gaban yaron nan kice bakya son gidan su bakya son shi, a Ina kika koyo Wannan d’abi’a? “Subuhanallahi Naziya me nake shirin ji”? Inna ni dai Don Allah ku yafemin Amma ni bana son komawa gidan nan nayi hakuri batareda nayi wa kowa korafi ba, yanzu idan  na koma mutuwa zanyi, wallahi bana sonshi baida hali  ba irin Ahmed bane, malam baka san shi ba.

Toh Hauwa tariga ta girma Y’ar taki, ni bazance komai ba tunda ta isa da kanta. Yafada tareda tashi yabar gidan kawai, a tarihin rayuwar shi itace ya’ ta farko data farayi mai musu da gaddama.

 

“Naziya me kikeso ki yi”? Kin taba ganin ko Y’ar nan malam ya yi magana ta amsa shi bare ke? Wane irin abu ne nake gani ni kulu yau? “Allah Inna bana son shi ya zan iya zama dashi ni dai bazan koma gidan nan ba. Ta tashi tana hawaye tareda shigewa dakin su, kwalawa shukrah kira Inna Tayi, “gani Inna. Kiramin Y’ar nan a waya. Tasan wa take nufi don haka takira Aunty Raliya ta bata, Inna tace “kuzo kuyiwa  Y’ar uwar ku magana ta canjo hali, nan tafada mata komai, tace karta damu za tazo tayi mata magana ita da Aisha. Dakin su ta koma tana kuka, tareda kudurin duk Abinda zai faru sai dai yafaru bazata taba Auren Khaleel ba, saboda tun farko jinin su bai hadu da juna ba, tayi hakuri ta zauna da Ahmed saboda tana son shi, Amma bazata taba Y’arda ta zauna da Khaleel ba, wai ma yaza ayi ta yarda da Wannan kwamacalar, bayan agaban shi yaga yanda Ahmed yake nuna mata so lokacin da suka samu sarari,

Shigowa shukrah tayi tace “Aunty wai fadan me Inna takeyi yi miki?  Kuka kikeyi  me yafaru?   Rungume shukrah tayi tareda jin wani sabon kuka,    “Shukrah bana son shi. “Waye bakyaso Aunty? ” Khaleel, I hate him, bana sonshi wallahi bazan zauna dashi ba. “Ni Aunty bansan me kike fada ba.

 

“Ya za’ayi kisani tunda Auren ya koyo mata taurin kai, Naziya ki rufawa kanki Asiri karki wahalar da kanki a banza idan Malam ya karb’i lamarin nan ba mai canja shi, don haka na hore ki kiyi biyayya ki gama lafiya shine kawai.

Hadiye kukan ta tayi, dif jin fadan Inna, Shukrah ta tashi tabar dakin domin tasan ba hurumin ta bane,  zama Inna tayi gefen ta tafara yimata nasiha akan bin duk abinda Malam ya zartar, shiru kawai tayi domin bata saba jayayya da iyayen ta ba, Amma zuciyar ta bata lankwasu ba, Sam bataji zata iya zama da wani kanin mijin ta ba, dama wani ne ba Wannan ba.

 

Yana tuki yana tunanin kalmomin ta,” ni bana son shi.  Kalmar datafi kona mai rai, don haka speed ya Kara, saida yagan shi cikin gidan su ya fito a zuciye, ya matsu gari bai Waye ba yagan shi yabar kasar nan, kwabewa yayi tareda watsar da kayan jikin shi ya zube akan kujera zuciyar shi mugun zafi da turiri takeyi, she is the first girl da ta kalli tsabar idon shi tace bata son shi, huci yake fesar wa saboda zafin zuciya.

Har  zuwa dare ya kasa bacci shi kadai yasan ciwon zuciyar shi, a kwance yake dagashi sai boxer  jikin shi na sheki kadaicin d’an uwan shi kawai idan aka barshi dashi wani Abu, amma yana ganin duk duniya ba wanda zai iya fahimtar halin da yake ciki, how he wish yayan shi na tare dashi, yafi son rayuwar shi fiyeda soyayyar Naziya, wadda ya Amince ta kashe shi akan yarasa d’an uwan shi gwara shi ya mutu, saboda yanzu ma ba Amfana zaiyi ba don ya dade da sanin bata kaunar ganin shi.

Turo kofar da akayi ne yasa yadago kanshi, fauzy ce, ta shigo cikin Sanyin jiki fuskar ta sharkab da hawaye, tana sanye cikin kana nan kayan bacci, kusan duk komai nata a bayyane yake Wanda shi ba abunda ya burgeshi ciki, domin zuciya ma saida natsuwa take samun wani feelings, halin da yake ciki ko tsirara ta shigo gaban shi ba tashi zaiyi ba.

Zubewa tayi kan jikin shi tasa mai kuka mai ban tausayi, “meye illa ta, meye aibuna da ka kasa bani koda sakon zuciyar kace? Khaleel Ina sonka why ni baka sona? nayi hakuri da duk wani halin ka, yau kusan sati biyu Auren mu ba wani kulawa baka ko zuwa gefen da nake, Khaleel nifa mutum ce Inada jini,  ni lafiyayyar mace ce, dole in bukaci mijina please tauye hakkin yayi yawa, sannan me nakeji?  Auren Naziya?  “That village girl”?.

Tunda take magana jikin shi yayi mugun sanyi, yes she is right ba ruwan Ubangiji da halin da yake ciki, tunda igiyar Auren ta na wuyan shi bai kamata ya watsar da hakkin Allah ba, amma this her last statement mess up things. Wani irin wancakalar da ita yayi kasa tareda mikewa yana nuna ta da yatsa ” look that girl, I value her more than you, she is more important to me right now, karki sake inji wani mum munan kalma daga bakin ki akan ta, duk wani Abu da ya shafi d’an uwana yanada muhimmanci A rayuwa ta, ko a mafarki naji kin kuma kiran ta village  girl sai na saba miki.

 

Tashi tayi tareda girgiza kai ” lallai Khaleel, tell me, yaushe kafara sonta?  This is not About yaya Ahmed ,this is about you, yes saboda naji yanda kukayi da salifa why kaki Amincewa da salifa ka amsa Naziya, why?

Zaburowa yayi ya nufota kamar zai shake ta, “baki Ajiye ni ba so don’t question me again, kuma kije kiyi duk tunanin da zakayi I don’t care, one last thing, in kinga ban Aure taba sai in bana raye, idan zaki iya zama ki zauna idan bazaki iyaba see your road. Yafada yana nuna mata hanya, juyawa tayi da gudu  tafita ya bita da tsaki tareda cewa “useless.

 

Dakin momy tafada har bacci ya dauke ta Wanda ta dade batasamu tayi irin shiba domin rasuwar Ahmed, yau ma da  taimakon maganin hawan Jinin da Aka bata ta samu yadan dauke ta, fadowar datayi tareda buga kofar yasa ta zabura tareda dafe kirji tana jin bugawar zuciyar ta yana karuwa, “kalu innalillahi, ke Fauziya lafiya kika bugamin kofa tareda fadomin daki kamar y’an fashi.

Kuka tasa mata mai karfi, kince zakiyi mai magana gashi yace sai ya Aureta, ni wallahi bazanyi kishi da yar talaka ba kuma Y’ar kauye. “Oh yanzu bazaki iya bari muyi maganar da safe ba? kinga bacci nakeji. “Allah bazaki runtsa ba Indai ni bazan runtsa ba.”Toh baki Yarda dani bane Fauziya? nice fa, bazan taba Amince wa a hada min iri da jinin talaka ba, saboda soyayyar da Ahmed ke mata ya fadi ya mutu yabar ni don haka bazan Yarda ta dawo ta karasa min gudan da yarage ba, kina ganin Y’ar nan kinsan ta gaji maita daganin ta mayya ce.

“Ni Ina ganin yana sonta ne fa. “No no no ba wani so, yaushe d’an uwan nashi ya mutu ke baki san soyayyar dake tsakanin shi dashi bane ko Auren ki ya karba saboda sa bakin Ahmed badon niba, a duniya Khaleel zaiyi komai saboda Ahmed Inada Wannan yakinin, don haka kicire zancen Khaleel zaiso yarinyar nan bayan yanada mace kamar ke. “Hmmm ni ai baya sona kema kin sani Khaleel baya son kowacce mace baida lokacin mace, Ina tsoron ranar da zaiso wata irin su basu iya fadawa soyayya ba, ranar za ayi biyu kuwa domin zan iya kashe macen da duk Khaleel yaso,  ni nayi dakon soyayyar shi don haka idan har akwai wadda Khaleel zai so to nice.

“Naji zo ki kwanta a nan don girman Allah kibarni in kwanta maganin nan aiki yakeyi ajikina. Da k’yar ta samu ta kwanta sukayi bacci.

Asubar Fari yabar musu kasar su batare da yajira sun tashiba, maid ya fadamawa tafada ma mommy ya tafi, Wanda saida tayi kuka sosai lokacin da yarinyar ta fada mata, wani gefe tana mai kewar Ahmed yaro mai biyayya, “Allah ya jikan ka yaron kirki”, zabin ka ne kawai ya sabawa ra’ayina Amma kai d’a ne nagari Ahmed, Allah yakai haske kabarin ka.

Koda ta nemi wayar shi, lokacin yayi nisa a sararin samaniya, Wanda yatafi da kewar Abu biyu, Wanda yana fatan kafin yadawo yarage tunanin su domin samun zaman lafiyar zuciyar shi.

 

Gefen Naziya haduwa sukayi washe gari Wanda Aisha tabi bayan Naziya tareda cewa “gaskiya  Innan mu Ki cire kara ki fadawa Malam gaskiya kar ya Yarda da had’in nan, domin tasha wuya a gidan nan batareda mun fada muku ba, nidai bana goyon bayan ta Auri wani kanin mijin ta, wane dadi ta tarar a gidan mijin nata da zata koma cikin shi?.

“Toh madallah naji ku kuma nasan inda tasamu zuga, Wato dukan ku kun canja hali banida labari? Malam ya fara fada kafin ya karaso ciki ya zauna, “Hauwa, ki zama sheda, da farko bani nayiwa Naziya zabin mijin ta ba duk da a Musulunce ni keda hakkin zaba mata mijin Aure a matsayin ta na budurwa, banyi hakan ba, can suka hadu dashi tace taji tagani,   duk Abinda ta fuskan ta a gidan Aure kaddarar tata rayuwar kenan,  kuma yanzu mijin ki ya tafi yabar wasiyya akan d’an uwan shi ya Aureki na fita hakkin ki  a matsayi na na mahaifin ki ba neman shawarar ki nakeyi ba, Agaban ido na da na yaron nan ki kace wai bakya son shi, saboda rashin da’a, to ki rubuta ki Ajiye Indai Ina numfashi, daga ranar da kika fita takaba daga ranar zan daura miki Aure da Ibrahim don Allah Naziya kifito ki nunawa duniya ni Malam Abu nayi miki Auren da bakiso, don haka nagama magana. “Kayi hakuri Malam” inji Inna da sai yanzu ta fara magana, don Allah karkayi wani dogon tunani kazartar da duk Abinda yake dai dai, nasan duk hukuncin daka yanke kana da taka hikima. “Malam Kayi hakuri kokarin lallashin ta mukeyi wallahi. Inji Raliya, tashi yayi kawai ya kade babbar rigar shi ya fita, Wanda sai lokacin tasaki d’an karamin kuka tareda toshe bakinta kar Malam ya jita, “Akul Naziya, Aure na sama da shekara talatin idan kikaja min bacin rai saboda boyayyan bakin halin ki bazan yafe miki ba. A’a Inna ya haka? don Allah karkiyi saurin yimata baki. Inji Raliya,  ba baki nake mata ba dawo da ita nake cikin hayyacin ta. Rarrafawa tayi da sauri ta rike kafar Inna. “Na tuba Inna wallahi bazaki kuma jin nace wani Abu ba akan maganar nan, ba zan kuma musu ba, ki yafemin don Allah Inna. “Allah yawa Rayuwar ku Albarka baki daya, Aisha kirika hakuri ke babba ce a saman ta in bazaki kwantar mata da hankali ba karki nemi tayar mata dashi.

“Afuwan Inna kuyafe mana. Tashi tayi itama tabarsu a cikin dakin, suna Kara tausar ta. Matsowa Raliya tayi tareda dafa ta tace ” ki share hawayen ki, jikina nabani Naziya zakiyi farin ciki fiyeda Auren ki na farko,    kinsan me?  Girgiza kai kawai tayi badon tana farin ciki ba sai don tana gudun bacin ran iyayen ta, “saboda Khaleel daban yake bazaki gane ba sai nan gaba keda kanki zaki fadamin. Allah kadai yasan Abinda ke ranta   amma ita tasan bazata taba son Khaleel ba domin jinin ta da nashi bai hadu ba, zaman ta da Ahmed soyayya ce sanadi Amma shi tasan zama ne bamai dadi ba. Haka suka wuni  suka tafi gidajen su, Wanda daga nan ta Kama kanta tareda  dukufa Addu’oi akan mijinta.

Wasa wasa aka fara aikin ginin malam Wanda batasan daga Ina Abun ya samo Asali ba,  cikin wata guda har angine dakunan Al majirai sunkoma andawo gyaran cikin gidan Wanda aka rushe gefen da suke ciki aka bugawa Inna flat Dan madai daici Da bazai cinye filin tsakar gidan ba sai dakuna biyu a waje, daya na Malam daya nasu Naziya. Aiki ne dayaja kudi Abunka da akwai su gamasu aiki birjik, mamaki takeyi sosai akan Wannan gyaran Wanda saida takasa daurewa ta tanbayi Inna shin Waye yake musu irin Wannan gyaran ne?  Tafada mata wasiyyar mijinta ce kanin shi ke isarwa, a ranar saida ta shiga daki tayi kuka sosai.

Tareda yi mai Addu’ar Allah yakai haske kabarin shi,  tasan tayi babban rashi a rayuwar ta,  a duk lokacinda ta tuna da kudurin shi nason ya huta da ita sai tayi kuka, yaso ya taba kirjin ta kamar me kunya ta hanata, Ina ma ana dawo da hannun agogo baya da ta Bashi dama yayi yanda yaga dama da jikinta kila data rage takaici, wani irin bakin ciki takeji idan ta tuna cewar Khaleel zata Aura domin tasani Malam baya magana biyu.

 

Cikin wata uku gidan nan yayi tsab bazaka taba gane shiba waje da ciki kowa  sai ya yaba a unguwar, Almajirai sun samu gata domin odar katifu irin na yan boarding akayi musu Wanda a wanna dalilin yasa tsangayar take Kara bunkasa. A gefen gidan momy kuwa tun bayan tafiyar khaleel da sati biyu Fauziya ta tattara nata tayi tafiyar ta Tareda cewa “wallahi sai mijin ta yadawo zata dawo bazatayi gadin wata uwar miji ba, Wanda hakan ya taba mommy sosai domin tasa ran ita zata tsaya ta debe mata kewa, wani lokacin ta kanyi kukan rashin Ahmed don dai tana fita aiki ne Amma zaman kadaicin yana mugun tabata, watannin Sam ba masu sauki bane a wurin ta. Gefen Fauziya a kullum suna waya da khaleel yana kiranta tareda fada mata tayi hakuri idan yadawo komai zai dai dai ta, domin yasan cewa  akwai hakkin ta a wuyan shi yana kokarin tursasa zuciyar shine kawai gudun hakkin ubangiji, bata taba fadamai cewa bata gidan  ba,  sai ranarda sukayi waya yafada mata yana hanya cikin satin bayan ya kwashe kyawawan watanni hudu a kasar ta China,

Kawai Mommy ganin ta tayi tana shiga part dinsu lokacin tafito zata tafi aiki, “A’a Fauziya andawo? ” eh bakya kaunar indawo din ne to na dawo. “A’a murna nakeyi ai gidan shiru ni kadai, yanzu dai zanje aiki in nadawo mayi magana, ta bita da harara, “Y’ar sa ido kawai mtswew.

Wanda Mommy murna takeyi domin ita zaman Fauziya a gidan ta Kara mata girma yakeyi tareda mutunci a cikin kawayen ta don haka duk yanda zatayi zatayi taga ta rusa maganar Auren Naziya da khaleel, zakuma ta gyaro zaman Fauziya da khaleel Indai ita tahaife shi……. 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 🌻🌻AUREN GADO🌻🌻

 

 

 

 

*Matar soja ce*

 

 

 

Daga marubuciyar

KUSKURE NA

BARIKI AUREN SOJA

MUK’ADDARI

WANAKE AURE

ZANYI BIYAYYA

Y’AY’AN GATA

And now AUREN GADO,

 

 

 

 

Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y’an 🇳🇪 Niger  ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,

 

2⃣3⃣&2⃣4⃣

 

………….. A katon filin jirgin yafito   yana Takawa daya bayan daya kamar wani prince, sheki yakeyi yana wani irin haske,  idanun shi dauke da katon eye glass, baka ko ganin kwayar idanun shi, fuskar shi dif take ba Annuri yakara haiba da cika ido, watannin hudu sunyi matukar taimaka mai wajen warkar da damuwar rashin dan uwan shi kadan, driver ne tare da manager dinsu ya tareshi, gaisawa sukayi ya shiga motar suka zuba mai duk kayan da yazo dasu, suna tafiya yana discussing harkar business din su Wanda an samu cigaba sosai a cikin watannin fiyeda shekarun baya, domin shi mai zafine kuma baida sanyi kamar yayan shi, yana bin diddigin komai ma’aikatan sun san an samu canjin boss ba wasa, kuskure kadan yagani ko yaji tun yana China zaisa ayi firing mutum a aiki.

Kamar daga sama suna zaune dai dai itada mommy suna hira mommy na Kara lallashin ta tareda alkawarin komai zaiyi dai dai idan yadawo tunda yafara sauraran ta. Kawai sukaji sallamar shi sama sama, wani irin zabura sukayi duka tareda sakin baki,  suna mai welcome, zama yayi kawai gefen mommy ya gaida ita tareda dan sakin fuska, domin uwa uwace koda kuwa abola take yawo, he missed her domin fushin da yakeyi da ita yasa tunda yaje baya kiranta baya son ko jin muryar ta sai in ita takirashi, he know she is wrong, kuma shima he is wrong, domin ba Wanda yabashi damar watsar da uwar shi, riko Hannun ta yayi tareda sakin murmushi, “mommy am back. I’m glad my son, ya harkokin ina ji a bakin manager komai na tafiya normal. “Yeah Alhamdulillah. Wani irin rawar kafa Fauziya keyi ta matso tareda zama gefen shi tadafa cinyoyin shi dake cikin blue jeans dinshi sabo dal, “Baby wannan irin surprise haka dama kafada, am happy wallahi. Ture hannun ta yayi tareda mikewa yace” OK bari inshiga ciki zanyi wanka in huta, mommy please am hungry. Jikin ta narawa tace bari in hada maka meal din ka just five minute,Ta wuce murna fal cikin ta, tarar shi Fauziya tayi tace “darling muje part din mu mana nan akwai takura ba sakewa”.

Mugun kallo ya watsa mata kafin cikin zafin rai yace “uban waye zai takuraki anan, now listing I know exactly what you are doing, ko ki dawo nan ko ki yi ta zama acan ke kadai, saboda bana ra’ayin zuwa wanna gidan if you are ready ga dakin ki can! Ya wuce abun shi.

“Kutumar uba wato dakin da Y’ar kauyen nan ta zauna yakeso ta dawo wallahi bazata dawo nan ba sai dai duk Abinda zai faru ya faru. Bin bayan shi tayi bayan ta gama dogon tunanin ta, lokacin harya tube ya daura towel, tuni taji wani irin feeling ya taso mata domin khaleel fa namiji ne complete ba algus ya ginu ya keru, wani fesar da zafin bakin ta tayi kafin ta matsa tana karairaya zata rungume shi.

Hannu yadaga mata “please, bana son disturbance, nagaji now get out.

Haba khaleel wane irin daukar Alhaki ne wannan? you’re my husband why All this?, ko bankai mace bane, Auren mu wata hudu Amma ace ko hug baka bani damar yiba. “Go and ask mommy idan ta Amince da hakan saiki dawo now out. Yafada yana wucewar shi bathroom. Fita tayi  kawai rai abace taci karo da mommy, me yafaru kuma kinfito da bacin rai? “Ba dole ba, yaza’ayi ace wai  sai na tanbayi izinin ki zan rungumi miji na? gaskiya kekam a bincike ki kina wa yayan ki asiri ne wane irin biyayya ce suke miki kike cutar dasu,  so kikeyi nima inyi rayuwa irin ta Naziya? wallahi ko kina so ko bakyaso sai kinganni da cikin khaleel. “Haba Y’ar lelen mommy zo kiji, ke baki iya siyasa ba keda zaki caba ado ki makalewa mijin ki, ya zakice banason hada iri dake Fauziya, duk soyayyar da nake nuna miki haba ki rika ragamin mana. “Nidai kiyimai magana yadawo gefen mu Ina jiran shi. “Jeki zanturo shi kin ji. Ko sauraran ta batayi ba ta fice, saida ya dauki kusan minti talatin yana kwance tareda runtse idanun shi a cikin ruwan, shi kadai yasan tunanin zuciyar shi, wani irin murmushi yayi na gefen baki, kafin ya fito ya dauraye jikin shi, ya daura towel ya fito, mommy da ya gani zaune da Abincin shi tana jiran shi yasa yace “oh my mommy am coming tank you, I really miss your cooking.

“Oh son kayi kasa kaya kazo kaci. Kananan kaya yasaka kafin yadawo yazauna, akaron farko yafara bata labarin komai kafin yayi shiru, domin tuno da dan uwan shi da yayi, “I promise, Yaya zanyi duk Abinda kake burin yi kafin nawa.  Shiru tayi tareda dafashi, “khaleel, mutuwar Ahmed gibi ne babba a rayuwa ta and all tanks to wannan Y’ar gidan talakawan, look son kaga idan Har na isa dakai kar inji ka yarda da Auren yarinyar nan, idan kana so ka ciremin kewar dan uwan ka kabi Abinda nakeso. kallon ta kawai yayi ya janyo Abincin shi yafara ci, bai kuma cewa komai ba har ya cika cikin shi fal ya kora da juice, “mommy zan kwanta domin nagaji sosai, later zamuyi magana.

Kallon dan rainin wayau tayi mai kafin ta kwashe kwanonin ta tafita, wato duk maganar ta bata bukatar Ansa, saida yaga ta fita yaja numfashi, “am sorry mommy she is my wife now! Auren mu ya dauru tundaga ranar da tafita takaba, don haka soon zata tare agidan nan.

Baccin shi ya shaka bayan ya rufe kofar saboda bai son damuwar Fauziya.

Tana can ta cika tab tana jiran mijin ta ga mommy ko zancen batayi mai ba saboda damuwar Auren Naziya yafi tsaya mata arai. Bai tashi ba sai la’asar yayi sallah ya shirya yafito domin yanada Abunyi, part din yayan shi ya leka yaga ba kayan salifa, wayar shi yaciro tareda kiran manager yabashi umarni, akan ya nemo mai best company na furniture’s a kano  saboda he want to renovate the house, baya bukatar tsohon Abu a ciki, saida ya gama tsara komai ya fita daga gidan.

 

 

Tun fitar ta takaba ta murmure tayi tas da ita ba ruwan ta da komai fitama batayi dama kuma ita bamai yawo bace, tana cikin gida tana taya inna aiki ko tana chat a wtstp domin yana rage mata tunani da kewar Ahmed dinta,  a kullum ta kalli yanda baya duniya Amma ya inganta rayuwar su Abin na mugun faranta mata zuciya, hatta da dakin su an saka musu gado da sabuwar katifa, dama basuda talaucin Abinci domin Malam ba mutum bane da ke zama, nema yakeyi iya karfin shi,  a zaune take yanzu a karkashin bushiya itada shukrah suna hira sama sama tana chat, tana cikin adon ta cikin riga da sket na   shadda orange sabuwa da Aunty Raliya ta dunka mata na fita takaba, dinkin yayi kyau sosai yayi cib a jikin ta, jikinta ba ko mayafi dankwalinta yadan zame kadan kana hango kwantacciyar sumar ta agaban goshin ta, yanzu Almajirai basa shigowa gidan saboda duk Anfitar dasu waje,    suna sakewa sosai, Inna ce ta fito dauke da robar gyada mai bawo ta zauna itama a wurin, “Shukrah sa hannu mu bare gyadan nan da ita zamuyi sanwar dare, waccan inta dauki waya bata ji bata gani. Ajiye wayar tayi tana Dariya, “kai inna ai zan Ajiye tunda ga aiki, Amma inna me yasa bakya son a bare miki gyada a injin sai barar hannu? “Kyuiya ke damun ku yanzu” mu da Ina mukaga wainnan Abubuwan, ko nikan masara sai mu niketa a dutse, Yanzu aiku yan gayune, inkai gyada ta injin a farfashemin rabi yabi bawo. Sallamar da akayi ne yasa suka amsa tareda dagowa, Inna ta saki baki tareda cewa” maraba da mutanen ikko, mai sunan Malam kaine a gari?, dukan su sakin fuskar su sukayi, Shukrah ce tafara cewa ” Yaya Sadiq oyoyo kaine? Matashi ne kyakyawa ba laifi ya matso wurin da suke Shukrah ta Bashi wurin zama ya zauna ya gaida Inna tareda gaisawa da Naziya tareda yimata gaiduwar rasuwar mijinta, Sadiq Almajirin Malam ne da yazauna a gidan kusan tun yana yaro yataso hannun Inna kamar d’anta, har makaranta yayi a hannun su yanzu yana business a Lagos kuma Alhamdulillah  ya samu Abun rufin Asirin shi, shima don har gida da motar hawa ya mallaka na kanshi, yanada rufin asiri dai dai gwargwado,  hira sukeyi tsakanin su domin ya zama dan gida basa mai kallon bare infact matsayin Yaya suke kallon shi,

Sallamar da Malam yayi ne tareda kuma khaleel yasa Inna ta tashi saboda kunyar taga khaleel, Wanda Naziya bata lura ma da shi ba, dariya takeyi har dimple dinta na   lotsawa, saboda sun saba da Sadiq sosai,, saida ya zo gab dasu ta shaki kamshin  turaren shi, dago kanta tayi sukayi two eyes ido cikin ido tuni Annurin fuskar ta ya dauke kamar yanda nashi ya dauke dif, dama ba wani fara’a yakeyi ba, mikewa tayi kawai ta dauki robar gyadar tayi kitchen zama sukayi su uku a wurin Shukrah na gaida su ta wuce itama, fuskar shi tamke suka gaisa da Sadiq, Malam yafada mai koshi waye a wurin shi, “Ibrahim Mai suna na kamar su Naziya yake a wurina, yana kasuwanci a ikko yau ya shigo. “Sadiq wannam shine mijin Naziya na yanzu”. Saurin kallon Khaleel yayi domin yana ganin shi yasan wani ne kuma  ya tara ko kuma dan wani,  wani iri yaji yace “Malam andaura ne? “Eh kamar yanda nafada maka rasuwar mijinta wannan dan uwan shine. Shiru yayi kawai shi yasan Abinda ke ranshi, fuskar khaleel a tamke yace “Malam zan iya ganin ta? “Bismillah ai gidanku ne ga dakin ta can kuje kuyi magana. Yafada tareda juyawa suna magana da Sadiq, “yanzu dai baka komawa sai ka kawomin Matar Auren ka Sadiq tunda dai kasamu rufin Asiri Bana son zaman magidanci ba iyali. “Insha Allahu Malam” kafin intafi zan nema.

Wucewa khaleel yayi hannun shi sanye cikin pocket din manyan kayan nashi, shadda ce fara Y’ar gaske, tayi matukar haska shi, dama ga iya wanka,

Zaune take tana cewa Shukrah” shi kuma wannan daga Ina?  kalla yanda ya fadowa mutane cikin gida. “Kai Aunty bakya ganin tare yakeda Malam kuma karki manta kin kusa zama Matar shi tunda ki ka ganshi yanzu, ni Ina tunanin ma kamar baya garine tun zuwan dayayi bai kuma zuwa ba sai yau. “I don’t care da yazo da kar yazo kinsan da Allah zai taimakeni Malam ya fasa zancen Auren nan da nafi kowa farin ciki. “You are too late. Yafada bayan ya daga labulen dakin nasu ya shigo, saurin tashi Shukrah tayi, ya kalleta” sister excuse us please. Yafada yana murmushi kadan, tace “tom” da sauri ta fice, karasa shigowa yayi, taji kamar ta zura da gudu, juyawa tayi tareda daukar katon hijabin ta ta zura. “Hmmm. Kallon dakin yayi dakyau yaganshi fes yana kamshin turaren wuta ba wani tarkace daga gadon su sai Karamar waldrp da akwatunan su sai mirror dake dauke da kayan kwalliyar su.

Matsawa yayi gaban mirror batareda yace mata komai ba, ya dauki turare daya ya kalla ya Ajiye. Kallo take binshi dashi kawai domin rainin wayan shi yawa ne dashi, kuma so take taji ya karasa maganar daya faro tun farkon shigowar shi. Ganin baida niyyar cewa komai gashi haibar shi duk ta cika mata daki, duk taji she is not comfortable at all. “Malam ka taimaka ka fadawa Malam baka ra’ayin Aure na, domin ni bana ra’ayin Aure yanzu, musamman dakai. “Sai da wancan kazamin ko da kike wa dariya kamar wawuya right? Yafada yana juyowa tareda matsowa kusa da ita. “Nidai koma meye ni bazan Aureka ba”. Hmm Ashe igiyar Auren a hannun ki zata zauna idan an daura? dago kanta tayi tareda kallon cikin idanun shi domin fadamai magana, “wane irin cin Amana ne zaisa ka Amince da Auren Matar yayan ka, kuma bayan kasan ba kaunar juna mukeyi ba? That’s your opinion not mine! and listing, Aure an daura shi tun daga ranar da kika fita takaba, don haka ko kiso ko kar kiso you’re under me, kina karkashin inuwar Aure na, sannan kina maganar cin Amana ko what ever, ai kece mai cin Amana har kin manta da Yaya na kin fara sakewa wani banza fuska kina dariya, listing to me, am not like my brother ni ba zakiyi min Abinda kikaga dama ba, wannan rayuwar da kikayi a baya ki gogeta this is Ibrahim khaleel, you better change your way, be a responsible house wife, if not bazakiji dadi naba.

Wani irin zafi zuciyar ta ke mata yanzu ji take da tana da karfi shakeshi zatayi har sai ya daina numfashi domin irin maganar dayake fada mata a sulale.

“Malam idan kana tunanin Naziyar daka sani ce a baya you are mistaken, inada nawa tsatstsauran ra’ayin idan naso, don haka karkayi mafarkin zanyi irin rayuwar da nayi da Ahmed a gidan ku, naso Ahmed shiyasa na jure wulakanci kuma kai kasani  ba zaman dadi a rayuwar da baso sai tsana a cikin ta. “Hmm that means you hate me? “We hate each other. Tafada tana murguda baki, “ni bazanyi zaman Aure dakai ba. “OK naji kuma duk na haddace and lokaci ne zai fada mana komai,  Malam ya tanbayeni yaushe zandauke ki da nace end of the month, yanzu nafasa so nake kitare a gidana domin inga ra’ayin waye zaiyi tasiri. “Nidai bazanje ba don Allah ni ka sakeni kafada musu kafasa. Har ya juya zaifita kalmar saki tasa ya juyo, tareda Kara tamke fuska, ” in your dream. “Ni bazan zauna da wata kishiya ba ai Kanada mata, ni kuma bazan zauna da namiji mai mata ba, Tafada ne kawai badon Abinda ke ranta kenan ba sai don ta rasa wane irin excuse zata kawo mai.

“get ready domin zama zakiyi da kishiyoyi ba kishiya ba, and saboda careless baki kosan bana gari ba, anyway am back tsarabar ki sai kin tare, bye. Ya fice cikin hanzari, tabishi da kallon mamaki, duk zafin nan da take ganin yanada shi bai nuna mata ba, wai da gaske an daura mata Aure dashi? Ya bata sani ba? Shukrah ce ta shigo tace “Aunty da gaske fa Malam ya daura muku Aure da khaleel ya sadiq kefada min yanzu. Zama tayi kawai tareda dafe kanta, ta Ina zata fara zama dashi, wace irin rayuwa zasuyi, yazata zauna da Ahmed yanzu shima ta zauna dashi?

“Aunty nidai karki sa tunani kiyi Addu’a Allah yasa kiji dadin Auren nan fiyeda na farko. “Hmm Shukrah, bakisan halin shi bane, ni bazan taba sonshiba. “Aunty kin sani fa  bakyau kaki mutum da yawa in zaki so mutum kiso shi don Allah haka in zaki k’i shi ki k’i shi don Allah.

Bansan  wane irin zama kukayi da Yaya Ahmed ba Amma ki kyautata zatonki kisawa zuciyar ki hakuri zakiyi farin ciki. Shiru tayi tareda mikewa ta fito domin tana bukatar Amsa wurin inna..

Zama tayi a kitchen din tareda daukar Alayyaho tana gyarawa “Inna yaushe aka daura min Aure ban sani ba?  Dago kai Inna tayi tace “kije ki tanbayi Malam ai kin San baya magana biyu, don haka karki manta da furucina, kuma kar inji musu ko jayayya akan zancen nan, kinji nafada miki kiyi ki yanka kitashi ki tuka tuwon nan ya dahu. Ta fada tana fita tabarta, wasu hawaye ta share masu zafi tareda ci gaba da aikinta, tayi Alkawari koma meye zai faru atsakaninta da shi ne zaiyi daya sanin Amince wa Auren ta.

 

Sai dare ya koma gidan su domin bai bar gidan Malam ba sai bayan magrib daga nan yayi gidan kawu, suka tattauna kafin yayi isha’i yadawo gida.

Lokacin Fauziya na zaune a falon cikin gida tana jiran taga inda zai bullo, mommy tuni ta shige domin batason rigimar ta, tsawon rana tana korafin yaki komawa gefen su, shigowa yayi da sallama, “me kikeyi a falo ke kadai Ina mommy? ” ta kwanta, Ina kafito inata nemanka a waya baka picking? Tsayawa yayi tareda kallon ta ” yaushe wannan yafara a tsakanin mu dake?  Aike na ki kayi ? OK naje wurin Amaryata ne. “Wace irin Amarya, khaleel Aure zaka Kara? “Don’t act like you don’t know about it,” salifa ka Auro min again ko wata ka samu? Wadda bakyaso ki fada dai itace kuma ba Aure nake nema ba Aure an riga an daura in kina lissafi daga ranar da zata fita takaba daga ranar ni mijinta ne, don haka next week zata tare nan gidan.

Wani irin ihu ta buga tareda zubewa ta zabga Ashar ” kutumar ubancan ni zaka wulakanta duk halaccin da nayi maka sakamako na kenan kishiya da wannan yarinyar, Wayyo ka cuceni wallahi bazan hada miji da wannan ba. “Toh sai ki bar mata dama itama bata ra’ayin kishiyar kuma in zabe za ayi kinsan bazan zabe ki in barta ba, saboda Amanar Yaya na ce, zanyi komai domin in kulada Amanar shi.

“Wallahi Khaleel baka isaba Indai nono na kasha saika saketa” Aure aka daura muku bada yawuna ba, lallai Modu ya kai karshen mugu kuma munafuki, na fada maka bana son hada iri da talaka bazaka gurbata min zuri’a ba, kuma zanyi fito na fito da duk munafukin da keda hannu a cikin hadin Auren nan , sun samu nasarar lashe min kurwar yaro na babba kaima sun fara galaba akan ka, ai dole akuma likamaka  tunda anga daula ba’aso abarta wallahi khaleel zakusan koni wacece muzuba nidaku da duk Wani dangin ubanka. Wucewa yayi kawai daki domin  maganar ta isheshi kuma baida Abunyi akai Aure dai an daura ba fashi shi yasa yace kar kawu yafada mata,

Kwana sukayi da fauziya basu runtsa ba, zata iya Yarda asiri akewa dan ta shi yasa suka samo kanshi inba hakaba me zaiyi da ita………. 🖊

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 2⃣5⃣&2⃣6⃣

 

 

 

 

………………  Kuma kasaurare ni idan har kai ka nuna isarka ta Auren wannan yarinyar nima ka jini da kyau, saika Auri salifa itama. Wani irin Kallo yake musu daga ita har Fauziya, “mommy kinayin duk wannan Abubuwan saboda wannan useless woman din ne ko, Toh ki fada mata itama tolerating dinta kawai nakeyi a gidan nan badon Ina son ganin taba, kin san cewa ba Wani Abu da aka doramin akai mai nauyi samada igiyar Auren ta?  Wallahi in kun Auro wata tare zasu tafi, wallahi bazan hana ku daura Auren wata ba, Amma igiyar a hannu na take, I won’t hesitate to cut it all. Ya nuna ta da tuni tayi tsit saboda jin maganganun shi, “try and make another commotion here” zakiga true colors dina one by one now move out of my way  ya fada cikin tsawa, ta fita da gudu saida ya ga tabar part din ya zauna tareda riko hannun mommy yace “sit my mommy let’s talk. Ibrahim kar ka maida ni Karamar yarinya na san me kake shirin yi, Auren salifa bazan fasa ba ehem. “Mommy mommy mommy”, please ki saurare ni         baso nake ki canja ra’ayin kiba domin nima nawa bazan canja ba kawai mu zauna mu fahimci juna, kinga ba Abinda nake kokarin yi sai cika burin Yaya Ahmed, bazan taba wasa da Abinda yake matukar kauna a duniya ba, nafarko ke nabiyu kuma Naziya, mommy Yaya Ahmed nason ki haka Matar shi, kun Aura mai salifa batareda yana so ba, ranar da ya rasu wasiyyar in Auri Naziya yabari ba salifa ba, mommy akwai alkawarin da Yaya Ahmed yayi a gabana akan Naziya, idan har kika dawo da salifa zaki taimaka min wajen cika mishi wannan Alkawarin, forgive your only son Mommy, Ina kokarin yimiki biyayya ne domin ku Amanar Yaya Ahmed ne a wurina. “Khaleel na dade da sanin akwai raini a tsakanin mu dakai. Zamewa yayi tareda rungume ta ” ba raini a tsakanin uwa da dan ta, sai soyayya da neman Albarka. “Toh in Albarka ta kake nema ka saki yarinyar nan ka zauna da zabin zuciya ta.

“Ita Naziya meye laifin ta?  “Kasan matsala ta akanta bana kaunar hada jini da ita idan ka sake ka Auro Y’ar nan bazakuji dadi naba Khaleel.

Tashi yayi kawai saboda ya lura tayi nisa kamar yanda shima yayi nisan, kuma ba wanda zai kirashi ya dawo baya, wannan Alkawarin zuciyar shine, he is ready for them tundaga kan naziya mai cewa bata Son shi har  fauziya da uwar gayyar. Wucewa yayi kawai yayi dakin shi tareda rufewa gam yayi baccin shi mai dadi, wanda Naziya bata samu ba, ta Kwana kukan Auren ta da shi,  tareda tunanin yanda zasu zauna inuwa daya, yaza’ayi ta Amince ko hannun ta ya rike.

ta kwana Alkawarin yanda zata gasa mai Aya a hannu yanda ba abarta ta rayu da mijin da takeso ba shima bazata yi zaman jin dadi da shiba, mommy kuwa ta Kwana tsara yanda zatayi da Naziya a gidan,

 

 

Washe gari ganin kawai sukayi Ana fitarda tsoffin kayan gefen Ahmed Ana shigo da wasu na yayi masu tsadar gaske da kyau,  fauziya ce ta fito da sauri tana kallon gefen, tasan halin khaleel kamar yunwar cikin ta, wato da gaske yakeyi sai ya kawo wannan yarinyar gidan nan, gidan ta shiga da gudu saboda bakin ciki mommy na zaune tafado falon kamar saukar Aradu, saida mommy ta dafe kirji saboda tsoron da taji, “oh ni Balkisu” Fauziya ki rika tunawa inada hawan jini kirika yin Abu a hankali kar kisa wata rana in zube a banza, “ba damuwa ta bane ni yanzu damuwa ta itace kifito kiga irin uban kayan da khaleel yasa ake sakawa a gidan Ahmed saboda wannan Jakar yarinyar. Tashi mommy tayi tareda cewa wane irin kaya kuma bayan wainda ke ciki ko morar su ba ayi ba?  Dukiyar da muka tara zai narkawa Y’ar talak……., shiru sukayi domin ganin Ana shigo da wasu irin new designer boxes wainda basu dade da fitowa ba wajen saiti uku, sunyi tsaye kamar ruwa yacinye su, kafin ya shigo da wata katuwar Leda a hannun shi, sanye yake cikin kanan kayan nashi na fama,  fuskar shi a sake yace musu suje part din shi a store zasuga wasu set biyu su kwaso su, zama yayi yana murmushi yace “mommy ki ga kayan Auren Naziya kisa Albarka. “Khaleel” zan matukar bata maka rai fiyeda tunanin ka, wannan Y’ar matsiyatan kake kashewa irin wannan Dukiyar haka kana hauka ne?, sannan duk wannan uban kayan way’enda kake cewa a kwaso kuma na uban waye? “Momy ki duba mana Abinda baiyi ba a karo mata. Ya duka tareda bubbude akwatunan, kayane na gani nafada karshen kudi kowane akwati kalar kayan da ke ciki, komai har nighties nasu akwatin daban, gefe daya Wani dan madaidaicin kit ne shakeda sarkokin gold, diamonds Harda tsadaddun passion way’enda sunyi kudin Wani zinarin, sakin baki momy tayi tace “khaleel”, way’ennan kayan ko Fauziya Y’ar gidan Wani ba akai mata irin suba,  don iskanci kasan kayan mata shine kabarni da siyan na fauziya?, ko kwandala baka bayar ba, yanzu akan wannan yarinyar ka narkarda Dukiyar ka haka khaleel? Shiru tayi lokacin da suka shigo da wainnan akwatunan, way’enda ya siyo ma Ahmed da niyyar ya hada a lefe suka boye,  English wears ne masu matukar kyau da tsada da dogayen riguna way’enda har hango yanda zasuyi a jikin ta yakeyi, Wani irin hawaye ne ya ciko idanun shi yana tuna yanda ya yi da yayan shi akan akwatunan, a zuciyar shi yace “Yaya she is going to wear them insha Allah.

Fadan mommy yasa ya dawo daga tunanin shi, “khaleel” ka nuna min ban isa ba ko ka nuna min kai kafi dan uwanka mallakuwa ko? yayi kyau, wallahi zakaga mai zaifaru muddin ka kawo Y’ar nan cikin gidan nan. Ta wuce fuuu. Fauziya ce dake fitar da hawayen bakin ciki ta matso “Allah ya isa tsakani na dakai khaleel , wato akwatin Auren ma da sadaki na duk bakasan zafin suba,  no wonder bakasan mutunci na ba banda wata kima ko daraja a idanun ka…. Wani irin hankada ta yayi baya tareda mikewa ya nuna ta, zaman yan bori tayi har tana dafe kugu, “look ba macen da keda damar fadawa khaleel magana sai mutum biyu daga mommy sai Naziya sune keda Iko da khaleel, thank God kin gane inda hakkin Auren ki yake, that’s hannun mommy so from today don’t ask me your hakki go ask mommy. Ya Kira masu aikin yace su kwashe mai kayan zuwa part din shi, idan masu aikin sa kayan sun gama su sakasu ciki, karku bar wurin domin za’a iya saka musu wuta saboda bakin ciki.

Suka kwashe suka fuce,  yana tsaye, “khaleel” nasan me ka keso dani infita in bar maka gidan ka wataya da Amaryar ka, wallahi yadda baka bani kulawa ba itama bazata samu kulawar ka ba, mu zuba cikin gidan nan. Tayi waje tana kuka,

Girgiza kai yayi tareda cewa “let me shower and go to her, am coming baby, kema zan zo inji kalar naki salon maganar naji na nan ya isa, now is up to you.

 

 

 

A  tsakar gidan suke tana hira dasu Sadiq yau ma ya shigo suna taya inna tsinke zogalen da zatayi musu dambu domin sadiq nason danbu sosai, hirar su sukeyi suna dariya, Malam yayi sallama, tareda khaleel yana cewa “iso Ibrahim kaima dan gidane ai basai ka jira iso na ba. Jin maganar shi baisa ta daina hirar ta ba infact bata ko dago kanta ta kalle shi ba, sanye take cikin doguwar rigar atanfa mai kyau dinkin ya matukar fito da yarintar ta da kyanta, idanun shi akanta suka sauka,  zama yayi gefe tareda gaida Inna, ta amsa ta kwashe zogalen ta ta mike, tabarsu dama ba Shukrah agida tana makaranta,

Malam yace “Sadiq kana cikin mata kuna aiki inka gama kafito muyi magana. Yafada yana fita, yi tayi kamar bata san Allah yayi ruwan tsiyar shi a wurin ba,

Har suka gaisa da Sadiq, taci gaba” ya sadiq kasan Ina son in karanta mass com, saboda aiki a gidan redio ko tv Abun na burgeni sosai. Tafada tana dariya, Wanda ke karawa fuskar ta kyau, da zaka kalli fuskar khaleel da zaka hangota kamar manja saboda ja, “kai haba ai mace tafi mutunci da aikin likita Naziya, ni da badon anyi min kafa ba da tuni na jefaki school of nursing ma. Dariya tasa, wadda saura kiris ta tafi da numfashin khaleel, mikewa yayi tareda fita a zuciye,  ya samu Malam a zaure, “Ibrahim harka fito? “Eh Malam magana zamuyi. “Bismillah Toh. “Nace ba laifi idan yau nadauke ta ta koma gidan mu? “Aa kaida Matar ka ai bawani laifi kawai ko yanzu ka so zaku iya wucewa, bari in fada ma mahaifiyar ta. “Toh zan tafi zuwa dare zan dawo in tafi da ita, ai badamuwa idan ba arakata ba ko? “Babu hakan shine daidai ma tunda ba Auren farko bane, Allah yabaka ikon rike Amanar dan uwan ka tareda sauke dukkan hakkin da ke wuyan ka. “Amin yace, yabi Malam suka koma ciki lokacin ta mike tsaye zata shiga dakinta, bin bayan ta yayi kawai,

Tana shiga taji mutum a bayan ta saida ta zabura, tayi baya kamar zata zube saboda tsorata datayi daganin shi, saurin riko hannun ta yayi domin zata fadi, ya fisgota zuwa jikinshi Wanda saida ta runtse idanun ta kafin tayi saurin ja baya tana fisge hannun ta, jitayi kamar ta warta mai mari, “me yasa zaka tabani?  Ta fada jikin ta na rawa, “oh ba atabaki ne? Ai bansani ba, yafada yana bata Wani irin kallo mai cikeda ma’anoni tun daga sama har kasa.

Saurin bin jikinta tayi da kallo tareda juyawa tana shirin daukar mayafi, yayi saurin matsawa, ” akwai Abinda zan iya yi idan har kika aikata Abinda ke cikin zuciyar ki, ni ba shashashan namiji bane, kina iya tsayawa a gaban Wani banza yanda kike so idan kinganni saiki rika neman Abun rufe jikin ki me kikeso ki boyemin?

“Kaga Ina jin kunyar ka don haka karka bari inbude baki infada maka maganar da bazaka manta daniba. “Say it  am ready to hear. “Kaga kana cin Albarkacin Ahmed shi yasa kake yi mun Abinda kaga dama Ina kyale ka, not anymore, tunda kace zaka wuce gona da iri, karka manta kai kanin mijina ne, matsayin mijin da kake kokarin dorawa kanka zuciya ta bata karba ba ban Amince ba.

 

 

“Hmm first in history, naji mace na deciding yanda zasuyi zaman Aure itada mijinta, yafada yana rike gemun shi cikeda rainin hankali, “husband, yes I am your husband believe it or not, and secondly, ni nake tsara rayuwar da nakeso inyi, inaso kije ki bincika tarihi na kiji bana daukar ra’ayin Wani, I only did what I think is right, ya zakiyi rayuwa me kikeso me zaifaru dake, duk nine zanfada miki yanzu, wannan rufe rufen jikin da kike yi idan naso zan iya hanaki saka ko pant da breziya a cikin gida na, watch out wannan mijin da kike gani bakisan waye shiba, and third, later in the night you are going to my house, enough of all this hira da kikeyi da katon banza, so get ready in time, first in history miji zaizo ya dauki Amaryar shi, ya matsa gab da ita tareda cika mata fuska da hanci da tsadadden kamshin jikinshi ya hura mata iska yayi ficewar shi kamar Wani walkiya,

Ya sumar da ita da kalaman shi, saida ya fita ta zube akasa tana hade jikinta, she can feel his presence up to now, a dakin jikinta kamshin shi duk ya Kama, kalmar shi na ko pant da breziya sai yana ra’ayi zata sa ya tsaya mata arai, lallai tantiri take gani a gaban idanun ta na bugawa a jarida, zata iya rantsuwa kalmar bazata taba futowa daga bakin shi ba, yanda yake behaving like gentle man, now she is mistaken, infact batasan me zai yi nan gaba ba, kallon tsintsiyar hannun ta tayi tanajin nashi haryanzu a nata, Wani irin Yar takeji fiyeda yanda takeji idan Ahmed ya riketa, hannun shi kamar Wanda yake massaging dinshi da baby oil, saboda softness ko ita mace hannun ta baikai nashi laushi ba, she can still feels his heart beat, lokacinda ta fada na second biyar, zuciyar shi bugawa take da mugun karfi. Tashi tayi tareda kwabe kayan jikinta ta zubar akasa, ta datse kofar ta koma zubewa akasa, kallon shape dinta nayi, ta tsaru dakyau jikinta nada tsari da Wani irin kyalli abunka da fara, juyowa tayi ta zubawa tukunyar fulanin ta ido nasan cewa yes Ahmed yayi rashi babba da bai more way’ennan Abubuwan ba, a cike suke tam a girke zaune Alamar bazasu taba kwanciya ba, tashi tayi ta kalle su tasa kuka ” am sorry Ahmed dana sani nabari kayi yanda zakayi dasu da nasan bazaka rayu da ni ba, bazan kasa kai maka hakkin kaba, yanzu tayaya zan iya bawa dan uwan ka kulawa, bazan iya ba kaine ka dace da duk wannan Abun ba kanin kaba, murje idanunta tayi tareda daura kuduri mai girma. Kiran da taji Inna nayi mata yasa ta zabura ta mike, wasu kayan tasa domin ta tsani way’ennan saboda kamshin shi da sukeyi,  ta fita idanun ta sunyi ja. “Toh” Malam yace Anjima zaki tare gashi wannan Karon ko shiri ba’ayiba don haka na Kira yayar ku tace tana zuwa kije ki hada Abun bukatar ki. “Toh” tace kamar zatayi ihu saboda damuwa, gwara zama da mommy sau dubu da zama da khaleel a wurinta, a tunanin ta tagama zama a wannan gidan sai gashi rayuwa takuma juyawa da ita ta bahagon hannu.

 

Tunda yafita gidan su yana barin unguwar yayi tafiya mai nisa yayi parking a gefen titi wajen da ba hayaniyar komai ya Dora kanshi a jikin sitiyarin motar shi, wani irin numfashi yake fitarwa da sauri da sauri, yanajin kamshin turaren wutar da take Amfani dashi akaya, he can feel her chest a nashi har yanzu, runtse idanun shi yayi da karfi yana dukan iska, fauziya tasha rungume shi by mistake bai taba jin haka ba, wani irin racing zuciyar shi keyi, itace mace ta farko da ta fara sashi yaji shi a namiji, bayaso ya nuna mata rayuwar Aure sai yakoya mata sonshi, sai ya cire mata bakin cikin zamanta na baya sai ya bata dukkan farin ciki, so yake yazama bawan mace a Karon farko, Amma sai yayi amfani da nashi salon, “Am sorry Yaya, zuciya batada k’ashi, batada limit, I don’t know when and how?  I think tun ganin ta nafarko yes that’s it, love at first sight.

“But kai take so, bana bakinciki because she love you, zan tayaka bata farin ciki I promise you bazan taba cutar da itaba that’s my promise to you my brother.

Hour guda cur ya kwashe yana tunani a wurin kafin ya wuce ya samu kawun shi yafada mai yau zata tare, yasa Albarka tareda Bashi shawara akan zaman Aure, da kuma akan mahaifiyar shi, sai kayi da gaske, ina fatan kasan halin Hajiya balkisu fiyeda ni yanzu, don haka Allah yabaka ikon sauke duk wani hakki.

Godiya yayi yatafi tareda wucewa gidan,

Bakowa duk sunfita, mommy taje wurin zarah domin neman mafita ita kuma Fauziya tayi gidan su,

 

Tabe bakinshi yayi ya shige  dakinshi ya kwanta yana murmushi, yana hango yanda maganar shi ta sa takoma kamar gunki, “this is just the beginning baby. Tafin hannun shi ya kalla, yana jin kamar har yanzu yana rike da tsintsiyar hannun ta, yasan dole taji yanda yakeji shima, ya dauki lokaci yana tunani kafin yayi bacci mai dadin gaske,

Gefen Naziya kuwa tana zaune batada zabi Shukrah ta zana mata lalle jada baki gefe Aunty Raliya ta shirya mata lafiyayyar kaza tasata ci, zama tayi ta nagi kayarta tasan aikin banza sukeyi kawai yanda Ahmed yatafi haka shima zai gaji ya sallamo ta, ba Abinda zai shiga tsakanin su, sayi sa gama. Haka ta murjeta da dilka tas, zuwa magrib ta yi wanka da ruwan kamshi da yaji hade hade, suka bata sabon kaya ta saka, tayi sallah,

Ta dade a sujudarta tana neman Allah ya taimaketa kar ya bawa duk wani makiyinta sa’a akanta,  bayan isha’i Malam ya shigo gidan ya zaunar da ita tareda yimata nasiha mai ratsa jiki.

“Naziya nasan zakiji a zuciyar ki banyi miki adalci ba, nasan bakya son wannan Auren, kuma nayi matukar mamaki da kike kokarin bujurewa hukunci na, shin kin manta bana yin Abu dakai, kin manta duk Abinda nake nema sai na nemi zabin Allah, na hango miki farin ciki Naziya idan har kin daure kin karbi kaddarar rayuwar ki, kije Kiyi biyayya Albarkar mu tare da Addu’ar mu tana tare dake, Allah yayi miki Albarka. Kuka takeyi kasa kasa hawaye sharkab a idanun ta, Inna ma tayi nata tareda sa ma rayuwar ta Albarka.

Sallamar shi ce tasa Malam ya fito tareda tarar shi cikin murna “sannu Ibrahim ka iso. “Eh Malam. “Toh Hauwa fito da ita ga mijinta, “wani irin nishadi yake jinshi a ciki, tun bayan mutuwar dan uwan shi yau ne yake jin kamar Ana wanke mai zuciya da ruwan madara.

Cikin manyan kaya yake sky blue yard na maza yanada wani kyalli kyalli kana iya hango farar singlet dinshi,  gayen yasan sirrin ado, kuma duk shigar da yayi kyau take mai saboda cikar zatin shi, ko dago kai batayi ba data fito cikin katon hijabi kalar kayan jikinshi, Wanda yana kallon ta yayi murmushi cikin duhun daren, wannan fitinannen kamshin nashi duk ya cika musu tsakar gida,

Inna gaisawa sukayi tace bari insa Shukrah ta kwaso kayanta. “Abar kayan zandawo inkwashe su gobe. Yafada tareda yi musu sallama ya fita, komawa tayi ta rungume Inna tasa kuka, jikinsu duk yayi sanyi, Malam fita yayi yana cewa idan kungama Shukrah ta rakota waje,…….. 🖊

 

 

 

 

*Wacce wainar zamu soya a gidan khaleel my fans, wane irin rayuwa ce zatayi tareda wainnan mutane ukun fauziya momy  and khaleel, meye ra’ayinku akan kudurin Naziya?  Waye zaiyi nasara a wnn tafiya khaleel or Naziya? ” muje zuwa time will tell insha Allah*

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 2⃣7⃣&2⃣8⃣

 

 

 

 

 

…………. Tunda ya dauki hanya take kuka kasa kasa, ta cusa kanta cikin cinyoyin ta, kukan tausayawa kanta takeyi, domin batasan me zata tarar ba idan ta koma cikin wannan gidan. Yana yi yana waigota baice mata tak ba saida ya shiga cikin tangamemen gate din ya parker, kashe motar yayi tareda kallon ta yace “enough munzo gida”, welcome back, ki sauka zanje insiyo miki kazar Amarci, ga part dinki can a bude ki wuce ciki kawai. dago kai tayi hawaye sharkab, “bazan shiga cikin wancan gidan ba” tunfarko ba aso zamana a ciki ba, yanzu ma bazan shiga ba inda nafara zama tun farko a ciki zan zauna. “Gidanki ne you can choose any place, go ahead sai nadawo. Ya ja baya tareda barinta tsaye takasa koda daga kafarta, sakawa takeyi da warwara ta Ina zata fara, Ina ta nufa can inda yace ko ciki ta tarar da Mommy. Juyawa tayi ta nufi hanyar main house, domin da zama da khaleel gwara zama da Mommy a wurinta yanzu.

 

A zaune suke a falon suna jiran me zaifaru domin sun sani tunda yafada ba canjawa, don haka suna jiran isowar ta, Sallama tayi a natse ta sawo kai, suka zubawa kofar ido domin ganin ita da waye, Fauziya Harda leke, sukaga ita kadai ce, mikewa sukayi gaba dayan su suka nufota tareda daka mata tsawa, ” tsaya daga nan mai farar kafa”, wato tsabar kin matsu kidawo cikin daula da kanki kika kawo kanki, Amma wannan yarinyar anyi mayya, to tsaya kiji,  kurwar khaleel ba irin ta Ahmed bane, shi ba karen ki bane da zai rika rawa kina buga mai ganga, tunda sun nace anlika mai, kurwar shi kur yafi karfin ku, wannan naman shi da d’aci don kiji jinin dana bazai shawu miki cikin sauki ba Y’ar gidan malamai.

Shiru tayi saida mommy ta gama tsab ta gaida ita, “momy Ina wuni”. Munafuka da ban wuni ba zaki ganni ba maras zuciya, yoh Ina zakiyi zuciya kina kwadayin a/c gidan Malam nakan buzu babu. Fauziya ce ta matso gaban ta tana huci “jaka akuya” in banda kina dakikiya ina ke Ina my Khaleel kema kinsan na wuce da Ajinki bare inyi kishi dake baki isa in hada miji dake ba.

Wani irin tafasa zuciyar ta takeyi, don haka saida ta gyara tsayuwar ta tace “Ai  Akuya nada rana domin akan yanka naman ta aci haka jaki ma domin yakan dauki kaya ko banza kinga shima yanada rana, Amma mutum mai kwakwalwar kifi shine Wanda baisan darajar dan Adam ba, dake mace ce mai daraja bazaki tsaya kina zagin iyayen wani ba, kuma Alhamdulillahi duk rashi da talaucin mu baki gan mu kofar gidan ku muna barar Abinci ba, sannan mijinki dakike magana dashi da rashin shi duk daya a wurina,  ni da zaki taimaka min da kinsa ya maida ni inda ya dauko ni yafimin kwanciyar hankali, kuma dake kin kai mace da kin taimaka tunfarko kin hana Auren nan, da banda masoyiya sama dake.

Wani irin daga hannu tayi zata zabga mata Mari taji anrike hannun ta carab, saurin juyowa tayi idanun ta a rufe ko gani batayi tace ” mommy kibarni in daki Y’ar gidan talakawan nan ba kyajin mugayen kalaman datake fadamin ni sa’arta ce.

Jin an watsar da ita a gefe yasa ta dawo cikin hayyacin ta, ta ganshi tsaye fuskar shi ba fara’a, yace “I know you will react like lunatic, shi yasa na dawo, kuma ki godewa Allah da hannun ki yakai fuskar ta yau da sai kin kwana gidan ubanki, tunda bada kudin gwamnati muka gina gidan mu ba.

 

“Khaleel banson dibar Albarka agabana kake tarewa wannan yarinyar fada, me kakeson nuna mana ne, tafimu mutunci da daraja kenan, Toh ahir dinka dani wallahi zanyi maganin ka da duk Wanda ya daure ma gindi ka kwaso min wannan yarinyar cikin gidana. “Mommy me tayi daga shigowar ta kuma agaban idanun ki take kokarin marar min mata, wallahi da abakin wanna igiyar da kuka daura mara Amfani yau. Baki dukansu suka saki sunkasa furta komai, ya juya gefen ta” kema bakyaji na nuna miki part dinki inda bamai damunki kin shigo nan, kinga bazan iya tare miki fada kullum ba let go to your part.  Matsawa tayi tana tura baki ni anan zan zauna bana son can. “OK as you wish, ya riko hannun ta ya nufi hanyar dakin shi da ita tana kokarin kwacewa, Amma karyarta domin ta riku, har wani hadota yayi da gefen shi ya wuce da ita cikin dakin tareda kulle kofar yabarsu a sume, suna shiga ta fisge tareda nunashi “karka kuma kokarin tabani banaso. “Ni kuma inason tabaki kuma bake zaki yanke wannan hukuncin ba nine zan yanke hakan ko Ina bukatar tabaki ko banayi nine zan zartar da hakan.

Juyawa tayi domin ta fita yayi saurin shan gaban ta ya rufe kofar da key ya cire yayi gaba Abin shi, “kazo ka budeni intafi dakina. “Excuse me? Kinada wani daki ne bayan wannan da kuma gidan da kikaki shiga? “Yes dakin mijina da na saba zama. Dawowa yayi da sauri gaban ta, ta zuba mai ido shima cikin kwayar idanun ta yake kallo tareda dage gira daya, “repeat that”, “say it again, yanzu in nuna miki am your husband and believe me zakisha mamaki na. Ja da baya tayi kadan, “nifa bazan Kwana daki daya dakai ba. “OK zamu gani yau, ni kuma bazan Kwana ni kadai ba as far as you are my wife, muje zuwa inga who will win. Kallon dakin takeyi tana tunanin lokacin da ta shigo cikin shi suka zauna akan gadon yana shayar da ita kalamai masu dadin gaske, namiji Dan soyayya yayi a rayuwa, she is missing him so much waye zai maye mata wannan gurbin?  Har wani tsigar jikin ta ke tashi idan tana tuna lokacin da yake taba ta.

 

Kallon gadon tayi taga ba Wanda ta sani bane, karewa dakin kallo takeyi yanzu take realizing an canja komai new, jin motsin shi yasa tayi saurin juyowa, tagan shi yana kwabe kayan jikin shi tayi saurin bashi baya tareda cewa “ai dama bakajin kunyar yawo tsirara a cikin mutane” ka girma bakasan ka girma ba. Bai tanka taba saida ya cire duk manyan kayan yarage dagashi sai boxer, ya fito ainihin namijin shi, tsarin jikin shi a bayyane kirar shi broad chest din shi murdadden hannun shi irin na ainihin maza naturally, Wanda duk macen da ta kalle shi sai ta afka mai lokaci daya, shiyasa fauziya takasa hakura dashi har gobe tana mafarkin kwanciya a wannan kyakkyawan jikin har safe,

Matsowa yayi tareda dafe west dinshi ya zo har gaban ta, zare idanun ta tayi tareda saurin runtsewa bayan ta mai kallo daya tana girgiza kai “wai kai meye haka kakeyi baka kojin kunya”?

Wani irin mugun murmushi yayi, that’s exactly what he is looking for a wurin mace me kunya, and its going to be so much fun, domin duk namijin da ya Auri mace mai kunya zai mori kuruciya da rayuwa mai cikeda nishadi,  “open your eyes or…..

Ja baya tayi tareda girgiza kai “kaga don Allah kasa kaya kuma ni kabarni intafi part din da kace. “You are late, now listing to me, open your eyes ko in cire boxer din and believe me kema sai kinyi necked irin nawa mun tsaya aga Wanda yafi kyau ba kaya. Da mugun gudu ta bude idanun ta tareda kallon shi cikin ido way’enda ba duk mace ke iya resisting kallon cikin suba, but sunfi mata saukin kallo akan jikin shi, ita da Ahmed bai taba mata irin haka ba Amma wannan marar kunyar Hmmm.

 

“What did you said?  Bana girma?  Yafada yana matsowa tareda yin murmushin gefen baki, irin na muguntar nan, da kuma enjoying each and every moment with her. Tana ja da baya har ta cimma kofar bathroom dinshi ta manne yana biye. Saida yaje gab ya kalli kofar, “just say it ba sai kin jan yo ni da wayau ba. “What?  Tafada tana zare idanun ta domin yafi karfin duk wani tunani da zatayi,

“Kice wanka kikeso muyi tare final, and bazan taba baki kunya ba, duk Abinda kike so just tell me yanzu zanyi miki shi.

“Kaga nidai ka matsa ba wani wanka da zanyi don Allah ka matsa in wuce. “Zuwa Ina?  Kinga dole cikin biyu ayi daya yanzu zanbaki zabi biyu kuma you must choose one if not today am going to loose my virginity. Yafada tareda dage mata gira daya, dan kallon shi tayi tareda Kara maimaita kalmar domin Sam bata kamo bakin zaren ba ita, “yes zaki koyar dani komai and believe me this your student can last more than two hours batareda ya gaji ba I promise, do you know ban taba yiba? please ki koyar dani ki bari inji ya Abun yake nima. Wani irin zubewa tayi tareda fita ta o c dinshi saboda tsorata, gaskiya khaleel tantiri ne, sai yanzu duk ta kamo bakin zaren ta kulla, innalillahi wallahi mugun dan iska ne. Kara biyota yayi jikin ta na rawa ya Kama hijabin ta ba tareda ta ankare ba ta jishi a kasa, Y’ar Kara tasa “don Allah kabari meye haka khaleeeel’ taja sunan da sai da ya bata wani irin kallo ya matso tareda riko kugunta ya zuba mata ido har wani irin ruwa ruwa idanun shi suka tara, bai taba sanin zai iya bawa mace so much time ba sai yau, kuma he don’t mind sukai safiya suna haka, “please call my name again please. Yanda ya kwantar da muryar shi tareda kashe ta yasa batasan lokacin da idanun ta suka shige cikin nashi ba, tana hango  way’ennan ruwan da suka karawa idon wani irin sirri Wanda bazata iya fadar shi ba. Hannun shi a west dinta kuwa jinshi takeyi kamar yana jonata da wutar lantarki, kai tsaye batareda yayiwa idanun shi shamaki ba ya saukesu akan kirjinta, rigar atanfar ta kamata sosai dinkin ya turosu har yana hango tudun su da tsagun kirjin ta tasama,

Hannun shi dake west dinta yakara damkar ta domin neman comfort, don jiyake tsab zai iya zubewa idan yaci gaba da kallon ta a haka, bai taba tunanin nonon mace zai burgeshi ba sai yau, “Hmm Hmm Hmm. Ya jera Ajiyar zuciya yafi sau goma, just don yana kokarin controlling kanshi he don’t want to rushed things, karya tsorata ta yasan shi ba irin Ahmed bane in yayi mata wani Abu zata iya gudun shi fiyeda tunani,

Matsawa yayi tareda rungume ta gam a kirjin shi, takasa koda motsi domin jikinshi na dauke da wani irin sirri ga dumi kamar heater Wanda batasan tsabar shaukin ta bane yasa ya dauki zafi,

Ajiyar zuciya yakeyi yana Kara shige mata, sai shafo bayanta yakeyi ji yake kamar ya tsaga jikin shi ya turata, ganin Rungumar taki karewa tayi saurin fisge jikin ta, bai tsaya wani dogon tunani ba yayi bathroom, ya saki shower akan shi,  shafo fuskar shi yayi, duk da ruwa na zuba a fuskar shi he can still feels his tears, yana tunanin wane irin so yakewa wannan yarinyar, komai nata is special to him, kamar aikin asiri jinta yakeyi kamar Rayuwar shi,  ya dauki dogon lokaci kafin ya iya wanka ya fito, tana nan inda ya barta a d’askare, “kije kiyi wanka ki fito ki kumayi Alwala Ina jiranki.

tasan musu tsakanin ta dashi bazaiyi riba ba gwara tabi a hankali ta tsira da mutuncin ta. Wucewa tayi saida ta kulle bathroom din, sauri yayi ya zura jallabiya ya fita zuwa part dinshi,  kallon bathroom din shi takeyi tana ganin yanda ya Kawata shi hatta da kayan shafe shafen shi a ciki suke  kamar wani mace komai nashi tsab tsab. Kwabewa tayi tayi wanka tareda saurin daukar towel ta goge jikin ta jin yana taba kofar yasa tayi saurin zura rigarta tareda mayarda skirt ba tare da ta saka Inner wears ba,  ta fito tana kame kame domin jinta takeyi kamar nicked dole zata samu excuse takoma domin ta saka.

 

Zuba mata ido yayi ya ce “zo ga kayanki tunda nan kika zaba mu zauna, gashi na dakko miki wasu kayan,   you’re Mrs khaleel ya zaki mai maita kaya?

Bude Karamar akwatin yayi da ya debo kaya a ciki, wata guntuwar rigar bacci iya guiwa pink mai guda biyu ya mika mata yace kisa wannan za kiyi kyau a ciki,

Zare idanun ta tayi tana girgiza kai, “ni basai na sakaba”. Tashi yayi ya nufota  yes basai kin wahala ba am here madam. Saurin fisgewa tayi ta koma bathroom din da sauri.

Sai dai Abin haushi bra dinta ta tarar ta fadi kasa harta dan jike dafe goshi tayi ta dauraye ta shaya akan karfen da ake rataye towels da sauran su, ta zura kayan tareda tsayawa gaban mirror ta zubawa kanta ido, kamar wata Y’ar India, kirjinta dake baje ta kalla tana hango dan karamin nipple dinta, saboda silk ne kayan sunbi sun lafe a jikinta,  jan ta saman tayi  domin ta dan rufe su, duk da haka ana gani, saida ya k’onkwasa kofar yace “madam am waiting for you” ta turo kofar ta fito bai kalleta ba domin yasan kwanan zancen don haka hijabin ta ya mika mata tareda shinfida dadduma biyu ya tada musu da sallah, raka’a biyu yayi tareda yin Addu’oi masu tsawo ya juyo ya dafa kanta tareda yin Addu’a ya tofa, bai tsaya dogon tanbaya ba domin yasan daga Ina tafito inba ayi wasa ba ma ta koyar dashi,.

Ajiyar zuciya  yayi “Madam nasan kinsan komai akan gidan nan” banaso ki yi rayuwar da kikayi a baya, shiyasa naso ki zauna a can part din, ba damuwa Ina nan,

But ni yanzu kinja nakasa fita siyo mana kazar Amarci kuma yunwa nakeji. Yafada yana kallon ta, “zaki iya nema min wani Abu inci please? na dade banci Abinci ba, please Ya kuma fada yana karkace kai, mike wa kawai tayi ba tare da ta ce mai komai ba ta fita da hijabin ta, ba kowa a falon ta wuce kitchen tunda tasan komai na gidan, tasan ka’idar Abincin shi, don haka indomie ta fitoda guda biyu kana na ta dan jajjaga tarugu da tattasai da tumatur daya ta dora a gas kafin ta yanka enough albasa ta soya mai kwai guda biyu,

In ten minutes ta kammala, ta dafo mai ruwan zafi mai hadi yana kamshi,  ta jera a tray ta dauka ta nufi dakin.

Yana zaune tsakiyar gadon yana danna laptop dinshi, fuskar shi kawai zata isar maka da sakon dake cikin zuciyar shi, a kasan gadon ta Ajiye mai  tace gashi. Dago kai yayi tareda zuba mata ido yace “tank you. Ya kife laptop din ya zare jallabiyar ya jefa mata, “ki fara kula da komai na mijinki daga yau. Harara ta watsa mai tareda matsawa ta bude waldrp domin ta Ajiye taga ba wurin da KO tsinke zai shiga, ta kuma bude wani side taga agogunan shi birjik kamar wani kantin agogo ta Kara bude wani taga guntayen kayan shi birjik duk yana kallon ta saida ta bude na karshen ne taga jallabiyun,, zata Ajiye yace “kisa a Dustin a bathroom bana mai maita kaya. “Tun farko me yasa baka fada ba kana kallo na saboda kawai baka kaunar in huta. “No inason kisan komai na mijinki ne, Kinada damar da zaki duba komai a dakin, dan murguda baki tayi Wanda yaganta sarai saida ya zauna ya bude plate yafaraci tareda runtse idanun shi komai nata is perfect, fitowa tayi ta nufi sofa ta kwanta tareda bashi baya, “kizo muci mana. “Banajin yunwa ni. “Hmm yace, yaci gaba da cin Abincin shi.

Bacci ne mai shegen dadi ya kwashe ta, saida yaci yayi kat ya kora da black tea, ya kwashe kayan ya mayar kitchen da kanshi ya dawo ya datse kofar, tsayuwa yayi akanta ya zuba mata ido, yayi murmushi, dukawa yayi yayi sama da ita kamar Y’ar tsana, a natse ya shinfideta a tsakiyar gadon, ya zare hijabin ya Ajiye shi agefe,   juyowa yayi domin ya gyara mata kwanciyar ta yayi kyakkyawan gani, “subuhanallah ya furta, domin rigar saman ta bude he can see them clearly, yanda suke baje so boosty kamar zasu fashe, Allah yagani shi baiyi niyyar rushing dinta ba Amma seeing this he can’t control himself, wani irin shaking jikinshi keyi ba wani tunani ya kife but hannayen shi akansu tun daga kasan su har zuwa saman yana wani irin lallashin su tareda murzawa a natse kamar wani barawon dake tsoron kar akamashi,

Jin kanshi yakeyi a wata duniya tadaban bai taba sanin haka nonon mace keda dadin tabawa ba sai yau, wani irin tashi jijiyoyin kanshi sukayi rado rado jikinshi har wani fitarda gumi yake duk da sanyin ac dake dakin, kamar kanshi zai tsage biyu yakeji wani irin murza jikinshi yakeyi a katifar gadon, ya rasa inda zai tsoma ranshi yaji sauki,  matsawa yayi yana mai kallon kyawawan lips dinta idanun shi sunyi mugun ja da cika da ruwan hawayen shauki, batareda ya cire hannayen shi a saman kirjin nataba ya matsa da lips dinshi saman fuskar ta saida ya lashi girar ta zuwa idanunta har karan hancinta kafin ya sakko zuwa bakinta cikin shakakiyar murya yace “ke ce mace ta farko da khaleel yafara tabawa duk da ke bani ne nafarkon ki ba, ke ce macen da nakeso infara kissing, yafada yana dora lips dinshi a bakinta, yafara lasa a hankali, abun mamaki jiyayi ta bude bakinta, Wanda da gudun vespa ya zura harshen shi, tayi mai mugun cafka tareda bashi wani irin tsotsa Wanda na tabbata idan idanun ta biyu bazai yuwu ba, Wanda ita a duniyar mafarki take ganin Ahmed ya kai ga burin shi na taba kirjinta tareda yin yanda yaga dama dasu har ya iso kan harshen ta yana cewa tayi mai kiss karta hanashi daga yau bazai kuma tanbayar taba, don haka ta zage ta dage ta ke bawa khaleel wani irin mahaukacin kiss Wanda ta kusa sumar dashi, Abunka da ba sabanba kuma yasamu mace karshen kwadayin namiji zabin zuciyar shi me kuke tunani.

Saukar hawayen shi akan fuskar ta tareda yanda yake dage rigarta zuwa sama bear hand dinshi na shafa fatar cikinta, har zuwa lokacin da taji saukar hannun shi a necked Brest dinta yasa tayi saurin dawowa daga duniyar mafarkin ta Wanda yake a reality ba tareda sanin taba, bude idanun ta tareda jin bakinshi cikin nata tanajin zafin yanda yake matsa mata kirji wani irin allan kafura tayi ta fisge kanta tareda mirginawa kasa tana zare idanun ta tareda jan rigarta tana rufe jikinta, ko Ina rawa yakeyi a jikinta,

Shikuwa wani irin juyi yayi ya kife kanshi a katifa domin dole yayi doguwar jinya, kamar katifar ta bude yakeji domin yanda yake soka jikin shi a kai, fadin halin da yake ciki shikadai yasani, saida ya kwashi minti talatin kafin ya juyo yaganta a tsaye tana kallon shi tana fitar da hawaye,

Tashi yayi cikin karfin hali ya nufota tayi baya tareda zubewa a kan sofa ta hade jikinta wuri daya tana girgiza mai kai.

Zama yayi a gefenta ya dafe kasan shi da hannun shi gudun karya yage mai wando yace “kuka? Why zakiyi kuka? Dagowa tayi cikin zafi “me yasa zaka tabani bayan kasan kai kanin mijina ne kuma ba wanna rayuwar a tsakanin mu Ahmed shine mai Iko da wannan bakai ba, why zaka wuce gonar da bataka ba. Wani irin d’aci yaji  a ranshi, ya kalleta ” listing to me, Ina fatan wannan kalmar tazamo ta farko ta karshe daga yau, Ahmed is my brother and I love him so much shiyasa har na iya kyaleki bayan kinfada min wannan kalmar, Amma ki sani baki isa kiyi min iyaka da hakkina ba Aure mukayi sadaki nabiya a gidana kike a cikin dakina, niba raggon namiji bane am healthy what do you expect from me, insa miki ido saboda gani lusarin namiji, now listing bazan iya bacci a haka ba bantaba sawa kaina kwadayin kwanciya da wata ya mace ba sai ke yanzu cikin biyu za ayi daya kibarni inci gaba da Abinda nafara ko in ratsa cinyoyinki wallahi kuma believe me nafi karfin ten minutes yanzu dabara tarage gareki.

Wani irin girgiza kai takeyi “don Allah kayi hakuri kabarni nibana so. “Ni kuma kiyi hakuri kibarni in karasa jin dadina, kuma kisaba tunyanzu wannan somin tabi ne domin ba yanda za’ayi inzauna dake a cikin gida daya in sa miki ido ba, bayan nasan ke wacece naji dadin ki bazan iya nesa dake ba am sorry……… 🖊

 

 

 

 

 

 

*Afuwan jiki da jini Alhamdulillah Ina samun sauki saidai, ko yanzu saboda banason inbarku da jira yasa na daure na dage nake typing a hankali, zan rikayin koda page daya daya ne har zuwa in murmure, aci gaba da yanda aka saba, masoya nagode da Addu’a masu Kira da masu turomin sakonni Ina matukar godiya am feeling better now*

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 2⃣9⃣&3⃣0⃣

 

 

*Aslm Masoya Ina matukar baku hakurin jina Shiru da kukayi saboda jinyar da nayi, Amma Alhamdulillah yanzu nafara warware wa kuma da izinin ubangiji koba yawa kullum zaku rika samun koda page daya duk ranarda nakeji na dai dai banyi Alkawarin kullum ba saboda yanayin da nake ciki, wainda sukayi min magana a wtsp kota waya ba amsa kuyimin uzuri ku fahimce ni yanzu haka sakonnin ku* *bansan ta Ina zanfara budesu ba, kuma don Allah ga number waya duk mai bukatar littafin nan ku tuntubi wainnan numbobin saboda bana son kiran wayar yana mun yawa 08032252760*

*08175479641 kutun tubi wainnan domin biya da kuma adding agrp nagode*

 

 

 

 

……………Kara hade jikinta takeyi jitake kamar tayi tsuntsuwa ta bar dakin,  saboda tsorata dashi da tayi,  Al amarin khaleel yafi karfin tunanin ta,  jitayi kawai ya janyo hannun ta ya fisgota tsakiyar cinyoyin shi, matseta yayi gam, tanajin yanda yake tsikarin ta da Abu mai shegen tauri kamar rodi, zagaye west dinta yayi yana mai dora fuskar shi saman wuyan ta, cikin wata irin murya yace, “are feeling my hardness? Umm am so so honey, all because of you baby. Jikinta mugun tsuma yakeyi yau tana ganin Rayuwar da bata tabaji ko gani ba, khaleel  is shameless, jin yana zame rigar saman yasa tayi saurin riko hannun shi, “don Allah kabarmin Rigata. “Kinsan musu won’t solve any problem? Just wait.  Yana cirewa ya  wurgar tareda saka hannu zai zame ta cikin, Abu daya ta fahimta dashi musunta ba Abinda zai hanashi don haka ta runtse idanun ta tareda sallama mai ragamar rayuwar ta taga iya gudun Ruwan shi.

 

“Oh my goodness, oh oh baby look at your bobby’s, jikin shi narawa yayi sama da hannun shi, ba wani jan Aji ko jira ya fara shafo nippy  dinta y’an kanana jajaye dasu ga kirjin a mulmule gwanin sha’awa, yarasa Ina zai saka wainnan beautiful creatures din,  “they are mine baby you are mine my wife, oh god. Dagata yayi cak zuwa gado Wanda sai yanzu ta bude idanun ta tareda  sallama mai ragamar rayuwar ta baki daya, ya mugun rikice mata murzasu yakeyi kamar bazai kuma ganin suba, gaba daya ya jika mata kirji da ruwan hawayen shi, baifi  minti talatin ba yasamu relief ta hanyar wanketa da wasu irin fitinannun ruwan shi masu dan banzan yawa, rungume ta yayi tsam tareda yi kamar zai tsage jikinta ya shige, first experience a rayuwar shi ana cewa ba maza virgin, shidai Allah yagani ko release zaiyi saidai cikin bacci yatashi yaganshi a jike, bai taba sha’awar kwanciya da wata y’a mace  ba all his life sai akan Naziya, yaji yes he is a man, duk da yaso ya fi haka lasting never mind next time.

Hawayen ta yake bi da kallo tareda karewa kyakkyawar fuskar ta kallo, soyayyar ta is something else a zuciyar shi, before feeling din daban ne but now al amarin ya Kara girma a zuciyar shi, hannu yasa tareda matsawa dakyau yana fuskantar ta, share hawayen yayi a zuciyar yace “bazaki kuma kuka because of me ba, I promise to make you happy ba kuka a rayuwar Aure na dake, bakisan matsayin kiba a zuciya ta, you mean the world to me.

Yana kallon ta har bacci mai nauyi ya dauketa, zuciyar ta na sama da    kasa, farar fatar ta ya zubawa ido, yana kallon yanda ya rufe mata kirji da blanket   so yake ya Kara kallon su Amma yasan zai hanata bacci don haka ya danne tareda   matsawa jikin ta ya rungume ta, batareda ya shirya ba bacci mai shegen dadi ya tafi dashi domin bayason yayi missing single moment atareda ita,  shi ba mutum bane mai son datti Amma what he is feeling a tareda ita bazai bari ya tashi ba.

 

Wanda a wannan daren yayi wa su momy mugun tsawo fauziya tayi kuka kamar zata mutu saboda bakin ciki domin khaleel ya gama nuna mata ita batada value a rayuwar shi, momy kuwa ba kukan da takeyi sai na za agurbata mata zuri’a da jinin talaka, kuma bazata taba Y’ar da da hakan ba,

 

Bacci sukayi mai dadin gaske Wanda khaleel zai iya cewa bai taba bacci mai cikeda dadi a rayuwar shiba, so much relief and comfortable,  bugun kofar da akeyi ne yafarkar dasu a firgice, domin bugun bana hankali bane, tashi sukayi a firgice har suna gware goshin juna, tayi saurin juya mai baya tareda kame blanket din gam tana mai tuna Abinda yafaru jiya, zaro idanun ta tayi “did he really do it? Or what, Tafada tana shafo kasanta taji pant dinta na nan Amma Abinda ya faru tsakanin ta dashi bazai taba bari ta iya hada ido dashi ba, binta yakeyi da kallo kafin a kuma buga kofar tareda kwala mai Kira, “khaleel kabude kofar nan ko inbata maka rai. Yaji muryar momy na fada, durowa yayi batareda ya bata lokaci ba ya   nufi kofa, budewa yayi dama shi badamuwar shibane aganshi a kana nan kaya, danno kofar sukayi yana budewa, fauziya ce da momy suka fado, Wanda Naziya kamar ta nutse akasa saboda kunya da kuma halin da take ciki.

Ja yayi tareda saka hannu ya rike haba yana jiran yaga me zasuyi,   fauziya ce ta kalle ta cikeda bakin ciki, “kedai anyi mara kunya a rayuwa, ki Auri yaya  kidawo ki Auri  kani ki iya kwanciya dasu saboda rashin ta ido. Ji tayi kamar ta shige kasa saboda kunya da takaici wani irin girgiza kai takeyi tareda jan blanket din tana kudun dunewa, kallon shi momy takeyi cikeda tuhuma” khaleel me nake shirin gani?  Baka bawa uwar gidan ka kulawa ba kafara da Amarya,  yaushe ka canja haka saboda mace, Ina ce kaki yarda har yau ka kula fauziya, ita wannan Zuma ta zuba anata da tana zuwa ka hauke ma?  Ke kuma tashi ingani munafuka, shine farko ko kinbi wani a waje aka likama d’ana. Tafada tana nufo gadon, ganin Abun nasu bamai karewa bane yasa ya matso kusa da su duka ya kalleta tana kuka tareda dunkulewa a gadon, “Momy ku fita muyi wanka kunga ko sallah bamuyi ba mun makara idan muka shirya zamu fito mu amsa duk tanbayoyin ku. Ya kalli fauziya fuskar shi a hade “you Ina tunanin Saina saki akan hanyar da ta dace zaki dawo cikin hayyacin ki kina wuce gona da iri  kibini a hankali. Kuka tasa tareda cewa “khaleel ban yafe hakkina daka danne min ba yanzu kiri kiri kaki kusan tata kusan wata nawa Ina gidanka daga kawota har ka shige mata, Allah sai ya sakamin. Matsawa yayi cikin zafi ” kina kiran wata mara kunya, bayan kece babbar mara kunyar kina maganar namiji ya kwanta dake bako kunya agaban mahaifiyata  kina matsayin budurwa, Toh bana ra’ayi idan kin gaji da Ajiya ki jika kisha kayanki am not interested, ba kida hakki atare dani bazan taba bawa zuciya ta Abinda bata ra’ayiba, now get lost. Ya nuna mata hanyar waje, tafita da gudu tana kuka momy ta kalle shi “kayi kafito we need to talk.  Tafita a hasale,  ya mayarda kofar    ya rufe tareda girgiza kai yayi bathroom cikin sauri ko kallon ta baiyi ba saboda lokaci yatafi sosai kusan karfe bakwai na safe,

Ganin ya shige yasa ta zabura ta janyo katon hijabin ta ta zura, takoma gefe da da hali yakama ta tabar dakin nan Amma su momy tasan suna falon bazata iya hada ido dasu ba domin takai karshen jin kunya, bai wani dauki dogon lokaci ba ya fito tareda matsawa ya Y’arfa mata ruwan hannun shi yana fitar da wani irin murmushi mai cikeda nishadi, “jekiyi wanka your water is ready. Kanta akasa ta mike bata ko kalle shi ba ta wuce Abinta, saida ta datse kofar ta kwabe yana mai binta da kallo “Hmmm zaki daina wannan boye boyen ne soon domin zan mugun cutuwa babe. Yafada yana murmushi. Saida ya tsane jikinshi ya ciro wata dakakkiyar shadda Y’ar gaske fara,

 

Ya baza kamshi tareda tayarda sallah, lokacin da tafito fitinannen kamshin shine yasa ta kalle shi a kai kaice, gayen akwai son kamshi sai buhun rashin kunya jarababbe. Samun kanta tayi da zuba mai ido tana tuno kalmar Naziya na haryau yakasa taba ta, to ita me yasa yayi saurin shige mata?  Jin  yana hura mata iska a fuskar ta yasa tayi saurin zabura tabar wurin tareda nufar dadduma ta tada sallah. “Hmmm tun yanzu kinfara tunani na haka?  Idan nayi megaba daya bazaki kuma iya nisa dani ba kenan, wow khaleel, you are great. Yafada cikeda tsokana tana jinshi,

Akwatin da ya shigo dashi ya bude ya ciro wata Atamfa dinkin ya dunku ga atamfar yi matukar yin kyau fara da blue mai dauke da manyan patterns, pant kawai ya fito dashi sabo dal ya Ajiye akan kayan, tana idarwa ta mike tareda nade sallayar ta ki juyowa. “Kizo ki shirya kafin su momy su kuma shigowa su ganki ba kaya. Kallon jikin ta tayi domin katon hijabin ta ne da kuma towel kawai wato yasan ba komai a jikinta.

 

Matsowa yayi ya Ajiye mata kayan tareda cewa “bana son bra this is enough, Yafada yana kallon kirjinta datake karesu da hannu, “dake mai wayau ce bazaki sha wahalar mallake niba domin Abu biyu da kikeda shi, find out urself ya fice yana murmushi, tabishi da kallo, yadaina bata mamaki yanzu saidai ta bishi da ido.

Falon ya fita yasamu fauziya tayi kaca kaca da kuka agaban momy, yana fitowa ya daka mata tsawa” ke lafiya kike mayar mana da gida kamar gidan makoki?

Harar shi momy tayi, ya zauna tareda dafata “good morning momy na. Yafada cikeda fara’a da nishadi fuskar shi na wani irin fitarda Annuri.

“Khaleel yanzu nagano komai wato son Matar dan uwan ka kakeyi tuntuni ko saboda rashin ta ido ace jiya ta tare har ka hauke mata sai kace Wanda ke matse to kaji mezan fada maka, “yanda banyarda Ahmed ya cakuda min iri da wannan yarinyar ba kaima bazaka hadamin iri da ita ba    kajini da kyau, idan ma kafara kusantar yarinyar nan Toh ni zan karkado duk wani kwai naka kuma yazama nafarko na karshe inka kuma kusantar ta ban yafe maka ba,  kallon momy yakeyi kawai baice uffan ba, yana tunani a zuciyar shi, idan har Naziya Matar shice Indai bai kusance taba sai dai in bai samu dama bane Amma duk duniyar ba Wanda ya isa yasamai katangar karfe atsakanin shi da ita, wani irin tashi yakeji tsigar jikin shi nayi saboda zancen kusanci da momy tayi “wow ya zata kasance how is he going to feels?  Duk gashin dake jikin shi ya mike tuni yasawa zuciyar shi kwadayin son jin ya Abun yake, nono want  solve any problem today, “khaleel kanajina kuwa?  Ina magana kanamin kunnen uwar shegu? “Momy copy that….. Yafada sauran kalmar na makale mai a baki ganin yanda tafito tana taku cikin natsuwa tuni ta dauke sauran hankalin shi  tayi matukar haduwa a atamfar ga shi koya tasa atamfa fitowa take as Matar bahaushe Y’ar arewa Wanda kowa yasan wankan atamfa awurin mace yafi kowane mutunci da daraja. A kirjin idanun shi suka dire, bayajin zai iya Kara hour guda batareda ya kuma makaleta ba, she is too much, saboda batasa bra ba kirjin suka Kara bayyana a breast cup din miss perfect, Yafada cikin zuciyar shi.

Binta sukayi da kallo har fauziya, wani irin mugun kishin yarinyar takeji ita tasan da salifa ya Aura bazata damu ba Amma wanna yarinyar, ta wuce da Ajin su kosunki ko sun so Y’ar talaka ce Amma jikinta yafi Kama dana Y’ar gidan sarauta fatar ta Sam bazata nuna maka rayuwar Vaseline takeyi ba da kuma zafin rana sai inuwar mangwaro, kosu basu kaita tsarin jiki da kyau ba, ba karya yarinyar ta hadu, jitake kamar ta watsawa fuskar nan acid adaina ganin kyanta,

 

“Gwara da kika fito zonan. Momy tafada cikeda hasala tareda kwalawa mai aiki Kira, kan naziya akasa ta matsa tareda dukawa agaban su ta gaida momy” Ina Kwana Momy. “Toh munafuka mayya mai siffar mayu, idan har kin cinye min kurwar Ahmed ta khaleel bazata lasu miki ba muzuba, ke kawomin ruwan gishirin da nace miki.  tafadawa mai aiki. Wanda lokacin yadawo hayyacin shi domin ganin Mezai faru, mika mata cup maid tayi tace “ungo shanye shi idan har jini na ya shiga jikin ki yau sai yafito Ana so aci gado ko to bada Dukiyar gidan nan ba, karba tayi jikin ta narawa yayi saurin mikewa ya buge cup din tareda riko hannun ta idanun shi a waje “idan naji ko amafarki kinsha wani Abu domin ki wanke min ciki wallahi bazakiji dadi naba zan nuna miki other side din khaleel now wuce ki koma part din da nace miki tunfarko domin bazan lamunci hasara ba enough of all this drama banason damuwa. Jikinta narawa tace juya ta fita jikinta na juyawa kamar da gay ya,  dama dama take nema tasamu zata tsere bazata kuma shigowa cikiba shima bazai kuma ganin ta a dakin shiba.. Kuka momy tasa na bakin ciki “wato nidai ban isaba ko khaleel kai bazaka taba yimin biyayya kamar dan uwan kaba Allah sarki yarona Ahmed Allah ya gafarta maka. “Amen Amen momy Yafada tareda kallon fauziya da tuni ta daina kuka ta buga tagumi domin fadan yafi karfin tunanin ta. Takasa gano manufar khaleel da ita a gidan nan.

“Ke kuma tashi ki koma naki gidan koda yaushe bakida aiki sai tasa ta gaba kina kuka zoki wuce indaina ganin ki anan. Yafada yana nuna mata hanyar waje. “Kaida zakaje aiki nidai nan yafimin dadin zama tunda gidan nawa mijin ma baisan hanyar shiba. “Ba inda zanje nadauki hutun Amarci domin soon zaki karbi mijin domin zan raba muku girki idan tayi nata days din zandawo gareki, shikenan?  Yafada yana tanbayar ta, ” haba khaleel nice fa uwar gidan yazaka fara da dakinta nidai banyar daba. ” OK tunda zabi nabaki zangani, momy ai dai nayi kokari tunda zanbawa kowa hakkin ta? Tashi tayi tabasu wuri saboda bakin ciki tama kasa magana, dakinta ta nufa tareda daukar waya tafara kiran zarah, tana dauka tasa kuka” zarah na shiga uku shima sun mallake min zuciyar shi, ke nafada miki kije min wurin malamin nan inji me zamuyi akai bazan Y’ar da da hada zuri’a da jinin talaka ba kinsan ni. “Aunty please relax nasan me nakeyi ki kwantar da hankalin ki ana kan aiki, Malam yace zuciyar khaleel akwai rauni akan Naziya Amma ita zuciyar ta a dake take don haka akanta za ayi aikin zata tsane shi sosai bazai tabajin dadin zama da itaba sai sun rabu, ki jekiyi baccin ki Aunty. “Hmmm har naji sanyi kuwa zarah wai, idan bukatar kudi yataso kifada inturo miki ko nawa ne Y’ar Albarka kinji. “Toh Aunty aike dole mu share hawayen ki tunda kina share namu.

 

Afalo kuwa da sauri ya fita bayan wucewar momy ya tuna ba hijabi a jikinta kuma akwai masu aikin gidan yanzu da safen nan a harabar gidan da masu gadi, wani irin mugun kishi yaji yataso mai ya fita cikin hanzari ga part din nata a rufe, tunda tafito ta ga mutane tako Ina Takasa fita taja ta tsaya a lungun shigowa falon domin tasan rashin dacewar fitar ta hakan ga jikinta a bude, yana fitowa yagan ta yaja dogon numfashi tareda dafe kirjin shi kamar Wanda yayi gudu, komawa yayi cikin sauri ya dakko mata hijabi tareda key ya mika mata “wear it, ta karba ba musu tasaka yayi gaba tabishi a natse har gefen ginin shi, yana budewa ya waiga yaga kowa na aikin gaban shi ya sunkuce ta batareda ta shirya ba tajita a sama, wani irin kwakume shi tayi saboda ta tsorata batayi zato ba tajita tana yawo a iska. Saida ya shiga da ita ya Ajiyeta tareda rufe kofar da key ya juyo tareda zuba mata ido kamar zaiga wani Abu a tartare da ita, kallon lafiyar ka take yimai rigar farar shaddar shi ya cire tareda rataye wa a jikin wani karfe dake farkon shigowa falon Wanda saboda hakan aka Ajiye shi, ido ta zuba mai bakar singlet ce tayi mai kyau sosai sai agogon shi na Rolex dake haska shi da katon Azurfan shi mai daukar ido kanshi ba hula sumar shi a nade Alamar gyara, haduwar shi bata lokaci ne fadar ta khaleel is very handsome and classy boy ba raini a tareda shi, bata ankara ba taji ya zare hijabin ya rataye tareda sungumar ta yayi  kan doguwar kujerar falon Wanda bai bata kowace damar da zata gudu ko ta hana faruwar hakan ba, wato she frank ne idan zuciyar shi nason Abu bata taba Y’ar da ya cutu, saurin ja baya tayi jikin kujerar ya matso tareda zubawa Abun kallon shi ido.

Muryar shi a shake yace “kinsan nayi hakuri for too long I can’t wait any longer, come close to me I want to suck. Wani irin girgiza kai takeyi tana rufe kirjinta da tafin hannun ta tareda cewa “wai kai bazaka gane bana son kana zuwa kusa dani ba please nidai kaga Ahmed ma bai taba yimin irin wannan Abubuwan ba don Allah ni ka kyale ni kirjina na zafi tunjiya please stop it.

Da wani irin salon shagwaba take maganar batareda ta shirya ba ko tasan tanayi Wanda yakara sakashi a cikin wani irin yanayin da bazai iya fitaba cikin sauki,  she is very adorable and innocent girl. Batareda ya shirya ba ya janyota zuwa laps dinshi ” enough karki zautar dani kwakwal wata is very small a wurin ki please, kinga ance kin asirce ni nima yes tell me ist true?  Wani irin kallon zautacce take mai, yes ya zauce bata sani ba akanta, daga jiya zuwa yau jinshi yake kamar a Aljannah, “Um tell me, me yasa kirjin ki ke zafi?  Nine, ko yanzu kiyi hakuri am here because of them now let me enjoy. Yafada yana nado west dinta da hanayen shi tareda dora kanshi saman kirjin ta ya na sauke ajiyar zuciya mai karfi, jitayi hannun shi na yawo a kan bayanta, tsintar zip din tayi a bude gaba daya cikin second kadan ya cillar da rigar yayi saurin maida fuskar shi akan kirjin dake shirin haukata shi ya wani irin basu kiss mai karfi yana “ba Wanda suka taba burgeni sai naki I love them. Cikin natsuwa ya dora harshen shi akan small nippy dinta ya wani irin lasosu cikin salo, batareda ta shirya ba ta gantsare mai kamar tana bashi head baki daya, yakara cusa fuskar shi ya zuko a hankali Wanda saida taji wasu irin ruwa nabin pant dinta saboda irin Abinda taji yana aika mata, akowane sako da lungu na jikinta, zullo takeyi kamar zata suma saboda bakin Al amarin da bata taba experiencing ba,  saida yayi yanda yaga dama dasu kafin ya dago jajayen idanun shi ya kalleta da wani irin salon kallo, “need more than this, ya zamuyi?  Yafada cikeda tanbaya tareda neman mafita, jikinta ya mugun mutuwa, zubewa tayi a jikin shi batareda ta shirya ba domin tayi mugun explode yafi sau uku, wato ita irin matan nan ne kankana sarkin ruwa,   “bake kadai kirjin ki ke ciwo ba nima inada ciwo kuma kece kikaja min ciwo sosai nakeji. Yafada yana rike kasan shi tareda shafo marar shi da tayimai wani irin tauri saboda cika bai taba jin kanshi kamar yanda yakeji ba yanzu, hannu yasa ya kwance tazugen shi ya riko hannun ta dake saman laps dinshi ya dora a inda bata Sam meyeba ko tunani bata dago kanta ba yafara shafo hannayen ta saman katon iccen dayayi wani irin haniniya tareda mikewa kamar zai cire saboda desire, inda takejin hannun ta Abun yamata mugun dadi Kara rikewa tayi da dan karfi Wanda saida ya zube a jikinta kamar ya suma ya saki mata wani irin nishi mai karfi tareda kankameta, ” baby you are soooo good  hold me tighter pleasesssss.  Saurin zabura tayi tareda sakin shi tana kakkabe hannu idanun ta a waje “nashiga uku. Tafada,  yanzu ne   tasan meta rike a hannun ta tashi tayi da gudu ta nufi hanyar bedroom  fadawa tayi ta kulle tana maida numfashi.

Wani irin dariya tabashi irin gudun data kwasa kamar ta riko maciji, ya rike tareda bajewa yana kyalkyala dariya…….. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 3⃣1⃣&3⃣2⃣

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

 

 

Ya dade zaune yana bin kofar da kallo, “babe that’s our room tunda shi kika zaba mana. Yafada yana murmushi mai kayatarwa saida yaji ya d’an dawo normal ya mike tareda mayarda rigar shi bayan ya kalli yanda taja duk wandon yayi squeeze,   cikin gidan ya koma tareda kiran maid yace tazo side din su ta hada musu breakfast idan tagama tayiwa madam magana tafito taci shi ya fita.

Naziya bata kuma fitowa ba saida taji bugun kofar maid tace “Aunty nice kifito ga breakfast. Bude bakinta tayi cikeda kasala tace ” ba kowane a cikin gidan? “Eh Oga ya fita yace ki karya sai ya dawo. Ajiyar zuciya tayi ta mike tareda cewa ” kije nagode. Saida taji ta tafi tafito falon ta dauki d’an kwalinta dake kan kujera ta kalli wurin tareda tuna what ever happened yanzu, mamakin shi takeji halin shi daban ya mugun canjawa kuma she understand know, khaleel bayaji domin ta lurada baiko tsoron kalaman momy like Ahmed dake mugun gudun fushin ta, zama tayi na tsawon lokaci tana tunanin banbancin halin su tareda irin nashi ra’ayin I don’t care, da kuma bin son zuciyar shi,

Sai karfe shadaya ta karya ta kwashe kayan ta nemi kitchen, yanzu ta lura komai na part din sabone bazata manta ba lokacin da Ahmed kenan ba wainnan bane a ciki, wainnan sunfi haduwa ko kitchen din kamar Aljannar duniya bare kuma bedroom din data shiga, kawai jitayi Abun ya burgeta taji tana son taga gidan baki daya,   dakunan sunyi matukar burgeta duka sai daya dayafi kowane haduwa da shan ado ga akwatunan ta sunkai saiti shida masu kyau da tsada waldrp din ta bude taga yanda ya tsara    komai kayane yan gida da waje birjik kowane side kaya daban harda iners kamar wani small shopping mall, samun fuskar ta tayi da saki ta zauna tareda zubawa ko Ina kallo tana tunanin shi just like that tafara hasaso rayuwar shi, daga jiya zuwa safiyar yau he changed all her thinking, duk wani baki nashi da take gani ya goge sai wasu kyawawan halayen shi dake maye mata gurbin duk wani kiyayya datakeji tashi, me ma yayi mata tunfarko?  Takasa tunawa sai wata zuciyar ke fada mata kanin mijinki ne this is not right, girgiza kai tayi tareda tunawa da ya’yan manzon Allah da ya Aurar da ya ta mutu yakuma bashi wata itama ta mutu yace da da wata da zai kuma Kara mai,  don haka tasani ba haramci a cikin Auren su sai dai zata dauki dogon lokaci kafin ta iya sakin jikinta dashi, karar wata sabuwar waya taji a gefen gadon ta mike tareda daukar wayar ta zuba mata ido kamar tana tsoro domin wayar nada matukar girma da kuma kyau, saida tayi ringing sau biyu ana uku tayi shahada ta dauka,

Shiru tayi domin batasan wayar waye ba kuma ba suna, “Hmmm madam kinga wayar ki kenan, that’s your phone ita zaki rike madam khaleel, and this is your husband number save it. “Nidai bana son waya inada tawa. Tafada cikin wata irin murya da batasan tafito ba. Ajiyar zuciya yayi yace ” Hmm you are my wife I can buy the whole iPhone company for you if you want, kinfi karfin wannan wayar, ni zanfada miki how wealthy I am, your husband is a rich man take it or leave it, but that the fact, and ki shirya very soon zamuje honey moon domin I have a lot to offer to you madam Ibrahim, I want to fulfill All my brother dreams, kullum so yake yi yaganki cikin farin ciki, bai samu dama ba, ni inada dama what ever you want just tell me I will do it right away, I don’t mind if you call me your savernt.

Kalaman shi sunyi matukar tasiri a zuciyar ta saidai kalma daya data tsaya mata da tasa ta bude baki batareda ta shirya ba, ” kanayin komai saboda Ahmed? Shiru yayi na d’an lokaci kafin yace “yes shine ya bani umarnin Aurenki, and bazan iya tsallake wa ba koda bana so zan iya takura rayuwa ta for my brother happiness. Kalmar batayi mata dadi ba taji wani iri Abun ya tabata wato saboda Alfarmar Ahmed yake Auren ta?  “Me yasa zaka takura kanka kayi Auren da bazai taba Baka farin ciki ba?  Ni baso nakeyi ba da kabarni na Auri Wanda nakeso. Wani irin d’aci yaji a kirjin shi, “Wanda take so? ” oh wannan Almajirin ko I no it, but last warning daga yau tunda igiyoyina na wuyan ki kar inkuma jin irin wannan maganar a kunne na, bazan dauka ba, any way is nice talking to you on phone, bazan dawo da wuri ba aiki ya rikeni daga lekawa office kinsan Yaya na keyin komai yanzu responsibilities sun hau wuyana da yawa,mata biyu gida uku Momy na office our business zaki taimaka min ai ko?  “Mata biyu?  Ta samu kanta da tanbaya batareda ta shirya ba kalmar ta fito, “yes two wife’s idan naga da hali salifa ma zata dawo kuzama ku uku but kafin nan zangina muku gidan da yafi wannan yanda kowacce zata wala.

Sauke wayar tayi, taji she can’t talk anymore just like that ta datse ta Ajiye,

Wayar shi ya bi da ido tareda cewa “what?  Idanun shi a waje domin he can believe it, kishi takeyi batason kishiya?  Or what?  Tafara sonshi ne daga small touch daya bata daga jiya zuwa yau or what? Ko kawai ta gaji da magana dashi ne?  So much question da yake bukatar Amsar su, dafe goshi yayi tareda cewa “babe if you are really jealous saboda ni I swear I will divorce fauzy I promise you, but I will find out first. Jinshi yakeyi kamar yayi tsuntsuwa ya bar office yagan shi agida this is very hard time for him he needs time saboda ita,

 

Ta dade rikeda wayar tana tunanin meke faruwa daga jiya zuwa yau, takasa kamo bakin zaren mikewa tayi tareda kwabewa ta daura towel domin tayi wanka kafin lokacin sallah,  katon mirror din dake bathroom din ta zubawa jikinta ido tana kallon kirjin ta da yayi wani irin ja saboda murza, Ahmed ta tuna dayayi mafarkin tabasu har yabar duniya, tace you miss my Ahmed you really missed. Tuna yanda ya kafa soft lips dinshi akansu taji wani iri Abu nabin jikinta, yanda yake squeezen dinsu ta tuna, namiji baida kunya domin ita a irin zaman su za amutu bazata iya koda rike hannun shi ba Amma shi daga zuwan ta first night ya murjeta tsab a gado yanda yake so ko a kwalar rigar shi.

 

Saida ta kwashe kusan hour guda kafin ta fito ta samu kanta da murje ko Ina najikin ta da kamshi da mayuka masu tsadar gaske da gyara fata,  ta fito zuwa cikin  dakin, inda tasamu kanta da zabo wata doguwar rigar Abaya Baka mai d’an kwali kato ta ciro Iner wears ta saka masu kyau bakake suma ta zura rigar ta shafa powder da wet lips saboda ita irin matan nan ne masu natural beauty ba saida make up ba.

Nade gyalen tayi kamar balarabiya, fadin kyau da tayi bata bakine, hijabi ta dora a kai tayi sallah, ta dade kafin taji karar wayar ta, dauka tayi tasan shine domin ba Wanda zai kirata, ” madam nagaji kuma inajin yunwa, please set food for me and water for bath I will be home in fifteen minutes insha Allah. Batace komai ba ya datse kiran. Tashi kawai tayi ta nade daddumar ta fito zuwa cikin kitchen, ko Baka ra’ayi zakayi sha’awar yin girki a cikin wannan kitchen din, don haka ta baje tareda hadamai lafiyayyan dishes din da yakeci, Wanda gidan ya cika da mugun aroma, ganin zobo dasu Abarba taji tana son ta hada, domin ko a gidan su sana’ar inna ce, cikin minti shabiyar ta hada komai ta zuba kankara tareda zubawa cikin lafiyayyan jug ta saka a firij,

 

Gyara wurin takeyi tana tunanin ba wannan kudurin ta shigo dashi cikin gidan nan ba, duk Ina tsarin ta da kuma kiyayyar Auren khaleel daga jiya zuwa yau ya zage ta girka mai Abinci, and this wanka, no ba saboda shi bane saboda ta bi maganar iyayen ta dasu Aunty, kuma tana tsoron wutar Allah, banbancin mutum mai ilimi da jahili kenan, Wanda shi kullum idan zai aikata laifi yasan makomar shi amma jahili yi yakeyi batareda tunanin gobe ba, don haka Allah yabamu ikon aikata mai kyau.

 

Motsin da taji ne yasa tayi saurin Ajiye towel din da take goge goge dashi, a tsaye yake ya nade hannu tareda zuba mata ido kamar zai cinyeta tayi mai matukar kyau ga wani irin Aroma da yayi mai welcome tun shigowar shi falon,  dukar da kanta tayi duk ta diririce domin duk ya cika mata ido da kitchen din, ga wani killer smile da yake watso mata Wanda ke Kara hanata tabuka kudurin zuciyar ta. Ganin ta daskare ya bude hannun shi Alamar tazo gareshi ta ki tareda juyawa ta bashi baya. “Ni dole inzo madam bazan iya ba ai. Yafada yana cire hannayen shi a saman kirjin shi ya fara taku a natse har wurin ta bai yi wata wata ba ya zagaye west dinta tareda dora habar shi a wuyanta yana lumshe idanun shi. “Wow wannan kamshin daga cikin gidan ki har kitchen din ki, Hmm I can’t express, you are amazing, you are beautiful adorable and Angel from god Alhamdulillah, kinsan ance wai idan namiji yazo gida ya tarar da Matar shi duk gajiyar shi na bajewa, Amma ni ba haka bane, duk lokacin da zanganki jikina Kara mutuwa yakeyi you are my weakness.

Kalmar tayi matukar tasiri a zuciyar ta, sannan yanda yake magana hucin shi na bugun gefen wuyan ta tuni ya saukarwa da nata jikin kasala, she can swear shine weakness dinta domin duk lokacin da ya matso gareta ta tashi aiki, sun dauki lokaci idanun su a runtse yace “A bani Abinci am hungry. Saurin cire hannayen shi tayi ta matsa tareda daukar tray ta bude firij ta dakko jug dinta ta dora mai komai yana kallon ta har tafita gefen kitchen din da ke daukeda dining ta Ajiye yana biye kamar rakumi, jan kujera yayi ya zauna tareda cewa ” nafa gaji kezaki ciyarda ni da kanki. Dago kanta tayi tace ” Aa ni bazan iya ba.

Kasheta yayi da wani irin salon kallo ya karkace tareda ciro wayar shi yayi dialing number fauziya, ringing daya ta dauka yace ” come to Naziya side now. “Why zanzo side dinta? “Inbazaki zoba karki dameni da surutu you can pack up and leave. Ya datse kiran, ya jingina a jikin kujera ya runtse idanun shi batareda ya kuma ko kallon taba, tunda ya Kira Fauziya fuskar ta ta sauya tuni ya zubawa handsome and well shape face dinshi ido dake dauke da wani irin kyakkyawan saje dayake karamai haiba da haduwa ido, girar idanun shi zaro zaro sunfito, pink lips dinshi, jin shigoqar fauziya yasa tayi saurin waigawa tareda zuba mata ido, mugun kallo ta watsawa Naziya Wanda itama akaron farko taji ta tsane ta. Tareda mayar mata da kallon tayi saurin matsawa zata fara ruwan fada” ke ni sa’ar kice zaki harare ni wallahi…… “Enough banson hayaniya zoki bani Abinci am hungry. Yafada fuskar shi a tamke, tuni kanta yayi wani irin kato tafara kwarkwasa ” OK baby ai badamuwa, matsowa tayi tareda jan kujera dab dashi ta bude Abincin tayi serve ta dauki fake tana zokalo prawns din tana bashi a baki,

Sai wani irin shigewa takeyi cikin jikin shi , shukuwa he is enjoying each and every spoon na favorite food dinshi kamar ita tafi kowace mace iya sarrafa tukunya,

Takasa koda motsi wani irin Abu taji ya danne kirjin ta kamar sanda yana sata jin wani irin kakarin mutuwa ko miyau ta kasa hadiyewa Wanda tarasa dalilin, wasu hot tears da bata shiryasu ba suka biyo kuncin ta, a gefen fuskar shi yake kallon ta Wanda jiyake kamar ya buga tsallen murna is true she is jealous, Amazing.

Juyawa tayi tabar falon gudun karma yaga metakeyi ta shige dakin tabarsu anan, tana shigewa ya karfi fake din yana wani irin murmushi mai kyau ” tank you dear, Yafada cikeda nishadi tareda saka mata abaki ta bude ta karba jinta takeyi a sama yau.

 

Saida yaci yayi kat ya janyo jug dinta ya tsiyaya zoban da kanshi,  kamshi ya bugi hancin shi nasu cucumber da abarba, kurba daya yaji wani irin kuzarin shi duk yadawo, best juice ever, yana gamawa ya ce “I need to bath muje can dakin ki hadamin ruwa, ya nuna mata wani daki daban, jikinta na rawa ta mike tayi dakin ta hada mai ruwan ya shigo tareda kwabewa ya rage dagashi sai boxer ya ce ta nemo mai kaya kana na  ya shige fuskar shi a tamke yanzu domin bayaso ta shigemai.

 

A dakin Naziya kuwa samun kanta tayi da kasa sukuni taji Sam bata gamsu da shigowar ta dakiba, kukan me takeyi to ai Matar shi ce kuma  tare tagansu meye nadamuwa?  Toh me ya hana ita ta dafa mai da kanta sai yaci fuskar ta? Wayar ta ta janyo ta Kira Aunty Raliya, tana dauka tace “Alhamdulillahi Naziya kin Kira duk hankali na natashe haka Inna Ina gudun injiki cikin matsala hope ba wata matsala ko? ” Aunty ba komai. “Kifadamin ba matsala keda Abokiyar zamanki koda mijinki ko uwar mijin ki? ” Ina gefena yanzu ta shigo. tafada wani kuka na kufce mata na rashin dalili, “Innalillahi, me tayi miki, ni Raliya, Abinda nake tsoro kenan wallahi. Saurin hadiye kukan ta tayi jin Aunty Raliya ta rude, ” Aunty batayimin komai ba shine yakirata. Anan dai dole ta war ware mata komai tareda fada mata duk Abinda zai iya faduwa a tsakanin su. Ajiyar zuciya Aunty Raliya tayi tace “Alhamdulillah, kingani ko Naziya, insha Allahu zakiyi farin ciki, a tsaye khaleel yake inada labarin shi saidai yanzu matsalar na wurinki ki gane kishiya gareki duk wata muguwar akidar ki da hango haramci da kikeyi ki cireshi ki dage ki mallaki mijinki zaman ku bamai karewa bane don inaji akwai Abinda Allah ya boye a Al’amarin ku. Ta dade tana bata shawar wari kafin su katse,  Ajiyar zuciya tayi tareda sawa zuciyar ta kwatan tawa batason tayi kuskuren baya, zaman ta da Ahmed wannan ce damar ta,

 

 

Sai da la’asr ta fito, suna zaune a falon, fauziya ansamu sake ta wani dora kanta a cinyar shi tana bacci Wanda haryagaji saboda neman magana yana gab da tureta yaji fitowar ta, wani irin saurin dora tafin hannun shi yayi akan fauziya yana wani shafawq kamar mai lallashin kwai, turus tayi kadan kafin tayi saurin danne ranta, domin ta canjo salo, ta matso fuskar ta a sake tace “me zakaci a dinner ko zata dafa maka ne?  Wani mugun kallo ya watsa mata ba haka yake soba shi fadan ta yake kwadayin gani da sunan kishin shi that’s means he is mistaken, don haka cikeda takaici yace bazanci komai ba, ya ture kan fauziya ya mike, zabura tayi yace ” zoki wuce part din ki malama, daukar dankwalinta tayi tace” muje tom. Har zai kuma gwaleta ya dai bita waje Wanda daga nan yayi mosque ko lekawa baiyi ba, cikin gidan momy ta shiga da gudu saboda takai gulma, tana zaune tana faman wayar tafado kanta cikeda farin ciki, ” momy aiki yafara kyau, yau yakirani har agaban ta ya nata jidani kuma naga harda kuka tayi,  “kai Y’ar Albarka, kice  dole mukara wa Malam kudi irin wannan zafin aiki kamar yankan wuka, bari kiga mai zai faru ma nan gaba dani take zancen, tashi kije ki shirya mai dinner ki caba ado ki baza kamshi  yau zakiga mai zai faru. “Kinfa san ban iya girki ba, uhm ki hadoni da mai aiki muje ta mun gyara. “Toh ke a haka zaki Kama mijin yakama ta ki gano halin khaleel Abinci yafi bukatar girkina tunda kina nan ki koya kamar wannan yarinyar rana daya ta iya dafa Abincin shi. “Nidai kidaina min kwatance da ita ni bantashi a wahala ba ita kuwa jikinta ya horu, nidai turon mai aikin muje. Tayi gaba abunta. Momy ta bita da kallo Sam bata ganin girman ta fauziya magana gatsau gatsau take fada mata.

 

 

 

Bai shigo gidan ba sai karfe takwas domin saida yaje ya gaida kawu da Malam Wanda bakomai ke kaishi wurin Malam ba sai neman karuwa da kuma nasihohin shi a kullum, Wanda yakejin dadin su,  saida yayi kamar bazaije part din nata ba, Amma zuciya ta ki barin shi kamar ana ingiza shi, baida zabi haka yabi son ranshi, a zaune take a falon ta canja ado zuwa wata silky gowan fubu mai kyau da karamin d’an kwalinta, ya shigo cikin sallama har wani irin sanyi yakeji yana ratsa jiki da zuciyar shi saboda hango ta a zaune a cikin gidan shi a falon shi ta saki jiki tana danna wayar da yabata gefe daya ga tsohuwar tata, zaman da tayi kawai Abun burgewa ne a wurin shi, ta lankwashe kafarta akan kujera, daga nesa ta dago kai tagan shi cikin jallabiya ta dukar da kanta kasa tanaci gaba da hira da Aunty Aisha, saida yazo gab ya zauna nesa da ita ya zuba mata ido yana shafa sajen shi cikeda damuwa, kulawar ta yake bukata very badly bazai iya hakuri da wannan ba he needs her, “Ina wuni. Tafada tareda sauke kafarta kasa,

Kallon ke bakya ganewa yake aika mata kafin ya ce “Hmm, yatsunta farare take murzawq kafin cikin dauriya tace “a dafa maka Abincin? ” Wai ke…  Sai ya mike kawai yace saida safe ki kulle kofarki zanje wurin da aka damu dani, wurin da ake sona basai na nemi a mun abuba in ansan Ina so. Ya fita kai tsaye saboda haushin ta. Binshi tayi da kallo kirjin ta na bugawa, ko yanzu shawara Aunty Aisha ke bata akan Abinda kefaruwa domin sun lashi takobin sai sun sa Y’ar uwar su akan hanya, kiran da taji ne yasa taga takira saboda taji  Shiru ba reply tace “ke lafiya ko yadawo ne inkyale ki? ” ya ma fita Aunty wai… Sai tafada mata Abinda yace.

“Kedai anyi banzar yarinya wallahi ace Sam bakida wayau kullum muna babatu saikace Y’ar kauye meye amfanin wayar ki bakya wtsp ne? Yanzu mata sun waye shiga grps sukeyi na sanin sirrin gidan Aure ki bari zan hadaki da wata marubuciya tana tareda mata da suka san sirrin rike miji ba boka ba malam kissa tafi magani, tunda ke ba kida wayau. “Aunty wacece wannan?”sai kinyi hankali tukuna,  yanzu dai bari inturo miki littafan Aunty feenah dana karanta zaki tsinci wani salon in kin so kiyi wasa. Ta datse kiran ta watso mata su ta wtsp ta sauka,  kallon jerin su tayi tareda kurawq kuskure na ido Wanda taji sha’awar karantawa  domin sanin meye kuskuren tauraruwar?

Saida tayi nafila like Always ta haye gado tareda daukar wayar ta domin batasan tayi tunani akan me yakeyi Ina yake, Amma wani gefen zuciyar ta nafada mata cewa yana can suna wasa kamar yanda yayi da ita jiya, wani iri taji ba dadi kamar mashi ne ya caki zuciyar ta,  saurin bude littafin tayi ta fara karantawa domin kawarda tunani aranta,

Batayi bacci ba har Asuba saboda sakai Wanda ta fahimci sakonnin cikin hikima, duk da itama ta lura tana so tayi kuskuren ta hanyar wancakalar da damarta, ba inda Abun ya burgeta sai ranar da Abdullah yafara romancing Ummu Ruman, tsigar jikinta saida taji ta mike , kuma taji tsoron yanda suka kare a daren farko har tafara hasaso idan hakan yafaru da ita, zaro idanun ta tayi data tuna lokacin da yasa ta rike gaban shi, dafe kirjin ta tayi ta tuna how thick taji Abun a tafin hannun ta, tashiga uku idan yace zaiyi, wata zuciyar tace Naziya stop dreaming momy bazata taba barin shiba kamar Ahmed,  tashi tayi tayi sallah ta maida baccin da batayi ba.

 

Gefen khaleel kuwa yana fita da daren part din Fauziya ya wuce domin bayaso momy tagano akwai  matsala tsakanin shida Naziya, tana nan a hakimce a falon anci lingerie  guntu ana jiran Oga, sai gashi, fuskar shi Sam ba walwala ya shigo ya zauna, yunwa yakeji, gashi yayo fushi yayo nan, tasowa tayi tana karai raya ta fada jikin shi, “baby welcome back, muje ka kwanta, tafada tana shafo kirjin shi, zuba mata ido yayi kamar ya watsa mata Mari  yakeji domin tabashi da takeyi karamai bakin ciki tareda kewar Naziya takeyi, yanajin inama inama……. 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 3⃣3⃣&3⃣4⃣

 

 

 

 

08032252760

08175479641 contact this numbers for more information

 

 

………… Kamar tana watsa mai wuta haka yake ji inta tabashi,   bai ankare ba yaga ta wurgar da yaloluwar rigar jikinta ta balle bra din ta jefar, saurin zubawa kirjinta ido yayi a cike suke tam amma sunyi sujada, basu burgeshi ba Sam bai ji koda inchi daya na sha’awar shi ya motsa  ba, runtse idanun shi yayi gam, the more he look at fauziya the more he’s missing Naziya, dafe kanshi yayi ya mike cikin hanzari yayi dakin shi dake part din ya shige tareda datsewa, ya fado katon gadon yabarta nan, ba Abinda yake hangowa sai Naziya her chest her perfect figure, her face, beautiful lips and sweetness dinta, gurnani yaja, “my diamond” you are the only woman who can move the man in me, Kwana yayi juyi sai da kyar ya runtsa tareda mafarkai masu dadin gaske akanta har ya samu yayi releasing, koda yatashi ji yake kamar mafarkin shi yazama gaskiya dama za ta zo gareshi dama za ta bude bakin ta tace tana son shi dama zata bashi kulawar da yake kwadayin samu, da yafi kowane namiji sa’a, he is craving for her love and care, when zai samu ? Dole ya kwantar dakai domin jiya kadai ya   cutu, ita ko a jikin ta.

Saida yayi wanka ya zura only boxer ya sa doguwar jallabiya fara Kal mai hula a baya,  ya fito ya kalli falon yaga ba fauziya, dafe goshi yayi ya tuna what happened, he is blaming himself, dole ya gyaro Al’amarin zaman shi da ita shima idan yana son nashi farin ciki, may be Allah na fushi da shi ta wannan hanyar shiyasa shima yake horuwa da soyayyar Naziya yaji yanda fauziya keji.zaiyi kokari ya tursasa zuciyar shi ya bata nata hakkin ko zaiga dai dai.

 

Daga masallaci bai tsaya wata wata ba ya nufi gefen Naziya Wanda yayi Amfani da extra key ya bude, wani irin numfashi yaja tareda sauke doguwar Ajiyar zuciya ya lumshe idanun shi, he don’t really know why, yake jin ni’im a duk lokacin da ya zo inda take, jikin shi mutuwa yayi ya nufi hanyar dakin ta, turawa yayi a natse, jingina yayi tareda sulalewa a hankali ya zauna domin kafafun shi are weak, kasala ganin ta ke saka mai, bacci takeyi akwance akasan dadduma gefe daya hisnul Muslim ne datayi Azkar, yasani ita batada matsala shine ke cikin babbar matsalar soyayyar ta, dakyar ya iya mikewa ya nufeta hijabin yayi kokarin zare mata, “Hmmm. Ya sauke Ajiyar zuciya, domin shimi ce ta kamata dam dam sai zani data daura tayi sallah, tayi matukar burgeshi dama zata iya tsayawa a gaban shi a hakan, yaushe zaiga tanayin Abu don ta burgeshi, dagata yayi sama, Wanda ta bude idanun ta kar, domin batayi nauyi a baccin sosai ba, saurin durowa tayi domin baida kuzari,

Kokarin kallon kanta takeyi taga ya zuba mata ido ko Ina yake bi da kallo a jikinta, komai nata is perfect, jikinta dai dai da shekarun ta tsarin ta west dinta dake dame like coca cola, kirjin nan masu cika da firgita brain din maza ya kurawa ido sunyi mai kyau a cikin shimin fara dal, saurin juya mai baya tayi saboda kunya, yana tsaye kyam, saida ya daga hannu tareda zare rigar shi yarage daga shi sai boxer ya matso tareda juyo da ita ta kalli murdaddun kafafun shi na maza dake cike da kwantacciyar suma irin ta zaratan maza, domin kasa take kallo,

 

“Hmmm kinyi bacci mai dadi harda kari ko? “Come” zoki saka ni bacci ni ma. Yafada yana d’an tura ta a hankali gefen gadon, zama tayi ya bita tareda kwantar da ita muryar shi kamar mai jin zazzabi yace ” kin iya yin bacci?  Tell me wane hali Yaya na yafi ni da kike sonshi?  Meye banda atareda ni, uhm tell me? Zuba mai ido tayi ga kamshin shi ya cikata ya rankwafo zuwa fuskar ta suna kallon juna cikin ido, wani namijin Baka iya hada ido dashi Amma khaleel mace bata iya kaucewa idanun shi, yasan duk inda kwayar ta ke boyewa yayi connecting,

Kirjin ta ya zubawa ido duk da tana rigingine suna nan cur dasu, hannun ta ya riko tareda dorawa a kugun shi yace “hold me tighter please”, ki koyi janyo ni zuwa jikin ki I need that very badly, I need you right now, Ina son natsuwa banda natsuwa, me zanyi kibani natsuwar ki. Duk ya gama kashe mata jiki kalaman shi sunfi na Abdullah Ummu Ruman, he is very romantic duk da ba soyayya a tsakanin su, to idan soyayya sukeyi kamar itada Ahmed wane irin jin dadi zatayi? Tuni zuciyar ta tafara hasaso mata rayuwar farin ciki da kuma soyayyar da tayi kwadayin samu tun a wurin yayan shi, shi bai da boye boye, bai da kunya, komai nashi straight forward yakeyi,

Batasan lokacin da ta rungume shi ba gam tareda runtse idanun ta domin bazata iya tsallake tarkon da ya d’ana mata ba, jin bakinshi tayi akan nata kamar Wanda yake saka mata remote control, bude bakinta tayi tareda welcoming dinshi duk tana hasaso soyayyar Ruman, yanda ta rike harshen shi yasa ya saki jikin shi akan ta domin zai iya suma, salon ta zai kashe shi, kamar zautacce yazamar mata duk ya rikice ya rude sai shanye mata miyan baki yakeyi kamar zaiyi maganin yunwar da ya Kwana da ita, har yasa tafara tsorata ta d’an fara tureshi domin har harshen ta da lips dinta sunfara zafi, ba karamin sha yake musu ba, fisgewa tayi ta mirgina tareda tashi zaune tana kauda kai saboda kunya, jikin ta na son bada ita, idanun shi kamar zasu shige ciki ya matso yana nishi tareda dorata kan cinyar shi cancakar kamar wata yar tsana, “stop running away karki kasheni kinji ko, please just relax I can’t take any of your rejection now. Hannu yasa tareda daga shimin ya wullar, “Ahhhhhh, Yafada da karfi ganin yanda sukayi wani bouncing ya kife kanshi saman su yana lashe each and every skin dake wurin, baya tayi ta zube domin khaleel mugun d’an Romance ne ya iya kashe ta da way’ennan touch din nashi.

Lokacin da ya riko niple dinta kuwa wani irin bankare mai tayi tareda zungura kafarta tsakanin  cinyar shi da ta Kara watsawa kananzir fetur, “Ahh Yafada tareda rike kan nippy dinta kamar zai cire ya damke su gam da hannun shi don ji yayi kamar da gangan tayi hakan, hannu yasa ya zame boxer dinshi cikin sauri tareda kokarin kwance zanin ta, lokacin ta dawo hayyacin ta tafara ture shi, tana girgiza kai domin da bata karanta littafin jiyaba kila sai yayi taji zafin Amma yanzu kam bazata yar da ba, sai dai ta yaya zata tsira domin har ya zame zanin yasaka tafin hannun shi saman gaban ta yana shafawa cikin zafi zafi har ya cisge pant din kamar yaki, Y’ar Kara tasa kadan tana  please stop kadaina banaso don Allah karka kasheni.. Bubbugata yakeyi yana lallashin ta tareda bude baki dakyar yana fisgo maganar ” please kibar ni inaso inji ya Abun yake nima karki hanani bantaba yiba zan iya mutuwa I want to test you inji please, Naziya ki tai make ni for the sake of my brother nima kibani kulawa kinji. “Bantaba yi ba” nidai ka kyale ni ni kabarni tafada tana yi kamar zata suma, baya jin zai iya sauraran ta ko  lallashin ta, ware legs dinta ya yi ya saita kanshi jikin shi na rawa da wani irin fisga, daga ganin shi kasan yafita a duniyar mu yayi nisa bayajin call, lalabe yakeyi Abunka da ba saban ba yarasa hanya baisan a kulle take ba so yake yajishi yana yawo ciki batareda ya sha wahala ba Amma bai tunanin zai samu hanya, tsabar dumin da yakeji yasa yayi explode tareda zubewa a jikinta yana shasheka, he is disappointed, wani tunani ne yafado mai ya zuba mata ido ” ist true yayan shi bai taba kusantar ta ba?  Yatuna this is the second time da take fadamai bata taba yiba. Wasu irin hawaye ne suka fara zubo mai masu zafi da mugun tausayin d’an uwan shi, yanzu haka ya tafi, yana kishin ganin su tare lokacin yana raye, Amma baitaba kawo yayan shi bai kusance ta ba, sheshekar kukan shi ya tsorata ta tazabura tareda tashi taja zani ta rufe jikinta ganin shi akaro na biyu yana kuka nafarko lokacin Ahmed na raye, na biyu kuma yanzu. Batasan lokacin da ta dafashi ba domin Allah ya sakawa zuciyar mace rauni da tausayi, ga wani yanayi dayake ratsa zuciyar ta a dangane dashi, Wanda batasan na meye ba she don’t hate him for touching her kawai tsoro takeji Amma idan a kan hakane bazata barshi ba gwara ta mutu da fushin Allah ya hau kanta, dagowa yayi jin hannun ta, yaga tana girgiza kai saboda kukan da hawayen shi.

 

“Why kika yi haka Naziya, meyasa kika hana d’an uwana kanki ya tafi a haka, kuma kikayi takaba da iddah bayan bata hau kanki ba Iddar why?  Bakya son shi ne dama, Toh ni kuma da nayi forcing dinki fa, so you don’t care about him gudun shi kike yi like me? Girgiza kai tayi domin bataji dadin Abinda yake fada ba baisan ba laifin ta bane, bata san lokacin da tace ” ban hanaka ba tsoro nakeji. “Yaya na fa” meye laifin shi kin san irin soyayyar da yake miki kuwa?, because of you he face a lot a wurin mommy why why why Naziya? Tashi yayi yana mata kallon tuhuma. Ranta taji ya baci haka kawai batasan lokacin da tace ” ni ko ban matsa ka Aure ni ba” da kai ma kana bin umarni irin na yayan ka gefe na bazaka shigo ba don haka in ka gaji let me go, bawai jin dadi ya dawo dani ba am trying inga na tursasa zuciya ta akan Abinda bata so. Tasa kuka mai tsayawa arai, tuni yadawo hayyacin shi domin ya gano ba laifin ta bane domin koshi Ambashi doka wadda zai ketare ta ta hanyar da bazaiyi wa mommy dadi ba, ya shirya nuna mata biyayyar da Ahmed yayi mata ya shirya nuna mata kuskuren ta domin kawo gyaran da haryau bata gane ba. Janyo Naziya yayi tareda rungume ta gam a kirjin shi yace “Am sorry”, tausayin Yaya na nakeji. Dago kanta tayi ta kalle shi cikeda tuhuma ” baka da kishine?  Why kake fushi akan haka? “Kishin ki? Ya tanbaya cikeda rainin hankali ” ke kina kishi nane?  Girgiza kai tayi. “Hmm, yace ” now enough of all this tears, muje muyi wanka kinga a she dukan mu dalibai ne na dauka ke malama ce zaki koyar dani, dukar da kanta tayi akan kirjin shi, saida yaji wani irin sanyi domin ya lura every moment sai yaga takara sakin jiki dashi Wanda har yanzu bai gano shakuwar su tafi tsakanin ta da Ahmed ba, cikin Kwana biyu cikin kashi dari na gudun shi Saura hamsin Wanda one more effort zai iya siyeta batareda ta shirya ba.

 

Mikewa yayi zigidir tayi saurin rufe idanun ta, “hhhh karya ne yarinya kima bude idanun ki ko indawo sai na bude wannan hanyar da ke rufe, “don Allah kasa kaya”, Kinsan Allah? open your eyes ko indawo, kima daina wannan kunyar bazan dauka ba, before Ina son mace mai kunya yanzu bana bukata ki bani Abinda nakeso kawai shine kulawa I need All of you. Tana kukan shagwaba ta bude idanun ta tareda cewa na bude don Allah ka wuce.

Matsowa yayi tareda zuwa gab da ita ya Kama kugu ya zubawa jikin shi ido yace ” look at her Y’ar gata ce ita zata ratsa hanyar da bata taba biba ranar akwai disvirgin biyu zakiyi nawa zanyi naki, nadauka you are the lucky one da zaki samu saurayi d’anye sabon jini sweet twenty five young handsome and rich guy only for you. Dago kanta tayi batareda ta shirya ba idanun ta sukaci karo da kyakkyawar kirar dake firgita Amare tace “innalillahi meye haka”?  Jikin ta narawa domin tana nan ko kwanciya bata da niyyar yi Abunka da healthy man,

“Hhhh” dorinar ki ce my diamond, zata zane ki da kyau don haka get use to it, let her be your close  friend, make her your toy.

“Don Allah” kadaina haba.  tafada idanun ta na tara ruwan tsorata da Abun,  OK ki kalle ta ko ki riketa ko muyi wanka tare yanzu, choose one. Ba arziki ta kalle ta cikeda tsoro tana kallon yanda yake motsa ta da gangan, ganin yanda duk ta firgice yasa yayi dariya ya juya ya wuce bathroom yana hango darun da zasuyi ranar bude wannan hanyar da yakejin is impossible ya shiga, ko dai bai gano kofar bane?, shikadai yake tunani har yayi wanka ya fito lokacin ta mike tsaye ta zura  hijabi, binta yayi da kallo. “Very soon zaki fara yawo a gaba na necked, bana son anayimin katanga da what is legally mine.

Wucewa tayi kanta akasa bazata iya da halin shiba……… 🖊

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 3⃣5⃣&3⃣6⃣

 

 

 

 

08032252760

08175479641 contact this numbers for more informations.

 

 

………….. Kuka Fauziya takeyi wiwi a gaban mommy tana fyace hanci, ” wallahi nagaji da zama da d’an ki” wulakancin ya isa haka, ni ba jaka bace kuma, sai na sabauta Matar son nashi da yake gani fiyeda ko uwar shi. “Ke ke ke banson rashin lafazin ki”, wata rana kikan manta ni na haifi khaleel, ki tasa ni a gaba kina fadamin duk Abinda kika ga dama, kin sani ko yau idan naso inkin bar gidan nan zan Auro mai wata ke kadai ce ya’. Wata uwar dariya tayi tace ” kutumar ubancan nagano ke kike hana shi ya kulani saboda na lura ma yanzu kishi kike da matan ya’yan ki, da kike son hanasu kusantar matan su kece zaki bude musu cinyar ki, Amma kedai akwai tshohuwar ban………. Gau taji saukar Mari a fuskar ta sai da ta zube akan hannun kujerar falon momyn, jikin shi na rawa yace ” ke kin manta da limit dinki kike zagin uwata uban waye ya tsaya miki a duk fadin kasar nan, kinsan me? na so in gyara zaman mu koda nine zan cutu domin kin sani bana sonki kina zaman tane ko? yanzu idan ta ba da Umarni zaki fita cikin gidan nan. “Sake ta” Y’ar banza ka dawomin da salifa tafimin ita idan har ni uwar kace khaleel, ka saketa ka saki……. Tayi shiru ganin Naziya kanta akasa bata ganta ba tun farko ta ci katon hijabin ta domin rufe adon datayi,

 

“Toh munafuka kema tare zakubar gidan nan yau idan nice uwarka ka fitar min da way’ennan bakaken irin yanzu daga gidan nan ko in sallama ka. Zabura fauziya tayi jikin ta na rawa “me zanyi da mata mazan d’an ki” Wanda bai iya kwanciya da mace ace watana kusan biyar gidan nan KO kiss din Arziki ban samu ba, ta matso kusa da fuskar shi “khaleel” ka rako maza duniya wallahi kaje kaga likita gwara ni nasan dadin Abun ko gobe na so zan fita zan hole kai ke ruwa. Wani irin kallon bakisan me kikeyi ba ya yi mata, “yes say what ever you want fauziya I don’t want you, bakida Abinda zanso bana ra’ayin ki ke kika nace har ki ka zo gida na, and zancen niba namiji bane kuma I don’t care ba ke na ke son kisan hakan ba, if you’re done talking rubbish leave my house. Yafada yana nuna mata hanya, “bazan tafi ba shaida ba kabani ticket. “Na sakeki” you can go now. Yafada kai tsaye.

“Kai rubuta mata uku”, ungo ta mika mai jota da biro, karba yayi ya rubuta ya mikawa momyn, fisga ta yi tare da kallon ta “zakiyi nadama mara Amfani Hajiya balkisu. Ta juya da gudu Kuka na cin ta, tana fita tadawo kan naziya, “Saura wannan mai farar kafar itama rubuta mata. Juyawa yayi yaga ta zuba mai ido kur yana hango tsoro cikeda idanun ta yace mommy ba kince indawo da Salifa ba? I choose in dawo da ita kawai akan in saki zabin Yaya na, she is my brother’s choice. Amanar da ya bar min ba zan iya cin Amanar shi ba sai indawo wa yayi duniya yabani Umarni da kanshi. Yafada yana riko momyn. Girgiza kai  Naziya tayi ranta na k’una magan ganun mommy ba sa bata mata rai Sam, Amma kalmar khaleel ta caketa,  juyawa tayi da gudu itama tabar part din, ya bita da kallo, sai da ta fice ya zaunar da mommy “Am sorry mommy karki kuma cewa in sake ta don Allah kinga sakamakon zabin ki ko yanzu kuma kince salifa I accept agaban Naziya for a reason karki tursasa ni tadawo gidan nan bazan iya zama da wata mace ba.

Kura mai ido tayi kur tareda Kama baki tasa salati, “khaleel bazaka iya zama da wata mace ba Amma kana iya zama da Matar gado?  Fadamin inji kodai tun d’an uwanka na raye kake son yarinyar nan ne ? ” yes mommy Ina son Naziya itace mace ta farko da na fara so bazan iya rayuwa babu itaba, ba saki a rayuwar Aure na da ita domin ita din cikon numfashi na ce, idan kukayi kuskuren rabamu momy nima zaki rasani, I love Naziya more than my life. Yafada har yana fitar da wasu irin ruwan hawaye domin neman ya sassauta halayen ta don uwace bai da yadda zaiyi da ita, kuma bata canjuwa. Kuka tasa mai karfi ” na shiga uku” ni balkisu khaleel Asirin yafi kamaka wato yarinyar nan da biyu ta shigo cikin zuri’a ta, Amma anyi bakar kaddara, saboda ita kasaki fauziya nasani badon niba innalillahi, wallahi zabi yarage naka ko ka Auro salifa ko kasake ta ko in tsine maka Albarka. Mikewa yayi tareda cewa ” mommy lallashin ki na ke yi ni ba Ahmed bane Amma nasan hakkin ki kuma nasan dokar da zan tsallake Allah ya hukunta ni don haka na zabi ki Auro salifa tazo ga filin gidan nan ba Abinda zata tsaremin saidai duk Abinda ya faru wallahi zunubin baya wuyana, domin Karin Aure yanada sharudda bazanyi Adalci ba bazan iya adalci ba Naziya daban ce. Ya fita domin duk zuciyar shi ta koma kanta, ya sani a cikin Kwana biyun sunyi mugun sabo yana ganin yanda yasamo kanta tafara sakin jiki dashi sosai.

Don haka jikin shi na rawa daga ciki zuciyar shi na kadawa haka ya fita zuwa part dinsu, tana zube kan kujera Kuka take Wanda batasan dalili ba kalaman khaleel nada nasaba da kukan ta, wato ita zaman yayan shi ta ke yi, komai ya na yi ne saboda d’an uwan shi, why zuciyar ta take son ya daina fadar hakan?why zuciyar ta ke kwadayin jin yace yana Auren ta because he wants her not because of his brother?. Dafata da yayi ne yasa ta dago idanun ta zama yayi tareda zuba mata ido ba tare da ya taba ta ba. “What happen ko wani Abu yafaru ne” ? ka mayar da ni gida.  Tafada kai tsaye, kur yayi mata kafin yace ” why?  Ba asona a gidan nan kuma ai Mommy tace nima ka sake ni, kai ma baka ra’ayin zama dani sai don d’an uwan ka, please let me go. OK you can go bazan rikeki ba. Yafada yana daga hannu sama. But ki sani ba kotu ko Alkalin da zai iya datse igiyar Auren mu Naziya, babu kalmar da zatasa ni Ibrahim khaleel in sakeki.  Fauziya has gone da gani sai ke yanzu, Alhamdulillah zan cika burin Yaya na, All his dream, bayason ya hadaki da wata mace and my dream is bigger than his, don’t you feel akwai Abinda Allah ya boye a karkashin zuciyoyin mu, bakyajin wani strong feelings akaina Naziya, ba kya jin yes Am your real man?, nine farin cikin ki, bakya ganin cikin Kwana biyu munyi shakuwar da bamu yi zato ba? why kika saki jiki da ni in babu wani boyayyan Al’amari a zuciyoyin mu?, kinsan zuciya ta na kun she da sakonnin da take aikawa ta ki ki ke karba batareda kin sani ba?

“Wani Auren zakayi ai”. Tafada tana kallon cikin idanun shi, “ba kya so ne?  Samun kanta  tayi da daga kai ta marairaice fuskar ta kamar zata kuma sa masa Kuka.

Wani irin murmushin farin ciki yayi tareda riko hannun ta ya dawo da ita kan kafarshi, ” are you jealous?  Kishina kikeyi?  Girgiza kai tayi. “Toh in ba kya kishi na kibari in karo Auren. Ya kuma fada yana kallon kwayar idanun ta mai cikeda wani irin sinadari dake Kara narkar da zuciyar shi,   Toh ka mayarda ni gida idan zakayi Auren. OK bari ranar da aka kawota zan mayarda ke saboda kin San kin batani bazan iya bacci ba tare da mace ba, before I don’t care but now you spoiled Mommy’s innocent child. Harar shi tayi ba tare da ta shirya ba,  kaine ka ke lalatani ai. Dariya ya kwashe da ita yana rungume ta kam wani irin nishadi yake ji a zuciyar shi a duk lokacin da suke tare baya gajiya da  kasancewa tare da ita,

Da wayau yacire mata hijabi. “Kinga wayon ya isa tunda kika yi kwalliyar bangani ba kinsa wannan katon hijab….. Hadiye miyan bakin shi yayi domin ganin kana nan kayan dake jikinta na boutique yellow riga da wando, kayan da ya siyo cikin akwatin da ya bawa yayan shi, Ashe shine zai Mora tun lokacin da ya siya kayan sun mugun burgeshi ne Amma a yau yaji zai iya biyan companin akan wannan adon, rigar nada guntun hannu ga wuyanta a bude sosai he can see her boobs kusan rabi sunyi wani irin kyau ga madai daitan hips dinta ma sunyi cif cif a cikin wandon kamar palazo ta saman ya kama ta kasan ya bude, fadin kyau da tayi bata baki ne, Abu na uku yanda ta saki sumar ta a gefen wuyan ta tayi kamar wata Amisha patel, domin jikin nata madai daici ne ba makusa, daskarewa yayi kawai kamar statue ya kashe ta da ido tagama kashe mai jiki, hannun shi na rawa ya daga  zuwa sumar kanta ya shafa har suna lumshe idanun su atare domin sakon nashi yaje mata shi kuwa feelings din dake taso mai nata bazai taba kwatan tuwa ba.

Wani irin zubewa tayi a jikin shi kamar ruwa, wani irin murmushi ya yi mai cikeda farin ciki, yana jin dadin yanda small touch din shi ke affecting dinta, he is lucky ba zata yi wahalar koyan duk Abinda yake so tayimai ba,  he is planning to spoil her so much, yanda ba zata taba mafarkin barin shi ba, so yake ya koya mata soyayyar shi yanda bazai sha wahalar samun kanta ba duk lokacin da yake bukata,

Hannun ta ta dora saman kirjin shi domin tana jinta cikin wani irin yanayi mara misaltuwa tareda natsuwa a duk lokacin da take jikin shi,  gam ya rungume ta tareda dora bakinshi dai dai kunnen ta yana hura mata iska a hankali cikin wani irin salo, “my diamond”, ki daina shige min haka zanyi Abinda zai hana ki zama fa yau, you have no idea how honey I am, you’re driving me crazy babe, let’s romance. Yafada yana mai tura harshen shi a cikin kunnen ta tareda shafa ko Ina na jikinta cikin wani irin salo, khaleel ya iya dora mace a network, tuni yasaka ta sakin jikin ta tafara shafa kirjin shi dake matukar burgeta saboda fadi, jitake dama ya cire rigar domin yanada soft gashi mai santsi dake Kara Kawata kirar jikin nashi, yanada tsarin mazajen duniya way’enda suka amsa sunan su, fadowar da mommy tayi cikin falon ne ba sallama tana ruwan masifa, to bita zai zai wato kina nan kin makalewa yarona kamar chewing gum, saurin zabura Naziya tayi kamar zata fadi, saboda kunya da kuma tsorata batayi zaton ganin ta ba,  saurin rikota yayi yadawo da ita a jikin shi domin itace zata rufamai asiri in ba hakaba momy zataga Abinda bazata so ba,  matsowa tayi tana salati tareda cewa ” Amma wannan yarinyar kunyi nasara sosai Ina bacci kun asirce mun zuciyar da’. “Mommy Mommy” please meke faruwa why are you here? Toh fa wato banda damar shigowa cikin gida na duk lokacin da naga dama saida izinin Y’ar gidan malamai? ” no mommy please ba haka nake nufi ba nasan zuwan ki akwai babban dalili. “Yes badon haka ba ba Abinda zai shigo da ni nan, Toh yama za’ayi kaso in shigo? ka narkar da Dukiyar ka akan Y’ar gidan matsiyata tunda kasan ba zaka samu Abun Arziki ba ga y’an mata nan na fita kunya ya’yan Arziki bana tsiya ba sai sauran d’an uwan ka. Jin yadawo dai dai ya saketa tareda cewa “wuce ciki Ina zuwa”. Domin kuka takeyi mai cimai zuciya domin kalaman mommy na da ciwo, don haka bata tsaya komai ba ta wuce ciki, bata taba ji ko ganin uwa mai hali irin na mommy ba, bata ko bata damar gaisuwa a duk lokacin da suka hadu don haka take shakkar haduwar su da ita a kullum, Ada tana ganin zama da Mommy yafi mata da khaleel amma tagano cewa khaleel din wani irin inuwa ne dake sanyaya mata zuciya da ruhi, shidin bangone Wanda idan ta jingina sai tajita cikin tsaro da Aminci,

 

 

Saida yaga ta shige ya maida hankalin shi kan mommy “meya faru yanzu momy?” Na Kira uban da ya daure maka kayi Abinda kaga dama na fada mai yau ko gobe nake son adaura maka Aure da salifa, ban Amince da zaman ka da wannan Y’ar ita kadai ba, tunda ka nace bazaka rabu da itaba, in har inada sauran mutunci na uwa a idonka kar ka fada mai ba tare da Amincewar ka bane inba hakaba ba zaka yi farin ciki a rayuwar ka ba khaleel. Ta juya ta fita fuuu. Yasani akwai hakkin ta na uwa kuma dole Tayi mai baki ya kamashi, don haka zaiyi yanda take so Amma bazata samu Abun da duk take so ba domin in har bai iya kula fauziya ba, ba yanda za ayi ya iya kula wata salifa don haka su zuba. Zama yayi tareda dafe goshi yana murzawa yarasa mafita, saida ya dauki lokaci ya mike zuwa cikin dakin, tana zaune tuni ta share hawayen ta ta dauki wayar ta tana karatun Auren Soja inda take ganin uwar miji tagari, gaskiya yasmin tayi sa’ar uwar miji, yaushe ita zata samu hakan a wurin Mommy?ta ga ta bata dama ta nuna mata ba ta da wani mugun nufi a tare da zuri’ar ta, kaddara ce ta Rayuwar ta wadda takeson ta rungume ta da hannu bibbiyu, domin ta Yarda Auren ta da khaleel shine mukaddarin rayuwar ta, *AUREN GADO* ne wadda zai juye ya zama hasken rayuwar ta, farin cikin ta, domin da mommy tace ya saketa sai da ta jita kamar numfashin ta zai tsaya, wane irin saurin shakuwa tayi dashi ba tare da ta shirya ba, tanaji kamar sun dade dashi fiye da Ahmed sometimes tana mantawa da wani Ahmed ma,

 

Sallama yayi ciki ciki ya tsaya tareda yin Ajiyar zuciya  ganin ta tana sha’anin gaban ta bata kuka, dago kanta tayi ta amsa tare da cewa “Mommy ta tafini ne? ” yes. Yafada yana matsowa ya zauna tareda fuskantar ta yace ” my diamond, zan angwance fa, kinsan ni d’an gata ne Yaya na mata biyu yabarmin yace in more, ta farko na dauka a bude take amma itama dal take a Leda ga kuma Amarya wadda ranar da ta Kwana Washe gari yatafi ya bar ni da ita, my brother really loves me.  wani irin kallo take yi mai Wanda bai gano fassarar shiba. Ki tayani murna idan na Kwana nan gobe zan canja sheka,  wo ni d’an gatan Yaya na. Yafada yana kwanciya agadon tareda mirginawa kusa da ita. Saurin sauka tayi kasa, “me zakaci”?  Saurin juyowa yayi ya zuba mata ido kamar ya mareta, he hate this character of her I don’t care about him, that means shike haukar shi akanta a kullum, ke wai me kika mayarda ni ne idan Ina important magana ki rika kawo min shirme ko banda lokaci sai na cin Abinci?  Am telling you Aure Mommy zatayi min yau ko gobe why can’t you show your concern? Yanzu ta gano shi yanayi ne purposely saboda ya gani ko zata damu to bazata nuna mai ba ai da wayon ta. “Ikon Allah” me kake son inyi?  Yanzu gashi ka fada Mommy take so kayi Auren kaima what is new?  Na saba da hakan Wanda nayi Auren soyayya dashi ma an Auro mai ita hankalina bai tashi ba sai yanzu da kai kafadamin kana Aure na ne saboda cikon burin Yayan ka , Toh me zanyi dukkan mu zabin shine kuma umarnin Mommy zakabi don kasamu tsira don haka banda damuwa she is welcome.

Ta kureshi kamar ya dora hannu akai yakeji ya kurma ihu cikin sauri ya duro tareda fisgota rashin sanin madafa yasa ya cafke bakinta da ke fadamai Abun haushi yafara tsotsa cikin mugunta harda ciccizawa yakeyi idanun ta a waje ga zafi gashi takasa ture shi saida yayi son ranshi ya tureta tareda nuna ta da yatsa, ” karki kuma furtamin kinyi Auren soyayya a rayuwar ki me kike nufi da nawa Auren, what is wrong with me?  Niba namiji bane ko bankai ki soni kiyi kishi na ba? Look ni inada kishin Abinda yake nawa koda ace ke zabin Yaya na ce now you are under me, ikona ce ke you must love me, dole kiyi kishina dole. Yafada yana fita saboda takaici yarasa Ina zai saka ranshi kishin ta yayi yawa a zuciyar shi,koda yayan shi ne ta Aura Abun na tabashi kuma duk da yasan ita din tashi ce zuciyar shi taki convincing dinshi sai ranarda yaga tazamo shi yazamo ita, don haka he is ready to make her his completely.

Zama yayi tareda yin dariya, this guy is strange, kalli yanda yake reacting itafa ta ma gano shi yanzu kamar yanda yake fada akwai boyayyen Al’amari a kasan zuciyoyin su ita mace ce don haka bazata taba bada kai da sauri ba dole shine zai sauke wannan ego din ya fada mata zuciyar shi, tagano shi fiyeda yanda yake tunani,   tana sane da kalaman fauziya akan yaki kusantar ta, ace mace wayayya like her yakasa kulata Amma ita daren farko yanuna mata shifa namiji ne kuma yanada lafiya, Wanda ita sheda ce domin idan ya rikice mata har tsoro takeji.

Part din Mommy ya nufa Wanda yayi dai dai  da shigowar motar kawun su, yayi saurin boye fushin shi ya nufeshi, suka gaisa yace ” muje cikin gidan Ina Hajiya”?  Mommy na ciki Ya fada suna tafiya,  tana zaune a falon tana kada kafa, suna sallama ta mike tareda cewa ” gwara daka iso domin jini na nagab da hawa saboda bakin cikin khaleel. Kallon ta yayi kawai domin yasan korafinta baya karewa, mommy me nakuma yi kince in Amince da zancen Auren salifa koda bana ra’ayi na Amince now what? Oh fadamai kakeyi nice nasaka khaleel nagode kaji shiyasa nake kukan Rashin Ahmed. Tasa kuka, tareda zama, kawun nasu ma zama yayi ba tare da yace uffan ba,  saida sukayi shiru yace ” Toh nidai nasaba da mugayen kalaman ki balkisu ba tun yau ba idan na yanke hukunci akan yarana kice namiki shishigi kuma idan fitinar ki ta tashi sai kin nemo ni kuma kinsan bakina ba shiru zaiyi ba,  don haka ni na isa nace khaleel bazai yi irin Auren da ki ka yi wa Ahmed ba, kina maganar nadama Hajiya balkisu har yanzu baki san Annabi ya faku ba, da zaki gano ita wadda kikeso   din ranar da kika Aurota aranar ya Kwana asibiti, da Naziya ce da baki kauna da kince itace ta kashe miki yaro, Amma da yake bakya tsoron Allah kinyi mukus, yanzu ko mutuwar Ahmed bai isheki ishara ba, duk bakiga ya dace ki kyale komai ki barwa Allah ikon shi ba, naji kin kashe Auren da  kika kulla ba tare da yaro ya Amince ba tun farko, wannan badamuwa ta bace yarage naki Allah ne ke nuna miki komai cikin sauki  inda ke mai kwakwalwa ce Amma toshashshiyar madiga……. “Ya isheka Muhammadu”, don bazan ce Alhajin ba, ko ince modu  kamar yanda kowa ke kiranka tunda kaki Kama furfurar ka, kuma kuji nan, wallahi in har ban Aurawa khaleel salifa ba sai in ba na numfashi, kuma kai kaji idan baka Aureta ba banyafe maka ba duniya da lahira mu zuba ni da ku shege ka fasa. Ta mike fuuu ta shige dakinta tareda mugayen kud’uri,  “kawu kaji me tace?  Ya fada cikeda damuwa domin kalmar ta girgiza shi, naji khaleel kuma mahaifiyar kace bamuda yadda zamuyi da ita, sai Addu’a, yanzu dai ya za’ayi?  Ko ka Amince ne a daura Auren?  “Eh kawu ayi mata yadda takeso ai ba akaina zata zauna ba,

Yafada tareda ayyana wani kud’uri a zuciyar shi, Wanda shikadai yasan tsiyar da ya shuka, haka ya raka kawun shi tareda zancen zai samu iyayen yarinyar ai shi namiji ne zai iya rikesu  duka don haka karya damu, koda kawu ya tafi bai iya komawa part din Naziya ba, dakin shi na nan ya shiga ya canja tareda barin gidan,

Direct gidan malam yaje……….  🖊

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 3⃣7⃣&3⃣8⃣

 

 

 

08032252760

08175479641 contact this numbers for more information

 

 

 

……….. Sun dade suna tattaunawa da malam akan rayuwa Kafin ya koromai zancen Karin Auren da Momy keson yi mai, Sai da yayi shiru malam yace “yanzu meye matsalar ka?  Baka da muhalli ne, ko baka iya daukar nauyin mata biyu ne?  Kuma meye dalilin sakin ita dayar Matar taka ba akan ka’ida ba?  Yanzu dai nasan ba mata hudu ba Kanada karfin da zaka ciyar da Unguwa guda ma, sannan lafiya kana da ita, sauran ka Adalci, karike Amanar su tsakanin ka da Allah kabi umarnin mahaifiyar ka kasamu tsira kamar d’an uwan ka. Haka suka dade sai karfe kusan biyar yabar unguwar, tun fitar shi take jin ba dadi domin ta saba dashi yanzu tafara sanin dadin Aure zaman ta da khaleel,  shine ya nuna mata ita mace ce mai daraja da lafiya a tareda ita, domin duk lokacin da ya kusanto jikinta bata iya misalta dadin da takeji hade da nishad’i, kewar shi ta dameta sosai har waya ta dauka sau ba adadi’ tana dubawa tareda tunanin kiran shi sai takasa, to me zatace mai inta Kira?  Ganin zata damu da yawa yasa ta janyo wayarta ta fara karatun littafin ta, y’ay’an gata yasata cikin nishadi’ sosai,   saida taga yamma yayi ta mike ta shiga kitchen, ta shirya mai dinner lafiyayya irin wadda tasan yakeso, Kafin tayi wanka, duk Abinda takeyi a yanzu bin zuciyar ta ne domin tana samun farin ciki ba tare da tayi tsammanin samun shi ba a cikin wannan Rayuwar Auren.

Yana tafe a hanya yana duba waya, wato ba zata iya neman shi ba koda zai shekara baya gidan?  Don haka saida yayi magrib ya shigo cikin part din, lokacin tayi wanka ta saka simple gown tana zaune tana lazimin ta, ya yi sallama ciki ciki, tareda wucewa gefen gadon ya zube rigin gine,  nasihar malam ta ratsa shi Amma baya jin kudurin shi zai canja sai dai ya kiyaye fadawa halaka Wanda yasan duk ta inda zai bullo ma Al’ amarin,  saida ta kammala ta mike tareda juyowa tace  sannu da zuwa. Bai amsa ba bai bude idanun shi ba,  harta juya tafita, saida ta juya yabita da kallo tareda sauke Ajiyar zuciya, ya tashi zaune yana shakar kamshin da tabar mai,

Shigowa tayi dauke da tray, binta yayi da ido kur harta Ajiye akasan gadon kan small carpet, baice uffan ba, tace ” ga Abinci. ba tare da ta kalle shiba,  “come here”. Yafada cikin bada umarni fuskar shi a hade, ta dago kai, kallon da yake aika mata kamar yana Amfani da igiya yana janyo ta ne, ba musu ta mike,  remove that hijab. Ba musu ta cire tareda ninkewa ta juya ta Ajiye inda take Ajewa, duk yana binta da kallo wani irin nishadi yake jinshi a ciki a duk lokacin da suke tare, dawowa tayi zata koma kasa ya riko hannun ta tareda janyo ta ya dora kan kafar shi, ” kina wahalar da ni da yawa fa” Ya fada yana mai dora hancin shi a wuyan ta,  kamshin ta mugun rikita shi yakeyi,

Nafita baki damu ba, nadawo kin nuna baki yi kewa ta ba,  bayan rabin zuciya ta na nan tunfita na, Ina tunanin ki nadawo ba hug ba welcome back kiss umm why kike horani?  Never mind gobe zakiga Amarya ta am getting married again. Yafada tare da dago idanun shi ya na kallon kwayar na ta  idon domin yaga reaction dinta,  Wanda Sai da taji zuciyar ta tayi wani irin tsalle kamar zata fito, kalmar ta caketa fiye da tunani, kallon are you serious?  take mai, Wanda ya ganota domin yana karantar kowane movement dinta saboda ya gano ainihin meke ranta, ” am serious, am getting married, Salifa zan Aura  gobe insha Allahu, ai badamuwa ko?  Tunda kinga yanda Auren ki yazo ba shiri haka nata ma All this romance karki damu I can handle but for you. Wani irin zamewa tayi ta sauka kasa tareda fasa kuka mai karfi ba tare da ta shirya ba, jitakeyi idan  batayi ba zuciyar ta zata fashe, zancen romance da wata, kwakwalwar ta bazata iya dauka ba,

Wani irin farin ciki yaji har kasan zuciyar shi, so he is right tafara jin shi a zuciya tunda har tafara bayyana kishin ta, Abun da yake kaunar gani a wurin ta, she dai yana so yaga kishinta akan shi wannan reaction din nata kawai yasa ya ji shi yana yawo a sararin samaniya saboda farin ciki, tuni zuciyar shi ta wanke fes ya sakko kasa kusa da ita zuciyar shi kamar Auduga fuskar shi kamar wata daren goma shabiyu,

Jikin ta ya shige tareda rungume ta gam a kirjin shi, yace  you have the right baby cry for me, I want it, I love that, I need your jealousy, and only you have the right over Ibrahim, love me please love me. Dago fuskar ta yayi tareda dora bakinshi dai dai hawayen dake gangarowa yafara lashewa yana bata wani irin salo mai kashe jiki, tuni kukan ya dauke dif. Saida ya sude hawayen tas ya dora  goshin shi saman fuskar ta, ” tell me meye matsalar? ” ba kya son inyi Auren ne?  Daga kai tayi kai tsaye, ” why baby” ? ni banaso. Tafada tana tura baki,  “ba akanki zata zauna ba ai”. You are going to touch her. Tafadi gaskiyar Abinda zai janyo mata ciwon zuciya, yanda yake romancing dinta ta ke jin dadi ba zata so ya yiwa wata ba.  Wani irin mugun kishin shi taji tanaji fiyeda Wanda taji lokacin Auren Ahmed.

 

“To ai kishiyar kice Already nagani ba Fauziya bace”. Ture shi tayi ta mike kaje kayi ni ban hanaka ba ka Auro goma ma ba ruwana.  Dariya yayi mai d’an sauti ta farin ciki,  ya matso tareda fisgota ya rungume west dinta ya dora kanshi a kafadar ta,  Hhhh admit it my diamond, kina kishina, kokarin ban bare hannun shi takeyi takasa, ” wait let have a deal with you”, Amarya ta is coming today or tomorrow, yanzu nayi Alkawarin if you give me chance, nasameki I will not touch her I promise you, yanzu Ina jiranki daga yau zuwa gobe bazan zo kusa dake ba if you are ready  meet me Ina gefen mommy, and make sure you dress sexy. Ya dago tareda kashe mata ido ya bar part din, saida ya dauki duk Abinda yake so yafita ta bishi da kallo, zubewa tayi kan gadon tareda dafe kirjin ta,

Dole ta Amince wa zuciyar ta akwai soyayyar khaleel mai karfi data shigeta farat daya ba tare da ta shirya ba, son shi ya damki zuciyar ta gangar jikinta tana jin kishin shi fiyeda tunani, domin karatun da takeyi yasa ta gama gano cewa shima akwai sonta a zuciyar shi, yes bazata so ya kusanci wata ba Amma kuma tasan hukuncin ubangiji zai iya hawa kanshi, tana da ilimi tasan komai bazataso kanta dayawa ba Amma zatayi Abinda ya dace, zata bashi mamaki she is ready ta mallaki mijinta ta hanyar da takeso don haka zata dage ta cire kunya tabashi kulawar da ta dace, meye kunya a cikin Aure, bayan cikon addini ne sunnah ce ta manzon mu ( s.a.w )mai k’arfi,  Ina koyarwar da yan uwa da kuma iyayen ta su kayi mata?   Da kanta tabawa kanta shawara, don haka she is ready now. Aunty Raliya takira tareda tanbayar ta yanda zatayi da wasu magunguna da tabata. Dariya da farin ciki Aunty tayi tace ” Naziya mafarki na zai zamo gaskiya, domin na hango ki cikin farin ciki a gidan khaleel, na hango miki rayuwa mai cikeda nasara da kuma Albarka, kin gani ko haka Allah ya tsara, naji zancen Auren shi wurin zarah, don haka ki dage ki rike y’an cinki da martabarki,  kinga kece ta biyu.. ” ai ita tafita dayar Aunty. Tafada kai tsaye. Toh Allah ya kyauta gaba nasan ayi haka, kuma ko yanzu kirike Allah ki rike Azkar ki kula da kanki gyara shine mace idan kikace bazaki gyara ba zaki zama bola a gidan mijin ki. Ta bata shawari masu Amfani da suka Kara mata kaimi da daura damara.

 

A ranar bata kuma ganin shiba har Washe gari, ko wayar shi bai kirata ba, tasan he is serious kuma zata nuna mai ita din mace ce mai dauke da nata irin Salon, Kwana tayi a internet tana koyan salo Kala Kala Wanda tayi Amfani da nata, da safe tana tashi ta tura mai text,  “good morning husband, how was your night? Ta tura hade da Alamar hasken rana da kuma hoton teddy bear mai dauke da hoton zuciya.

A zaune ya Kwana a part din mommy yana aiki a computer tareda yin booking flight to bangkok  shirin shi yakeyi sosai domin yanada tafiya agaban shi da ya kirkiro wadda zata zama da manufa biyu, yanayi Amma rabin zuciyar shi na wurin ta, yana a takure ne sosai Amma dole ya daure yayi wannan aikin in yana tare da ita ba uwar da zai tsinana sai lalubeta karshen ta yayi aika aika batareda ya shirya ba,   don haka har Asuba idon shi biyu haka yake famar aikin shi, saida yayi sallah yaci gaba,

Sakon ta da yashigo ne yasa ya dauki wayar tashi duk da baisa rai daga ita bane,  ware idanun shi yayi, yayi saurin budewa. Farin ciki ko ihu zaiyi saboda murna, sakon nata means a lot to him, ya karanta yafi sau Ashirin harda ture laptop dinshi yayi gefe ya kwanta yana runtse idanun shi, tareda dora wayar a kirjin shi. Saida ya dauki lokaci kafin ya daga ya fara mata reply, ” Hmmm morning wife, are you missing your husband touch?

Tana zaune tana jiran sakon shi ta kagu, taji shigowar text harda tashi zaune tayi ta bude, ba amsar da take so taji ba kenan taso taji yace mata yakasa bacci like her amma let go, ta mayar, ” I can’t help it”.

Wani irin buga kafa yayi,  duk kalmar da tafito tanada muhimmanci a zuciyar shi,

“Me too I couldn’t sleep all night long.

Mayar mai tayi, ” then come back.

“Really?  “Yes. Saurin kiran ta yayi, tayi dariya tareda picking, Ajiyar zuciya ya sauke yace ” are you serious baby?

” uhm. ” you know what am going to do if I come. “Is your right”. Tafada kai tsaye. “Really baby”?  Yafada with so much excitement, Zaki sani in karya duk wani plan dina baby, ko yanzu tun text dinki na farko look at me, bafa ganin ki nayi ba am hard like rock, you are the only woman who can move the man in me, duk lokacin da na kusanto ki zanji inada cikakkiyar lafiya, do you feel the same baby? ” um um please stop it ina jin kunya zankashe. Tafada tana rufe fuskar ta kamar yana ganin ta, shy baby  look ba kunya a rayuwar Aure kinga am frank so nake ki zama kamar ni idan bukata na kikeyi koda Ina office just give me a call and tell me, husband please come back it scratching me. Wani irin dariya yabata harta kyalkyace tareda rufe baki, he is funny wallahi, wani irin farin ciki ne ke bin zuciyar shi jin dariyar ta akaron farko, Alhamdulillah Yafada, “my diamond” tayi shiru domin sunan yana yimata dadi is she really a diamond? , yace ” stay happy always, yaja numfashi yana mika, ” please come to mommy side kinji am so so so honey bazan iya fitowa a hakaba ta cika wandon you can come.

“Da safen nan Mommy na nan inajin tsoro.” dodo ce ita kizo please kiga Abinda kikayi coursing Yafada yana mika tareda dafe jikinshi gam yana runtse idanun shi saboda zafi domin na yau daban ne.

Kashe wayar tayi ta nata saka da warwara, saida ta dauki lokaci ta mike, tafada wanka ta mulke in and out na jikinta da kamshi, ta samu wata Oman gowan mai shegen kyau da tsada kamar weeding gowan ta zura light brown taji adon dutsina kamar wata princess,  Naziya akwai sirrin kyau da iya ado kuma duk shigar da tayi saita fito tayi kyau.

Kitchen dinta ta shiga ta samu madara mai dumi tasha domin batajin yunwa,

Batasan me yasa zuciyar ta ke ingizata zuwa gareshi ba, don’t blame her, domin khaleel ba irin mazan da zuciya ke iya jawa aji bace duk ego din Naziya ya hambarar cikin sauki, Wanda shi a gefen shi yasan ba zata zoba don haka juyi yayita yi kafin ya zabura ya iya watsa ruwa ya dawo dai dai, mommy ce cike da farin ciki ta turo kofar dakin nashi lokacin ya shirya cikin wata dakakkiyar shadda green tana maiko sumar shi yake tajewa, fuskar ta a Washe tace d’an Albarka bazaka fadamin a nan ka Kwana ba?  Aida tuntuni an kawo maka breakfast, yanzu zoka ci kaji. Tafada tana ajiyewa a kan gadon, ” good morning mommy. Yafada yana zama gefen ta, ya riko hannun ta, he love her but he hate her ways of thinking, takasa gano illar Auren da zatayi mai, saida yaci yagama tanata tsaro mai zancen Auren tareda cewa “nasan zaka dawo hanya ai don kaima kasan baka kyautawa rayuwar kaba khaleel duk fadin kano an san da arzikin ubanku tun yana raye bare yanzu da kuka Kara bunkasa kuka ginu ace baka Auren Y’ar da duk kano zata dauka asan yes kayi aure nima infita anuna ni ace ga surukar wane kuma uwar wane y’ay’an ka su fita a nuna su ace jikokin wani ne a garin kano ai shine farin ciki. Saida ta gama yasa tissue ya goge bakin shi ya juya dakyau ya kalleta ya riko hannun ta, ” Mommy na meye laifin Naziya?  Tana da mugun haline? Gidan su ba tarbiya ne?  “Talauci ne banaso kasani bankaunar hada iri da talaka shiyasa nafada maka karka sake ka hadomin jini da talauci. ” Hmmm mommy meye ribar Auren fauziya danayi?  Meyasa kike so ki hadani da salifa?  Mommy I don’t want to argue with you, banaso kice na bijire miki amma ni har a abroad nasha ganin ta tana yawon banzan ta,…. “Dakata, sunada kudi Ina kakeso ka gansu a Zaure da Almajirai ko suna kulle a gida bayan sunada Abinda zasu huta?  ” mommy understand yarinyar nan gwara fauziya da ita you… “Quit Ibrahim Aure dai yau sai andaura kuma yau zata tare yau nake so ka shiga dakinta domin jikoki nake so daga tsatso mai daraja ba gidan malamai ba.

Mikewa yayi OK sai tazo tayi gadi tareda zaman jiran agama budar kai, ai al Ada ce mai muhimmanci dataja har yayana yabar duniya baisan dadin Aure ba. Ya dauki key ya fita abin shi, yabarta sake da baki, khaleel baya wani ganin girmanta take gani baisan mutuncin taba kamar  Ahmed,  “Allah ya jikanka yaron Albarka”. Tafada tana share hawayen kewar Ahmed tafita da kayan Abincin da yaci.

 

Yana fitowa tana fitowa cikin adon ta mai daukar hankali, tayi matukar tafiya da hankalin shi, saidai ganin mai gadi da masu aiki dake kai kawo yasa yaji wani irin mugun kishin ta tuni ya hade rai yayi saurin cewa ” go back, cikin kausa shashshiyar murya, mai cikeda umarni da tsantsar kishi, yayi saurin rufa mata baya, domin bata tsaya wata wata ba ta juyan saboda yanda fuskar shi ta juye kamar bashi bane dazu yake kwantar da murya a waya, a tsaye ya ganta ya doge daga nesa,  ban lamunci ganin adon ki awaje da rana ba bayan kinsan akwai gardawan banza a ko Ina, wallahi zakija musu asara idan kika kuma fita batareda hijabi ba, ke ki nemo nikab kirika sawa if necessary sai kinfita da rana. Ya juya ranshi a bace, by the way, Ina ma zataje?  Ya manta y’an da sukayi da ita a waya saboda kishi,

Yana tuki yana dukan sitiyarin motar shi, saida ya koma gefe ya faka motar ma ya kife kanshi,  bai taba tunanin yanada zafin kishiba sai akanta, zuciyar shi har wani tsalle takeyi, kuma gashi dole ya fito da ita ayi mata passport,  domin shi kadai yasan shirin shi, dukan iska yayi, Allah yagani bazai kawowa wani katon banza Matar shi ta tsaya yana kallon ta cikin camera ba zai iya shake shi, wayar shi ya ciro tareda kiran manager dinsu yace yaza’ayi asamu mace photographer tazo tayiwa madam a gida?  Yace za’asamo mai yau, yayi Ajiyar zuciya tareda kiran ta, kamar jira takeyi dama tunfitar shi take dariya kishin shi ma dariya yabata domin tana tunanin bayau suka saba ganin taba a gidan, wani irin farin ciki takeji a zuciyar ta now she relax domin inda kishi da so, don haka tanaji a jikinta yana sonta domin Abinda yakeyi da ita yafi karfin wasiyyar d’an uwan shi,   tanata tunanin moment dinsu dashi taji karar wayar da yabata, mikewa tayi da sauri ta dauka don shikadai ke kiranta da ita, picking tayi tareda yin shiru, saida yaja numfashi yace “am sorry for shouting at you diamond, kin tashi kishin da bansan ma dashi ba do you know, you look very pretty and beautiful?  “Sorry ai kai kace inzo insame ka. Tafada cikin Y’ar shagwabar da batasan daga Ina tafito ba, “Hmmm really babe wurina zakizo Yafada jikin shi na rawa saboda farin ciki, yes dole inbi umarnin ka domin Aljannah ta na karkashin kafarka Ina gudun tsinuwar ubangiji.

Ajiyar zuciya yayi tareda hamdala, ba Abinda yafi ka Auri macen da ta ginu akan addini a rayuwa. ” am coming back home soon my diamond don’t change that dress please zanzo inkalla in more, and am Ina mana wani shiri ne  zan d’an dade kadan kidafa min lunch ki jirani a gefen Mommy, bye. Ya katse wayar yana tayar da motar cikin sauri, domin tun baije inda yayi niyya ba jiyake kamar ya koma saboda ya shiga jikinta yayi yanda yake so, yanzu ne zai samu damar da yake mafarki akanta domin tagama sakin jiki dashi sosai, “babe am coming for you get ready. Yafada yana jin yanda jikin shi ya mugun motsawa saboda ya kwadai tu,  “control madam you get in don’t worry yourself. Yafada yana murmushi mai cikeda farin cikin da baya iya boyuwa, ko office da yaje kowa mamakin sakewar shi da farin cikin shi yakeyi domin tun rasuwar d’an uwan shi basu kuma ganin fara’ar shiba, fara’ar shi sai yana tareda Naziya, ita din wata bangoce  mai yaye mai dukkan  damuwa batareda tasan da haka ba, da bata a rayuwar shi ya rasa Ahmed saiya susuce, Ahmed yayan shi ne ubane kuma bango mai muhimmanci, Wanda bai tashi rushewa ba saida ya gina mai Wanda zai jingina yaji sanyi,  itace Naziya, haske ce wadda mommy ta kasa hangowa farin cikin yaranta biyu Wanda take wa kallon banza ita ba Y’ar kowa ba, Addu’a yakeyi just once mommy ta gano Naziya itace surukar kwarai,

Bayan sun gama wayar bata bata lokaci ba ta shiga cikin kitchen tareda zuba tagumi tana tunanin me zata dafamai da zata burge shi yau?  Dariya tayi domin tasan me ta shirya a ranta, I will change you I will make you test our food our tradition today d’an China. Tafada tana dariya, don haka ta fara kokarin dora mai tuwon danyar shinkafa da kuma    miyar taushe, lafiyayya, domin anzuba mata komai a gefen ta, tundaga kalolin namomi har zuwa kan kayan miya da duk wani Abun amfanin kitchen kamar part din Momy, don haka ta dage ta zage ta yimai lafiyayyan girki da yaji namomi ta kuma hadamai zobo domin ta lura yaji dadin shi ranar nan, cikin hour daya ta kammala ta zuba a new warmers masu kyau, sai tunanin yanda zatayi takai cikin gidan kamar yanda yace, zata jira shi first a nan har yazo ko zai Amince ya shigo cikin part din ta yazo yaci, tana gudun haduwar ta da Momy, batason cin mutuncin ta zagin da take mata yana mata ciwo a kullum don batada y’an da zatayi ne bata koyi yiwa babba rashin kunya ba kuma uwar miji dole ta kawar da idanun ta ta to she kunnen ta domin khaleel yana kokarin taka mata birki ba kamar Ahmed ba,

 

 

 

Momy nacan tayi busy sai taya kawayen ta takeyi ana tsara gefen salifa,  jinta takeyi a cikin farin ciki yau, duk yanda zatayi ta raba khaleel da Naziya sai tayi,  haka malanin su yabata tabbacin khaleel bazai taba kusantar Naziya ba  muddin tabashi Abinda yabata ta zuba mai a Abinci, kuma tayi  nasarar bashi yaci, don haka batada fargaba yanzu target dinta shine yanda zatasa ya kula salifa,  saida suka gama tsara gefen y’an da sukeso kafin su koma gefen ta su baje suna tattaunawa itada su Zarah, “Aunty yanzu hankalinki ya kwanta ko? ” eh zarah ai ni nasan  banda kanwa kamarki, jini nane banaso ya hadu dana talaka kuma Alhamdulillahi wannan malamin yamun komai. “Toh Aunty idan kika hana khaleel kusantar Naziya kinada tabbacin zai kula salifa?  “Kibarni dashi aiba shi ya haifi kanshi ba, ni zansa yaje gareta. ” Aunty khaleel ba Ahmed bane kinsani. ” eh kinsan ya akayi ya A mince da zancen Auren salifar?  Toh kiyimin shiru zakiga mai zai faru. Rungume ta tayi tana dariya ” yayi Auntyn mu na Y’ar da dake.

 

 

Yana hanyar shi ta komawa gida malam ya kirashi a waya, Wanda shine karon farko da yataba daga waya ya kirashi, yayi mamaki sosai saida ya faka ya kirashi back, suka gaisa cikin mutunci yace ” kazo gidana yanzu idan baka komai, muna tareda kawun ka yanzu haka. dafe goshi yayi  ya manta ma da zancen Aure yasan kan maganar ne suke neman shi, don haka baida zabi haka ya burkita ya nufi hanyar gidan malam din,

 

 

A zaune suke cikeda Almajiran malam manya,  ya parker daga nesa ya karasa Wanda kamshi da haibar shi kawai zaifada maka shi din wani ne, kawun shi na gefe suna magana, ya tsuguna ya gaida su kafin ya zauna a tabarma, kanshi akasa, “Alhamdulillahi Ibrahim yanzu muka dawo daga daura Auren ka, Wanda nayi kokarin kiranka tun lokacin Alhaji Muhammadu yace inbarka kanada uzuri, Toh yanzu dai nauyi ya hau wuyan ka, mata biyu, sai kayi kokarin kwatanta Adalci, Allah ya tayaka riko. Wani irin bugawa kirjin shi yayi tunda Malam yafara magana, Allah yagani ya tsani salifar nan fiyeda ma fauziya, Adalci Hmm. Yafada a ranshi,   yanaji har sukayi suka gama doguwar nasihar su, kawun shi ya mike yace shi yatafi gida sai sunyi waya, Malam ya kalleshi yace ” Ibrahim me yasa ku matasa yanzu kuke sakaci akan Addu’a, bakwa neman tsarin ubangiji tareda kariya a tareda ku, bayan kunsan akwai makiya da mahassada atareda ku a kowane lokaci zasu iya kawo maku hari, karkayi wani tunani ba Abinda ya sameka kawai ka rike Azkar ka kuma dage da sallar dare,  Allah ya Kara tsare ku yakuma bada zaman lafiya. “Amen yace kamar dole sukayi sallama

Yana wucewa malam ya Kira Amintattun Almajiran shi yace suzo zasuyimai sauka yanzu, ya tashi ya shiga cikin gidan yasa Inna ta girka musu Abinci mai yawa, harda kaji yasa aka Kama yace ayi miya,

Inna tasan Indai malam yayi irin hakan to karya sihiri zaiyi Wanda tasaba, kuma ba ruwanta da bincike aikinta kawai takeyi don haka ta dage ta tado Shukrah suka fara aikin su………. 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:33 AM – Fiddausi Yunus: 3⃣9⃣&4⃣0⃣

 

 

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

 

 

………… A zaune take tayi tagumi, domin Momy har part din ta shigo take fadamata tafito ta jira a gefen Amarya domin taga harkar Arziki bata tsiya irin tasu ba,  batada zabi dole tabi umarnin ta tabiyo ta, Wanda ba Abinda ya daga mata hankali da duk Dukiyar da aka narka a part din, domin iyayen ta basu ginata akan hassada da ganin k’yashi ba, saidai kuma Abinda takeji na daban Wanda tasan dalilin hakan, haka momy ta tasa ta sukaje part din ta tayita yimusu girki badon babu masuyi ba sai don ta dai kuntata mata domin ta bata mata rai, yes ranta na baci domin ita ma mutunci tanada wannan dunkulalliyar tsokar a Kirjin ta, itace zuciya, daurewa takeyi saboda tarbiya da biyayya ana gaba da aka ginata akai, bazata taba yiwa momy ba dai dai ba da izinin ubangiji domin ita din uwace ga mazajen datake Aure,  busy din datayi na tsawon lokacin yasa bata damu da rashin dawowar shiba duk da zuciyar ta na kanshi,

Sai ana magrib ta koma gefen ta, ta yi wanka domin ta gaji da kayan dake jikinta, sai lokacin yadawo shima, bai shigo gidan ba,  ya wuce cikin gidan, suna zube a falon sunata shewa ga magrib ta gabato bamai shirin tashi, sallama ciki ciki ya shigo ko jinshi basuyi ba sun tsinke, Momy na sakin magana, ” yau zaku gani sai khaleel ya Kwana tareda salifa a cikin gidan nan Indai suna na bilkisu mai gadon zinari, inda Malam ba bakin ciki, yau Ina cikin kwanciyar hankali, domin duk Abinda nasa gaba sai naga bayan shi…… Saurin juyawa yayi batareda yaji karshen zancen ba domin zuciyar shi zata iya bugawa, idanun shi kamar garwashin wuta saboda bakin ciki, ace wannan uwar cikin kace haka, he don’t want to know more, zuciyar shi kamar zatayi tsalle ta buga saboda bakin ciki, bai nufi gefen naziya kuma fita yayi kawai a motar shi, aguje, saida yayi nisa da gidan ya parker ya zuba goshi akan sitiyarin motar, da ace zai iya kuka da zuciyar shi tayi sanyi,

Saida yaji ana kiran isha’i ya dago kanshi,    wayar shi ya ciro tareda kiranta, a zaune take akan dadduma ta zuba tagumi, Ina yake meke shirin faruwa?  Kodai itama salifa zai bata kulawa kamar y’an da yake bata tunda wsiyayyr yayan shi yake son ya cika, yanzu rayuwar da yakoya mata cikin kwanakin zaiyi da Salifa?  Taji karar wayar dake gefen ta kamar jiran kiran nashi takeyi ya dauka da sallama, wani irin natsuwa yaji tafara dawomai a zuciya,

“Hmmm Naziya ‘ yakira sunan ta cikin wani irin salo tareda sanyi, tanajin muryar shi saida tasan akwai damuwa, ” please will you do as I said? Yanayin da yake ciki yasa taji harshen ta na amsawa ” yes. ” please get ready as I said, kinyi min Abinci? ” yes. “Take it were I told you am coming, set water for me. Ya katse kiran, kawai taji jikinta yayi sanyi kuma taji tana son bin umarnin shi batareda musu ba, don haka ta mike tareda duba waldrp din da ya shirya mata kayan bacci, taciro wata baka mai shara shara iyakarta  guiwa, hannun ta d’an siriri sai kokon bra Wanda dai dai yake da kirjin ta har sun wani irin tasowa gwanin burgewa da rikita namiji, ta zura wani d’an guntun wandon kayan Wanda Ana ganin shi saboda shara sharan net din,

Zani ta dora a kai ta dauki hijabi ta zura, dinning table dinsu taje ta shirya Abincin a basket tareda rufewa da farin kyalle mai tsafta,  saida ta rufe gidan ta fita a natse tana jin tsoron karonta da Momy, ko motsi tayi kanajin y’an da take tashin kamshin Humrah, hade da tattausan kamshin perfumes din ta, Allah ya taimaketa duk sun watse suna gefen Amarya domin tarbon ta, Saurin shigewa tayi cikin sauri  ta na jin dadin rashin haduwar ta da Momy,   tura kofar tayi taga dakin fes sai dai laptop dinshi da yabari a bude bai rufe ba,  saida ta Ajiye Abincin a center table, ta nufi gefen gadon ta zauna tareda zubawa laptop din ido, tasan bakyau bincike Amma kawai jikinta ke turata tareda zuciyar ta, tasan kan computer kadan a school don haka she can operate laptop, budewa tayi tareda zubawa hoton farko dake kan screen din   hoton tane, Wanda batasan lokacin da ya dauketa shiba, kuma ba yanzu bane, zaro idanun ta tayi domin ta tuna lokacin Ahmed nada raine ranarda suka hadu a gefen shi, ana shirin Auren shi da Salifa, ranar da ya hanasu sakewa,   har yabata haushi, wani irin murmushi tayi tana hango reaction dinshi, wuce hoton tayi tareda ganin nashi yana kwance a beach daga shi sai boxer idanun shi rufe da eye glass,    yayi matukar haskawa kyanshi da kuruciyar shi ta bayyana, sajen namiji bai taba bata sha’awa ba sai nashi domin ya kwanta lup lup a kan kyakkywar fuskar shi, kirjin shi ta zubawa ido Wanda ko Ina kwantacciyar suma ce, har tsintsiyar hannun shi ma da kafafun shi, khaleel is very handsome and classy ta Y’ar da, har manta kanta tayi wurin kallon hotunan shi bata ma damu da nata da take gani ba,  wainda badon tayi nisa akan kallon shi ba, da ta yi tunanin why yake bi biyar rayuwar ta tun tana Auren yayan shi?

Ba hoton da yafi burgeta a ciki kamar Wanda yake cikin sweeming pool idanun shi a kan camera, “Hmmm shiyasa kake son yawo ba kaya saboda kanada jiki mai daukar hankal…… ” yes All yours baby. Taji sassanyar muryar shi mai cikeda kasala da Y’ar sauran damuwa ya zuba mata ido kamar ya hadiye ta,     wani irin zabura tayi ta kife laptop din tareda sakkowa cikeda kunya bataji shigowar shi ba, hotunan shi sun dauke mata hankali har ta manta kanta,  nade hannu yayi ya tsaya daga bakin kofar saida ya dauki lokaci kafin ya fara takowa bayan jan dogon numfashi,kanta a kasa ya matso gab fa ita, ” my pain relief. Yafada cikeda kasala, “you are allowed to touch my things, ni din kaina ikon kine mulkin kine you can check me in and out, you have the right over Ibrahim I told you um, Hmmm am exhausted muje kitayani wanka please. Saurin dagowa tayi tareda girgiza kai ” no please bazan iya ba. “Don’t worry bazan cire boxer ba, ba yanzu kike kare min kallo ba kaya ba, muje ciki ki kalla ki more mijinki ne kin riga kin ganni meye na kunya, nifa so nake idan Ina kusa All this clothes are not needed. Yafada yana kokarin daga hijabin ta, rikewa tayi domin tasan bazaici Abinci ba inyaga shigadar dake jikinta yanzu, ” your food is ready. “Tank you wife am very hungry, bari inci inyi wanka baki daya, ko yatsan ta baiyi kokarin rikowa ba sai numfashin da yaketa ja saboda kamshin perfumes din ta dake ruda mai kwakwal wa, juyawa yayi ” set the food I forget something. Ya juya da sauri, Wanda yana fitowa momy na shigowa falon, ta saki fuskar ta tareda cewa “kaga Angon Salifa Ashe kana nan?  Sakin fuskar shi yayi like nothing happened ya d’an matsa ya rungume ta yana gaisheta, amsawa tayi tareda cewa Ina zakaje?  “Abu na manta a mota am coming. “Kadawo nan Ina jiranka karkaje  gidan ka kana jina? “Yes. Ya fita saida ya dakko ledar kafin ya kalli matan dake shirin tafiya y’an rakiyar Amarya, ko kallon gefen su baiyi ba don baida lokacin kowa yanzu sai na Naziya, ya koma tana zaune a falon rikeda wata gora Y’ar karama,  matsowa yayi “gani  Momy any problem? ” yes zauna. Ba musu ya Ajiye ledar ta kalla tace ” meye a ciki? “Kaza ce. Ba wani jan dogon zance Yafada. Murmushi tayi, “Toh ga tawa gudun muwar kasha, nasan yau yarona zai san yayi Aure. Ta fada tana mika mai gorar kallon maganin yayi akwai rubutu a jiki, man power ne  na bature, ” I don’t need this Momy. Yafada yana juya gorar fuskar shi a ya tsune, ” you need it domin Ina tantama akan ka ace tun shigowar fauziya harta fita ka kasa kusantar ta, Anya kanada lafiya Khaleel?  Gashi sai yawo zance yakeyi agari kai ba namiji bane, inaso ka tabbatar wa dakowa cewa kai jinin babanka ne kuma kanada lafiya inba karfi ne bakada wannan zai tai make ka.

Juya gorar yayi tareda Ajiyeta ya mike, ” Momy lokacin da kikewa Yaya Ahmed Abubuwa har nafara zargin ko bake kika haife shiba?  Yanzu nagano kila nine ba d’an cikin kiba ko kuma dukan mu bakece mahaifiyar mu ba,  idan har ke kika haifemu bazaki rika threatening din mu irin hakaba, me kike so yanzu?  Kince in Auri zabin ki she is here, to kuma why kikeso kisani inyi Abinda zuciyata bata ra’ayi bana bukata, let everyone talk am not a man I don’t bloody care, ni am tired zan shiga daga ciki in huta good night. Yafada tareda daukar ledar shi  ya wuce tareda datse kofar shi da key, she can clearly hear his voice, Wanda taji jikinta yayi sanyi, bai kamata yayiwa momy magana irin haka ba he is not copying from his brother, shi zuciyar shi daban ce,  don haka bataji dadi ba, koda ya shigo zama kawai yayi tareda kallon ta ” come and feed me madam. Idanun shi har sun canja color, ta matso tareda zuba mai tuwon da ya tuki ta daura su a farar leda daya ta ciro tareda bude kular miyar ta zuba a gefe, tareda namomi, yana bin plate din da kallo, saida ta gama tace bismillah. Dariya yayi kadan domin he can remember when last yaci Abinci mai nauyi koda rana bare dare,  tasan dariyar da yake  yi don haka baiyi zatoba yaji lomar tuwo a bakin shi, tuni ya hadiye tareda zuba mata ido ya kasa cewa komai, kashe mai ido tayi  , Wanda tuni yazama kamar wani rakumi da akala batareda ya shirya ba ya cinye leda daya, Abincin yayi mai dadi sosai, ta ciko cup da zobo ta bashi ya karba saida ya shanye ya mika mata, kawar da kayan tayi gefe domin tasan bata isa tabar wannan dakin ba yanzu don tasan momy na falon, “Saura wanka. Mikewa tayi ta nufi bathroom ta fara hadamai a bathtub,  motsin shi yasa ta juyo bayan ta gama, yana dogare a jikin kofar ta matso ” na hada bari in fita.batasan kallon shi ba kaya firgita ta yakeyi, shammatar ta yayi ya janye hijabin tareda sakin shi kasan bayin Wanda ya zuba mata ido tundaga Kirjin ta har zuwa cibiyarta da yake gani, cikin rawar jiki ya zare zanin, ” Hmmmmmm, kawai ya iya fitarwa saboda ya dauki caji full battery, d’an Kara ja yayi da baya ya na karewa shigar kallo, bazai taba gajiya da kallon kyakkyawar kirar jikin ta ba,  ganin zai iya sumewa batareda ya shirya ba yasa yayi saurin zame boxer dinshi jikin shi na rawa,  idanun ta waje ta juya mai baya saboda shi bayajin kunyar tubewa tsirara a gaban ta, ba ruwanshi da kunyar tsiraici yana katon namiji dashi, kirjin ta har wani tsalle  yakeyi domin taga wani irin bouncing da Aliyar shi tayi  tayo waje kamar tana fusace, matsowa yayi cikin sauri ya manne a jikinta kamar magnet, tareda danna jikinshi tsakiyar cinyoyin ta ta baya domin yasamu ta rage tsallen da zullon da take mai, muryar shi na shaking yace” don’t turn your back on me again, ki kalle ni nakeso kiga irin baiwar da Allah yabawa mijinki just for you, baby we are one, mu saba da juna mu saki jiki da juna, Rayuwa nakeso mu shinfida ba kunya ba boye boye don’t hide anything for me. Yafada yana lasar wuyanta har zuwa kunnen ta, hannayen shi na yawo tundaga kugunta zuwa saman kirjin ta, wani irin nishi taja domin bata iya daukar romancing nashi musamman in ya karasa makasar ta wato her weak point, batareda ta shirya ba taji rigar ta akasa yasa hannu ya zame  d’an wandon cikin A zama, ta kan kameshi domin akwai haske a bathroom din bazata iya tsayawa a gaban shi a tsirara ba akwai kunya sosai, kamar ta karawa kananzir fetur haka ya kasance bai wani tsaya wata wata ba ya mata wayau ya kwace jikinshi yaja baya tareda zuba mata ido, baya ko iya budesu da kyau saboda jarabar data gama tadomai, Y’ar Kara tasa ta nufeshi da gudu ta shige jikin shi domin boyewa, saida yakusa zubewa domin kowane Abu tayi batasan ya yake kasan cewa ba, “Ahhhh Yafada tareda kankameta ya cirata ya ware cinyoyinta suka zagaye west dinshi, dakyar yake daga kafa ya shiga bathtub din, atareda ita sarkafe a jikinshi kamar zata fasamai kirji ta boye don kunya, kokarin cirota yakeyi ta hana, gashi yanaso yayi Abinda zai kawo mai saukin halin da yake ciki taki bashi dama, wani murmushi yayi tareda sauke hannu yashafo bayanta Wanda saida tayi zillo tareda sakin jiki yay I nasarar sauke hannun shi a kasan ta batareda tayi zatoba, duk wata gaba ta jikin ta ta saki zubewa tayi ta manta da wata kunya domin khaleel ya san inda zai kassara ta cikin ruwan sanyi,  cikin minti biyu tuni ya maida gangar jikinta kamar gawa juyata yakeyi a cikin ruwan yanda yakeso, ba inda bai leka ya sude ba tas tas, ba wani liquid na jikinta da baiji test dinta ba, badon yasakata akan network ba da zataji zafi a kirjin ta da rabin wasan akansu yake karewa har wani irin ja sukayi saboda murza da tsotso,  lokacin da yakai inda taji a littafi,  kuka tasa mai jikinta na rawa tace ” Khaleel zaka kasheni ne please kabarni haka manaaaaaa. Dakyar ma maganar ke fitowa, Wanda batada masaniyar bayaji baya gani neman samun natsuwa yakeyi ta kowace hanya, domin bayajin halin da yake ciki yau zai kawo cikin sauki,  marar shi tayi mugun cikan da dole fa sai yaje inda yakamata yayi Ajiyar Ruwanshi masu daraja da Amfani ajikin mace, duk ta saki tayi lakwas, tashi yayi ya dauraye su kawai ya janyo towel ya goge mata jiki ya sungume ta zuwa dakin batareda anyi wankan Arziki ba, shinfideta yayi tareda kashe wutar ya matsa gaban waldrp din shi ya ciro wani oil ya murza a gabanshi domin samun saukin kurdawa don yagama kurda yatsanshi ko wane lungu yaji don haka dole ya nema musu sauki,

 

Saboda irin murzatan da yayi yasa tuni ta  wani irin baccin gajiya yafara daukar ta, hawa gadon yayi tareda danna wani Abu wani irin labule ya zagaye su, yayi saurin raba kafafunshi yayi mata runfa tareda dora goshin shi saman fuskar ta, ya lashi girar ta zuwa idonta, ” hey wake up, dakyar take bude idanun ta, “I want to sleep am tired. Tafada a hankali, “hhh you are joking baby me akayi kofa farawa baayiba, tuni ta bude idanun ta kar, “me kayi min a bathroom zafi nakeji fa sosai. “Baby come on karki zama raguwa mana that my finger let have fun yanzu ne zakiji dadin Abun wancan wasa ne let make this night memorable. Ya cafki lips dinta, tuni ya kwadaita mata jin dadin don haka daga cikin Abubuwan data koya daga gareshi da kuma littafi ta hada ta ruko wuyanshi domin bashi more access da zasuji dadin like he said,

 

Y’an da  take karbar harshen shi tuni tasa yakara daukar zafi ya sauke hannun shi a tsakiyar kafafun ta tareda fara murza clit  dinta Wanda tuni ta ware mai kafar dakyau, kamar y’an da yakeso ya saita kanshi cikin wayau, batareda yabata another chance ba, ya d’an na kanshi da karfi,  Wanda ba Arziki crown dinshi ya samu bula hanyar da saida tayi wani irin Y’ar Kara kadan,

Karar su ce su biyun ta hana aji sautin wurin da kyau domin su duka Kara suka saki dagashi har ita,…….

 

A zaune momy take tayi tagumi a falon tun tafiyar khaleel yabarta cikin tunani kalmar shi ta sanyaya mata jiki, badon tayi data sani ba sai don tayi believe an mallake mata da’  anjuya mai kwakwal wa, Salifa tashigo falon cikin shirin kayan bacci tana karairaya, tace ” mom Ina angon najira har nagaji tundazu?  Duba karfe goma harta wuce, dago kanta tayi cikin takaici ” ke banson iskanci Amarya daren farko bazaki jira miji yasameki da kanshi ba wace irin wayewa ce wannan?

Kamar wadda tasha wani Abu, ” kaji mom yazaayi kina gani nasha magun guna har overdose inyi bacci a haka bazan iya ba haka wancan karon saida na Kwana a wahalce yazo ya mutu yabarni da Abu a mara, ni kice yafito kawai muje ko ni in……. Ihun da sukaji ne yasa sukayi dif tareda kallon kofar dakin khaleel din da  karar ta fito, Wanda momy taji muryar su duka biyun…………. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 4⃣1⃣&4⃣2⃣

 

 

 

 

 

08032252760

08175479641 contact this numbers for more information

 

 

 

 

……………Azabar da taji a kasan ta tafi ta Ummu Ruman, kafafun ta tuni suka fara rawa ta fara kokarin cireshi a jikinta, tareda bude baki tasa sabon ihu saboda kokarin shiga yakeyi dakyau don crown dinshi ne kawai a ciki, he wants to deep down, bayaso ya kuma ihu don haka ya Kama lips dinta kamar sune zasu taimaka mai, ta fisge tana shura kafafu domin neman wurin tsira, ” khaleel zaka kasheni ne please kabarni haka ka cire Wayyo Inna, Wayyo Ahmed, kafada mai baka taba min mugunta ba, Shukrah, Aunty Raliya,  Aunty Aisha, Wayyo malam, ya sadi….. Wani irin dannawa yayi da karfi saboda jin tana kiramai mazan da zuciyar shi zata buga, shifa ko Ahmed duk kaunar da yake mai akanta baya iya boye kishi shi, jin shi yakara kurdawa yasa ya buga sabon ihu tareda cewa cikin fushi da sambatu irin na Wanda baisan me yakeyi ba, ” Ki daina fadin sunan wani namiji a bakin ki my diamond, you’re my wife my own only, Ahmad ba gidan shi bane nawa ne, ni ke sonki nafishi sonki, I love you more than my life my pain relief, wannan gidan nikadai zan shige shi, kema ki rike ni karki barwa wata nan kawai nakeson shiga kibarni ciki pleasesssssss matata.

Fadin sambatun da yakeyi bamai faduwa bane, Wanda tunda ya kuma turawa ta sume mai, Wanda a falon kuwa Mommy saida ta kusan zubewa, zanin ta dake daure saida ya kwance yana shirin faduwa ta dafe Salifa,  wani irin kishi da bakin ciki ya rufe Salifa ta hankade ta Wanda tayi ido biyu da gorar maganin data bashi yaki sha, ta watsa mata harara, ” Amma Mommy Sai kin gane ni kika kawo domin ki wulakanta ni a cikin gidan nan, kin mayarda ni Karamar bazawara yanzu kin dawo kin kuma Auramin d’an ki da baida mutunci, Toh wallahi bazan dauka ba don ba kwantai kukaga nayiba da kuke gare gare dani keda mommy na, ace nice Amarya bazai kulani ba sai wata can Saura, in an raina ma fauziya hankali ni ba’ a isa ba gidan nan mu zuba. Ta fita fuuu tana tada iska, tabar mommy a sume Wanda Sam ba kalma guda daya data shiga kunnen ta wadda Salifa ke fada, tashin hankalinta baifi Wanda ke faruwa a cikin dakin ba, ita kadai tasan rashin hankalin da ta shiga ciki, jin ihun khaleel bamai karewa bane don haka taja shekararrun kafafunta tayi cikin dakinta ta garkame, shikenan khaleel dai yagama da Rayuwar ta wato nuna mata yakeyi shine ya kyeta Naziya, shiyasa yazo mata har cikin gidan ta da Matar son nashi domin ya tozarta ta, tarasa Ina zata tsoma kanta taji karar wayar ta, ganin sunan kawar ta momyn salifa yasa ta dauka jiki a sanyaye, “Kawata…… “Dakata balkisu banson iskanci da rashin mutunci ke kin san ni kin san halina nafiki duniya karki sake kisa rayuwar yata a gararin iskancin ku zan watsa kasuwar uban kowa ya kwashi kason shi a hannu…. ” haba yi hakuri kibarni indauki mataki ai ni na haife shi Kawata to ki zuba ido kiga mai zai faru, Allah ya huci zuciyar ki, ki lallaba min Salifa don Allah muci ribar Abun.  Kashe wayar tayi tana zakici ubanki balkisu don amfanin kaina na yarda da wannan Auren muje zuwa.

 

Kiran Salifa tayi tareda lallashin ta tayi hakuri burin su dai ya cika, ” ki daure mu shawo kanshi kuna kwanciya tare zance ya kare bazai kuma kallon ko balkisu ba bare wata Y’ar gidan malamai, zamu mallake shi da duk Wani Abun Da suka mallaka. ” Toh ni a haka zan Kwana gaskiya dana sani da na nemi mafita. ” kefa kinada jarabar tsiya yau kawai shine bazaki iya hakuri ba? ” mommy kinsan me nasha kuwa nidai an cuce ni gaskiya. ta katse kiran tareda kwanciya tana juyi tareda neman mafita.

 

 

Hour guda ya kwashe a kanta batareda yaji yagaji ba, Wanda ita tun zunguri na uku ta sume saboda shi din ba kadan bane, Abunka da sabon shiga kuma bai bi a hankali ba, Toh Abune da ba asan dadin shiba yau kuma anfara  ji yake kamar ya dawwama a ciki, yasha kuka tasha Alkawura Wanda bata ji ko daya ba, lokacin da yayi release ne ya jita a sake, bayan yadan natsu,  kallon fuskar ta yayi yaga idanun ta a kafe,  zabura yayi har kugun shi na amsawa domin shima akwai rashin sabo a tare da shi, yace ” innalillahi, Naziya “baby, my diamond. Duk ya rude jikin shi na rawa bai wani damu da tsiraicin shiba,  ya dire ya dakko gorar ruwa mai sanyi ya diddile a fuskar ta, shiru, don haka yayi bathroom cikin sauri ya hada ruwa mai zafi ya dawo ya ciccibe ta sai a lokacin yaga jinin dake gadon yayi staining ba sosai ba Wanda yariga yasan normal ne a wurin budurwa mai mutunci,

Sai da ruwan zafin ya ratsa ta kafin ta jawo numfashi, riketa yayi yana mai jin tausayin ta da kuma kanshi domin dai yasan ya gama shiga hannun Naziya, ta gama dashi daga yau, shi bawan tane tunda ta leka dashi duniyar maji dad’i, wani irin kallon so tareda adoration yake  mata, no word can express how he is feeling right now, Abu biyu kawai yake iya furtawa “Am sorry  please stop crying”. Domin jin kukan yake har cikin zuciyar shi, sai da ya tabbatar ta gasu kafin ya saki ruwan ya kunna musu shower ya shiga ciki, da kanshi yake cuda ta tana tureshi domin taji ya fita ranta fit, saboda mugunta da azabar da tasha kuma tana jin wani irin zugi a tsakiyar kafafun ta, ruwan da yasaka tane yasa taji d’an sauki,  amma koya ta motsa tana ji sosai, da dubara yake watsa mata ruwa a tsakiyar tana warewa ba tare da ta sani ba, domin ruwan na taimakon ta sosai, ganin haka yasa yana gama musu wanka ya kuma tara wani ruwan dumin, ba musu ta zauna, tsugunawa yayi ya zuba wa Kirjin ta da suka wani irin ja saboda murza sun d’an Kara kunbura, da gudu yaji Hajiya na Kara tashi, dukar da kanshi yayi ya kalla, “hay young man, don’t kill my wife enough. Yafada a bayyane yana dariya, saurin dago kanta tayi ta kalle shi domin taji sarai, don haka tuni tayi narai narai zata sa kuka, mikewa yayi tareda cewa ” look my diamond, tasan dadi baza ta bari a hutaba let go inside ya isa haka. “Wayyo Allah, wallahi na gaji, zaka kasheni, don Allah karka kuma kaji zan mutu inka kuma, yunwa nake ji kafafuna ciwo kirji na kasa na kaina hannu na, yanzu zan mutu inka kuma,Yaya khaleel ka tausaya min. Fuskar ta gwanin tausayi, Wanda sai da yaji wata irin dariya na shirin kufce mai, ya gimtse tareda dagota cak, sukayi ciki, zaunar da ita yayi kan kujera ya rufeta da katon towel ya kwashe zanin gadon ya dakko wani ya d’an shinfida duk da bai wani iyaba,  kanta akasa saida ya matso again tace ” don Allah kasa kayan ka. domin mugun tsoro wannan Abar ke bata gata tana mike, murmushi yayi ya wuce ya dakko towel ya daura, ” na rufeta my diamond, Amma nima inada complain, baya na, kinganta ma  ya fara yana bude towel din, “kinji mata look. Kauda kai tayi tasa mai kuka, Saurin rufewa yayi tareda rungume ta gam a kirjin shi, “don’t cry baby yau bai Kama ta kiyi kuka ba, ya kamata in faranta miki ne the way you make me happy, you have no idea how happy I am right now, yes am married today, ni ango ne yau, you have to be strong, idan nace miki zan kyaleki har safe ban kuma ba karya zanyi miki, bana son karya ban iya taba, kukan ta ya kuma karfi, tana girgiza kai domin she can’t beg him again, tashi yayi ya dakko ledar naman da ya zo dashi yana bude wa, ” kinga our Amarci is special, Amarya na cin kaza ta biya ke saida kika biya zakici. Ya fada yana dariya tareda kashe mata ido,

Yunwa take ji sosai, domin ji take kamar ya kwashe harda y’an hanjin ta, don haka ta zage ta kwashi nama ba Arziki, like he said ta biya kuma tasan y’an da ya fada zai kuma ba fasawa zaiyi ba don haka ta sadakar  yau mutuwa zatayi don haka ta zage ta cika cikin ta na karshe.

Saida yaga tayi kat, ya bata madara mai sanyi tasha kadan, shima yaci ya kora, da kanshi ya kuma daukar ta zuwa bathroom ya wanke musu baki,

Duk ta sadaukar a wannan daren, tana ji tana gani ya dawo da ita ya shinfide tareda kashe hasken dakin, ya wurgar da towel din jikin shi ya hayo,

D’an ja tayi gefe da nisa, ya matso tareda shigewa ya manne jikin shi mai matukar kanshi da laushi, ya hadu da nata, ” Baby, tank you for being my wife, tank you for disvirgin me in this memorable night. Ya fada yana dariya tare da manna mata kiss a gefen kumatu, “please zanyi bacci.  tafada gwanin tausayi, don Allah kadai yasan halin da take ciki, “how can you feel sleep ?  Bai kamata muyi bacci a wannan daren ba, bakisan halin da nake ciki ba baby, this is our first night, first time, we need to practice more, kinga nima am in pain, but I need to test you more and more a daren nan, do you know, this is the sweetest thing ever. Yafada yana shafo tsakiyar cinyoyin ta, saida taji wani irin yar a jikinta, ga dayan hannun shi kwakume da kirjinta yana murzawa,

“Baby Yaya na yayimin duk wani gata da Adalci a rayuwa ta, domin da yafara sanin ki kafin ni, zanji ba dadi duk da Ina matukar son shi, kin san bantaba son wata mace ba sai ke?  Da tafara lumshe idanun ta zata runtsa taji wannan kalmar da tafi kowace dadi, wadda ta goge duk wani ciwo da take ji nadan lokaci, juyowa tayi tareda fuskantar shi batareda ta damu da tsiraicin suba, duk da ba wani haske bane sosai but they can still see each other clearly, cikin kwayar idanun ta ya kalla, ” I love you Naziya, bansan why kika kasa gano hakan ba, nafara sonki tun daga ranar da na raka Yaya na gidan ku the first time I saw you, I feel hurt when ever kuna tare da Yaya na, I felt very jealous I cried sometimes because is impossible to get you, I course my heart for loving my brother wife, my brother really loves you, but I love you more than him Naziya, that is why I call you diamond, you have no idea how special you are. Yana fada yana kissing lips dinta, fadin y’an da take jin kalmomin nashi a zuciya ba zai misaltu ba,  tarasa me zata ce, kawai matsawa tayi ta shige kirjin shi suna feeling chest din juna, saida ya runtse idanun shi, domin he can feel her chest a nashi kamar ya suma, tuni yakai mak’ura, duk da labarin bai kareba, yace ” to be continue, now feed me make me the most happiest ango please.

Ba karamin wayau take ganin yake shirin yi mata ba a yanzu domin kab ya siye zuciya da gangan jikinta cikin sauki,  tuni ta sakar mai ragamar rayuwar ta baki daya, sarrafata yakeyi ba tare da ya tsaya cutar da kanshi ba, he wants to satisfied himself in this memorable night, tun tana iya mayar mai da wasannin da yake mata har tafara gazawa, jikin shi na rawa ya fara neman hanyar, kamar ba ita ya kutsaba dazu ko yanzu jiyayi wurin ya rufe, saidai ita ba haka bane, domin yana dorawa taji muguwar azaba tuni ta farka daga duniyar dadin romance din da ya kashe mata jiki dasu, tayi wani irin Y’ar Kara kadan tareda saka hannu ta rike gaban shi badon ta shirya ba.

 

Wanda batasan me ta aikata ba, domin wani irin zabura yayi saboda dadi ya ce “Ahhhhhhhhh, babe hold it tightly yana wani irin gurnanin da yabata tsoro, saurin saki tayi jiki na rawa, Wanda yasa bai wani jiraba ya ware kafarta ya danna da gudun gaske, ai ya riga ya bude hanyar, a gaskiya ba Abinda yakai rayuwar Aure dadi musamman ka Auri Abinda ka ke so to ka gama morewa, don haka saida ya ji shi can inda bai samu zuwa dazu ba, Wanda Naziya kuka ya gagara sai jan dogon nishi, saboda azabar zafi, bubbuga shi takeyi tana girgiza kai domin she can’t talk, Ina shine ke ihun da bazai taba gane me takeyi ba,  kafin minti talatin tuni ta kuma sume mai, Wanda shi idan ya kyaleta mutuwa ma zai yi, domin wannan dadin idan yabarshi a daren nan zai bar uwar shi  shima,

 

Ta yabawa Aya Zakin ta  ba tare da ta sani ba, domin ta dade a sume, shikuwa yasha budurin shi, yau yake ango ya Kira sunan mommy ba iyaka tazo tagan shi, yau ya girma ya zama big boy, he is a man today, come and see Mommy am healthy, I don’t need anything zan iya Kwana akan Naziya ita kadai. Wanda yake fada ba tare da ya sani ba, sai kusan karfe hudu, ya samu yaji shi dai dai Wanda ya zube a gefe yana nishin gajiya shima, bayan shi ya rike, Amma marar shi kamar an wanke mai ita tas saboda yayi mugun juye,

 

We can say, mommy sai da ta kulle kofar ta gam ta daina jiyo sambatun khaleel, Wanda ta Kwana da mummuan kuduri a ranta, mugun zafi jikin shi ya dauka, domin wani irin zazzabi ne ya rufeshi, haka jikinta kamar wuta, da kanta ta dawo hayyacinta ba tare da ta iya motsa koda yatsar taba, idanun ta a rufe, shigewa yayi jikin ta ya rungume yana hawayen farin ciki, Naziya is beyond imagination, duk da bai san mace ba yasan ita din ta daban ce, bazai taba gajiya da itaba mutu karaba shida Naziya, baiga Abinda zai sa yayi rayuwa bata ba, ta zamo jinin jikinshi tsokar zuciyar shi farin cikin shi uwar ya’yan shi insha Allahu.

 

Baccin da bai iya yiba kenan, saboda zazzabin jikinsu, numfashin ta ma zafi yake fitarwa, saida aka Kira sallah ya daure ya shiga bathroom, Amarya ke gashi, Amma shi ma yau dole ya shiga ruwan zafi, ya gasa jikinshi yaji d’an sauki kadan ya tara wani, ya dawo ya dauketa, jinin da ya kuma gani yasa yaji tsoro. “Blood again?  yana sakata ruwan suka fara canjawa, jikinshi na rawa ya dawo ya canja kaya tare da fito mata da doguwar riga a waldrp dinshi,

Ya koma tana kwance kamar ruwa, yanzu yafara daya sanin Abinda yayi mata, ko motsi bata iya yi, ba Abinda ke bashi tsoro irin jinin da yake gani, don haka cikin sauri sauri ya saka mata riga ya zura mata hijabi, karfe biyar da rabi, ya kin kime ta sukayi waje, Wanda yayi dai dai da Mommy ta fito, ta bishi da kallon wulakanci, ” Ina zakaje yanzu da Asuba?  ” Mommy hospital she is bleeding. Please kisa maid ta goge kasan dakina ta gyara min gadon.

Tana lafe kamar matacciya a kirjin shi,

Tana jin komai saidai bazata iya motsi ba, ” ka nuna min ban isa da kaiba ko, Toh listing to me, idan kuka Fita yanzu kadawo min da ita cikin gidan nan sai na tsine maka, daga inda zaku je ka kaita gidan ubanta, daga yau tabar gida na, kayi Abinda zaka iya nima yanzu zanyi nawa mulkin muzuba nidakai zamuga waye a sama.

Shiru yayi kadan har yayi gaba ya kuma tsayawa, “Mommy don’t please. ” nafada maka idan yarinyar nan tadawo ban yafe maka ba khaleel Allah ya isa nono na daka tsotsa. Juyawa yayi kawai ya Fita. Zuciyar shi na wani irin d’aci, tanajin komai don haka wasu hawaye kebin kuncin ta, a hankali ya Ajiyeta a motar ya share hawayen ta, bai iya cewa komai ba, burin shi dai ya kaita Asibiti a dubamai ita koma meye zai biyo baya, a natse yake driving, har ya isa family hospital dinsu, ba bata lokaci yasamu babbar likitar wurin doctor Asiya, ta karbeta, tace “Sir Ibrahim meye damuwar?  Zuciyar shi daya yace “check her well she is bleeding doctor. “Tana da cikine?  No is our first night. Yafada yana komawa gefe tareda nade hannu a kirji, kallon shi tayi ganin irin full confidence din da yake magana, ta girgiza kai, “this Ajebotas Hmmm”, wayewa ce taja ko kudi ko rashin kunya?  A ranta take magana, tace “excuse us Toh zan duba ta. Wani irin kallo ya mata yace “she is my wife. “I know but bazan iya aikina kana tsaye ba you have to go out. Fita kawai yayi domin yana cikin stress ya bar ta, masallaci ya nufa mafi kusa domin ya sauke farali.

Saida ya kwashi hour guda yadawo, lokacin har tasamu bacci an daura mata drip da Allurai,

Likita yasamu tace “we need to talk sir” let’s go to my office.

Saida ya matsa gaban gadon da take kwance, fuskar ta harta fada a dare daya, wani irin tausayin ta yakeji, hakurin ta yayi yawa, a hankali yake fahimtar ita din batada hayaniya tanada hakuri mace ce mai biyayya, Naziya bazai iya hadata da komai ba yanzu a rayuwar shi,   Kirjin ta ya shafo ya Fita,

A zaune doctor din take tana rubuce rubuce, yaja kujera yace ” Any problem doctor? ” yes sir, please kar akuma yimata irin haka, domin taji ciwo ta ciki shiyasa take bleeding, akiyaye gaba arika bi a hankali ba guduwa zaiyi ba you have just started ne, yanzu drip din da na bata zai taimaka mata tasamu karfi, at least tayi two weeks stitches din su warke. “Stitches?  Ya tanbaya cikeda damuwa, ” yes ba da yawa bane kadan ne, ka bata two weeks everything will be Aright. “Tank you doctor. Yafada ya Fita tana binshi da kallo, “yarinya dole kiji jiki irin wannan miji naki daga gani kin boni.

 

 

Zama yayi tareda yin tagumi ya zuba mata ido kamar zai cinyeta, ” you deserve to be happy baby, why Mommy ta kasa gano cewa kedin kinfi sauran matan da take so ne , why she hate you?  Kyakkyawar fuskar ta ya shafo yayi Ajiyar zuciya, tareda ciro wayar shi a Aljihu ya shiga contact yana searching numbers,  ganin number da yake nema yasa yayi dialing,  ringing biyu aka dauka, mikewa yayi ya matsa, ” Aunty Ina Kwana. “Khaleel kaine ?  Ince ko lafiya?   “Lafiya Aunty sai dai muna Asibiti da Naziya yanzu, please inba damuwa inzo in dakko ki? ” Toh meke damun ta haka harda Asibiti?

Bai taba sanin yanada kunya ba sai yau da yake magana da Aunty Raliya,  don haka ya sosa keya yace zazzabi ne kawai. “Toh yanzu Baban yara zai Fita zanbiyo shi, wane Asibiti ne?   Yafada mata, tace tana zuwa, yayi godiya tareda Fita yasamu doctor. Yace yana bukatar taimakon ta, “please sister din madam na zuwa you have to explain to her Ina so ta tafi da ita tasamu kulawa kafin in tafi da ita gida, kar asamu matsala gaskiya, two weeks is too much for me. Yafada da zuciyar shi daya, ido kawai ta bishi dashi tace ba matsala, yayi godiya ya tafi………. 🖊

 

 

 

 

 

Not easy for me guys sorry please �

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 4⃣3⃣&4⃣4⃣

 

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

………… A gida bayan fitar su da sauri ta fada dakin nashi, taga zani daya a kasa ga nakan gadon ma yayi kaca kaca, wani irin turnuki taji a zuciyar ta, wato khaleel da ace Asibiti ta haifeshi da tace anyi mata canje, ta manta da kana haihuwar Wanda yafika tsaurin ra’ayi,   kwalawa mai aiki Kira tayi, ta nuna mata dakin cikin takaici ” clean this mess right away. Ta Fita sai zagaye takeyi tana neman mafita tarasa ta Ina zata bullowa Al amarin khaleel, Zarah ta Kira tunda farar Safiya, ” Aunty lafiya fa safen nan?  Tafada cikin tsoro, ” Ina fa lafiya zarah, ni bangane aikin malamin nan ba waya rana yayi wata rana kuma lamari ya barkace. ” meyafaru Aunty? ” khaleel….. Tafada mata komai in details. “Kema Aunty ke keja ki cire idanun ki aiki ai ahankali yake farawa kuma idan kika matsa za ayi biyu don tsab khaleel zai sallami salifa. “Bazaiyi ba don yana tsoron tsinuwa ta shiyasa ko yanzu na fada mai karta dawomin gida inba hakaba banyafe mai ba. “Kash Aunty me kikayi?  Kinsan dai bazai sake taba, what up ya nema mata gida daban? Dafe kirji tayi ta tuna da kalmar shi bazai taba sakin Naziya ba, kuma tasan halin Abinta, “zarah kice na bato lamari?  “Gaskiya Aunty wata rana bakya shawara kike aikata Abu, bakya yin Abinda ya dace. “Zan janye tsinuwar bari inkirashi in lallaba shi don karya sauke akan salifa. ” zai aikata kinsani sarai bai barin Abu abanza.

Kashe wayar tayi ta fara neman shi jiki na rawa. Lokacin ya fito daga Asibiti domin duk hankalin shi na cikin dakin yanda yabarshi yasan momy bazata gyara ba, yaji karar wayar ta, dauka yayi kamar nothing happened, ” khaleel Ina kakai yarinyar nan?  Shine tanbayar da tafara yimai, yayi shiru kadan yace ” Ina hanyar dawowa am close, ya kashe wayar.

Yana dukan sitiyarin yana fesar da numfashi, ” I will fight this battle alone Yaya Ahmed, Allah ya jikan ka ya biyaka da Aljannah. Yafada yana jin duk wani damuwar sa  ta  gushe da ya tuna da cikin ni’ima da farin cikin da ya Kwana,   Aure dadi, Naziya karshe ce a cikin mata, tuni yafara kewar ta yaji kamar ya juya ya koma  ya rungume ta, jin kanshi yakeyi a sama,  koda ya shiga gidan ya parking, masu aiki na gaishe shi yana amsawa cikin fara’a da wani irin Annuri. Gefen momy ya wuce, tana tsaye tana zagaye taja doguwar Ajiyar zuciya ganin shi, ta tashi, matsowa yayi fuskar shi a sake ya zauna a gefen ta ” momy good morning, dazu na Fita ba a natse ba. Kallon fuskar shi tayi tana hango sheki da Annuri tareda kwantaccen farin ciki a fuskar shi,

“Khaleel Ina ka kai ta?  Answer me? ” Momy in her condition Ina yakamata inkaita inba hospital ba?  And forgive me if I did anything wrong to you, Ina so inyi miki biyayya momy nima one day kiyi min Addu’a exactly yanda kikewa Yaya na, idan nabata miki rai, forgive me bakin ki guba ne dafi ne, fushin ki damuwa ne,  Ina sonki mama na, please ki tayani son Abinda nake so, Momy kin tanbaye ni why I marry Naziya without rejection?  How can I reject the woman I love more than my life?  Momy Ina son Naziya tun Yaya na na Auren ta batareda nasan zan mallake taba,  kince karta dawo cikin gidan nan, bazan dawo da ita  ba, insha Allahu I will obey you Momy. Ya zabura ya kama hanyar dakin shi takasa cewa komai, sometimes sai zuciyar ta taso tausar ta saita kasa so take ta bashi hakuri Amma tunanin Alkawarin da tayiwa kawarta da kuma ego dinta ya hanata tana kallo harya shige dakin lokacin maid din na kokarin shinfida mai wani bedsheets, wani irin tsawa ya buga mata ” ke uban waye yace ki taba min kaya?  Get out.

Jikinta na rawa ta fice, ya kwashe zanin gadon masu stain ya kwabe ya shiga bathroom da kanshi ya wanke su tas Abinda bai tabayi ba wanki irin wannan,

Saida ya gama ya dawo cikin dakin ya canja bedsheets da kanshi, ya daura towel ya shiga bathroom saida ya hada ruwa mai zafi ya shiga ciki shima domin shikan shi yana bukatar su, kwanciya yayi yana wani irin murmushi mai cikeda da ma’anoni, “baby this is your work fa, kinsani gashi, all my joint are paining me, what a sugar. Yafada yana sude lips domin he can still feels her sweetness,

Imagine yake idan ta warke how he is going to spoil her, yanda bazata iya rayuwa batareda shiba, ” we are going far away   from all this problems. Ya dauki dogon  lokaci a cikin ruwan kafin ya fito, zama yayi gaban mirror ya fara kalkale ko Ina na jikinshi, kafin ya fito dakin, saida ya gama nazari kafin ya fito da wata farar shadda, ” am ango today. Ya zura harda hula ya ciro agogon shi ya daura tareda katon Azurfan shi,

Kamar ka sace shi ka gudu, haka ya baza kamshi, ya kwashi wayoyin shi ya fito harda nata,

 

Yana fitowa tana sawo kai cikin karai raya da sanabe, lokacin da tayi arba dashi saida ta kusa zubewa saboda ya tafi da imanin ta, ” wow is he really my husband? Oh my gosh. Kamar invisible haka ya ganta, ya fito da wayar shi dake Kara ya yi saurin picking, “Aunty kinzo ne?  OK gani nan zuwa. Yafada yana wuce ta cikin sauri.

Kamar doluwa haka ta tsaya har ya bacewa ganin ta yabarta da fitinannen kamshin shi.

Saida Momy ta fito rikeda jaka zata tafi aiki  taganta a tsaye kamar wata yar kwaya tana bin kamshi, “Salifa lafiya?

“Hmmm Momy. Tafada tana matsowa cikin salon iya shege, ” kin iya haihuwa what an Angel. Tafada tana rungume ta, ” kingan shi kuwa?  He look very handsome and classy, wow I love him wallahi yafi Ahmed komai wow gwara da ya mutu na Auri wannan……… “Ke meye haka banson hauka,  agaban Idona kice gwara da Dana ya mutu?  Banson rashin hankalin ki da rashin iya magana. ” Allah ya baki hakuri Momy yau ba kida laifi ganin khaleel yasa ba Abinda zai batamin rai yau. Ta rungume ta, ” Momy kisa yau yazo gareni please. Cireta tayi a jikinta ” matsa min zanje aiki karinyi latti. Kawai ta iya fada domin Abun ya mata wani iri wannan idanun ta budewar su ya wuce misali,

Fita tayi tabarta tana faman tsallen shauki da son khaleel, momy da kanta ta shiga motar ta ta tayar idan ka kalleta zaka gano cewa jikinta a mace yake yau,  kawai maganar da Khaleel ya fada mata ce ta dameta musamman kodai ba ita ta haifesu ba?  D’an cikinta na tantaba akanta, is she that bad?  Me tayi musu wrong a rayuwa da har yafada mata irin wannan maganar?  A haka ta tafi  jikinta yayi matukar sanyi.

 

 

Asibitin ya shiga, saida ya nemi likitar, tace ta sallameta ruwan ya kare kawai zata rika yin sit bath ne, akai akai har dinkin ya warke, nama yiwa Y’ar uwar ta bayani. Tafada tareda rubuta musu wani cream mai saurin warkar da ciwo, ya karba, ya Fita, saida ya d’an tsaya a kofar dakin da take domin kunyar Aunty Raliya yakeji sosai kafin yayi ta maza. Yana tura kofar, ta dukar da kanta kasa domin basai yace komai ba wannan fitinannen kamshin nashi ya isar mata da sakon isowar shi, sallamar shice ta biyo baya,  Aunty ta mike daga kan kujerar ta amsa fuskar ta cikeda fara’a. “Harka iso khaleel?  “Eh Aunty yafada yana mai kallon cup din hannun ta dake dauke da kunun gyadar da Aunty tazo mata dashi.

Juyawa tayi tafita kawai domin basu space, Wanda hakan yakeso dama, tun shigowar shi yake satar kallon ta,

Tayi mai kyau so yake ya matsa jikinta har wani irin fisgar shi gangan jikinshi keyi zuwa gareta, don haka Aunty na Fita ya daga kafa cikin sauri ya isa gefen ta ya zauna tareda karbar cup din ya Ajiye, taki yarda su hada ido dashi domin ita kam tasan kunya duk Abinda ya faru Ina taga karfin zuciyar hada ido dashi,

Ji kawai tayi ya rungume ta gam a gefen kafadar shi, “Am sorry baby nasa anyi miki stitches, ba laifina bane, lafin kine you are so sweet, so so sweet that I can’t control myself, you deserve a gift, but not here, ya dago kanta ta runtse idanun ta, ya ce ” please open your eyes kinji I want to see them.  Kara runtse idanun tayi don kunya takeji, ” oh come on, meye kunya a tsakanin mu yanzu, kin zama ni nazama ke we shear the same bond same blood I can feel you all over my body and my soul,

Lafewa tayi luf a kirjin shi, bata bude idanun ta ba kuma batace komai ba,

” why are you always silent?  Talk to me feel free, complained let me know what is going on in your heart even once please, Momy a kullum tana miki fada duk kalmar ta  akanki batada dadi it hurt and touch me, ke kuma you don’t even react, why?

Sai lokacin ta dago tareda kallon shi cikin ido ” me kakeso inyi?  In Rama?  ” you have the right. Yafada yana mata wani irin kallo. ” girgiza kai tayi ba tarbiyar da aka dora mu akai ba kenan, babba kullum adai dai yake yaro ke laifi, me tayi wrong?  Saboda tanaso ku Auri mata dai dai da Rayuwar ku?  She is right tanada dama kuma uwace ta isa, kuma ra’ayi da burinta takeson cikawa, kayi mata biyayya please give her what she want.

Hade fuskar shi yayi, ” do you know what that means?  ” yes ka sake…… Bakin shi yayi saurin dorawa akan nata ya fara tsotsa cikin zafi zafi, har tanajin yana cizon lips dinta da d’an mugunta saida ya dauki lokaci ya janye, ” don’t repeat that, it hurt to hear from your mouth, na tsani kalmar rabuwa dake ko a mafarki, don’t even imagine that again, Aure na dake mutu ka raba takalmin kaza ban rabu dake tun farko ba sai yanzu, mahaukaci ne ni, rabuwa dake yana nufin rabuwa da numfashi na, zan iya rabuwa da kowa bazan iya rayuwa babu ke ba.

Wani irin sanyaya mata zuciya da gangan jikinta kalaman shi sukeyi, duk sun warkar da wani ciwo da damuwar ta, yes da zata iya bude baki data fadamai itama bazata iya rayuwa bashi ba, tsanar da taji wasu Amare na yiwa Angwayen su just  saboda sunyi musu biji biji ita ba haka bane a zuciyar ta, she love him more, yes tana son khaleel saboda shi din namiji ne tsayayye d’an ra’ayi in yace yes baya canjawa, ba kamar Ahmed ba, shine ya cika burinta shine yazamo mata mijin da ke share hawayen ta da damuwar zuciyar ta, yes she love him koda shi baya sonta, domin ita har yanzu gani take yanayi ne domin yayan shi,

Jin hannun shi a saman kirjinta yasa ta zabura ta kalle shi, kashe mata ido yayi tareda rada mata” Allow me, I missed them tunfa jiya yafada yana maria raice fuskar shi kamar wani jariri,

Ture hannun shi tayi “Aunty na jira. Dafe kai yayi ya duro, ” kinga kinja mun shanyata. Hannu yasa ya sauketa,  yace “walk slowly karki karamin wasu kwanakin kisa in suma.

Shiru tayi kawai don yaci ta gano cewa shifa baisan kunya ba, hijabin ta ta gyara ta zura silifas dinta, Aunty Raliya tayi sallama, yace “ya gama kimtsawa Aunty muje. Gaba yayi cikin sauri, sukuma suka biyo shi, satar kallon shi takeyi,   yana tafiya, a karon farko tana hango mazantaka da jarumtar shi komai nashi Abin burgewa ne, sai Ajiyar zuciya takeyi har suka isa wurin dalleliyar motar shi,

yanzu take lura da lamarin shi, a koda yaushe sabuwar mota take ganin shi da ita, saboda Alfahari ko rashin sanin Abinda zaiyi da kudi ne ya janyo?

 

Saurin zagaya wa yayi ya bude mata gaba tareda kallon ta yace “here. Zagaya wa tayi a natse take tafiya domin zafin da takeji, a hankali ta zauna, Aunty Raliya tuni ta shige baya. Saida ya fita cikin Asibiti yace “Aunty kinyi magana da doctor? ” eh tafada min komai yanzu ba damuwa muje gidan nawa da ita, Amma banson malam yasani don zai iya yin fada. ” no ba Wanda zai sani, in one week ma zanzo indauke  ta. ” Allah ya kaimu. Tanajin su batace komai ba sai sauke hannun ta da tayi gefen break, Wanda kamar jira yakeyi ya dora kyakkyawan hannun shi akan nata, ya damke tareda murzawa kadan, kallon shi tayi cikin sauri tareda nuna mai Aunty da ido,   yagane me take nufi ya basar tareda dauke kanshi yasa a titi, tuki yakeyi cikeda nishadi da farin ciki, Aunty Raliya kuwa batama san me sukeyi ba tana danna wayar ta tareda yiwa Aisha bayani ta wtsp don bata yin Abu batareda sanin kanwar tata ba,

Naziya kuwa hannun shi ta kalla,   haka kawai ta kasa dauke idanun ta bata taba ganin namijin da Agogo ya zauna a tsintsiyar hannun shi ba kamar khaleel, ga sumar dake kwance a ko Ina har bayan hannun shi, takasa dauke idanun ta akai ga kasalar da ya sakarwa gangar jikinta saboda y’an da ya ke murza tafin hannun ta. Komawa tayi ta lafe tana kallon hannun har suka isa unguwar su Aunty Raliya, yana tsayawa Aunty Raliya ta bude tafita, itama ta juya zata bude ya riketa gam, Aunty tace ” kushigo khaleel, Naziya falo a bude yake. Tayi gaba, datse kofar motar yayi tareda matsowa yace ” kema kina son agogon mijinki?  Yes mata da yawa nafadamin agogo na yimin kyau a hannu, gashi kema ya burge ki. Kwace hannun ta tayi cikin haushi tace ” su yake burgewa meye Abun burgewa a nan?  Dariya yayi ya fisgota zuwa tsakiyar cinyoyin shi, tace ” meye haka a waje fa muke inwani ya ganmu fa?

 

 

” Nida matata ne Ina ruwan wani, kuma ai ba maiganin mu sai dai mu ga mutane. ” let me go?  “Let go inside together bangaji da ganin kiba, kinsan yakamata by now ace muna can cikin bargo muna shan dumin juna amma kinja mana, “wait yaza ayi yau inyi bacci?  Yafada yana matse fuskar shi, “akwai matsala gaskiya. Ya shafo kanshi ji yake kamar ya fasa barin ta anan Amma yasan bazai iya fadawa Aunty Raliya ba. Sauke ta yayi cikeda damuwa ya bude motar tana kallon shi, ya zagaya ya bude gefen ta, kamar wata kwai haka ya dagota, saida ta matsa saboda unguwar akwai idon jama’a gashi anga first class car kowa dole ya kalla, ita tafara yin gaba ya bi bayanta baya ko kifta ido,

Tafiyar ta yake kallo yasan akwai matsala, yayi dariya kadan, ” khaleel kazama namiji. Cikin dan madai daicin falon ta shigar dashi kafin tace Ina zuwa. Tayi gaba, Aunty Raliya har ta hado mai breakfast a tray, tace “ungo jeki bashi yaci daga gani ko karyawa baiyi ba. Ba musu ta karba takoma falon, yana ganin ta ya mike ya karba, ya Ajiye tareda cewa “bakowa ne agidan?  ” eh yaran suna school megidan ya fita aiki.

“Hmmm yace ya nufi kofar da ta shigo ya kulle tareda dawowa ya kulle ta falon ya janyota kasan carpet din ya zaunar da ita a natse , hijabin jikinta ya cire mata, ya kalli tulin kirjinta yaga ba bra domin bai samu tsayawa ya saka mata ba, hannun shi ya dora tareda shafowa suka ja Ajiyar zuciya a tare, tuni lafiyar shi ta harba ya shige jikinta yana jan numfashi, ” baby zan wahala wallahi da yawa, how can I spend two weeks without…….. Ya dora bakinshi saman wuyan ta ya tsotsa har zuwa kirjinta inda yake d’an bayyane saboda wuyan nada fadi, sai dada sauke wuyan yakeyi badon badon ba ko…. Hmmm, manne kawai yakeyi yarasa Ina zai sa kanshi, ” ki lallabani in bar gidan nan kar inyi barna,   yaja dogon numfashi.

Muryar ta a shake domin shidin ba namijin da zai taba mace ta ture bane don haka duk lokacin da ya kusanto ta bata iya tserewa ko me yasa?  Cikin  rawar murya tace ” ga breakfast kayi ka tafi. ” you are the best breakfast for me now. Yayi saurin cafkar lips dinta yanasha kamar su zasu bashi natsuwa, saida ya kwashi tsawon lokaci, yaji karawa kanshi damuwa ma yakeyi, saida taji tausayin shi badon akwai dinki jikinta ba, ba Abinda zai hanata kashe kanta a yau ta rayashi koda a zauren malam ne, domin jitake kamar su kasance tare kar yaje ko nan da can.

Da kyar tasamu yaci breakfast din kadan ya mike tareda cewa ki cewa Aunty sai nadawo Anjima. Ya ciro wayar ta ya d’an ka mata tafiya jikinshi a mace.

Yabata tausayi sosai,

Kwashe kayan tayi ta koma ciki, Aunty na zaune ta tashi ta karba ta wuce tana cewa kizo ki shiga ruwan zafi kiyi wanka.   Saida ta gasa jikinta sosai ta fito Aunty tabata wata doguwar rigar da zatayi mata, tace ” kisa ya kawo miki kaya mana. ” uhm tace, saida tasha magani ta kwanta a kujera Aunty ta zauna tace ” Naziya, meke faruwa ne agidan naku? ” bakomai Aunty likita ce tace Ina bukatar hutu…. ” no mezaisa ya kawomin ke akwai matsala inada wayau fa niba yarinya bace, yanda nake ganin Abinda ke faruwa tsakanin ku yanzu nasan kuna son juna keda shi, kuma dole ki fuskanci matsala, Ina kishiyar ki take?  “Ni Aunty ko ganin ta banyi ba, kuma momy ce tace idan yadawo dani cikin gidan bata yafe mai ba. “Hmm Allah ya kyauta’ to yanzu shi yacemin zai dawo ya dauke ki meye plan dinshi? ” Bansani ba don baice komai ba akai.

“Shawarata kibi mijinki duk yanda yakeso ba biyayya akan sabon Allah, koda kuwa umarnin uwar shi ce don haka Ina respecting dinshi namiji ne khaleel jajurtacce ki natsu ki saki jiki ki rungumi kayanki.

Sun dade suna hira har Aunty ta shiga kitchen ta barta domin dora lunch, wayarta ta janyo, so take ta kirashi  tana tunanin me zata cemai she is Already missing him, shikuwa office dinshi ya wuce, yana zaune dafe da kanshi saboda damuwa, bayajin zai iya komawa gidan su bata ciki bazai taba jin dadi ba,  yaga ringing daya na kiranta kuma ta kashe domin harta fara dialing ta kashe don batasan me zata fada mai ba,

Murmushi yayi ya ce ” just call me mana why this plashing?  Ya d’an jira kadan yaga bata kiraba, kawai yayi dariya ya dauki wayar shi ya mata transfer na ten k kai tsaye, saida yaga sunje ya tura mata message “no need to plash Mrs khaleel.

Kunya taji sosai dataga kudin da ya turo mata all her life bata wuce na dari biyar tun Ahmed na nan sai gashi ya turo mata na dubu goma kai tsaye me zatayi dasu?  Kuma ma ai tanada kudin kiran kawai kunya takeji.

Jin shiru bata kiraba yasa ya kirata, ba wani jan Aji tayi picking hade da sallama cikin sanyin murya. “Mrs khaleel ya akayi ne?  Are you missing your husband? ” no kayana nakeso akawo min. Tayi saurin fada. “No problem koda missing dina kikeyi, ni Ina kewarki Ina office nakasa sarrafa Kaina……. 🖊

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 4⃣5⃣&4⃣6⃣

 

 

 

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

 

…………” Ina jiran kayan. Tafada tana kashe wayar ta, tareda runtse idanun ta tana tunanin dama zata iya yimai hira tareda kwantar mai da hankali da tayi, domin yana bukatar abokin shawara, ba ruwan shi da kowa yayan shi ne abokin shawarar shi, gashi baya duniya, Abubuwa na faruwa Wanda yake hadiyesu batareda complain ba, she like his style na tsayayyen namiji jajircecce yafi Ahmed karfin zuciya,  a haka bacci mai dadi harda mafarkin shi ya dauketa,

Gefen khaleel kuwa, bai iya tsinana komai ba ya koma gida, part din ta ya shiga yayi wanka ya canja zuwa kanan kaya kafin ya janyo troly ma dai daiciya ya fara zabar mata kaya, duk manyan kaya ne sai hijabai, kafin ya dauka yaje ya saka a motar shi, ya shiga gidan Momy, tana zaune tana waya Yanayin sallama ta kashe  tareda sakin fara’a, “Ibrahim kadawo?  Nakira manager yace kana office. “Eh am just coming back. “Fita zaka yi?  “Eh zankai wa Naziya kayan ta indawo ne. Yafada kai tsaye, ” Ina zaka kai kaya?  Ka sake ta ne? ” why zan saketa Momy likita ya bata bed rest so na kaita gidan ya Yar ta ta huta. Wani irin kallon takaici tayi mai ” khaleel karya dokata kake son kayi?  ” ko kusa Momy bazanyi Abinda kika yi Allah ya isa akai ba. ” then what is your plan khaleel karka yi wasa dani fa ranka zai baci fiyeda tunanin ka. “Am sorry momy I wouldn’t insha Allah. Ya juya, ta rasa yazatayi da annoying boy din nan nata, duk Abubuwa sun cakude mata.

 

Key yabawa driver tareda yimai kwatancen gidan Aunty Raliya, domin yanada uzuri idan yaje bazai dawo cikin lokaci ba zata dauke mai hankali, wata motar ya dauka yayi sabon titi gidan Kawu, Wanda yasan by that time yadawo daga aiki, saida ya shiga har cikin gidan kamar y’an da suka saba ya gaida matan gidan kafin ya isa falon kawun,

“Khaleel kaine?  Ya gaida shi ya zauna akasan dadduma, kafin yace, ” kawu nazo ne akan tafiyar da nafada maka, zantafi cikin satin nan insha Allahu. “Masha Allah toh ai badamuwa tunfa harkar cigaba ce kuma hakan nada kyau saikayi kokarin dawo da duk wasu dukiyoyin ka nan gida zaifi, saboda halin kasashen can, Allah ya taimaka yasa Albarka.”Amen Amen. “Toh da matan zaka tafi ko kai kadai?  D’an shiru yayi kadan kafin yace ” da Naziya zantafi kawai saboda Momy…. Ya kora mai Abinda ke faruwa, “kai malam balkisu bata girma da rigima kullum, toh Allah ya baka ikon daukar duk wata jarabawa.

Daga nan  ya dawo gida, Wanda ya samu driver ya dawo, dafe kai yayi tareda ciro wayar shi ya fara kiran ta.

 

Lokacin da taga sakon kayan ta shak’a sosai, wato ya samu Abinda yake so shikenan ta tashi aiki, har baya marmarin ganin ta tunda ya aiko da kayan,  shiru tayi fuskarta a turbune har Aunty Raliya ta gano ta tace ” toh su naziya ansan dadin miji, shine ake fushi don baizo ba, ko dai inkirashi infada mai yazo ya dauke ki?  “Kai Aunty niba haka bane. ” don Allah can sakarya karki fito ki nunawa mijinki soyayya, Allah yabaki miji karshen ado ki tsaya wani jan aji wata ta siye zuciyar shi kinsan dai bake kadai bace, don haka ungo wannan,. Ta mika mata cup mai hade da Zuma mai hadin magani, “shanye kibani cup yanzu banda sanya kitashi ki tsuma kanki mace ba gyara hoto ce don batada banbanci da naman da ba  magi.

 

Kunya taji ta shanye ba musu ta mika mata cup din, she is ready ta gyara domin khaleel zata iya komai saboda shi, yanzu haka damuwar ta ko yaje wurin salifa ne, shiyasa takejin kishi sosai, khaleel ba irin mazan da mace zataso ta raba da wata bane. Jin karar wayar ta yasa ta sauke Ajiyar zuciya ta dauka. “Am sorry baby kinga kayan? ” nagani. Tace, “bazaki tanbaya me ya hanani zuwa ba?

” no need ai nasan kanada wani nauyin da zaka sauke. Fuskar ta a hade tafada tana nufar cikin dakin Aunty Raliya don kartaji me take fada.

“Nauyi???  Oh haka ne yanzu na tuna da inada wani nauyin, kinga d’an gata ko, bari inje in samu second wow Ibrahim you are very lucky Amare biyu in two nights. Kit ta datse kiran tareda kashe wayar baki daya. Dariya yayi cikeda nishadi ya nufi part din ta, kamshin ta kamar tana nan tuni yaji kasala. ” my weakness my pain relief, you are not here to heal my wounds. Ya zube a sofa ya runtse idanun shi yana hango each and every moment dinsu da ita, tuni yaji ya rasa natsuwa, ” oh god I can stay away for too long baby.

 

Gefen Naziya kuwa, ai kirjinta kamar zai fashe saboda kishi harda kwallar ta, saida Aunty Raliya ta kirata ta fito suci Abinci,

A wunin a cikin damuwa tayi shi har dare,

Ta kunna waya tana jira ko zai kirata shiru, harta kwanta tana kallon wayar, Wanda Aunty Raliya tuni tayi turaka, tabarta ita kadai a dakin sai d’an karamin yaron ta,

Khaleel tunda ya dawo mosques ya kulle part din ya koma cikin gidan, anan momy ta hada mai Abinci yaci ta zauna tana tayashi hira, yana faman tura bayanan shi ta internet, shigowa tayi cikin lingerie baka Y’ar guntuwa, saboda rashin tarbiya ta ratso harabar gidan kai bako hula kafarta sai takalmi mai gashi na bedroom.

Kirjinta a rukuun su bako bra tana tafe tana warware duwai wai Wanda kana gani kasan saida aka hada da taimakon bature, kamshin perfumes din ta ne marasa dadi yasa ya yi saurin dago kanshi ya ganta, lokacin yaji wani irin Amai da tashin zuciya, Wanda duk sanadin kwabe kwaben da akayi ne don jan hankalin shi da tsafin malamai, hanky din da ke gefen shi ya dauka ya rufe hanci tareda mikewa yace momy” am going inside.

Yayi gaba Abinshi, da system dinshi, ” OK good night my son. Tafada cikeda fara’a, itako Jakar juyawa tayi gaban momy. ” momy see nayi? Daga kasa har sama ta kalle ta, fauziya ma tafita fasali, “amma da kinsa bra zaifi salifa, kuma kin biyo tsakar gidan nan a haka gamasu gadi tundaga part din ki? ” oh what is there nida gidan mijina wazai samin ido, please zanbishi ciki don Allah kije ki kwanta da wuri bamason takura kar sai muna tsaka da hutawa muji motsin ki, good night. Ta juya tana kada mata duwawu kamar wata sa’ar ta. “Kan uba Amma salifa kina neman Abun da zanci uwarki keda uwar taki me daure miki gindi….. Saurin juyowa tayi a zafafe, ” what?  Kamar zata kifeta da Mari tace “mai maita inji balkisu, uwata kika zaga?  Fada inji wallahi yau har hakorin makkan ki sai ya futo. Kirji Momy ta dafe tareda zaro idanun ta duka waje tace ” salifa ni kike fadawa haka?  Ni kike zagi? ” fin uwata kika yi da bazan zageki ba ke wacece, now excuse me kafin kisa infara tsiya ya anan nayi mugun hadi. Tayi ciki.

Bakin momy sake ta zube a kujera ” na shiga uku ni balkisu, Salifa haka zamuyi dake tun baki samu gindin zama ba?

Jeki Y’ar banza ai Wanda zaki tarar dai dai yake da iya shegen ki, yarinya inason kafaki inason in lallaba shi ya kulaki kifara da haka, toh kije ki karata na tsame hannu na, kuma ko gobe idan naso zan Aura mai wadda tafi uwarki kudi shegiya tanbadaddiya.

Dakyar taja kafarta tayi cikin daki tana tsinewa Salifa.

 

Yana shiga saida yayi bathroom ya yi brush domin kwanciya ya canja zuwa short bako singlet ya fito, inda yayi turus domin ganin tayi dai dai ta ware kafafun ta yana hango har kanfanta, “kut, ke uban me kikeyi anan?  Yafada yana yamutsa fuskar shi domin Allah ya gani minti talatin shida ita sai ya Amaye y’an hanjin shi, wani irin juyi tayi tana mika domin emergency tasha yafara aiki kuma overdose,  “dake nake sakko min a gado  kafin ranki ya baci uban waye ya kiraki nan?

Ganin bazai zo ba ya tsaya unnecessary talks, ta taso tana layi hade da lankwasa, ” tana zuwa ta fada jikin shi, ” saika kirani ne?  Kaifa mijina ne nazo ne ka rayamin wannan daren, so nake kasani ihu kamar yadda kasa wannan Karamar yarinyar, don’t worry kaima sai nasaka ihu, Allah ya horemin dadi. Saida yagama jin zancen ta ya jefar da ita gefe, “fyade zakiyi min kenan?  Ok go ahead. Shine kawai ya iya fada, ya matsa zai kwanta a kujera, domin he just hate that bed, ta batamai gadon shi mai cikeda tarihi, tashi tayi ta kuma matso shi kamar zatasa kuka, ” haba khaleel macece nifa mai lafiya niba irin fauziya bace I can’t take it I need you please give me my right, tana kokarin rungume shi . “if you touch me once again…….. Yafada yana nuna ta cikeda gargadi mai tsauri,

“Mutuwa zanyi idan baka bani Abinda nakeso ba yanzu am honey wallahi please help me, meye wai a ciki mace kamar ni inzo Ina sallama maka jikina me daraja da tsada kana guduna, yanzu gani na kawai a haka ya isa ace ka yayyaga kayana kafara bani wuta Amma ka tsaya jan aji, don’t worry ba Wanda zaisan daga zuwa na ka kusance ni ,I know All this long sai jiya ita ka nemeta, ni am matured bazaka sha wahala ba zantaima ka mak…… Tureta yayi nesa dashi ya mike a zafafe, ” no need to prove your character to me I know you in and out, and listing, all my life bantaba zina ba don haka bazanyi rayuwa da mace irinki in gurbata zuri’ata ba, and yes don’t even dream again akan ni Ibrahim khaleel zan hada jikina da naki, ke nifa bawan Naziya ne kishi nake tayata banaso wata tana rabar matani yanzu ma dole inyi wankan tsarki, second, only her can move the man in me, ganin ki nakeyi kamar wannan wayar, Ke kin isa ki mayi mafarkin bin hanyarda my diamond tabi, she is a diamond, Unique my first lady and last,  third, kina tunanin akwai Matar da zatasani ihu idan ba Naziya ba a duk fadin duniyar nan?  Ita kadai ce mace a idanu na you are not woman enough for khaleel,  now if you can excuse me I have something to do, get out. Ya nuna mata hanyar waje, wasu irin hawaye ne masu mugun zafi da takaici ke zubo mata, cikin zafin rai da kuma wai wayewa tayi wani irin kai hannun ta gaban shi tace “Wayyo khaleel wannan ai tafi karfin ta dole tayi ihu, ni ce size dinka nice mace dai dai da fitinar ka nice zan iya gamsar dakai insaka…… Kallon hannun ta yayi   ya daga hannu ya wanketa da wasu irin hot hot slapped har uku,  tuni ta sakeshi ta zube tareda sa ihu, hannu yasa badon yasoba yajata kamar leda ya watsa wajen dakin ya datse kofar shi.

Saida ta bugu da bango, Kara tasa mai karfi, har momy ta jiyo,  kuma tasan ba kukan dadi bane wannan, tafito da gudu. Lokacin shi ya datse dakin shi yayi bathroom domin dole ya wanke jikinshi in and out.

 

“Ke me yafaru kuma?  Momy tafada tana shirin dafata, ta buge hannun ta tana kuka tana rashin kunyar, ” karki tabani tunda bakida wutsiyar da zaki bani, wallahi Wannan yarinyar ta wanke ta bashi ya shanye baya ganin wata mace sai ita ace yaga mace kamar ni gabanshi kamar lagwani…… Barin wurin momy tayi domin bazata iya jin wannan rashin kunyar ba, ita da akwai Alkunya a tareda ita har yanzu. Ta shige tana tofin Allah tsine, da ace batayi mata rashin kunya ba da ta taimake ta Amma yanzu haka shawari take wadda zata ture mata gwamna tin shegiyar yarinya,

 

Saida yayi wanka kusan na minti talatin kafin ya fito, ya fesa room fresheners Kala Kala saboda karnin ta ya fita mai a dakin,

Saida ya kimtsa ya hau kujera yaja wayar shi, “Am missing you my diamond, ya kirata, Wanda har lokacin takasa bacci zuciyar ta na wurin shi, jitake kamar tazama kuda taje wurin shi, tayi wani irin sabo dashi da yanzu ko Kwana ba’ayi ba tafara ji ajikinta, lallai tana yimai zazzafan so,  tana ganin kiranshi ta wasu hawaye masu zafi suka zubo mata, “bazan dauka ba sai yanzu zaka tuna ka Ajiye ni anan. Tafada cikeda wata irin shagwaba da batasan dalilin taba, saida ya kuma Kira ta kusa tsinkewa, tayi picking domin zuciyar ta batada karfin da zata iya rejecting dinshi, tana sakawa a kunne tafara  kana nan kuka, Wanda tuni ta sagar mai da gabobin jiki da kuma zuciyar shi, “oh my god baby what is that?  “bansani ba ai hoto kazo ka Ajiye dole ka manta dani anan.

Wani irin sanyi yaji har cikin tsokar jikinshi yayi wata Y’ar dariya mai Kara kadan, har taji sautin ta cikin kunnen ta, “kinfi karfin hoto my love you are my life my strength my diamond my pain relief. Ajiyar zuciya ta sauke, batasan lokacin da murmushi ya subuci daga fuskar taba, kalaman shi tuni sun sanyaya mata zuciya, “me kakeyi tundazu? ” gaskiya ko karya zanfada miki?  “Gaskiya. ” hhhh Ina tareda Salifa she just left. Tuni ta maida fara’ar tayi tsit, ” hello my wife, are you there?  Yafada cikeda tsokana, ” talk now ki tanbayeni what happened, “matsalar kuce ni zankwanta. Tafada a d’an hasale. ” hhhh yes matsala ce babba kuwa,Amma rashinki a tare dani shine babban matsala, I can’t sleep baby, do you know what, magana dake kawai yasa hankali na yatashi, baby I need you more wallahi.

Wani irin tashi taji tsigar jikinta nayi saboda y’an da yake kashe mata murya yana hura mata iska cikin kunnen ta cikin wayar,

“Kina sit bath din kuwa?  How is the place, yafara healing?  Shiru tayi domin bazata iya bashi Amsa ba, ” oh god kinga anbani cream da zamu shafa wurin ya warke da wuri na manta, zan shigo da safe inshafa miki kafin inje office, hope zaki bari inga ciwon namu?

“Um um. Tafada ” why?  Toh ni zan baki   nawa kigani kinjimun nima har ko Ina nawa na ciwo, tare zamuyi jinyar ai, nima an bani bed rest bazan kuma aiki ba sai mun warke, “kunya hirar ke bata don haka tayi Saurin canja zancen, “Ina so inje gida gobe. Saurin hadiye maganar yayi ” wane gidan?  ” gidan malam nayi kewar Inna. ” Hmm kodai bakyason magana dani shiyasa kikeso kituna min akwai saurayin ki a gidan da kikeson gani right?  Zaro ido tayi  saurayi?  Ni banda saurayi ai d’an uwana ne fa muntaso tare. “Ya isa gaskiya banaso kina zuwa gidan idan yana nan. “Toh ai bakomai tsakanin mu kuma ba anan yakeba yanzu haka ma yana lagos ya koma. “Kut are you communicating with him?  Yafada cikeda kishi, don har cikin zuciyar shi baison sadiq din nan,

Jin yanda yake magana tasan kishi ke damun shi don haka tace  ” nafasa zuwa shikenan? “Hmmm better. Kinga lokaci ya tafi ki kwanta kiyi  bacci gobe early morning zanzo gidan, good night. Ya datse kiran batareda yaso ba kawai yanaso ta huta ne, ya kalli jikin shi dake wani irin dripping, ” hey relax zamu hadu gobe. Yafada yana murmushi, mikewa yayi ya shiga bathroom yayi alwala domin shifa yasani bashi ba bacci, haka itama ta Kwana a dadduma batareda ta runtsa ba tana Adduar Allah ya Kara mai kaunar ta ya kuma kade musu fitina a tsakanin su Allah ya karkato mata da hankalin Momy ta gano ita bamai cutar da su bace, saida tayi sallar Asuba ta kwanta, Wanda bata tashi ba sai da Aunty ta tasheta.A hankali ta sakko tace” Aunty Ina Kwana. ” lafiya kalau ki yi wanka khaleel na falo. Idanun ta a waje tace “karfe nawa yanzu?

“Don Allah wuce ki shirya yana tareda Baban yara. Cikin sauri   tayi wanka ta shirya cikin wani lafiyayyen dinkin Atamfa ten pcs sket   da dinkin ma ya zauna a jikinta sosai, Aunty ta bata lafiyayyar humra ta shafa ciki da waje ta gyara sumar ta ta zubota baya tareda murza dauri akai na yayi janbaki tasa ja a karon farko kuma taga tayi matukar yin kyau, har zata zura hijabin ta tafasa ta zura   slifas dinta mai kyau da ya Kara haska fararen kafafun ta, kamar

Ka sace ta ka  gudu, tafiya takeyi cikin natsuwa har ta iso bakin kofar falon, cikin natsuwa tayi sallama, mijin Aunty Raliya ya amsa tareda sakin fuskar shi, “kaga uwargida na sai yau nake ido biyu dake, lallai Matar manya. Cikin jin kunya ta gaida shi kanta akasa, Wanda khaleel tun shigowar ta ya zuba mata ido, saidai wani gefen kishin ta kamar yasa ya sume yanda tayi kyau gashi ba KO hijabi wani na ganin ta, tuni yayi wani irin fici fici da ido,dole tabar gidan nan yau bazai yuwuba don baya kaunar KO yaro ne ya kalleta bare wannan katon mutum……… 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 4⃣7⃣&4⃣8⃣

 

 

 

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

……….. Tashi kawai yayi mijin aunty Raliya ya ce ” toh uwar gidan zantafi kwadago. Ya mikawa khaleel hannu sannan ya fita, gyara zama yayi tareda ciro wayar shi ya fara danna wa yana hade rai, kallon reaction dinshi takeyi saida taga abin nashi da gaske ne ta matsa tareda zama kujerar da ke gefen shi tace ” Ina Kwana?

Juyowa yayi ya watsa mata harara kamar wani mace, Abin ya bata dariya, babbar yarinyar Aunty Raliya ce  yar kimanin shekara sha biyar ta shigo da tray dauke da kayan breakfast ta gaida shi, ya kalleta yayi murmushi tareda tanbayar sunan ta, tace “zainab. Yace “good, ya ciro kudi dayawa a wallet ya mika mata taki karba yace ” come on jeki raba da kannin ki, sannan ta karba cikin jin kunya ta fita,

“Mungode…. “Quit my friend, ke bakisan Abinda ya dace ba ko?  Yafada yana watsa mata wani irin kallo in and out. ” me nayi?  “Oh you don’t really know? Alright kici gaba da yawo tsirara a gaban katti suna karewa jikin ki kallo don wulakanci kifito cikin ado gaban katon namiji.

Wani iri taji domin ita kallon Yaya takewa mijin Auntyn don yasan ta tunda kuruciya ta manta da ba muharramin ta bane, “kayi hakuri bazan kuma yin haka ba. Kanta akasa ta ke maganar cikin kwantar da murya, Wanda tuni ya tausasa zuciyar shi yaji wani irin sanyi tareda yin hamdala, kallon ta yayi cikeda so da tsantsar kewar ta ya mike saida ya rufe kofofin ya dawo, tsugunawa yayi a gaban ta ya kura mata ido kur, kafin ya gyara zama ya riko hannun ta, ” come. Ba musu ta tashi ya zaunar da ita tsakiyar cinyoyin shi tareda dora fuskar shi saman wuyan ta yana leka rigarta inda yake kallon kayan marmarin shi, ba wani jan Aji ya zura hannu ta saman wuyan rigar ta, saida taja numfashi tareda sakewa a jikin shi domin akwai wani sirri a tafin hannun shi da duk lokacin da ya tabata tanajin tabin har kwanyar ta, tuni shima yaji ya hau network, y’an da yake cusa hannu cikin jikinta yana cakuda duk wata natsuwar ta yasa duk ta rikice ta manta da wani  ciwo da ke jikinta duk da ciwon ba wani da yawa bane, kuma jikinta nada kyau, gata batada raki irin na wasu matan, in watace shikenan tafara gudun miji, wani irin juyowa tayi tareda rungume shi gam ta dago fuskar ta ta lalubi lallausan lips dinshi ta dora nata  yayi shiru tareda zuba idanun shi akan ta, jin harshenta mai d’an danon dadi yasa yayi saurin fara tsotsa tana tsotsar nashi kamar wata kwararriya, Wanda ta koya ta hanyar karatun data dorawa kanta yanzu,  ta zagaya da hannayenta kugunshi ta rike naman wurin cikin wani irin salo, Wanda tuni yafara nishi sama sama yana rawar jiki, cikin sauri ya zare bakin shi yana fisgo magana” babe Ina so inyi please zaki barni,?  Kin daga min hankali. Yafada yana zuge zip din rigarta cikin sauri sauri ya cire tareda ajiyewa ya kwantar da ita a kasan carpet din ya zuba wa kirjinta idanun shi da suka canja Kala, ” let go to our guest house baby, hannu yasa yana zame hannun bra din tareda janyeta kasa, inda ya samu yanda yakeso mutanen nashi dake Kara habaka suka  kara habaka  saboda jagwal gwalasu da yakeyi, tuni ya dora bakinshi saman su ya kama niple dinta, saida tasa Y’ar Kara ta bankare mai tareda rike shi kamar zatayi fitsari, ” stop dinki na…… Tafada tana jan kalmar cikin rashin sanin Abinda takeyi, d’an tsaya wa yayi yanzu yadawo seance dinshi domin ya tuna maganar doctor, zubewa yayi gefe ya dafe kanshi ” oh god khaleel. Daga ganin halin da yake maganar kasan ba sauki sai dai mazan taka tasa ya tashi tareda ciro cream din da yazo dashi cikin pocket, tana kallo ya bude ya dawo gabanta tareda sa hannu yafara jan sket din ta sama tayi saurin rike hannun shi tana girgiza kai, dago idanun shi da suka canja launi yayi yace “wait my friend. Ya cigaba saida ya daga sama dakyar saboda ya matseta,   ya kalli pant dinta baki kalar bra din, ya haska fatar ta, wani irin dirty thinking yakeyi, dama a gidan su suke daga ita sai bra zatana yimai yawa yana kallo, dayaji desire ya more meyafi ranshi, murmushin gefen baki yayi domin tunanin nashi da yawa, runtse idanun ta tayi domin bazata iya kallon shi ba don batasan me zaiyi ba,  taji ya shafo saitin kasanta yace “ahhh baby you are wet. Domin pant dinta yayi jagab da ruwan dadin ta, Kara runtse idanun ta tayi saboda kunya jikinta na mugun bada ita, ” baby na zatayi jarumta Ashe?  Get well soon mu more bazakiyi kukan komai ba my wife. A natse ya cire pant din saboda rashin kunyar shi harda haska wayar shi kamar mai kallon tv yana wani irin narka idanun shi yana karewa each and every part kallo domin sanin me zaiyi next time, ganin stitches din ma sun warware sai sheda da jan da wurin yayi yasa yace “how did I get in to this tiny hole?  Domin wurin kamar na wata Y’ar shekara goma, saida ya gama leketa in and out ya bude maganin ya shafe wurin yana wani irin lallashin shi da lailaya shi, don yasan wannan kofar ba wadda za a wulakanta ko ayiwa garaje bace hanyace wadda bazai taba mantawa da ita ba da bazai gaji da binta ba Kofar nadauke da sinadarai masu tsayawa a kwakwal wa he don’t even know how to describe it, jin yanda yake mata ne yaki karewa yasa ta janye tareda tashi da sauri ta sauke sket din ta ta dauki rigarta saida ta gyara zaman bra din ta ta mayarda rigar yana kallon ta, saida ta gama ta matso kanta akasa domin daukar pant dinta, dake kan kafar shi yayi saurin dauka yace ” nawa ne wannan, nine na janyo ya jike nine zan wanke shi da kaina. Fuskar ta a marai raice tace ” please kabari mana, bani don Allah. ” nop, ya ce tareda dorawa ya shinshina yaji wani irin kanshi, na miski da take Amfani dashi Wanda ya mugun huda jikinta, saida yayi wani irin lumshe idanun shi yace” wow  baby harda can ma kamshin shi daban?  Am very lucky to have you as my wife, kinsan Ina son kanshi, inason tsabta and Allah yabani mace mai kamshi tako Ina, tashi yayi tsaye ya matsa kusa da ita ” I feel like liking that place right now wallahi allow me. Saurin ja da baya tayi yayi dariya yace ” oh come on not here zsmuje wani wuri only me and you zan koya miki rayuwa zan bataki baby zan shagwaba ki, zaki zama queen ni kuma king dinki Ina so mu shinfida rayuwar soyayya da zai zamo tarihi, daga Auren gado zai zamo Auren soyayya mai ban mamaki, you are my choice baby I love you and I can’t live without you.

 

Wasu irin hawaye ne da batasan dalilin fitowar suba suka biyo kuncin ta, kalmar I love you daga bakin shi this is not the first time dataji ta, amma bata taba tunanin kalmar is serious ba daga bakin shi sai yau domin ido cikin ido yake aika mata da sakon, kuma tana hango gaskiyar Abinda duk yake fada ta cikin kwayar idanun shi, how she is zata iya bude baki tafada mai yanda takejin shi a cikin zuciyar ta amma Kash batasan kalmar da zata fara da itaba, she is not good in words like him,

Jin hannun shi akan fuskar ta yana share hawayen yasa ta karkace kai tana mai kallon you are special, yace ” why kuka?  Bakyason kalmar?  Bazan kuma fada ba, Am sorry, kinji yanzu zantafi Anjima zansa azo nan ayi miki hoto Ina bukatar passport dinki zanyi Amfani dashi. “Inada su amma suna gidan mu baka hana akawo min kayana ba.

“Wane gidan?  Gidan malam. ” kice gidan su Shukrah, ke kinada gidan da ya wuce nawa ne?  Sannan me matata zatayi da kayan da tayi rayuwa dasu da wani namijin?  Your husband is a rich man baby so chill and enjoy, kinada damar da zakisa akawo miki store guda har gida Mrs khaleel.

“Hmm you are too proud. Tafada tana kallon shi ta gefen ido, “oh sorry I forget bakyason mai kudi ko?    Yana dariya, “by the way thank you, zanje gidan yanzu  in karba dama Ina tunanin how zaki tsaya wani ya miki hoto, jini na zai hau.

Murmushi tayi she is enjoying the moment, komai yayi Abun burgewa ne a wurin ta yanzu,  he is such a shinny  moon, dake haske filin zuciyar ta, dakyar tasamu yaci Abinci kadan itama ya dura mata, Wanda saida suka kwashe kusan hour biyu tare kafin yace zai tafi dakyar domin yanada Abunyi da yawa,

 

A haka kwanakin suke tafiya Wanda wani gefen farin ciki, wani kuma akasin haka, Al amarin salifa da Momy kullum gaba yakeyi domin gaba daya khaleel ya kauracewa gidan saboda ita, sometimes zai Kwana ma a gidan batareda sun sani ba Salifa tayiwa momy tijara harta gaji haka momyn ta,  kullum tana hanya,

Yauma momyn zaune take tana waya da zarah, ” waini bangane kan Al amarin nan ba zarah, kudi nake narkarwa aiki kamar yayi kyau sai kuma komai ya ruguje, ni so nake ma yanzu idan zai raba Auren khaleel ya raba harda na Y’ar banzar nan,

Fitinanniya yarinya kamar jinin ayu, kullum tana kallon Idona tana fadamin inturo mata Dana ya kwanta da ita. ” ai Aunty kinsa me kikayi tunfarko kinsan Y’ar nan gwara fauziya da ita amma kika nace toh kima gode Allah Khaleel din bai juyuwa da sai kinyi kukan Abun ni yanzu Ina labarin Naziya ne Ance min ana ganin motar shi gidan yayar ta Raliya kinsan muna unguwa daya ne. “Zarah al amarin khaleel yafara bani tsoro yanzu haka Kwana biyu bansashi a Idona ba, kuma manger dinshi yafada min kullum sai yaje office. “Nidai kisa kawai yadawo da ita gidan kila wani wurin yakaita gashi yana yawo gindin Y’ar uwar ta gani  nan kanwar uwar shi ko ya kalli kofar gidana, tadawo  koma meye kina gani amma wannan jikan matsafan wallahi nan gaba ma shafawa zakiyi ki rasashi baki daya. “Tir da bakinki zarah, ba shegiyar yarinyar da zata rabani da tilon dan da yarage min inaji Ina gani, ni sai Anjima zaki tayar min da hawan jini dama kwanan nan kullum high yakeyi. Ta datse kiran tareda mikewa tana gungunin duk inda yake sai yadawo taji meyake nufi zatagani wacece uwar shi cikin ita da dangin Naziya.

 

Gefen khaleel kuwa yayi matukar yin busy, yagama shirin tafiyar su tsab Washe gari jirgin su zai daga zuwa bangkok, batasan komai ba yadai fada mata ta shirya zaizo gobe su tafi, gashi tun ranarda yazo da rigimar sa mata magani bai kuma tsayawa sunyi wata doguwar hiraba, dayazo yake tafiya saboda aikin dake gaban shi, he has a lot of responsibility akanshi yanzu na campanonin su,  don haka kanshi yayi zafi.  A yau yakeso ya hada duk Abinda zai iya bukata a tafiyar,   don haka baiko je wurin Naziya ba duk da tanason ganin shi gashi tana kewar shi sosai, ya saba mata da wasanni yanzu kuma ya dauke  ga wutar sonshi data gama ruruwa a zuciyar ta, dama take nema ta baje kolin tarai rayar shi domin ta mallaki kayanta kamar yadda a kullum Aunty Raliya ke bata shawari, ta cire kunya ta zamo magajiya ba karuwa ba a gidan mijinta,

Taci buri takuma dauki Alwashin bashi mamaki, don haka shirye take tsab da zuwan shi, tana murna da duk inda zasuje she is ready for him, ta tsumu Aunty Raliya ta tsumata ta gyareta sosai tareda taimakon Aunty Aisha,

 

Sai misalin karfe takwas ya  shigo gidan, ko ciki bai shiga ba nan part din Naziya     ya tsaya saida ya hada y’an kayan shi ya yi wanka  ya saka kana nan kaya yayi part din Salifa, tana zaune tana layi kamar wadda tasha maye, toshe hancin shi yayi domin if he is not mistaken warin giya yakeji, jin yayi karo da kwalba yasa yaji wani irin mugun takaici cikin tsananin zuciya ya juya domin no need ya tsaya yimata magana bata cikin hayyacin ta. Gidan Momy ya shiga a zafafe, tana zaune tana aikin wayar da zarah, sallama yayi ciki ciki ya shigo, tayi saurin kashe wayar tareda zuba mai na mujiya, ganin yanda yake haki kamar Wanda yayi gudu kan iska.

“Kai lafiya, Ina kashiga Kwana biyu?  Yanzu kafadomin gida kana cika kana batsewa, khaleel dai dai nake dakai   Indai nice uwar da na haifeka zan nuna maka na isa, wato saboda nasa kafitar min da wannan jinin matsafan shine zaka dauke kafarka ka manta da hakkina na uwa ka tare gindin d’an gin malamai ko khaleel?

Cikin takaici ya dago kai, ” haba Momy yanzu wannan yarinyar da kika nace sai kin lika mana tafi Naziya a idonki momy go and see that girl, she is drinking in my own house, wace irin macece Y’ar musulma tasha giya cikin gidan Auren ta, bazan zauna da ita ba gaskiya zan saket….. “Akul khaleel karka fara sakin ta sai kafara sallamar wannan Mayyar kafin ka saki salifa no matter what tafimin Y’ar gidan matsafa da ke neman rabani dakai.

“Momy haka zakice bayan ga gaskiya a bayyane?  Ok am leaving  bazan dawo ba saikin rabani da wannan Auren domin wallahi momy koda zaki tsine min inbi duniya bazan zauna in hada jikina da na wannan kazamar ba. Ya juya da sauri tana kiranshi yayi waje. Tana biye tana Kira yaki waigowa saida ya shige cikin gidan shi tayi gefen salifa, ” bari inga Y’ar banzar nan, wannan wannan yarinyar bazata shiryu ba.

Koda ta shiga tana kwance ta kelaya Amai, haka ta toshe hancin ta tareda fita da sauri kar itama tayi tana     tsinewa Salifa “wannan ya’ akwai Y’ar banzar  wallahi bari inkira uwar ki ita ta dauki mataki.

Ganin motar shi taji sanyi tasan bazai tafiba ta koma cikin gida….. 🖊

 

 

 

 

“Insha Allah gobe ma zanyi kokari inyi posting saboda baku samu update ba sosai wnn satin kuma naso typing din yayi tsawo yau Amma Allah yakaimu da rai da lfy kuna raina masoya Allah ya Kara mana hakuri baki daya. Amen

 

 

 

 

*Matar Soja *

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 4⃣9⃣&5⃣0⃣

 

 

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

 

 

……….. Ko waya bai iya kiran Naziya ba wadda ta cika tayi fam saboda yanda baida wani lokacin ta yanzu bayan yamata sabo mai wahalar mantawa, she is missing him, salon shi mai rikita ta Mata kwakwal wa da gangar jikinta, duk lokacin da ta tuna dashi sai taji tsigar jikin ta na tashi, Kwana tayi juyi har garin Allah ya waye, Wanda gefen shi kuwa da bakin ciki da takaici ya Kwana, a afarko yana dayasanin shirya tafiya ya bar Momy ita kadai, Amma yanzu baida wani choice sai na yabar musu garin kawai kowa ya    huta he is going  batareda wani regret ba, yana son jin muryar ta Amma yasan zata gano yana cikin damuwa domin zafin da yakeji bazai iya boye shiba zata gano shiyasa kawai ya hakura,   Amma baiyi bacci ba Sam, sallah yayi tareda yiwa d’an uwan shi Addu’a har Asuba, jirgin su sai karfe shida na yamma zai tashi don haka bai fita da wuriba sai kusan karfe takwas, ya kirata lokacin tagama kunbura, saida ya Kira sau uku tayi picking tareda yin shiru kamar ruwa ya cinye ta, ” yau jan Aji akeyimin bama gaisuwar? ” Ina Kwana, tafada ciki ciki, “lafiya gimbiya jiya ko a kirani? “Kai meya hana ka kirana?  Kuma yanzu ma kalla sai karfe takwas kake kirana. Cikin shagwaba tareda narkewa take mai maganar, ” are you waiting for my call my diamond? Wow Ashe ni d’an gata ne a wurinki baby. Numfashi yaja tareda yin Ajiyar zuciya, yace ” get ready karfe shabiyu zanzo muje gidan malam muyi musu sallama. Shiru tayi kadan tana tunanin Ina zasuje? Bata tanbaya ba domin bincike ba aikin tabane don haka amsawa kawai tayi yace zai wuce office letter, kashe wayar yayi, tabi da kallo, when zata samu dama itada mijinta?  Yaushe ne zasu kasance atare batareda ya matsa ko nan da can ba, me nayi miki momy meye laifina,  talauci aibu ne?

tasani Indai mutum yace bayasaon ka toh kawai kasa idanu tunda Wanda ya halicceka yana sonka, Abinda momy takeyi bai taba damunta ba sai yanzu da take kaunar zama tareda shi gashi momy ta haramta mata komawa gidan shi, batasan inda zai kaita ba amma ita tasan ba inda yafi mutunci sama da dakin Auren ta, batada mafita ta tattara ta fauwalawa ubangiji.

 

Da sassafe momyn salifa tazo Wanda har lokacin takasa tashi tana kwance cikin Aman tana shara baccin ta, koda suka shigo haka Momy ke toshe hancin ta, ” kingani ko Hajiya har yanzu ace tana kwance cikin kazanta yaza’ayi khaleel ya zauna da ita yana ganin irin wainnan Abubuwan?  Idan ta saba shaye shayen ta a waje tayi Aure an rufa mata asiri ta shigo tanayi wane namiji ne zai zauna da ita….. “Ya isa mandiya wato kina nufin ya’ta batada tarbiya?  Bayan kin haifi Abinda yafi karfin ki bayajin maganar ki, ai shine Abun tir ba Salifa ba yakawo santaleliyar yarinya ya Ajiye ba biyan bukata me kikeso tayi inbatasha Abinda zai cire mata damuwa ba, don haka bani wuri in kintsa abata kina wani toshe hanci kamar kinga kashi. Takasa cewa komai kawai fita tayi domin tafita masifa

Tana ayyana dole ta nemi mafita don bazata Y’ar da da wannan iya shegen nasu ba,   tana fita momyn salifa ta kulle kofar ta dawo tareda bata fas a kumatu, zabura tayi dauke da Ashar” kutumar ubancan wane shegen…… Tayi ido biyu da momyn ta, ” momy meye haka don Allah Ina bacci na mai dadi kizo ki tasheni da Mari meyakawo ki gidan suruki early morning please?

“Ubanki dake kabari yakawoni Y’ar banza, wato bazaki daina daga kwalbar nan cikin gidan nan bako, nace ki hakura da duk wani iskanci har burin mu ya cika Amma kina wannan Rayuwar a gaban idanun shi yazai zauna dake?  Zama tayi tareda kallon Aman, ta kwalawa maid dinta Kira, ” clean this mess ta wuce tabar momy, tashi tayi tabita tana bambami ” wato na zama karya inyita haushi ko?  Kwabewa tayi tsirara agaban uwar Wanda ba wani Abu bane a wurinta tace ” tunda gani dutse ba namiji ba chilling ba kwalba bazan iyaba. ” kice dai ba y’an iskan kawayen ki y’an madigo, salifa tanbadewar ki tayi yawa wallahi ki rage kodan y’an cutukan nan. “Kinfa shiga rayuwa ta ne  because of your greediness, meye bandashi you have money momy me zakiyi da kudi, inada big girls a kasashe masu kudi dake da burin mallakamin duk Abinda nakeso  a fadin duniyar nan kin nace sai na Auri wannan mugun d’an wulakancin, Momy I don’t want to deceive myself , that guy hate me with passion yasan ni munsha haduwa a bangkok with my girlfriends, I can’t west my precious life here. “Oh baby na daura towel din tom kije kiyi wanka kifito muyi magana. ” nop Ina fitowa zanfita niba dutse bace inada appointment. “Ok ba kince kina sonshi ba?  Shiru tayi kadan tana kallon momy, ” meye amfanin son?  Abinda nakeso bazan samuba guduna ma yakeyi  tun zuwa sau biyu nasa shi a ido na. “Jiya yashigo shi ya ganki a wannan halin uwar tafada min komai, kinga ga dama tasamu kin yi sake da lokacin da ya shigo kin samu kinja hankalin shi kin shafa wannan turaren da bazai kuma tsallake dakin ki ba Amma kinja mana asara. ” oh Momy nida nasa wannan turaren har dakin shi naje ba Abinda ya faru sai don yazo nan? ” kinga halin ki ko, wayace ki saka kifita waje wani yaji kamshin?  Keda akace miki shikadai zai shaka Amma kinje kinyi min Asarar kusan million a banza batareda ribar ko dubu daya ba, mtsww kinada kayan haushi ni natafi kiyi duk tsiyar da kikaga zaki yi tunda bakida ganewa Abinda kikesha duk ya sa kwakwal war ki bata aiki.

Haka ta tafiyar ta batareda ta nemi Momy ba, Wanda tabar salifa da cizon yatsa, da ace jiya bata kwafsa ba da ta rage mugun zafin data dauka nashi koda ta hanyar yimai fyade ne domin tasan y’an da zatayi seducing dinshi dole ya biye mata kobaya so Indai ya kawo kanshi har wurinta, saidai Kash ta kwafsa. Haka ta sheka  wanka cikin kana nan kaya kamar zataje club ta maka katon space tareda d’an wani yalolon gyale  ta dauki key din motar ta tafice.

 

Karfe shadaya tagama shiryawa cikin wata doguwar riga Y’ar saudiya mai shegen kyau taji stones tana sheki, ta yana gyalen ta tafito kamar balarabiya, takwashe lokaci mai tsawo kafin ta gama shiryawa saboda kawai ta burgeshi,Wanda Aunty ta yaba,  tace ” kaga  madam khaleel gaskiya zaki rikitashi irin wannan ado haka, ga kirjin sun kunburo hips dinta d’an dai dai ya bayyana saboda shape din rigar duk da bawai takamata bane Amma tafito da perfect figure dinta,

Karfe shabiyu dai dai ya Kira wayar ta, lokacin tana shan wani hadi mai shegen dadi da Aunty tabata, na Zuma da kanun Fari da kuma mazarkwaila ga dadi ga aiki mata. Ganin kiranshi yasa ta Ajiye cup din tayi picking ” Ina waje let go. Ya datse kiran, mikewa tayi tace “Aunty yazo.

Wani turare ta dakko mata domin ita batasan Ina zasuje ba, ta ce ta shafa,

 

Tun daga nesa ya zuba mata ido ganin y’an da take tafiya cikin natsuwa, saida ya kalli ko Ina yaga ba idanun mutane yasamu natsuwar kare mata kallo, har ta iso bakin motar, batareda ya motsa ba,  ita sam bata ganin shi ta rasa dalilin da yasa duk motocin shi kamar na matsafa saboda tinted glasses danna motar yayi tareda bude mata, dukawa tayi ta shiga, ya juyo da kyau ya zuba mata ido itama ta kalleshi cikin adon manyan kaya,  yayi matukar haduwa harda hula wadda sai jefi jefi zaka ganshi da ita, idanun shi dauke da katon eye glass daya karamai haiba da kyau, batasan lokacin da ta shagala da kallon shiba, shima kare mata kallo yakeyi shikadai yasan me yakeji, baiki ya kwantar da kujerar motar nan yayi mata kaca kaca ba domin tasa mai zafi, numfashi ya fesar mai zafi, ” don’t dress like this inkin san ba agidan mu mukeba, I feel like striping you necked  right now. Ya fada muryar shi a shake. Kunya taji ta dawo hayyacin ta tareda gaida shi, ya amsa “mubar nan kafin inyi miki tsirara anan gidan surukai.

Tayarda motar yayi tareda riko hannun ta gam da dayan hannun shi domin rage zafi y’an da yake murza hannun ma nasa taji wani iri a jikinta ga hannun shi laushi kamar na mace, domin baya wahala,  waka ya saki na su p square na no one be like you yana bin wakar a natse cikin kwarewa tareda d’an juyowa yana kallon ta, turo baki tayi domin wannan glass din da yasa haushi yake bata yanzu duk da yayi mai kyau ita burinta taga kwayar idanun shi da yanda yake aika mata da kallon shi mai cikeda tasiri a zuciya da gangan jikinta. Yana ganin reaction dinta baice uffan ba har suka isa kofar gidan malam Wanda tundaga nesa ya faka ganin cin cirindon mutane  ya zare glass din ” oh god zamu juya fa. Yafada yana matse rai, Wanda ita dai murna takeyi tazo gida zataga Inna, jin kalmar shi yasa tayi saurin juyawa, ” saboda me?  ” can’t you see, maza cike yazan bari kifita cikin wannan adon su kalleki?

“Almajiran gidan mune sun sanni batun yauba meye a ciki please don Allah muje. Tafada cikin marai raice wa, ” excuse me, kikace sun sanki?  Ba Wanda ya sanki sai Ibrahim khaleel, don haka if you want to go in call Shukrah ta kawo miki katon hijab if possible harda nikab am not a fool.

“Don Allah meye haka? ” kishin iyalina.

Yafada tareda gyara zama yana cewa ” call her or  mu juya yanzu we have a plight to catch time is going.

Wayarta ta daga domin Allah yagani bataga samu taga rashi ba don haka ta Kira Shukrah tace don Allah takawo mata hijabi tana waje, karbar wayar yayi jin Shukrah na tanbaya wane irin hijabi kuma meke faruwa?  ” Shukrah ki kawo mata please muna jira harda nikab please. Dariya Shukrah tayi tareda mikewa tana cewa “Aunty kinyi Aure.  saida ta dakko mata kato cikin kayanta nagida sabo tareda nikab domin tanada su tafadawa inna tana zuwa Yaya khaleel nakiranta a waje.

Fitowa tayi tana kunshe dariya harta matso gaban motar ya zuge glass yace ” Shukrah tank you for saving her da bazataga Inna ba yau.  Gaidashi Shukrah tayi tareda mika mai ya karba ya mika mata tana tura baki ta zura, gefen ta shukrah ta zagaya tace “Aunty kece da irin wannan shigar yanzu Yaya khaleel ya taimake ki da keda malam ma. ” Shukrah kyaleta saboda tasamun hawan jini yasa takeson fita a haka yanzu. Ya bude motar yafito tareda zagayo wa gefen su harta daura nikab din ya bude mata ta fito, yace “wow koke fa yanzu?  Harara ta watsa mai cikin wasa yace “I will pay for that look letter. Yayi gaba yana murmushi, matsowa Shukrah tayi tareda cewa “Aunty wannan irin love, when how?  Gaskiya kunfi matching da Yaya khaleel look at him, inama kinki Y’ar da, Dana shige ni. Tafada cikeda tsokana, ta kai mata Dan dukan wasa, har suka isa kofar gidan ta wuce Abunta ciki shikuwa yayi wurin da malam yake da manyan Almajiran shi,

 

Tana shiga ta kwalawa Inna Kira cikeda doki da kewa, tana zaune tana kulle kullen ta tace “Aa Amare da rana?

Zama tayi suka gaisa Shukrah ta kawo mata zobon Inna mai sanyi tasha tana lumshe idanun ta “I miss this. Inna fuskar ta dauke da walwala da farin ciki, tace “Y’ar nan kina can kinyi shar dake ni Ina nan kullum tunanin ki tunda nasan bakiso wannan Auren ba Naziya, da Alama wannan Khaleel yana kulamin dake tunda har kinsaki jiki kinyi fes, kai Alhamdulillahi.  Murmushi kawai tayi tareda dukar da kai saboda kunya, haka suka shigo tareda malam ya gaida Inna cikin girma mawa kafin malam yace “sunzo yimana sallama ne zasuje can kasar waje. Saurin kallon shi tayi Wanda idanun shi na kanta kur ko kunya baiji aganshi,   ya kashe mata ido daya, wato tafiya zasuyi shiyasa yake neman hoto,

Wanda duk batasan shirin shi ba,

Sunkai karfe hudu a unguwar barinta ciki yayi shikuma ya fita waje wurin malam saida ya kirata ta mike batareda ta gaji ba tayi missing Inna, Shukrah ta rakata bayan tasha nasihohi wurin Inna da malam, yabawa malam kudi sosai yace akarawa Almajirai Abinci, domin yasan in shi zaibawa bazai karba ba, Shukrah ma yabata yace tasiya kayan kwalliya, wayar hannun Naziya ya karba ya mika mata bayan ya cire layin yace ” kiyi manage kafin inkawo miki sabuwa. Tayi tsalle tana godiya domin ta mugun lora wayar tunda taganta,  murmushi Naziya tayi tareda karajin shi cikin zuciyar ta yanda yake sakin jiki da yan uwanta All that ego da take tunanin yanada yau bata gani,

Haka suka tafi fuskar ta kamar gonar Auduga tana Kara daura damara,

Gidan kawu sukaje Wanda ta yaba da karamcin su,  sun karbeta hannu biyu, hardai uwar gidan da taji dama haka Momy takeyi da ita.   Sunyi mata shatara ta Arziki kafin yace tafito sutafi, kamar karta tafi ga y’an matan da dama sun d’an saba tun lokacin Ahmed.

Karfe biyar da rabi suka isa ainihin kofar gidan su Wanda bai shiga ciki ba yace ta jirashi ya dakko kaya,    ido tabishi da shi, har ya shiga katon gate din, bai wani dauki lokaciba ya fito dauke da akwati madai daiciya, ya saka a bayan motar, “nakira Aunty nafada mata sai mundawo jirgin mu yakusa tashi.

Yafada yana tayarda motar, tareda kiran manager dinsu yace su hadu Aminu kano Airport yanzu,

 

Abun kamar wasa taganta a filin jirgin Wanda all her life bata taba mafarkin zuwa ba, yau gata wai jirgi zata hau zuwa wata kasa, ta zubawa sarautar Allah ido, suna isa manager na isowa, yace “naso muyi wanka before going Amma har anfara announcing, hanata fitowa yayi   ya bashi envelope ya kaiwa momy gobe da key din motar if he needs him zai kirashi. Saida yaji ana Kara Announcing yace ta fito baida yanda zaiyi,

Fitowa tayi still da katon hijab dinta saidai ta cire nikab din yanzu domin tagaji, suka gaisa da shi sama sama kafin ya sallameshi ya rike hannun ta suka wuce.

Wai yau ita naziya ce zaune a cikin jirgi first class seat tunda jirgin na y’an kasuwa ne, yana zaune a gefen ta ba wasu mutane sosai a wurin ya daura mata belt tareda d’an saka hannu ya rungume ta domin supporting dinta don yasan karon ta nafarko kenan, Wanda tayi matukar kokari wajen natsa kanta da dauriya karta nuna kauyancin ta,

Sai gasu a sararin samaniya,  jirginsu ya daga, taso tayi sallama da Aunty Raliya  Amma yabawa Shukrah wayarta,  sai muyi musu fatan sauka lafiya…….. 🖊

 

 

 

Me kuke ganin zaifaru da rayuwar momy masoya, ga khaleel ya tsallake ta batareda tasani ba ya dauki Y’ar da bataso ya bar kasar, ga momy nan dauke da sabon shirin kashe Auren shi tareda nemo mai wata Matar, muje zuwa dai ankusa isa, inda nakeson kaiku da Yar dar Allah.

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 5⃣1⃣&5⃣2⃣

 

*Alhamdulillah naga masoya na Asali, naga kuma masu mugun gajen hakuri, yau ba bawa mai hankali da zaiyi wa kanshi fatan ciwo, tsawon lokacin da nafara rubutu inba wani kwakkwran dalili ba bana kaunar infara typing in tsaya, na rubuta littafi bakwai wnn ne na takwas hakan bai taba faruwa ba, nafada nakuma nafada nabada hakuri mutanen da sukasan halin da nake ciki sunfito sunyi bayani, Amma wai duk da haka wasu zasu rika daukar waya suna tanbaya ta Ina posting dinmu Ina update sister kin ajiyemu kin kyale mu, kuma abin mamaki masu complain din duk wainda suka biya dari biyar ne, Allah sarki akwai sister da tabiya dubu uku Ana bata prvt wlh tun ranar da ta tanbaya nafada mata banda lfy bata kuma bina tace update ba, haka akwai masu dubu biyu dubu daya duk ba wadda tayi complain saboda lfy itace komai idan ba lfy ba Abinda bawa zai iya yi a rayuwa, kuma ciwo inba na Ajali bane yanada iyaka don haka masoya nagode sosai da sosai masu complain kuma Allah ya baku hakuri bazance komai ba*

 

 

08032252760

08175479641contact this numbers for more information

 

 

 

……………Bacci tasha sosai a kafadar shi, Wanda ya raba dare yana kare mata kallo, wani irin farin ciki yake jin shi a ciki, finally zai kasance tare da ita, zasu rayu su biyu ba wani shamaki ba Wanda zai hanasu sakewa.

Washe gari tunda safe sakon shi ya iso wurin Momy lokacin ta shirya fita aiki, cikin adonta na manyan mata, taci karo da manager din khaleel, yace “ga sako inji mai gida Hajiya. Ya shigo da motar tana sake da baki ya faka wajen Ajiyar motocin su, saurin bude takardar tayi taga  Atm din Ahmed da nashi na gida tareda takardun gidan dana company, wani irin faduwa gabanta yayi,  me wannan sakon ke nufi?  Saurin kiran manager tayi ganin zai fita tace ” kai zo Ina mai gidan naka da yabaka wannan sakon?

“Hajiya ai tunjiya yabar Nigeria bai fadamin inda zaije ba tareda madam dinshi. Ya fita Abinshi domin shidai ya isar da sakon.

Dafe kai tayi tareda jan kafa takoma cikin gidan, tana shiga falon ta zube, ” shikenan ya tafi ya koma, Wayyo Allah na ni balkisu

Nashiga uku na. Tasa kuka mai karfi, Wanda saida masu aiki suka firfito a rude suna tanbayar lafiya?

“Duk ku wuce kubani wuri munafukai magulmata.  Da gudu suka koma, Wanda yayi dai dai da shigowar salifa cikin wasu arnan kaya duk jikinta a bayyane, “yau kin tunada mutuwar Ahmed ne Momy?  Tafada cikin izgili, “mutuwar ubanki natuna mai farar kafa, yakamata ingano cewa keba Alkhairi bace a rayuwar ya’yana Amma nakasa gano hakan saida nayi sanadin d’ana ya gudu yabarni, nashiga uku na ni balkisu.

Matsowa tayi a fusace ta shake wuyan Momy batareda duba girma ko shekarun taba, ” ubana sa’an iskancin kine?  Eh, kuma yanzu ne kika gano cewar ni ba Alkhairi bace a rayuwar ki, kina tunanin  don Allah na Auri d’an ki tunfarko?  Dukiyar nan mukewa bawani Abu ba, tunda bazan samu kan mijin ba meye amfanin Auren. Dakyar ta kwaci kanta tana jan numfashi da kyar tasamu ya dai dai ta,  Wanda lokacin har idon Salifa yakai kan takardun dake zube akasa, saurin kwashe wa tayi tana dubawa  ” kawosu nan dukiyar ya’ya na ce bakida hakki a ciki. “Hhhh niko keda hakki da Dukiyar mazaje na, Ina tuminin takaba na na Ahmed?  Yanzu shima wannan kisa kawai ya mutu domin bazai dawo miki ba, tunda nikuma nasamu wannan yanzu kinga gida ya zama nawa office company motoci.

Tashi tayi tareda kallon ta ” sharia kuma tazama banza kenan da zaki mallaki Dukiyar mijina da ya’ya na daga sama ni balkisu Ina kallon ki. “Watch and see Hajiya balkisu zan nuna miki inada manya asama, Wanda zai tsaya miki kinja ya gudu don haka bakida wani gata, kibini in labaki cikin gidan nan ko kina kuskure wa in watsaki waje couse this is all my property. Tafada tana juyi tareda kada jiki, ta fice Abinta, cikin kaduwa ta dafe baki “na janyo ruwan kashe kaina. ranar ba inda ta iya zuwa, koda ta Kira kawarta kin dagawa tayi domin Y’ar ta tashafa mata komai, don haka ta tattaro inata inata tayo gidan, suka baje a side din salifar suna y’an da sukaso batareda sanin momy ba. Domin kirjin ta ciwo yakeyi tana cikin tsananin tashin hankali, kanta har wani nauyi yake mata, waye zata fadawa ya taimake ta yadawo mata da Khaleel?  Modu, tayi saurin mikewa tareda daukar key tayi waje cikin sauri, ta manta ranarda kafarta ta taka zuwa gidan shi Amma yau batada wani zabi dole taje.

Saida tafito taga motar kawar tata, batabi takaiba domin khaleel ne damuwar ta idan yana nan komai zai dawo dai dai don haka dole tasa yadawo kota halin yaya.

 

Shikan shi Alhaji yayi mamakin ganin ta yau a gidan shi, saidai yanda ta saukar da kai yafi bashi mamaki” Baban yara shin ko kasan da tafiyar khaleel?  Shine maganar ta tafarko bayan sun gaisa, yace mata “ya akayi Hajiya balkisu?  Nayi matukar mamaki da na ganki gidana yau. “Nidai bashine matsala taba, Ina so inji in kasan inda yarona yaje? “Bansani ba toh, ai d’an ki ne kece uwar shi kinfini Iko da mulki akanshi don haka kike zuba sarautarki a matsayin ki na uwa, yau ya akayi kike neman shi a wurina?   Kije ki nemeshi duk inda yaje. Wani irin takaici taji y’an da yake fada mata magana a kai kaice, ” toh ai kaima akwai hakki a wuyan ka tunda Amana d’an uwan ka yabar maka, don kasa ga rufemai idanu shine zaka bari zuri’ar shi ta watse, shi wancan ya tafi, wannan kuma ya gudu yabarni, don girman Allah nidai kafadamin inkasan inda yaje.

“Bansani ba kitashi kibani wuri, kedaman matsalar ki jahilci kije ki nemi ilimin addini kafin ki mutu cikin duhu domin kalaman ki Sam bana mai ilimi bane, da kinada kwakwal wa da kin gano mugun halinki duk shine ya janyo miki halin da kike ciki, kuma bakiga komai ba inda wainnan mutanen banzan da kike tareda sune, kije sune zasu cire ma Y’ar mutane hakki da kika tsana kika hanata sakewa da mijin ta tunfarko kuma Allah ya nuna miki Aya akan dole dai saita rayu da jinin naki da bakya kauna, meye laifin talauci ke kika bawa kanki Arziki?  Ko ke cikin Arzikin aka haifeki, saboda kawai kinshigo cikin zuri’ar mu kin lashi jar miya kinfi uban kowa daga kafada….. Kuka tasa mai ciwo tareda mikewa ” basai kaci mutunci naba modu, basai katuna min da Asalina ba, nasan duk inda nafito Amma kasani inda sa hannun ka dana yabarni sai Allah yasakamin. Ta juya tafita tana kuka, a hanya ta Kira zarah tasa kuka, ko bayani takasa yimata, ” Aunty lafiya yada kuka kuma?  ” Ina cikin masifa zarah khaleel ya dauke Naziya yabarmin kasar baki daya sannan yanzu wannan tsinanniyar itada uwar ta sun tare min agida….. Ta kora mata komai.  tasa salati, tareda cewa Ina zuwa Aunty Anjima ki kwantar da hankalin ki.

Kuka takeyi sosai yanzu take nadama mara Amfani tunba aje ko Ina ba, domin babu abin tashin hankali a wurin ta sama ga tafiyar khaleel.

 

 

Sun sauka lafiya Wanda cab ke jiransu already a filin jirgin, tayi matukar gajiya tayi bacci harta gaji, tundaga filin jirgin take baza idanun ta domin tasan wannan kasa tanada cigaba sosai a fadin duniyar nan, domin ta hada al umma daban daban yare Kala Kala, dafa kafadar ta yayi tareda cewa ” welcome to bangkok madam. Fuskar shi dauke da murmushin farin ciki, kallon gajiya tayimai ya ce ” sorry muje ga mota. Ya bawa driver umarni ya kwashe kayan su suka shige baya yana kwakume da ita, kallon bakin shi takeyi Wanda take mamakin y’an da yake zuba yaran Japanese da driver kamar yaren da aka haifeshi dashi, saida yaga tana kallon shi yayi murmushi tareda cewa ” zankoya miki different language anan Chinese Japanese harma Hungarian language Wanda duk sun tattara a wannan kasa, kuma idan bakin sani ba bazaka banbance suba domin kusan duk kalar idanun su daya da. Dora kanta tayi a kafadar shi domin wata irin kasala takeji wadda bata taba jin irin taba a jikin ta.

Yasaka hannu tare da rungume ta, ba Abinda yakai mai wannan dadi a rayuwar shi, ganin shi tareda ita a wannan kasa da yake mafarkin ganin ta a ciki,  burin shi yagama cika a rayuwa, sai Ajiyar zuciya yake yi, ita kuwa kallon hanya takeyi tana shakar iskar wannan kasa mai matukar burgewa, ko Ina tsab tsab har suka isa unguwar da yake zama, gidajene kamar quarters ba wani hayaniya sai kukan tsuntsaye, cab din na tsayawa ya saketa tareda bude kofar yace ” let go madam we are home our small world. Fitowa tayi tana kallon KO Ina, gidan ba wani kato bane akan gidan su dake kano, Amma tasani a irin wannan kasar wannan gidan kudin shi sai yafi karfin wancan, gashi yaji fulawoyi masu bansha’awa da furanni,

Masu sanyin kanshi, fitowar wata mata Y’ar China ne daga cikin gidan zata iya kaiwa kimanin  shekara  arba’in tana sanye da afron na girki, fuskar ta sake tana mai welcome da yaren sinanci ya amsa tareda nuna mata madam dinshi, da gudu ta Kara so tana rungume ta tareda zuba mata yaran da ko zo inkasheki bazata jiba,  kayansu ya shigar ita kuma ta rakota har ciki jikinta na rawa, kamar rakumi da akala haka ta bita,

Kamar yanda kasashen na waje suke basa cika tarkace a cikin gidajen su haka shima nashi simple ba wani hayaniya sai sai dai kasan koma meye kudi ne a ciki, saida ya shigar da trolley da Jakar shi ta laptop ya dawo tareda cewa ta hado musu Abinci madam is hungry yace ta shigo bedroom ta yi fresh up su rsma sallolin su, dama akagare take da wanna Matar me shegen zuba da bata gane komai,   tuni ta cire hijabin jikinta suna shiga ta ga kujera ta zube kwance domin tayi mugun gajiya jikin ta kamar anyi mata duka, kwabewa shima yayi tareda daura towel ya juyo, yaga yanda ta kwanta tana shirin yin bacci, murmushi yayi  mai d’an sauti,  ya matso tareda tsugunawa gaban ta, ya dukar da kanshi dai dai bakinta ya bata light kiss, tayi saurin bude idanun ta, murmushi ya sake mata kafin yace ” bacci? Wani irin lumshe idanun ta takeyi gwanin sha’awa, Abun ya burgeshi sosai yaji tsigar jikin shi na Tashi Wanda ya dade yana controlling tareda Addu’ar neman dama, yau gashi gata a cikin gidan su sukadai, harshen shi ya Dora saman girar ta ya lasa tareda matsawa har kan hancin ta ya gangara lips dinta ya rike na kasan gam yana Ajiyar numfashi, bajewa yayi zaune akasan tareda rungumota zuwa jikin shi, zare bakin ta tayi cikin kasalar da yasakar mata tace ” bacci nakeji, kuma bamuyi sallah ba. “Uhmm. Kawai ya iya cewa tareda saka hannu ya dago doguwar rigar dake jikinta ya zare ta ya wurgar, jikinshi har wani irin mazari yakeyi kamar mayunwacin zaki, ” zakiyi bacci letter baby sallah kuma zamuyi yanzu, na matsu da yawa I can concentrate idan ma nace zanyi alwala bazata zauna ba yanzu… Yafada muryar shi na sarkewa, “please nagaji my body is weak, bari inyi wanka tunjiya fa banyi wanka ba muna cikin jirgi. ” kamshi kikeyi baby ke mai tsaftace ko zaki shekara baki yi wanka ba I don’t mind I can leak your body in and out right now. Yafada yana dora bakinshi a wuyan ta yafara lasa tareda karasa maganar shi, ” yaushe rabon da inyi baby sau daya fa nayi testing kika lasa min Zuma ai nayi namijin kokari ko ke kinsani.

Ganin fa da gaske yakeyi tace ” OK wait muje gado jikina zaiyi ciwo a nan please. Tashi yayi da sauri zai dagata tace “zan iya, yana bin hips da kirjinta dake cike tam da kallo wani irin shanyewa idanun shi keyi, tafara takawa cikeda tsokana da daukar hankalin shi domin taga duk duniya jikinta na mugun daukar hankalin shi, saida tabashi tazara tayi hanyar da taga ansa washroom da gudu tana cewa ” nayi maka wayau. tareda yimai gwalo ta kulle kofar ta ciki.

Da baya baya yayi tareda dafe kai ya fada gadon yana juyi, ” zaki shigo hannu yarinya you must pay for it. Yafada yana murmushi mai cikeda farin ciki.

Tana shiga ta jingina da ginin tana kallon kanta ta katon mirror din dake bathroom din kallon jikinta takeyi, ” yes dole zata rikita namiji domin tasan ita kanta bata gajiya da kallon kyakkyawar kirar jikin ta, a ce namiji kamar khaleel mai matukar aji da girman kai yau shine ke nuna mata so da naci haka, ita tasan mai sa’a ce domin tasamu miji na fita a nuna ma kawaye Ajin farko,

Ta dade kafin ta murje jikinta tsab da sabulai masu kamshi da kuma turarukan wanka,  ta tsane jikin ta ta dauro d’an karamin towel tareda nade kanta da wani saboda ta jika gashinta da ruwa domin small touch from him yanzu zata fara tsiyayo ruwa don shidin namiji ne na karshe,

Murmushi tayi ko yanzu za ayi daga idan ta fita, don haka ta d’an daure fuskar ta kadan ta bude kofar tareda fitowa batareda ta kalli gefen shi ba, Wanda shikuma yana nan a kwancen tana bude kofar ya bita da kallo yana bin mulmulallun kafafun ta har zuwa rabin cinyar da ke bude, dogon numfashi yaja tareda saurin tashi zaune ” zata kuma rikita ni, yafada a bayyane har tajishi,  tayi saurin daukar katon hijab dinta ta zura tareda ganin dadduma a gefe, yayi saurin mikewa ” wait for me bari nima inyi infito. Ya wuce badon hakan yaso ba sai dan ganin rashin walwalar fuskar ta data sosa mai rai kadan, farin cikin ta yake son gani ba bacin ranta ba, bayason ya takura Rayuwar ta, he love her, ganin ta a karkashin shi kawai is enough for him don haka bazai taba takurata akan Abinda bataso ba koda zai cutu. tuni ya saita kanshi ya zura jallabiya tana nan inda take ya ja musu sallah, duk saida suka rama wainda ake binsu duka, ta d’an kishingida idanun ta a rufe tana Azkar, mikewa yayi ya fita, yaga cook din ta shirya musu komai a dining, yadawo tareda cewa ” let go and eat food is ready. Ya juya ya fita, kafin ta ce komai kamar walkiya ya fice,  wani iri taji, why ya canja yanzu yanzu kuma?

Hijabin ta cire tareda bude trolley din da yazo dashi taga iners dinta danashi ne kawai sai  wasu dogayen riguna dake cikin akwatin da ya hadawa Ahmed rugunan sunada kyau sosai da matukar tsada dayar ja ce daya kuma blue sunji stones da beads suna daukar ido gasu roba irin masu kama jikin  nan ko hannu dayar batada daya kuma hannun ta guda daya anyi crossing dinshi daga wannan kafadar zuwa dayar,

Mai hannu din ta zura bayan tasa iners, saida tasa taga rigar dogon tsagu gareta tundaga kasa har kusan cinya, gata doguwa, tsaki tayi tana cewa wannan wace irin rigace, asarar kudi.

“Ba Abinda zan siya miki ya zama asarar kudi domin nasan zaiyi kyau da jikin ki. Taji muryar shi a bakin kofar, Wanda ya dade a wurin yana kallon ta yana murmushi saida tayi magana ne yabata amsa, tafito kamar wata model a cikin rigar, sumar kanta dake jike ta nannade gwanin sha’awa ta kwanta kamar style ya kalla, yace “zomuje food is waiting.

Kanta ta taba tana waige waige ya matso tareda dukawa ya sunkuceta bridal style, “you look pretty like that, suna fitowa mai aikin na shirin tafiya, tayi mai sallama batareda ta damu da Yanayin da suke ciki ba Wanda su ba wani Abu bane a wurin su,   saida ya zaunar da ita ya duko tareda daga kanta zuwa saitin bangon dake dining din,  zare idanun ta tayi ganin tangamemen hoton ta dabatasan ma lokacin da ya dauketa ba, kur ta kurawa hoton ido tanaso ta gano wane lokacine?

Muryar shi taji,

“Ranar da kika kusa sa zuciya ta ta buga saboda kishin ki, Wanda bansan me yasa kikabi Yaya na part dinshi ba, kinsan cewa nashiga cikin mummunan yanayi because of your love,   zagayawa yayi tareda tsugunawa gaban ta ya riko hannun ta gam,  kece macen da nafara yiwa kuka a duniya, kin san irin fanfon da shedan ya rika yimin saboda soyayyar ki?   ranar da kika shigo dakina kuwa kikayi ten minutes, Hmm ko yaya na ranar da kyar na danni zuciya ta na iya yimai magana, and because of that bankuma kwanciya a gadon ba, impact ban kuma samun natsuwa ba saida na canja gadon,   duk a tunsni na kunyi making love ne a kai,Hmmm you want understand my pain at that time nikadai nasan halin da nashiga, bantaba mafarkin zan mallake ki ba sai gashi Abinda Allah ya tsara, Ashe zanyi rashin wani gefe ne na rayuwata kafin insamu wani gefen da zai ragemin zafi da radadin rashin yayana mai sona,

Dagowa yayi ya zauna a kujerar gefen ta ya zuba mata ido ” why bakyason mu?  Tanbayar tayi mata wani iri, ta kalleshi cikeda tuhuma. ” yes nasan momy nada nata kason na hana yayana samun farin ciki daga gareki like he dream, but what about me?  I try alot domin ganin na baki lokaci domin Ina matukar bukatar kulawar ki Amma naga kamar Ina takuraki ko?  Yafada cikin kwantar da murya kamar mai lallashi, “mata biyu bayan ke idan sha’awa yasa nake like miki dana bisu suma, do you know fauziya har cikin gidan nan tana zuwa?  kinsan mata nawa nake gani tsirara?  I love only you Naziya, I want only you by my side forget about Auren gado koda yaya na bai bar wasiyar in Aureki ba, I want let you marry another man, I must marry you Naziya because I truly love you, kuma zanci gaba da nuna miki son gaskiya ba wai sha’awa kawai nakeji naki ba, let eat. Yafada yana bude plate plate din manya dake dauke da different dishes kaza roasted fish da kuma his fevourite, kallon shi takeyi magan ganun shi sunyi mugun tsuma ta tareda sanyaya mata zuciya,,wani irin kallon nayi sa’a take yimai har yafara cin Abincin shi.

Yanda aka gasa gazar yasa taji miyanta ya tsinke tuni taji yunwar duk ta taso domin rabon ta da wani kwakkwaran Abinci tun jiya don haka janyowa tayi tafara yanka da wuka da fake takai bakinta, ya mutse fuska tayi domin ba test Sam don haka ta ture ta janyo cup ta tsiyayi fresh milk ta fara sha, ” what?  Yace, domin yana kallon duk Abinda takeyi. ” if you can eat muje indafa miki wani Abun, yafada yana ture plate din gaban shi. ” no Ina ne kitchen din inje?  Mikewa yayi ya nufi hanyar tana biye dashi, saida ya nuna mata store da komai, ta ciro indomitable kuda biyu kanana da kwai, yaja kujera ya zauna yana binta da adorable look. Komai nata abin burgewa ne a wurin shi, saida ta ciro carrot dasu green beans ta yanka, dasu albasa ta daka pepper a wani d’an karamin turmin dake wurin na sinawa mai kyau, kafin ta kunna gas tasa pan da ruwa duk yana kallon ta, ta fita ta dakko kazar ta dawo, saida ta yanka dai dai kafin ruwan ya tafasa ta saka indomie da naman kazar ta zuba komai domin batada wahalar dahuwa domin su kayan lambun suma su dahu, saida taga ya kusa dahuwa ta fasa kwai biyu akai ta juya, ta zuba albasar ta,

Cikin minti biyar kamshi duk ya gama cika shi, yakasa daurewa ya matso inda take yana kallon Abincin ta murfin glass din, tareda lumshe idanun shi yace “am very lucky, a zuciyar shi, juyewa tayi a plate ta saka fake daya, “nagama. “Hmm muje. Yafada, suka koma dining, duk ture plate din gaban shi yayi ya zauna tareda daukar fake batareda ya kalleta ba Yasaka yafara ci yana lumshe idanun shi, kallon shi tayi irin ya haka?  Ya kashe mata ido, ” ga girkin matata why zanci na wata, kuma irin wannan kamshi I can’t resist gaskiya.

Tare suka ci yana faman sakin layi, har suka gama ya kwashe komai yakai kitchen, ta biyoshi da niyyar wankewa yace mai aikin zata dawo tayi suje su huta.

Dama ta gaji don haka ba musu ta nufi dakin saida ta dauki comb ta taje kanta tsab ta nade da band domin ya bushe, in so samu ne ta tube wannan rigar domin ta matse ta gaskiya, amma tasan me zai biyo baya, d’an juyowa tayi taganshi kwance dai ya idanun shi Alamar a rufe suke,  tasan bacci shima yakeji don haka taja Ajiyar zuciya ta daga rigar ta cireta a hankali ta matsa tareda kashe hasken dakin sai hasken waje kawai dake haskowa, Wanda tuni ya bude idanun shi dama ba wani bacci lamo yayi yana shayar da idanun shi, gyalen jallabiyar ta ta nade jikinta dashi ta matso cikin sanda kamar wadda zata yi sata ta kwanta a hankali, duk yana kallon ta tareda sakin murmushi, yaki ko motsawa saida ta kwanta tafara tunanin kalaman shi na dazu, wani irin shauki da natsuwa tareda wani irin feeling dinshi taji she also love him and missed his magical touch, runtse idanun ta tayi tana cewa ” were is your promise Naziya?  Bakyason ya Kara sonki ne?  Gashi ya yi bacci ya kyaleki zakiyi wa kanki tsakiyar da ba ruwa idan salifa ta mallake miki shi ki tsaya sanya yagaji da jan Ajin ki ya koma mata. Wani irin mashin kishi taji ya caki zuciyar ta, she can let that happen because itama tanada matukar kishin shi fiyeda yanda taji akan Ahmed, juyowa tayi yana rigin ginen har yanzu kirjin shi a bude dagashi sai short idanun ta suka sauka akan kyakkyawan kirjin shi mai dauke da suma  kwantacciya,………. 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 7:34 AM – Fiddausi Yunus: 5⃣3⃣&5⃣4⃣

 

 

 

 

 

 

……………….yana jin duk motsin ta kuma yana shakar iskar numfashin ta dake Kara rudashi, he is trying karta gano idanun shi biyu domin mugun jin dadin yanda take kallon shi yakeyi,  Amma Addu’a yakeyi can kasan zuciyar shi akan ta matso zuwa jikin shi, and he swear zai bata zumar da bazata taba manta d’an danon ta abakin taba. A hankali ta dora hannun ta zuwa kirjin shi tareda matsawa cikin natsuwa ta manne da gefen kafadar shi, Wanda laushin kirjinta ke gogar damtsen hannun shi, wani irin juyi kasan marar shi yayi saida yaja numfashi kamar zai shide, a gaskiya yayi mugun namijin kokari da bai fallasa kanshi ba, kafin yayi wani Abu yaji lips dinta akan nashi tana bashi light kiss.. Tana kokarin dauke bakinta yayi saurin bude idanun shi ya zagaye west dinta tareda jan numfashi ya kalleta da jajayen idanun shi da sukayi mugun canja Kala, ” baki isa ba gaskiya, wane irin kwalele ne wannan, you see I try not to disturb you why did you wake me? Diri diri tayi na rashin gaskiya tana shirin matsawa ya riketa gam tareda kallon kirjin ta da ke cikin bra sun turo sosai, hannun shi ya sauke a bayanta a hankali ya balle ta tayi saurin zubewa a kirjin shi domin kunya, don har yanzu akwai kunyar shi a tartare da ita, “Auchhhh baby sai kuma kin kuma hukuntani ta hanyar yimin bulala da wainnan balloons din masu laushin gaske… Gyalen da ta rufe jikinta tuni ya fice tarage daga ita sai kamfai,  birkita ta yayi kan gadon tareda hayewa kanta yana karewa jikin ta kallo dai dai inda zai iya gani,

Kwayar idanun shi da sukayi ja take kallo batareda ta ji kunya ba domin kamar wani irin magnet ne kejan idanun ta zuwa nashi

Wani irin son shine ke dada ratsa zuciyar ta, y’an da yake tafiyar da soyayyar shi ba kunya ba wani shamaki kamar ba indiye KO bature na matukar burgeta, Auren miji Wanda ya iya soyayya da kuma iya tarai rayar mace a ko Ina abin so ne,

Wani irin mika tayi jin bakin shi akan nippy dinta tayi saurin rike kanshi tareda Kara dannawa domin duk duniya yagama gano weakness dinta, don haka tuni ta sallama mai ragamar Rayuwar ta cikin sauki tana mai taimaka mai da duk Abinda zata iya yi, Wanda cikin minti goma ya gama jikata sharkab da ruwan hawayen shi tunkafin ya isa garin maji dadi, kalaman soyayya kuwa tasha su cikin sambatu,

First night dinsu is difficult for him kafin yasamu jin dadin saboda shima bai saba ba but this night is wow, domin zai iya cewa kamar wata Zuma ce aka narka da madara aka karamai akan wadda yasha na farko, ita kanta batasha wahala ba zama ta iya cewa kamar tafishi jin dadin Al amarin yau wani irin kwakume shi takeyi batareda ta gaji ba, sun murji juna kamar ba gobe a wannan ranar, Wanda yasha mamakin yadda yake dirzar ta Amma batayi mai raki ko dayaba,

Ita kanta batasan wuyarda tasha ba, saida ta mike zasuje wanka taji bata iya hada cinyar ta, saurin komawa tayi gefen gadon ta leka kasanta taga yayi wani irin kumburi da ja harda wani jini jini kadan, ta zare idanun ta zata saka mai kuka, Wanda yana rigin gine bai kaiga tashi ba yana kare mata kallo, saida yaga Abinda takeyi yayi saurin durowa tareda tsugunawa gaban ta ” yaya? Ware kafafun ta tayi “kaga ka kuma jimun ko?  Fuskar ta a narke, “oh sorry ba stitches kawai saboda you are tight ne shiya sa kinga nima zugi takemin kinjimun nima yafada yana nuna mata hajiyar da ke nan a mike har yanzu. Kallo tayi kadan tagani da gaske shima yadan kwaile kadan, yayi murmushi ganin yanda takalla kamar wani Abun tsoro, mikewa yayi ya sunkuceta sai bathroom tsayar da ita yayi ya hada musu hot water saida ya shiga yazauna ya d’an runtse idanun shi saboda zafi yace ” kema zomuyi sit bath, kinga dukan mu daya ne this is our second time. Yafada yana dage mata gira cikeda tsokana, hannu yasa ya janyota tareda zaunar  da ita tsakiyar kafafun shi, hannayen shi ya saka tareda zagaye Kirjin ta ya wani irin rungume su gam yanayi yana wasa dasu, tanajin yanda yake sukar bayanta dayan hannun shi na ware kafafun ta domin ruwan ya shiga.

Lafewa tayi a kirjin shi tana jin dadin yanda yake jagwal gwala mata jiki tareda ruda mata shi, bazata taba gajiya da touch dinshi ba, bakin shi a kunnen ta yana hura mata iska, ” my dream has came true baby, Matar da nake ganin bazan taba samunta ba yau gani gata we are one, Ina yadda naga dama da jikinta batareda shamaki ba, you are mine Naziya only mine, ni nakine dama kin mallake ni kinsamu Ibrahim khaleel mulkin kine sai yadda kikayi dani, zan iya rabuwa da kowa saboda ke Naziya I love you…….

Wani irin juyawa tayi domin she can’t resist him this time, ta hade bakin su tareda bashi long kiss saida taji numfashin su na shirin tsayawa ta zare idanun ta fal da hawaye ta rike fuskar shi ” I love you too khaleel I love you, nima Ina sonka kawai nauyi nakeji, how zanso d’an uwan ka kuma ince yau kai nakes…. “Shhhhh stop that, Ahmed is my brother and kinsan irin soyayya da shakuwar dake tsakanin mu dashi, what ever happened that is our destiny, let accept our destiny mu rungumi juna ki nuna min soyayyar ki danake kwadayin samu please don’t be shy kinji, let start new, dagani sai ke zanbaki duk Abinda kike so a duniyar nan Indai kudi zai siye shi, inkuma zuciya ta kikeso you already have it, zaki  iya cire wa duk lokacin da kikaso, yafada yana kashe mata ido,

Dakyar sukayi wanka suka fito bayan dauro alwala.bayan sun idar yace tayi bacci yanzu, ” kinsan kinci bashi dayawa zaki biya duka. ” wane irin bashi naci?  Tafada tana kwanciya akan gadon,, ” kinsan lokacin da nake zuwa gidan Aunty Raliya hakuri kawai nakeyi nake dawowa batareda na danne kiba a falon ta shiyasa na rage zuwa kar inyi abin kunya gidan surukai, to yau kuma dole Kibiya. ” Nagaji fa kaima ka gaji don Allah kayi hakuri nan da sati biyu. Wani irin kallo ya watsa mata tareda Y’ar harar wasa, ” Saboda gani sakarai ko, toh hakurin da nayi a baya yanzu bazanyi ba yarinya ki saba kawai, waya fada miki ma ana gajiya a harkar nan, nidai bazan taba gajiya ba ko yanzu don inada Abinda zanyi ne dana Kara, ko inzo ne only five minutes. Yafada yana kashe mata ido, kifewa tayi tareda juya mai baya domin    bacci takeji kuma batada amsar bashi tunda shi bayajin kunya.

Dariya yayi ya fita yana sosa kai, bacci tayi sosai har zuwa magrib, shikuwa fita yayi yayo mata shopping kamar hauka, tareda duk Abinda yasan zata bukata a gidan na Abinda zata iya ci,sai a lokacin ya tashe. Tana cikin jin dadin bacci taji ana hura mata iska a idanun ta mai dumi, a hankali ta bude, nata suka sauka cikin nashi ” hy sleeping beauty lokacin magrib yayi wake up . yafada yana dagata, duk jikinta ya mutu tayi salati tareda direwa kawai tana murza idanun ta, ya bita da kallon burgewa komai tayi burgeshi takeyi, matsawa yayi tareda rungume ta gam, ” kije kiyi wanka ko in yimiki ne? Girgiza kai tayi tace ” zanyi bansan lokaci ya tafi har haka ba. Tafada tana yin gaba bayan yasaketa,

Shiga bathroom din tayi ta kwabe tareda fara yin wanka, turo kofar yayi ya shigo dai dai tana dauraye jikin ta, tayi saurin kallon shi tareda kwabe fuska ya zubawa ko Ina na jikinta da kallo yana hadiye miyau, saurin karasawa tayi ta janyo towel tana harar shi ” meyasa ka shigo baka bari na gama ba?  tafada cikin shagwaba, matsowa yayi  jikin shi kamar Wanda kwai yafashewa yariko west dinta yana jan numfashi ” why nida halalina?  Yafada yana kokarin kwance towel din ta rike tareda fisgewa tayi waje da gudu tana dariya, Saida ya zauna kan sink na d’an lokaci ya dawo cikin hayyacin shi kafin ya sosa kai shima ya tube zuwa wanka.

 

 

Da kanta ta koma kitchen domin muguwar yunwa takeji rabon ta da Abinci tun rana,  store din tagani da su spaghetti da shinkafa irin nacan shiru tayi nadan lokaci kafin tayi tunanin mezatayi,  shinkafa fara ta dafa ta hada stew da naman kaza, bayan ya idar da sallah ya dauki wayar shi ya fara kiran manager domin jin ko yakai sakon shi yace mai yakai suka dade suna tattaunawa a tsakanin su kafin  ya Kira kawun shi, shima sundauki dogon lokaci yana mai nasiha akan idan ya d’an dai daita Al amuran shi a can ya dawo domin hakkin mahaifiyar shi da kuma Matar da yabari tunda akwai igiyar Auren shi akanta.

Sai da gaban shi yafadi da ya tunada akwai wata salifa wai, momy kan dama dole ya nemeta saboda uwa uwace Kuma so kawai yake ta fahimci kuskuren da ta tafka tundaga farko.

Shiyasa bai san me takeyi ba har ta kammala ta shigo, Saida sukayi isha’i yace “suje restaurant akwai Wanda ake dafa Abincin da zata iya ci,  tace ta dafa musu Abinci ai. Ta mike tareda fitowa yabita da kallon mamaki, ya tashi ya bita falon, harta fara serving nashi, kamshi nayimai welcome, ya  shaka tareda matsawa ya rungume ta “yaushe duk kikayi wnn aikin madam? Murmushi tayi kawai tace” let eat karya huce. Tafada tana cire hannayen shi a jikin ta, ya zauna fuskar shi tuni ta cikada walwala da Annuri farin cikin, zama yayi ya kwashi dadi tareda hamdala,

Ya za ayi yaso wata mace yanzu bayan ta hada komai, kyau ilimi hakuri uwa uba ga tarin Zuma. Yanaci yana kallon ta, itama taci sosai saboda yunwa dazu ba wani koshi tayi ba yana kallon yanda takecin kaza yagane tana kaunar chicken, Wanda ita kanta tarasa dalilin dataci wannan naman da yawa haka.

 

Tsakiyar falon ya koma bayan sun kwashe komai lokacin misalin karfe tara na dare akasar bangkok Wanda yayi dai dai da karfe daya na daren kasar mu Nigeria, domin banbancin awoyi, wanka taje tayi tareda duba wurin waldrp din dake dakin tana duba trolley din su taga bata wurin, budewa tayi taga ya shirya mata sababbin kaya makil tundaga dogayen riguna riga da sket su jeans passion na mata har zuwa kan  kayan bacci masu matukar kyau da daukar hankali, wani iri taji, wato tana bacci yayi duk wannan Abubuwan bata sani ba. Wani irin tausayin shi taji domin tasan duk Abinda yakeyi yanayi ne domin yafaran tamata,  wani nazari tayi na d’an lokaci akan Rayuwar shi, yanada murdadden hali shiyasa baida tsoro halin shi daban dana Ahmed shiyasa yazama jarumi tsayayye.

Wata riga ta zabo guntuwa iya guiwa ja rigar tayi mata kyau sosai daga ita sai d’an pant mai irin v shape din nan, gaban rigar nada kokon brah da yakamata dam, rigar ta haskata sosai ta gyara sumar ta tareda feshe jikinta da kamshi ta kalli mirror tagan y’an da ta fito kamar ka saceta ka gudu. Motsin da taji ne yasa tayi saurin juyowa, ya tsaya a bakin kofar ya nade hannu yana kare mata kallo tundaga kasa har sama, bazai iya magana ba sai ido, ganin yanda yake kallon ta tasan ya yaba don haka cikeda yanga domin daukar hankalin shi ta matso kusa dashi tace ” naga kaya nagode sunyi sosai Allah ya Kara budi da Arziki, wato Ina bacci kafita har kayi wannan aikin bansani ba?  Lallai nayi bacci sosai, muje muyi kallon KO?

Kur ya mata ko kiftawa bayayi, ” she hardly talk, don haka duk lokacin da take magana Abin yake matukar dauke mai hankali, domin muryar ta shape din lips dinta, yanda take magana, yana tafiya da zuciyar shi baki daya, bare yau ga wanna shigar data mugun rikita shi, fisgota yayi cikin sauri zuwa kirjin shi domin yasamu saukin Al amarin, muryar shi a sarke yace ” ba wani kallo bayan kin cikamin ciki da Abinci kuma yanzu kinzo kin rudani what you expect from me now?

Wani irin daukar Amare yayi mata tareda switching light yana cewa ” let watch each other babe….. Suka shige blanket domin farantawa juna rai tareda manta duk wata damuwa da suka baro a 9ja.

 

 

Sati biyu suka kwashe suna murza soyayyar su, ta murje tayi bulbul da ita, kullum cikin kwaso mata kayan gayu yake , a cikin garin kuwa ba inda bai zagaya da ita ba, wasa wasa itama tafara cin cimar shi ta mutanen sinawa, har tanaso ta fishi zakewa, yana matukar mamakin tama yanzu, gashi duk matsin da yake ganin yana yimata bata nuna gajiya warta, sunyi matukar shakuwa, soyayyar su suke sha sosai, koda yaushe suna like da juna, kusan kullum sai tayi waya dasu Aunty Raliya harma dasu malam domin ya d’an karo mata wata sabuwar wayar ta yayi, gashi d’an zaman nan yana ta koya mata tuki idan sun d’an fita, ko Ina suka wuce kallon su akeyi, shikuwa haka zai kwakume abarshi gam yace ” baby da zaki Y’ar da da kin rika zama a gida ko ki saka nikab kafin jini na ya hau ko mu daina fita.

Dariya kawai takeyi tace ka cika kishi Zaauji. Sunan dake matukar faranta mai zuciyar shi.

Yau basuje ko Ina ba kwance take tana cin roasted  lobster taji yaji, yanzu tafishi sanin dadin sea food, daga ita sai wani arnen guntun wando passion na mata da shimin shi data kamata dam, tazama Y’ar gari don baya kaunar ganin ta cikin manyan kaya, kamar baby doll, ya shigo cikin kanan kaya ya murje yayi kyau sosai yana tafe yana waya da manager dinshi na Nigeria, ” kaje gidan ka dubamin lafiyar Momy na nakira wayar ta bata shiga. Yafada cikeda damuwa domin haka kawai yaji yana son yaji muryar ta domin yasan a duniya Momy nason ya’yan ta gashi ba Ahmed shima ya mata yaji, kuma yasan no matter what dole ya sauke hakkin uwar nan, kallon shi takeyi kamar ta lashe shi takeji, saboda kyau da kuma cikar haiba ga iya soyayya ta kowanne fanni don haka yayi nasarar sace zuciyar ta baki daya,

Kashe wayar yayi tareda rike kugu yana kallon Abincin da takeci, tareda kallon y’an da take kallon shi kamar mayya, matsawa yayi ya d’an bata fuskar shi, ” baby!  Wannan pepper din will affect your health is too much, koni banacin yajin su saboda is too hurt amma look at the way you are eating this please. Yafada yana zama kusa da ita tareda dafa kafadar ta, ” uhm ni dai inajin dadin shi ne inba yaji baya mun dadi sosai karka hana ni don Allah.

Fuskar ta ya kalla data marai raice saboda shagwaba yace, ” is OK but idan nayi Ajiya anan no more pepper OK!yafada yana shafa cikin ta dake dame cikin shimi tareda zubawa welcome dinshi ido,

Kallon shi tayi cikeda tuhuma ” Ajiya kuma?

” yes now, my little prince or princess, oh god baby am earger when please zaki bani baby?  Zaro ido biyu tayi ” ciki?  “Yes ciki baby. Yafada yana kallon kwayar idanun ta da yanda ta budesu cikeda tsoro,

“Gaskiya akwai wahala ban shirya ba. Tafada tana tura baki. Dariya yayi ya dora lips dinshi a saman d’an mutsilin bakinta ya tsotsa kadan tareda saurin cirewa ” oh my god baby this kind pepper. Yana hura baki saboda zafi, tayi dariya tareda tashi ta haye cinyar shi ta mayarda bakinta tana. ” ai sai ka karasa min bayan yafara dadi zaka cire. Ta hade bakin su tana lashe each and every corner na bakinshi domin jinshi takeyi kamar sweet saboda test, tuni tasa yayi lakwas tareda sake mata ragamar bakin da jikin shi ta dora hannun ta daya akan kirjin shi tana cusawa ta cikin rigar shi domin tayi wasa da nippy dinshi da suka zamar mata toy,

Hannun ta ya rike tareda d’an cire bakinshi idanun shi na wani irin shigewa yace ” baby if you touch me that way am going to strip you right here.

Wani irin kallo killer smile ta sakar mai tareda kashe mai ido kamar yanda yake mata ” am ready for th…., bakinta ya cafka ya cirata sama cak sukayi master bedroom………… 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/20/21, 5:42 PM – Buhainat: 5⃣5⃣&5⃣6⃣

 

 

 

 

 

…………… Shafa mata mai yakeyi bayan komai ya lafa har sun sheko wanka tana lafe a jikin shi kamar wata jaririya, sai jujjuyawa takeyi a jikin shi, “hay” kinga banason Ina matsa miki Amma kina kureni fa baby, kinfasan inada lafiya, zan iya Kwana Ina baki aiki but ina jin tausayin jikin nan kar in jawa kaina jinya kin ga bazan iya hakurin Kwana daya ko wuni batareda na yi aiki ba, kinga kin sabamin zaki bani breakfast lunch and dinner every day, shiyasa nake lallabawa. Idan ina period fa ya zakayi?  tafada tareda kallon shi. Tureta yayi fuskar shi a hade, that is my rival bazai zoba saboda yasan ma bazan iya hakuri ba. “Dariya tayi tareda cewa ” zakayi dole gashi sai nayi one week. Hararar ta yayi ” sai yazo ingani look karki sa jini na yahau tun yanzu ma, wait ba every month akeyi ba?  “Yes  yanzu satin mu na uku anan da sauran time. “Aa nifa ya kusa zuwa yamayi latttin zuwa koda naje gidan Aunty banyi ba…. ” oh stop this story please ya mike tana mai dariya ya kwabe towel din jikin shi tareda juyowa ya kalle ta, “yazakiyi da ita da kike wannan maganar sati daya, bayan koda yaushe tana mike bata taba kwanciya because tana ganin ki…. Hannu ta daga sama tana dariyar tsokana tace ” baruwana bani bace kaga masu laifin nan. Tafada tana janye towel din jikinta a hankali ta saman, suka yi mai hy. Saida ya kusa zubewa yaja numfashi tareda hadiye miyau masu kauri, ” you see. Fuskar shi kamar yayi kuka, ” kinja sai na Kara wallahi haba don Allah. Ya nufota a sukwane yana wurgar da towel din hannun shi, tayi tumbling tana kyalkyale mai dariyar tsokana domin tasan tagama kunno shi,

Wasan tsere suka farayi a cikin dakin tana zille mai, Saida ya gaji batareda tabari ya kamata ba ya zauna a sofa cikin wayau yace “Ahhhhh cikina zan mutu…..

Wani irin tsalle tayi tareda direwa kanshi saboda tsorata tana “me ya sameka zauji?  Fisgota yayi yasa Dari ya, ” nakamaki. Ya cafki Abin da ta rikitashi dasu yana murzata domin debe takaici, koda zai making love da ita sau dubu baya taba gajiya da ita don haka ko yanzu tuni ya nemi kwanciyar  hankalin shi a jikinta.

Wanda taji wuya sosai a hannun shi, Saida ya tausaya mata, bayan sun natsa tasa mai kuka ” nidai karka kuma yimin irin haka Allah zangudu Nigeria inbarka anan.

Lafewa yayi a jikin ta yana maida numfashi, “am sorry baby kece ai, kuma ai duk inda zakije saina biki, I can’t do without you. Bayan kece kika nuna min hanyar datafi kowace dadi, baby Aure da Wanda kakeso akwai dadi, nasani idan zan zauna da wata mace bazan taba jin dadin da nakeji yanzu ba. Ya tashi tareda d’an matsawa zai sauka yace ” Umm tunda inada wadda nakeso zanyi manage in hada da Salifa inji ya abun dayane ko da banbanci, don haka mukoma Nigeria din ko?  Tashi tayi tareda sa mai kuka tana jifar shi da filo da duk abinda yazo hannun ta, dariya yasa yana cewa ” Subuhanallah baby kina so ki kone ne kike dukan mijinki?

Biyoshi tayi tareda murde mai fatar gefen ciki ” yanka ka ma zanyi da ita idan naga ka kalleta. “Auchh baby this is wickedness mana, kaina bisa wuya wane ni inyiwa Naziya kishiya. Yafada ta sakeshi ya ruga yana cewa “bayan wadda kikeda ita fauziya ma zata dawo ai. Yafada bathroom ya kulle kofar don yasan sauran. Kishin shi da take nunawa kiri kiri na bala’in burgeshi, zai iya cewa shine first man da zaiso yaga ta daki wata mace ko tayi fada akan kishin shi don haka yana jin dadin tsokanar ta da zancen kishiya.

 

Nigeria

 

Tsawon satikan da suka wuce bamasu dadi bane a wurin Mommy, domin zan iya cewa ta hadu da kadarin ta, Salifa da mahaifiyar ta sun mayarda gidan ta d’an dalin y’an iska, tanaji tana gani sun maida ita Y’ar kallo, gashi sun toshe duk wata hanya da sukasan zata samu taimako, sun kori duk ma aikatan gidan sun kawo nasu har mai gadi wani bamaguje suka kawo mara imani tareda bashi umarnin kar Wanda ya bari ya shigo musu gida Saida Y’ar dar su, kab y’an uwanta sama sun dauke kafa sai zarah, ga ta ita kuma tabi mijinta south Africa, hatta da motocin ta duk sun kwashe sun hanata fita saboda sun tsorata ta ta hanyar nuna mata kwalba daukeda zuciyar khaleel, “kinga wannan, duk ranar da kika tsallake dokar mu sai mun fasata kirasa shi baki daya domin muna fasata kwanan shi ya kare. Shiyasa batada zabi sai zubawa sarautar Allah ido, tariga tagama nadama a Rayuwar ta, meye laifin Naziya?  Yarinyar nan dai dai da kallon banza bata iya ramawa, ta zageta, ta hantareta, ko sau daya bata daga kai ta kalleta domin taji haushi ba,

Kuka tasa  data tuna yan da ta takura ta lokacin Ahmed, da irin katangar da tasa musu atsakani, da yake Ahmed yarone mai biyayya har yabar duniya bai ketara dokarta ba domin ta sheda.

Wayyo Allah ni nayiwa kaina, ni naja na rasa dana, ni na hana kabar koda kwanka ne a duniya da zai ragemun radadin rashin ka d’an Albarka, nasan da kaine bazaka taba gajiya da mahaifiyar ka ba d’an Albarka, Ahmed kagama da duniyar nan lafiya Allah ya baka sakamako mai kyau a kiyama ka yafemin d’an Albarka.

“Ibrahim nagode daka sa na gano kuskure na, nagode  daka tsaya da kafafun ka, da na kuma tafka wani kuskure Allah ya tsare min kai. Shigowar su ne kamar wasu karuwai cikin sashin ta yasa tayi saurin goge hawayen ta, Salifa ce da momyn da wasu kawayen nata irinta, suka zube suna mata kallon rainin wayau, “kinga balkisu dafa mana Abinci muci yunwa mukeji ga kuma baki sunzo masu aikin nan duk basu iya girki mai test ba. Tafada tana mikewa “ni bari inshiga daga cikin dakin inkwanta kafin  ki kammala. Kallon kawar tata tayi “Yanzu Hajiya sharifa abun yakai can ki kwaso min karuwa….. Wani irin kwashe ta Salifa tayi da kafafun ta, ” kiga karuwa a zuri’ar d’anki kinji. Kara tasa kugunta ya Amsa saboda girma ga jiki, momyn salifa tace “Ashsha uwar miji cefa so kike ki kone an salee na?

“Sai na fara konata kafin ni inkone idan bakinta bazai mutuba,  kuma ki wuce ki dafa min Abinci ko in karasa ki wallahi in binne ba Wanda zai bincike ki.

Dariya kawayen sukasa harda tafawa, ta mike da kyar taja kafa zuwa kitchen, tana share hawaye ta sai rariya da kudinta.  Haka ta baje ta zuba musu girki badon Allah ba, kuka kuwa ai yazama mata sana’a, tanayi tana hakkin ki ne Naziya.

Fitowa tayi domin ta shirya musu Abinci tasame su hade a kasan carpet suna romancing juna kowace da Y’ar uwarta salifa kuwa ko rigarta ta cire tana shan yaji dayar na sha mata nono a tsakiyar falon Momy,  tray din dake hannun ta ta saki saboda firgita da tsoro. Yau taga Rayuwa, Innalillahi wa inna ilaihirraji’un. Tayi taslima da karfi, Wanda karar try bai dawo dasu hayyacin suba amma salatin mommy yasa suka juyo, ko a jikin su salifa ta buga mata tsawa ” meye kamar baki taba ganin romance ko shan nono ba bayan kema kinyi da tsohon mijin ki, oh come on ki zo ki bamu Abinci yunwa muke ji. “Babe bari mu koshi mu koma can part din nan akwai sa idawa. Ko momy ta fito sai tayi tofin tsiya kafin tayi shiru.

Duk inda tashin hankali yake yau mommy ta gama ganin shi da jin shi, subuhanallah me ta yayubo a rayuwar ta?

Jikinta na rawa ta tattara su plate din ta koma ta kwaso wasu ta shieya musu komai, wani irin zazzabin tashin hankali ke kamata, takasa koda magana.  Tana gama shirya musu Abinci ta koma dakin Ahmed domin dakin ta kawarta ta shiga,

Kafin kace me jinin ta ya mugun hayewa.

Ba waya ba yanda zata iya kiran likitan ta.

Domin har wayar ta sun dauke tana cikin tuminin takabar salifa wai.

Ciwo ya rufeta ba mai kula da ita. Haka take cikin wahala har safe, Wanda su suna cin Abincin su suka bar mata gidan zuwa nasu domin karasa masha’ar su,

 

Kwana biyu tayi cikin mugun Yanayin dakyar take iya tashi tasha koda ruwa tafita hayyacin ta sosai Wanda a ranar khaleel ya tura manager Wanda yana zuwa yaci karo da sabon mai gadi da ya hanashi shiga gidan, wai Hajiya tasa dokar kar Wanda ya shigo Saida izinin ta,

Wanda dai dai lokacin da  kawayen nata suka fito zata rakasu kanta ko d’an kwali tana sanye da wasu matsiyatan kaya na rashin tarbiya mai gadin ya ruga ya wangale musu gate suka fita, haka manager ya saki baki da ido yana kallon salon iskanci, har zata juya ta koma ta gan shi ya zuba mata ido, kare mai kallo tayi, ta yaba gayen very young and handsome ba laifi shima.

Matsowa tayi tana karairaya ” hy handsome me kake nema?

Kallon banza ya watsa mata yace Hajiya nake neman Oga khaleel ya ce inzo induba ta. Yafada kai tsaye, ” kai waye?  ” manager dinshi, zan iya shigowa?  Hadiye miyau tayi saboda jin sunan khaleel tace ” yeah ofcos shigo.

Shigowa yayi kawai yana kallon gidan duk ya fita hayyacin shi domin ba wasu masu aikin kirki suka kawo ba,

 

Part din Hajiya ya shiga  Wanda a nan ya sameta ta rarrafo da bin bango da kyar tafito domin muguwar yunwa takeji duk da tana cikin ciwo.

Yayi matukar firgita ganin yanda ta fada cikin sati biyu da bai ganta ba, tana ganin shi taji wani irin sanyi da farin ciki don haka ta zaburo, Wanda tuni ta zube Tim a kasa tasa Kara. “Subuhanallahi Hajiya. Ya nufota da gudu domin ya taimaka mata Wanda yana matsawa yaga ta sume.

Cikin gaggawa ya Kira Asibitin da yasan suke zuwa yace  likitan yazo domin bazai iya dagata ba Abunka da ba kadan ba.

 

Yadai taimaka ya jata saman kujera Saida likita yazo suka kaita dakinta da taimakon nurses da aka zo dasu, Abunka da kudi tuni aka fara bata kulawa cikin gaggawa,  sun dade akanta kafin likitan ya fito yasamu manager, ya zare glass din idanun shi, ” Ina me gidanka yake yakamata ya fita da ita kawai kai tsaye idan yana son ta samu kulawa domin da Alamun tasamu mutuwar barin jiki sakamakon hawan da jinin ta yayi sosai.

Hankalin shi ya tashi domin bai san ta Ina ma zai fara wannan fadawa khaleel ba halin da ake ciki,

Don haka ya Kira kawun su ya fadamai komai yayi salati yace gashi nan zuwa yanzu.

Saida ya dauki uwar gidan shi kafin ya tafi shima,

Halin da suka sameta a ciki  ya mugun daga musu hankali, cikin gaggawa kawu modu ya ce a mayarda ita Asibiti zaifi kafin a Fita da ita. Fita yayi  yana neman wayar khaleel, Wanda yayi dai dai da fitowar Hajiya shaeefa da salifa domin ganin meke faruwa a gefen mommy da manager yazo, basu taba zaton khaleel zai waiwayo taba sai sukaci karo da kawu modu yana saka waya a kunne, kallon shi sukayi a tsorace domin basuda gaskiya, aiki ya lalace bayan su sunyi farraku a tsakanin ta da duk wani Wanda zai taimake ta, how yanzu ba aje ko Ina ba ga modu a gidan… Murya kasa kasa salifa tace ” mommy meye nake gani me Alhaji  yazo yi nan?  Aikin ya karye ne?  Mun shiga uku. ” ke don Allah yimin shiru wa ya isa ya karya aikin  boka ai ko ita ban barta haka ba bare khaleel bari kigani bazai zoba ya  Riga ya tafi shikuma wannan me ruwan mu dashi.

Ajiyar zuciya tayi, “Hmm har na ji tsoro domin nafara jin kamshin dollar’s din da zan mallaka.  Fitowar da akayi da ita ne yasa suka bisu da kallo , ba Wanda ya koma kansu har sukabar gidan da ita,

Juyawa tayi cikin gidan ta momyn ta bita, sai zagaye takeyi, ” kingani Ashe batada lafiya ne wallahi khaleel zai zo mommy ni tsoro nakeji. ” relax baby me zai faru idan yazo?  Bare bazai zoba wannan nadewar da kikaga tayi bazata kuma mikewa ba  bakin ta bazai taba budewa ba bare tafada mai me yafaru, don haka Ina zuwa bani jakata in fita yanzu.

Itadai tafara tsorata domin khaleel ba namijin da za ayi wa iskanci a kwashe lafiya bane.

Saida suka bata special room a Asibiti kafin kawun ya Kira manager yace bani number da yake kiranka da ita.

 

Lokacin suna zaune a falon su suna kallon season film na Philippines tana lafe a jikin shi kamar mage shikuma hannun shi na cikin wuyan shimin jikin ta,  yaga kiran manager dama jira yakeyi, saurin tashi yayi ya gyara zama tareda ciro hannun shi cikin rigarta, yayi cutting call din ya kira shi, ya akayi ne?  Lafiya kalau ga Alhaji. Ya bashi wayar,  gaisawa sukayi kafin yace ” khaleel kazo fa domin Hajiya jinin ta ya hau yanzu haka tana Asibiti anyi admitting dinta, jikin yayi tsauri wannan karon kayi kokarin dawowa ko a turota can.

“Innalillahi wa inna ilaihirraji’un, Ina zuwa kawu insha Allahu. Ya kashe wayar hankalin shi tashe, ya dafe kai, jin yake bai kyauta ba Sam na barinta da yayi, dafashi tayi ” me ya faru ne?  Dago idanun shi yayi, ” we’re going back to Nigeria mommy ba lafiya tana hospital. Yafada cikeda damuwa, “Subuhanallah, Allah ya bata lafiya, bari in shirya mana kayan mu tom. Tafada tana mikewa, ya riketa, ta tsaya, ”  ki zauna inje indawo mana.” no ni dai zan je kuma kaga bamusan Yanayin jikinta ba gwara mutafi gaba daya, koda zamu dawo tareda ita zamu dawo.

Rungume ta yayi ” bakya tsoron me zatayi?  ” me zatayi?  Uwace fa ta isa ne kuma kome takeyi tana yi ne saboda  tana son mu don haka muje mu fara shiri. Kara damke ta yayi yana mai kisin din wuyan ta, har Saida taji tsigar jikin ta na tashi tayi saurin janyewa ” karka hanamu shiryawa Malam let’s go. Tafada tana dariya tareda ruko shi tana janshi yabita yana murmushin karfin hali, daurewa yakeyi karta ga tashin hankalin shi, amma a dame yake.

Duba time yayi yaga karfe hudu na yamma a kasar yace let me check in akwai available plight mu tafi yau kawai.

Yafada yana dubawa a wayar shi.

Tausayi yabata sosai domin duk kokarin shi na ganin ya daure abun yaki yuwuwa domin damuwar a bayyane take a fili.

 

Ita ta shirya musu kayan da zasu bukata,

Kafin ya shigo cikin sauri ” let get ready akwai jirgi mai sauka  Abuja. Yafada yana shigewa bathroom. Tashi tayi itama ta bishi har yafara wanka ta tsaya daga nesa tareda zuba mai ido cikin hanzari yake Abinda yakeyi,  domin duk hankalin shi ya koma gida. Hmm khaleel ne zata biyoshi bathroom ya share?  Lallai a dame yake, don haka bata matsa ba Saida ya gama ya matsota ” quickly baby. Ya fita, tayi Ajiyar zuciya ta fara itama.

Ten minutes ta shirya domin ta lura a hanzarce yake, mai aikin shi da yabawa hutu ya Kira yace tadawo kan aikin ta na kulada gidan zai koma 9ja.

Sai zuwa tsakiyar dare jirgin su ya daga,

Like you know is a very long journey, don haka ko yanzu Saida suka Kwana a hanya da sassafe jirgin su ya sauke su a filin jirgin na babban birnin tarayya. Tayi matukar gajiya, fiyema da tafiyar su domin jikin ta mugun kasala takeji  da batasan Ina ta samo asali ba. Domin ita batada ganda ko kadan,

Cikin doguwar Riga take maroon  tayi matukar murjewa tareda Kara kyau, kafarta cikin low pass baki mai kyau sai Y’ar Karamar Jakarta data rataya,

All eyes on her, gayu sai baza ido sukeyi sunga mai zafi, ya ankare don haka tuni ya matso tareda rungume kayan shi a kafadar shi saboda kuraye,

Sai da tayi dariya domin ta gano shi yace “what?   “Bakomai. “Hmm I don’t know why kikayi irin wannan kwalliyar?

Bafa kwalliya a fuska ta. Yes yakamata kisaka katon hijab kinga nan ba can bane sunayin kamar su  dauke min ke bazan iya ba zaki dawo da saka hijab malama,

OK malam, Tafada tana jin dadi tareda dariya, plight ya Kuma sama musu zuwa kano, Wanda ba Wanda ya fadawa ya shigo 9ja, har Saida suka sauka a  kano ya Kira manager yace ya sa akawo musu mota suna Aminu kano airport.

Jikin shi na rawa yace gashi nan zuwa, da kanshi ya  zo tarbar su.

 

Sun d’an jirashi a reception kafin ya iso,

Ya musu barka  da Zuwa kafin ya  dauki kayan su ya zuba a motar, suna tafe yana tanbayar shi jikin Mommy, yace tana Asibiti har yanzu su wuce ne kai tsaye?  ” no bari muyi dropping madam  dina a gida first sai mutafi. ” A’a mu wuce kawai ban gajiba nima inaso in ganta.

D’an hararar ta yayi kadan, yace toh su tafi. Tanbayar shi tayi da ido what?  Ya share. Saida suka isa hospital din ya  fito itama zata fito yace kidaina magana a gaban wani ke bakisan yanda muryar ki take ba ko? Oh shine matsalar?  Sorry Zauji. Don’t repeat that. cikin bada doka ya fada. Suka jero kamar taurari,

 

 

 

Adakin mommy ce kawai kwance sanye da na urorin dake taimaka wa jikinta, su kawu modu da uwar gidan shi suna zaune a waje domin dokar Asibitin. Suka iso, sunyi matukar mamakin ganin su haka da sauri,  Dama ka taso Ibrahim?  eh kawu ya mai jikin?  Toh tana ciki kaje kaga likitan first. Wucewa yayi yabarta a wurin, ta gaidasu cikin girma, mama uwar gidan kawu ta rungume ta kamar Y’ar ta cikin jin dadi sannu  Y’ar Albarka.

A zaune yake doctor na yimai bayanin basu gane kan Al amarin nan ba yau jiya da aka kawota da Alamar improvement amma yau jikin ya Kara nauyi bayan duk na urorin dake taimaka mata. Dafe kai yayi yace, Zan iya zuwa in ganta?  Yafada idanun shi sunyi ja tun baiganta ba, likitan yace  “yeah sure muje…….. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/21/21, 7:43 PM – Buhainat: 5⃣7⃣&5⃣8⃣

 

 

 

 

 

 

…………… Tunda ya shiga ya hango ta a zube a gadon ya shiga tashin hankali, idanun ta ta bude a karon farko ta zuba mai idanu, so take ta motsa jikinta amma bazata iya ba, bakinta takeso ta bude bazata iya ba, domin har d’an karkacewa yayi kadan, ta rame a cikin Kwana kadan, wasu irin hawaye ne masu zafi suka biyo kumatun shi, for the first time yana regret na bijirewa umarnin ta koda zai mutu, saboda soyayyar uwa da d’a sai Allah, da kyar yaja jiki ya matsa wurin ta tareda dafata yasa kuka mai ciwo, “Am sorry mommy na am sorry”,  nasan da yaya Ahmed ne bazai taba barinki a cikin wannan halin ba, gashi ni na barki mommy, am not a good Son mommy am sorry.

So take ta lallashe shi tare da nuna mai baida laifi amma bazata iya ba, sai hawaye da kebin kuncin ta itama, dagowa yayi cikin sauri, ya share mata hawayen ” please don’t cry momy”, zanfita dake ko ma wacce kasa ce zaki warke da izinin Allah. Yayi saurin tashi ya koma wurin likitan.

“Doctor zan iya tafiya da ita China kai tsaye ba wata matsala?  eh babu saidai mun dorata akan medication na tsawon sati daya, muna so muga ni idan maganin ya karbeta nan da Kwana uku munga cigaba basai ka Fita da ita ba, so have some patience sir khaleel.

Haka ya fito a sanyaye idanun shi sunyi jawur, tundaga nesa taji ba dadi tana ganin Yanayin shi tasan ba lafiya,

Har ya matso tareda bawa manager umurni kai tsaye fuskar shi ba walwala, “take my wife home”

Ya juya yana Kara yiwa kawu bayani, jikinta yayi mugun sanyi y’an da yaki ko kallon ta kuma tana ganin damuwa karara a fuskar shi, daga dawowar su mommy tafara shiga tsakanin su ne ko kuma ciwon tane yasa ya shiga wannan mood din?

Kasa tafiya tayi ta matsa ina dakin inganta kafin in tafi?  Tafada cikin kwantar da murya,

“Kije gida no need, batada lafiya banason Abinda zai daga mata hankali kuma.

Kallon tuhuma take mai ba tare da ta gano manufar shi ba ta juya cikeda sanyin jiki domin batada zabi,

“Hajiya ina zan sauke ki?  Shiru tayi kadan tana tuna ai ba a gidan shi ya dauketa ba don haka ko yanzu gidan Aunty Raliya tace suje domin batasan me zata fada ba in taje gidan malam.

Tunanin Yanayin shi takeyi a zuciyar ta, they are just fine kafin suzo Asibiti, meya faru? Haka take ta tunani har suka isa gidan Aunty, akwatin ta ta cire tace yaje da nashi kawai.

Aunty Raliya tayi matukar mamakin ganin ta kamar daga sama Saida ta tsorata.

“Naziya saukar yaushe?  “Yanzu muka shigo”… Tayi mata bayanin mommy ce ba lafiya tabar shi a Asibiti, “to ke meyasa baki wuce gidan kiba?

“Aunty ba anan ya daukeni ba da zamu tafi ko kin manta meya faru? toh Naziya naga kuna lafiya kalau da mijin ki me zaisa ki dawo gidana? ” ko in tafi gidan malam ne ?  Tafada cikin fushi kadan da ya hadu dana khaleel ga tanbayoyin Aunty Raliya ga wata irin anger da takeji a zuciyar ta, “Aunty Matar shi na cikin gidan wadda akeso ya Aura mezan je inyi a can?

A’a kanwata duk dai haka bata tasoba, welcome back little sister, irin wannan fushi daga ganin ki kinyo mana tsarabar d’an China ne ko bangkok?

Kinga y’an da kika koma kamar atabaki jini ya fito jikin ki kamar wadda aka saka a engine, ai da badon nayi miki kyakkyawan sani ba bangane ki Naziya.

D’an murmushi tayi kadan, duk da haka zuciyar ta nakan khaleel, Sai da ta huta, Aunty Raliya ta bata Abinci taci kadan ta watsa ruwa, Aunty Raliya ta zauna gefen ta “Naziya akwai matsala na lura, meke faruwa ne meke damunki?  Shiru tayi da kamar bazata yi magana ba Amma bata iya boyewa Aunty damuwar ta, da in ina tafada mata Abinda ke damunta.

“Mtsww kin dagamin hankali a banza, kika sani ko ciwon nata yayi zafine shiyasa kika ganshi haka, banson shirme ni banga Abun damuwa a cikiba.

Ajiyar zuciya tayi, badon ta gamsu ba imfact fushi ma takeyi dashi, don haka baccin ta ta shaka sosai don tagaji da zaman jirgin.

 

A Asibiti sai bayan ta wuce ya bita da kallo yana hango reaction dinta yasan ta shiga damuwar canjawar shi, and he can’t help it domin ganin mommy cikin wannan Yanayin duk ya dagula mai lissafi, sannan gashi yanzu Yanayin da yaga ta tafi ya kuma hargitsa mai tunani, bayason barin mahaifiyar shi kuma he wants to go to Naziya, haka yayi ta sintiri gasu kawu sun wuce gida yace sutafi su huta tunda yazo, dama ba azama damai jinya don haka suka tafi.

Ko yunwa bayaji duk da baici Abinci ba ko a jirgi, wallet dinshi ya ciro tareda wayar shi ya canja layin shi zuwa na gida yafara tunanin kiranta, lokacin tana bacci kuma tunda suka sakko 9ja batabi takan wayar ba don haka bata kunnata ba, jin ta switch off ya dafe kai, malam yakira suka gaisa, “Ibrahim kun dawo gidane naga number kasar mu? ” eh malam mommy ce ba lafiya shiyasa muka dawo ba shiri.

“Assha subuhanallahi toh kuna ina yanzu?  Yafada mai Asibitin da suke.

Malam na kashe wayar ya tashi daga wajen ya shiga cikin gidan yasamu Inna kulu, yace ” Hauwa bari inje Asibiti mahaifiyar Ibrahim aka kwantar harma sun dawo suma. Ta jajanta Abun kafin tayi mai adawo lafiya, wani Almajirin shi babba  da yazo gaida shi ya kaishi a roba roba har Asibiti.

 

Cikin girmama surukin nashi ya tarbeshi suka shiga har dakin mommy, malam ya jajanta tareda gaida ita tabisu da ido,

“Um um Ibrahim wannan ciwo nata tun yaushe ne?  “Jiyane suka kawota Asibiti Amma bansan yaushe tafara ciwon ba. Yafada yana dukar da kanshi, “Assha, toh me likita yace akwai sauki ko Alamar samu?  Ya mayarmai da yanda duk likita ya fadamai, ya girgiza kai yace Allah ya sauwake zata mike da izinin ubangiji karka damu ciwo jarabtace daga Allah Kuma jinya na kankare wa bawa zunuban shi don haka kataya ta da Addu’a, Ina ita Naziyar? Yace tana gida, ga shirme itada zata tsaya tayi jinyar mahaifiyar taku me ta tafi yi gida kuma?

“Ni nace taje ta huta zata dawo.  Yafada kawai. Sannan malam yayi shiru.

Zuciyar shi shima tana wurin ta dan ba halin yabar Asibitin ne, bayan tafiyar malam ya koma dakin tareda zama ya zuba mata ido, zuciyar shi ta Kara karye wa “Am sorry Mommy for leaving you behind, ban kula da Amanarki da yaya Ahmed yabarmin ba. Hawaye ne suka zubo mai har kan hannun ta, ta bude idanun da su kadai suke aiki tana juyawa Alamar yadaina kuka, da tanada bakin magana da ta fada mai duk Abinda yafaru zatayi Amma babu, haka yayita kula da ita sai magrib ya fito domin bin dokar Asibitin ya shiga motar shi da yasa manager ya kawo mai,

 

Gidan shi ya tafi kai tsaye batareda tunanin komai ba, lokacin su Salifa sun baje a falon Mommy har da kawayen ta y’an iska ga mommyn ta a gefe tana waya akan akawo Mata sabbin gold tunda duniya tasu ce, sai da ta gama ta juyo tana kallon kawar Salifa da hannun ta ke cikin rigar salifan tace ” kufa bakuda kunya Ko kadan ina wurin don iya shege bazaku bari intashi ba, ku yaran zamani bansan meke damunku bane ga maza agari ga Alhazai ga d’anyun jini kubi,  don iya shege junan ku kuke lalubewa,  kuma ku kashe min hayakin nan ya ishheni haka kuyita bankadar shisha kamar Abinci.

 

“Old lady bazaki gane dadin bin jinsi bane sai kin d’ana yaseen. “Aa barikin da nayi baikai can ba kudai kuje kuyita yi ni yanzu tunda dukiya tasamu banda matsala kuma kusa ido kwanan nan zata karasa domin boka yafadamin ya fara aiki ya sakar mata ciwo a hankali zata karas………… Kasa karasawa tayi ta maida kalmar ta ta hadiye mukuth kamar ta hada da makogoron ta, tayi saurin mikewa tana diri diri don ko motsin mutum basuji ba. Tun shigowar shi gidan yasan akwai matsala domin yayi horn har yagaji ba mai gadi yatafi yawon shi, don haka da kanshi ya bude ya shigo tareda rufewa da katon kwado,

Salifa tayi mugun nisa don ba karamin jin dadin tabawar takeyi ba har wani cije lips takeyi idanun ta sun sauya tuni,

Taji salatin mommy, cikin zin zafin yanda take kokarin hanasu jin dadi tace ” my God mommy please ki bar nan munaso mu huta if you can’t wat……. Ai tafi  mommy firgicewa ta tattaro rigarta ta na rufe kirjin ta da kyar ta zabura, mommyn ta na rawar  kafafu da murya tace “khaleel yaushe ka.. Ka.. Da… Wone?  Kagan mu nan muna d’an jajanta jinyar balkisu ne zanyi girki muje dubata banaso mubar part din ba kowa ayi sata. Tanayi tana kame kame.

 

Tunda ya shigo yake kame a jikin kofar falon ko motsi baiyi ba tunfara maganar mommy har zuwa yanzu, bazai iya misalta tafasar da zuciyar shi takeyi ba, nade hannun shi suke Saida ya gama kare musu Kallo tsaf idanun shi sunyi mugun kadawa, dukkan su bamai fuskar mutunci ko shigar Arziki, ya juya ya kulle kofar da key tareda cirewa ya jefa pocket ya nufo tsakiyar falon yana karewa ko ina Kallo.

“Hmmm I gave you ten minutes kafin inyi fresh up I want you to clean all this mess. Ya fada yana nuna musu falon da yayi kaca kaca domin sun maida shi dandalin iskancin su.

Shigewa yayi domin akwai tsananin gajiya a jikin shi, sai da ya  tube ya shiga bathroom  ya hada hot water ya shiga, zama yayi ya runtse idanun shi, ” mommy kinga me kika janyo mana ko? kinga irin zabin naki. Yafada yana mai zubo da hawaye, yanzu yaji zuciyar shi ta samu sukunin da zaiyi Abinda yake ganin ya dace don dazu inya biye zuciyar shi kisan kai zaiyi, ya tuna da maganar Hajiya sharefa. Zabura yayi ya dauraye jikinshi ya fito daure da towel.

Waldrp dinshi da yasan akwai kaya ya bude ya ciro kananan kaya guntun wando da Riga T-shirt bakake an rubuta handsome and Arrogant, da farin Zane,

Shigowa tayi cikin karairaya wai ita mai miji, domin sun zugota taje ta yi mai kissa tunda baice komai ba, baiga komai ba, don haka Jakar ta biyoshi dai dai yana daukar wayar shi yaji maganar ta.

“Darling welcome”… wani irin juyowa yayi a hargitse tareda sa kafa ya bata wani irin shoot da bata san yana zuwa ba, don haka wani irin tumbling tayi har jikin kofar ta buga kai Tim, ba shiri tasa Kara.

Wandon da ya cire ya dauka yasa cire belt din jikin shi. Ya rike wutsiyar Alamar da karfen yake son yin hukuncin, tuni har sun shigo a tsorace saboda ihun salifa.

Idanun shi a rufe yace ” kuma kunshigomin dakin ne da dattin ku”? toh duk sai kunci ubanku yau sai kungane kun shigo inda bai dace da iskancin kuba,.

Rufe ido yayi yana musu kan mai uwa da wabi har mommyn ma tana zuba salati, “d’an nan zaka iya dukan balkisu Ashe ? Indai zaka b…ai wani irin hambarin da yabata Saida tayi zaman y’an bori, kin saka mahaifiyata cikin ciwo bayan ita ba Abinda take nufinki dashi sai Alkhairi kinzo kin kawo min karuwai cikin gida har gefen uwata kuna iya shege, a kuma gabanki suke lalacewar su don kina tsinanniyar uwa, I think my mother is worst, Alhamdulillah nasan bazata taba aikata irin wannan halin nakiba, domin ta bamu tarbiya mai kyau but you, look at your daughter in front of your eyes……..

Wani irin bakin ciki ya kuma tokareshi ya Kara rufesu da duka sukayi falo suna zuba ihu, mommy da rarrafe da jan gindi ta Fita tana ” ni ka daka khaleel ina Suruka….. “Kina karasawa sai na sumar dake wallahi” surukin uban wa ni na  Auri Y’ar ki ko kitanbaye ta  ko yatsar ta na taba Kallo, ke har kinada Y’ar da Khaleel zai Aura? look nace ku gyara gidan nan kunki wallahi billahi idan Nafita nadawo bakuyi ba zakusha mamaki na…. “Ya isa don Allah malam kai din wa da zaka zo kana dukan uwata da kawayena? Toh bazamuyi ba ka kashe mu kuma kokaki ko kaso ni Matar kace igiyata na wuyanka kuma bazaka biyamin bukata ba dole in nemawa kaina mafit…… Wani irin kwashe ta yayi da kafafun shi ” tir Allah ya tsare ni in hada tsalkakakken jikina da najasa, wallahi da in zauna dake a matsayin mata gwara in mutu gauro, kuma inke kadaice mace khaleel bazai taba Aure ba, igiya ko na datseta duka ukun aje acigaba da karuwancin da license dama kin saba ko da mijin ki zai baki kulawa ba isarki zaiyi ba dabba Alade tunkiya kawai, and ke kuma, ya nuna mommy, “ba Wanda zai Fita wannan gidan sai mahaifiyata ta warke idan  bata warke ba ko naga wani Abu yasameta wallahi za ayi gudu, don duk sai na nakasa ku. Ya bankada ta ya wuce tareda bude kofar ya Fita ya kuma kulle su a ciki.

 

Gefen Naziya ya nufa yana nan a garkame a y’an da yabar shi, ya rike kai that means ba nan tazo ba. Wayar shi ya ciro ya Kira manager yace” ina ka kaimun madam?

“Tana janbulo can tace inkaita.

“Nan ne gidana why zaka kaita can kuma bazaka fadamin ba. “Sorry sir bansani ba ne. Ya datse kiran cikin haushi ya Kara gwada kiranta ko yanzu shiru, ya nemi number Aunty Raliya, lokacin suna hira abinsu sun gama cin Abinci,

Daurewa kawai takeyi Amma zuciyar ta na wurin shi tayi mugun sabo dashi zaman su a can tsawon satunkan nan baya Fita ko ina suna likeda juna yasaba mata yau daga dawowa nan ya shareta, zata rama ne itama.

Karar wayar Aunty ce tasa ta kalla taga number shice ta basar Aunty tace “bani wayar to ni in dauka in baza ki daga ba.

Picking tayi tareda sallama, ya gaida ta cikin girma ta tanbaya mai jiki yace Alhamdulillah jiki, kafin yayi shiru yakasa tanbaya ko tana nan. Aunty tace ” ga mutuniyar nan. Ta Ajiye mata wayar tareda Fita Abinta tana cewa nabarki lafiya nayi wurin neman lada tsaya yanga ke.

Tana kallon wayar taki dagawa ya katse ya kuma Kira taki dauka, yace ” tofa khaleel ka shiga uku yau. Ya Kira yafi sau goma taki dagawa haka ya hakura ya kyaleta dole yaje karbar hukunci in yana son yazauna lafiya da zuciyar shi,  a daren dukan su basu runtsa ba, khaleel Kwana yayi tsuki ga takaicin su Salifa ga kuma fushin Naziya, ga wani horo da jikin shi kemai wai bazai runtsa ba tunda bata kusa saboda sabo da yayi, zaune ya tashi yanajin kamar yayi tsuntsu yagan shi a gaban ta saboda kewar ta, “kin lalatani kinaso kuma ki gujeni baby no way wannan fushin is unacceptable, bazai yuwuba dole gobe kidawo nan I can’t take it.

 

Daren ya mugun yimai nisa, haka itama Amma saboda Yanayin kasalar da takeji daga baya tayi baccin ta, Assalatun farko yayi masallaci da badon kar ace lafiya ba zuwa zaiyi yayi gadin ta har gari ya waye ya ganta hankalin shi ya kwanta. Zama yayi yana gadin safiya, sai yanzu ya tuna da su Salifa ma, ya koma ciki tareda dakko key ya nufi kofar ya bude, suna shahsheme a kasa, Hajiya sharefa kugu yayi tsami ko motsi bata iyayi salifa kuwa hannun ta a kunbure Kwana tayi kuka saboda azaba daga gani ta targade ne. Suma sauran sai nishi sukeyi zasu iya rantsuwar ba mahalukin da ya taba musu irin wannan wulakancin na khaleel.

 

Taka hannun salifan da yayi ne yasa ta saka Kara mai karfin da ta tashe su har mommyn tana “wannan y’a akwai ki da shegen raki saikace nima ba ciwon nan ne dani ba wannan akwai  tambadadden…. Tayi tsit ganin shi duk suka mike tareda fara bashi hakuri ” khaleel kabarmu mutafi yanzu kaga mun gyara ko ina wallahi bazamu kuma shigowa gidanka…. “Kuma nafada muku bazaku bar gidan nan a banza ba bayan kunyi sanadin kwanciyar mahaifiyata Asibiti”,  Kujera ya samu ya zauna tareda dora kafa daya kan daya yace yanzu inaso inji duk Abinda yafaru bayan bana nan kafin inbarku kufita gidan nan oya I’m all ear’s. kayi hakuri bab…. “Kul kika kirani da wannan sunan ni ba sa’anki bane, call me sir khaleel ko sir Ibrahim. “Sir khaleel nidai naso in tafi mommy ce tasa ni zama wallahi ni na hakura da Auranka tunda naga baka damu dani ba, Amma mommy….. Ta bude mai bakin Jakar tsab momyn ta na mintsilin ta karta fada maganar takardaun Amma Kash tuni tayi b’ara, “takardun ka da managern ka yakawo suna nan ban tabasu ba wallahi. Dafe baki yayi yana mamakin greediness dinsu duk Abinda suke dashi wato bai ishesuba nashi suke hari da Dukiyar mommyn shi. “Wato 419 kuke yi kenan?  Shine kukazo har gidana zakiyi in the name of Auren hadin zumunci, you know what? mommyna harga Allah so take zumuncin ku ya kullu shiyasa ta matsa mana domin Y’ar ki dagani har Yaya na, Ashe ku zuciyar ku sharri kuke nufin ta da shi, alright zaku ga karshen cin Amana kuwa. “Wayar shi ya ciro ya Kira manager yace ya zomai da police yanzu yanada y’an 419 a gidan shi. Tuni suka fara kuka mommy na rokon shi kawayen nacewa ” mudai meye namu aciki kawai mu masoyane abarmu mutafi ba ruwan mu da rigimar gidanku, salifa kinga kunjefa mu a matsala daga Zuwa hutawa. Karku damu zaku huta a bayan kanta. Ya mike tareda Fita ya rufesu ganin suna kokarin biyoshi suna roko. “Mommy kinga masifar da kika jefamu ko nafada miki halin khaleel kingani bantaba zuwa prison ba yau zaki sa in shiga bayan inada Abinda zai isheni Rayuwa ta ko wacce kasa nakeso inada manyan babe da zasu kaini in more, now look what you have got us in to, wallahi bazan yafe miki ba mommy.

Ga Y’ar banza don wa nake duk wannan abun badon ke nake yi ba saboda banaso ki wahala…. “Oh really? All tanks to you now we are going to rot in jail”.

Ke kibarni inji da kwankwaso na dakeyi kamar ya fita da gangar jikina.

Kuka tasa tace ” ni hannu na bakya gani ya kunbura dakyar nake dagashi wallahi, nidai Allah ya isar min. “Gawa?  Inji mommyn. “Ga duk Wanda ya tsargu. Tafada tana murguda bakin ta saboda tsantsar rashin tarbiya.

“Toh mu muyiwa wa Allah ya isa ke Ko uwarki ?, saboda jarabar ki yau kinja mana masifa mu bamuci ko fucika ba. Amma kunci ni shegu matsiyata la’anannu kawai jarababbun ba.. ai tuni dambe ya kaure  suka fara jirgar ta mommy na ihu gashi bata Iya kwakkwaran motsi. Karku kashen ya’. Basu daina ba Saida khaleel ya bude kofar, sunyi mata lilis duk sun jijjimata da kunba, police yabawa izinin shigowa yace duk su kwashe su. Tana numfashin wuya dakyar haka aka jasu keeeee, aka watsa bayan mota, mommy sai rokon shi takeyi yayi biris, yanzu burin shi yaje yaga farin cikin zuciyar shi ko a wane halin take?

 

Wanda tunda ta tashi suka hada lafiyayya breakfast da Aunty suka shirya a basket, ta kintsa cikin wata tsaleliyar doguwar Riga Y’ar Oman ta nade kanta da mayafin, ba fushi yakeyi ba na ba dalili zai sha mamakin ta tayi kyau na fitar hankali dole duk Wanda ya ganta yasan Matar wanice,  mijin Aunty a lokacin da zai Fita ya saukesu a Asibitin, tundaga harabar take baza idanun ta ko zata hango shi, Saida suka tanbaya dakin aka nuna musu, bashi ba Alamar shi yana can yana dealing dasu mommy, takara cika, sai a lokacin taga mommy, tayi matukar tausaya mata har wasu hawaye taji sun zubo a kuncin ta, kai Rayuwa d’an Adam ba bakin komai yakeba yanzu mommy Y’ar gayuce haka kwance ko motsi bata iyawa, matsawa sukayi bakin gadon ta dafa hannun ta, tace “Sannu mommy Allah yabaki lafiya. Ta bude idanun ta ta zuba mata ido sai hawaye, so take ta bude baki tafara bata hakuri Amma ba hali, hannu Naziya tasa ta goge  mata hawaye, nurse ce ta shigo ta tanbaye ta za a iya bata Abinci?  Tace eh su bata mai ruwa saboda bakin daya d’an juya.

Dama sunyi kunun gyada, “Aunty Raliya ta zuba mata, da taimakon nurses Suka d’an dagata saboda nauyin jikin ta jingina mata  filulluka, cokali tasa tafara bata kunun Tanayi tana gogewa saboda dawowa yakeyi kamar jaririyar da ake koyawa cin Abinci, ido kawai take binta dashi da hawaye, sai sannu sukeyi mata, Aunty Raliya tace ” kinga shirmen ki Naziya ki tsaya tunjiya saboda kula da ita kin kama kin tafi. “Aunty laifin shine ko bari baiyi na gantaba Ashe jikin yayi tsanani har haka ne, yanzu bazan koma ba zan tsaya da ita anan inkinje ki sa akawomin ko Kala biyu ne masu saukin sawa.

 

Tunda yagama dasu cikin gaggawa yayi wanka ya shirya cikin d’an kareriyar shadda Arsh guntun Riga tasha dinkin gayu na maza, ya fito yafada mota, hankalin shi ya kasu kashi biyu, mommy da Naziya, don haka ya yanke hukuncin zaije Asibitin first ya dubata don yasan inyaje wurin Naziya zai iya mantawa da kanshi acan,  koda ya isa Asibitin yasha mamaki, Wanda tundaga kofar dakin kamshin ta yafara yimai welcome, wani irin Ajiyar zuciya yayi tareda murmushi kadan yace ” my happiness tunkafin ya ganta……. 🖊

 

 

 

*Matar Soja*

10/22/21, 12:00 PM – Buhainat: 5⃣9⃣&6⃣0⃣

 

 

 

 

 

 

……………. Ita kanta ta san ya isowa tunbai karaso ba, don haka tuni ta Kara hade fuskar ta tamau domin tayi mugun daukar fushi dashi, tuni ya ji wata natsuwa ta ziyarci zuciyar shi, cikin takun kasaita ya shigo, hade da sallama kasa kasa idanun shi a sama, domin ba Abinda yake buri sama da yayi ido biyu da ita, yayi matukar kewar ta, sai jera Ajiyar zuciya yakeyi tunda ya sauke idanun shi akanta, gangar jikin shi tuni ta amsa gayyatar ganin ta da tayi tank God ma manyan kayane a jikinshi, a bu biyu yanzu zai hanamai rungume ta ya rafe zafi, nafarko Aunty Raliya na biyu momy, don haka ya saita kanshi yayi gyaran murya, tareda gaida Aunty, tamai ya gajiyar hanya da mai jiki, ya Amsa cikeda jin kunyar ta.

Kafin ya matsa gab da gadon, taki ko dago kanta sai bawa momy kunun take tana gogewa, he wants to touch her amma no way, don haka ya waske yana fisgo maganar “momy sannu. Ido ta juyamai Alamar amsawa, fita Aunty Raliya tayi domin amsa waya, yayi Ajiyar zuciya yayi saurin riko hannun ta batareda damuwa da idanun momy ba saboda he can’t help it, tayi saurin dago kyawawan idanun ta masu rikita shi tace ” meye haka agaban momy please stop. Tafada tana karkata kanta, ” why kika ki tafiya gidanki kikatafi na Aunty Raliya?  Hannun ta take kokarin kwacewa amma takasa don rai ita tasan kunya, momy Naji Nagani wani irin dadi takeji y’an da yarinyar ta nuna mata kulawa ga kuma Alkunya da zata iya mikewa itama zata basu wuri su zanta da junan su, Amma ko yanzu abun mugun faranta mata rai yakeyi har ya nuna a fuskar ta, “let me go please. Tafada” I want sai kin fada min dalilin da kika tafi gidan Aunty kuma nakiraki kinki daukar wayata kuma kinki kunna taki why?

Dago kanta tayi ta kalle shi cikin fushi tace ka sakarmin hannu idan kai bakajin kunyar idanun momy ni inaji please let go. “Never ever, if I let you go in zauna da wa?  “Your second wife  da kakeson kasancewa da ita that’s why ka koreni batareda kama bari na duba lafiyar Momy ba jiya that’s why na koma inda dama ka dakko ni kafin mubar kasar nan, ni nasan matsayina banda wani value a wurinka, kuma am not here because of you, nazo saboda nadamu da lafiyar momy tana warkewa shikenan.

Wani irin kallon what is wrong yake mata,  momy feels bad saboda itane duk wannan mis understanding din ita tajawowa d’an ta, kallon Naziya tayi taga ita din dai data raina ita tafi dacewa da d’an nata ga hakuri da tarbiya, don haka taji duk duniya ba Abinda takeso yanzu kamar ta warke ta gyaro kuskuren ta,

Mikewa tayi da cup din ya Kara rikota, ” Naziya please stop it, ko so kike ki dagamin hankali  um?  Dagowa tayi taga momy ta rufe idanun ta, ta ce “I said let go of me. Shima kallon momy yayi kafin ya Kara matsota cikin rage murya sosai dake dauke da damuwa, “meye nayi kike kokarin horani haka please am sorry koda ni bansan laifina ba kiyafe min but I can’t handle your anger on me.

Fisgewa tayi ta yi bathroom domin dauraye cup din da spoon, ya runtse idanun shi tareda dafe kai ” oh my god khaleel ka boni. Yafada tareda binta cikin sauri, tana kokarin fitowa ya maida ita tareda datse kofar, “kallon shi tayi fuskar ta a tamke “meye haka Aunty Raliya zata iya shigowa kuma kasan momy dai Nagani ko? ” Hmm so what?  In zaki yi kokarin horani da irin wannan new attitude din ya kikeso ni inyi behaving, tell me? Look am not use to this, and I can’t take it any longer please forgive me if I wrong you.

Ji tayi yakara tunzura ta wato shi baisan laifin shiba, don haka cikin zafi ta dago tareda cewa ” ba Abinda kayimin kawai bana son damuwa leave me alone OK.

“Hhhhh story, rubbish, you are insane Naziya, leave you alone, ni khaleel?  You are dreaming wallahi, ban hakura dakeba tuntuni sai yanzu da kika gama shigewa cikin rayuwata kika yimin dalla dalla, hannun shi yasa cikin  sauri ya fisgo kugunta ya hade ta da Kirjin shi, Saida yaji kamar ya shekara bai kusance taba saboda shauki da kewar ta, “Ahhhhhh Hmmmm. Yafada tareda kankameta kamar zai mayarda ita cikin jikin shi, kokarin kwacewa takeyi ya hanata dole tayi lakwas tana sauraran bugawar zuciyar shi tareda rawar da jikin shi keyi kamar bai saba rungume taba” baby banyi bacci ba jiya kinsaba min da yin bacci kina saman kirjina bayan kin shayarda ni zumar ki tareda madarar ki mai rikita kwakwal war mutum, why kike fushi dani why kika barni nikadai jiya why kike son ki gujeni bayan kinsan zuciya da gangan jikina bazasu dauka ba?

Samu tayi ta fisge haka kawai taji yanaso ya tayar mata da feelings a Asibiti a banza yabarta da Abin kunya, tana juyawa ya kuma hade jikin shi da bayanta yasa hannu ya rungumo Dukiyar fulanin ta tareda matsawa kadan yana gwama  numfashi, “Am honey, kinji let go home yanzu zamu dawo please baby. Yafada yana goga mata jikinshi, she can feel how hard he is, tayi saurin bude kofar domin takai gab ta fisge ta gudu.

Matsawa yayi baya kadan ya dafe bango tareda runtse idanun shi ya dade a wurin kafin ya d’an dawo hayyacin shi,

Ta gyarawa momy kwanciya tareda komawa gefe taja kujera ta zauna, Aunty Raliya tashigo, Wanda har lokacin bai fitoba, tace “ni zantafi nabar yara Allah yakara lafiya Ina khaleel din?  ” gani Aunty yafada kanshi kasa domin yasan for sure yadago fuskar shi zata ga canjawar idanun shi, yace “bari muje in sauke ki tom, “Aa Wallahi ga mota nan megidana ya aiko yaron shi Allah ya bata lafiya.

Godiya yayi mata Naziya ta rakata ya zauna tareda bin bayanta da Kallo yana tausaya wa kanshi, Saida Auntyn ta tafi tadawo,

Still fuskar ba walwala, ya kalleta cikin da tausayin kanshi yace ” muje ne?  Banza tayi mai ta dauki Jakarta karama ta ciro wayar ta ta kunna.

Tafara game, karkace kai yayi yana kare mata Kallo tundaga fuskar ta har zuwa kirjinta har kafafunta data zame takalmin ta dora daya kan daya, jajur dasu mulmul, ya hadiyi miyau Kut a zuciyar shi yace ” kinada Abinda duk zakija min aji yarinya is your time.  Haka suke zaman kurame Wanda har doctor ya shigo tareda duba momy yafita, suka cigaba da zaman haka badon zuciyar shi nasoba sai dan baida yanda zaiyi, idanun ta akan su  momyn khaleel din ma kebata tausayi yanzu da tanada baki da ta lallashi Naziya domin ta rikemata yaro hankalin shi ya kwanta,

Sallamar su Shukrah da malam harma da Inna da sadiq ne yasa ta zabura cikin matukar murna ta nufesu, shima mikewa yayi cikin girma mawa ya gaida surukan nashi, malam yace yamai jikin?  Sukace Alhamdulillahi.

Matsawa tayi zata rungume Inna tace ” ke bani wuri ingaida mai jinya mara kunya. Shukrah tayi dariya tace Aunty nidai Rungume ni nayi kewar ki. Suka rungume juna yana kallon duk wani motsinta kamar ya sace ta ya gudu yakeji,  ganin ta yakeyi kamar ma bai taba Rayuwa da itaba,

 

Komawa sukayi gefe itada Shukrah su kuma suka matsa jikin gadon suka fara gaida ita, “Sannu Hajiya Allah yasa kaffara ne. Inji Inna da sai yau suka hadu da juna ido da ido, kallon iyayen Naziya takeyi tana hango tsantsar datti jantaka a fuskokin su, malam yace “kulu  ciromin Ruwan zam zam din nan da kunnen magaryar. Yafada yana  zama gaban gadon,  a wurin ya balle Y’ar Karamar robar Inna tabashi cup ya juye ya fara Addu’a  a ciki tareda mutsika ganyen magarya yace Naziya zo ki karba ki juye a gora kuna shafa mata a hannu da kafafun ta har fuska sau uku a yau.

Malam ya dade da sanin wasu mutane basuda yadda shiyasa bai hado komai ba yayi wannan agabanta idan taji sauki bakinta ya bude zai iya bata wani,  a take Naziya ta yi y’an da malam yace Wanda tunda ake shafa mata a kafafun takejin wani irin sanyi hade da jin jikinta na rage nauyi kamar tace kar Naziya tadaina, a ranta nadama takeyi mara Amfani wasu hawaye take fitarwa na rashin bakin da zatayi godiya,

Khaleel kamar ya goya su yakeji y’an suka nunamai karamci da kulawa, yana Kara godiya da Allah ya hadashi da surukai nagari, basu dade ba suka tafi, yarage daga shi sai ita, matsowa yayi yace “am hungry madam in baza abani Abincin cikin rigaba abani Abincin da zanci. Yafada yana rage murya tareda kashe mata ido, mikewa tayi ba musu ta zubamai Wanda su Inna suka kawo shinkafa da naman zabbi,

Ta hado mai da ruwa mai sanyi domin akwai dispenser a dakin ta Ajiye ta juya.

“Kinsan tun jiya banci komai ba kuma kinsan bana iya cin Abinci nikadai  yanzu kizo muci. “Ni ba wannan nakeso ba.  Tafada tana tura baki. “Oh lobster or crabs?  Yafada cikin mamakin y’an da ta juya cin wainnan Abubuwan. “Ni shrimps nakeso. Iyakar gaskiyar ta tafada, ya fara cin Abincin shi Saida yayi kat yasha ruwa, ya gyara zama, zuwa tayi tadaga plate din ta saka a, basket tadawo tareda tsayamai akai, “yunwa  nakeji nima. Tafada cikin fushi domin yasan sarai me takeso, ” bude idanun shi yayi yace ga Abinci nan kici in kuma nine muje sai kin koshi.

 

Komawa tayi  can kusa da momy ta zauna, Abinta ta share shi, tashi yayi ya fita, Wanda yana fita y’an uwan shi suka shigo daga gidan kawun shi.  Haka tayi ta karbar baki bayanan har zuwa magrib ta rage ita kadai, ta kuma shafewa momy jiki da ruwan Addu’ar, anan take shinfida dadduma tayi sallah domin kayanta a yalwace suke, bai shigo ba sai bayan isha’i.

Ya matsa tareda gaida momy kafin ya ce ta tashi lokacin tafiya yayi su tafi gida don ba akwana anan. “Ba inda zanje inbarta ita kadai intana bukatar wani Abu fa? ” nurse na nan. “Am not going nama fadawa  doctor zantsaya kuma ga ruwan maganin ta Anjima zankara shafa mata, kai katafi.

Kamar ya dora hannun shi a kai ya buga ihu yakeji, “look kinga banason musu kitashi mutafi. Momy naji kuma tana gani so takeyi tayi magana ba dama,

Tashi ma tayi ta haye gadon dake dakin extra ta kwanta tareda jan net bayan ta saukewa momy nata, tabashi  baya.

Abun ya matukar konamai rai don haka a zuciye yabar Asibitin, yayi gida.

Inba haka tayi ba bazai taba barinta ta Kwana da Momy ba ita kuma so take ta kula da ita saboda tasan a duniya batada ya’ya sama da Ahmed da shi gas hi ba Ahmed Khaleel kuma namiji ne, kuma bai kamata wata nurse na wani kula da itaba,

Don haka ta zamo mata ya’ koda bazata godeba zatayi domin Allah.

Wani irin farin ciki momy keji ganin y’an da Naziya ta jajurce wuni guda tana bata kulawa. Sai dai rashin jituwar su yasa abun ya taba mata zuciya, ba Abinda take buri yanzu sama da ganin farin cikin khaleel da Naziya.

 

Gida yatafi kai tsaye badon yasan zai iya bacci ba, ya  kwanta yanata fushi a kujera ga gidan bakowa cikin shi sai masu aikin shi tsoffi da yadawo dasu, harma da mai gadi bayan ya kora Wanda suka kawo.

Har karfe goma na dare yakasa natsuwa haka ya canja zuwa kanan kaya  ya dauki key din motar shi ya kuma barin  gidan.

Naziya Saida ta kuma shafe momy tsab da ruwan Addu’ar ta kunna musu waya tasa kira’ar sudais cikin suratul bakara tareda Ajiyewa kusa da gadon momy ta koma nata ta kwanta bayan taja mata bargo, murmushi kawai momy keyi najin dadi ya’ daga sama wadda tafi ma d’an ta damuwa da ita,  haka tayi baccin ta mai nauyi cikin salama tareda jin duk wasu igiyoyin da suka daure jikin ta suna kwancewa a hankali. Ita kanta Naziya tana bukatar hutawar domin d’an baccin ma da takeyi na rana yau bai samuba don haka tana kwanciya yayi awon gaba da ita,

Kamar a mafarki takejin hannun mutum a Kirjin ta tareda jin nishi kasa kasa, wai don ma yana controling kanshi karya samata ihu a Asibiti. Jin jikinta na canjawa yasa tayi saurin bude idanun ta, dayake akwai d’an duhu sai hasken dake shigowa kadan daga window domin tayi switching light din, mugun tsorata tayi jin mutum laulaye  da ita gaba daya hannayen shi damke da kirjinta gam, sanin zata iya samai ihu yayi saurin rife bakinta yana rage murya tareda cewa ” it’s me baby.

“Hmmmm tayi saurin dafe kirjin ta ta zabura tana sauke rigar ta daya kwashe mata.  Matsowa yayi ya janyota tareda zaunar da ita saman kafafun shi ” hey relaxed, kinga fushina ba inda zaije nadawo because I can’t sleep,  the house is too big for me, please baby I really needs you kinsan bazan iya hakurin da nayi a bayaba, karki yimin irin wannan horon.

Y’an da yake magana ya mugun bata tausayi  don haka ta d’an natsu a jikinshi,

“Kai wai bakajin kunyar idanun momy ne in taganka fa?  Ni dai kayi hakuri inna dawo gida kabari momy ta warke.

“I said I can’t why don’t you understand?

Yafada cikin tsawa da fada, “you are my wife ya zaki rika garani saikace ba halalina ba  how many times kikeso in lallaba ki?

Momy Saida ta farka saboda tsawar da ya bugawa Naziya, cikin ikon Allah ta bude bakinta tace “khaleel!  Kamar daga sama sukaji muryar ta duk da maganar bawai ta bude sosai bane, da gudunsu suka matsa kusa da ita,  Naziya tayi saurin gyara kanta ta kunna wutar dakin suka ganta tana kokarin mikewa, wani irin farin ciki ne yasa ya ji duk wani bacin ranshi ya kau ya rikota tareda   cewa “momy you talk, kuna kintashi zaune?  Cikin so much excitement, itama ta matso kusa da ita tace “sannu momy tana boye hawayen idanun ta domin tsoro biyu ne ya hadu mata, ga fushin khaleel ga tsoron Abinda Momy zata yimata tunda kuma daga  gani sauki yazo, kallon ta tayi kafin ta kalli khaleel dayayi kicin kicin tace “meya miki kike kuka?  Khaleel meyasa bakada hakuri da daren nan kana yiwa yarinya ihu duk da gajiyar da tayi..

Wani irin hawayen farin ciki ne ya Kara shatatowa daga idanun ta, batayi zaton haka daga momy ba, shikan shi yaji mugun dadi don haka yace ” tanbaye ta ni ba Abinda nayi mata impact in kukane ma nine yakamata inyi ba itaba, do you know momy tundazu nake lallabata muje gida ta nace ita nan zata Kwana tare dake saboda taurin kai.

Hannun ta datakeji ya saku sosai guda daya ta mika tareda riko hannun Naziya zuwa kusa da ita, ” Zo kinji daina kuka inbakya son zuwa ba mai matsa miki kinji, Amma in saboda nine kitafi gida ki huta kinga am OK zan iya gyara kwanciya ta zan iya tashi hannu na dayan nan ne da kafar hagun nan nakejin su a rike, Alhamdulillah nagode wa Allah nagode miki keda iyayen ki Naziya Allah yasa ki gama da duniya lafiya. “Amen Amen Sukace, farin cikin su baya misaltuwa a wannan lokacin, tace “in kina son binshi kije da safe kya dawo.

“Banason zuwa momy ni ina nan. Tafada  batareda ta kalli khaleel ba,

Fuskar shi ya tamke yayi banza da ita,

Tace “kije kiyi kwanciyarki kinji kibarni dashi nasan kin gaji.

Wannan canjin na momy yafi komai faranta mata zuciya don haka bataso tayi Abinda zata bata mata rai har su koma Y’ar gidan jiya don haka ba musu ta  wuce Abinta,  momy tace ya tashi ya kashe hasken ya kunna musu na wayar shi magana zata yi dashi kar hasken ya damu Naziya zatayi bacci. “Ya tashi cikin murnar ganin momy taji sauki ga kuma canjin hali da ya lura tayi  tuni ya goge mai duk wani fushi da yakeyi ya hakura da Abin da ya kawoshi ya zauna tareda gyara mata zama don tace ta gaji da kwanciyar jikinta na ciwo,

“Khaleel bansan ta ina zanfara magana ba. Tafada tana dukar da kanta tareda share hawayen ta da hannun ta mai lafiya, yayi saurin rikewa tareda girgiza kai ya share mata hawaye tareda cewa “don’t say anything momy kinga jikin ki bai gama dawo wa dai dai ba, banaso kiyi tunanin kinyi mana ba sai dai ba, ke mahaifiyar muce dole mubi Abinda kikeso, am sorry for everything momy. Shafa fuskar shi tayi tareda murmushi “nice zan baku hakuri banzamo muku uwa tagari b…. Rufe mata baki yayi ” enough for all this talk momy ki huta, komai ya wuce kawai lafiyar ki itace damuwa ta. “Khaleel Salifa….. “Leave everything to me momy am here don’t worry yourself. “Akwai Abinda nakeso infada maka akan Salifa. “Nasan komai momy ki kyalesu I will handle everything. “Hmmm tom  don Allah karka kai Naziya cikin gidan nan su cutar da ita……. 🖊

 

 

 

 

 

*Jumu’at kareem to All my fans Allah ya sadamu da Alkharin dake cikin wnn ranar Amen *

 

 

 

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/25/21, 11:14 AM – Buhainat: 6⃣1⃣&6⃣2⃣

 

 

 

 

 

 

…………….Bai fada mata komai ba akansu kawai gyada mata kai yayi, sukaci gaba da magana kasa kasa, tana tanbayar shi me yasa yake son takurawa Naziya, “khaleel kabi yarinyar nan a hankali karka kure mata hakuri fa. “Momy so kike ki shagwaba ta inkina fadar irin haka please karki fada Agabanta taji, nifa ba Abinda nayi mata impact ita yakamata kiyiwa fada tana juyani y’an da takeso. Yafada yana d’an daure fuskar shi, murmushi MOMY tayi na farin ciki da kwanciyar hankali ta dafashi da hannu mai lafiya. ” kasan bazan bari kasa min ita kukaba, wannan yarinyar farin ciki yakamata tayi ba kuka ba, khaleel kataba ganin ta daga kai tamun koda kallon banza, duk da Abubuwan da na rika yimata?  Ka duba yarinyar nan iya zuciyar ta ta tsaya jinyata batareda ta duba duk cin mutuncin da nayi mata ba a rayuwa. Takarasa wasu hawaye na nadama na biyo kuncin ta, “duba kagani mahaifin ta batareda ya duba duk halin da na jefa Y’ar suba ya kuma daukar ta yabaka, saboda karfin Alkwari da soyayyar da sukeyi wa d’an uwan ka, yau maganar da nakeyi Albarkin Naziya nakeyin ta, da bata cikin rayuwata nasan wulakanta zanyi khaleel Hajiya sharefa tayi mun Abinda bantaba zaton kawa zata iya yiwa kawarta ba,All I want zumunci tsakanin mu ya Kara karfi Ashe…. Hmmm Salifa kuma..

Takarasa kalmar kuka na kufce mata. Tashi yayi ya rungume ta ” is OK Momy please komai ya wuce ki manta dasu, kuma nima ki yafemin da na bijire miki kuma natafi na barki.

“Aa bakayi laifi ba khaleel hakan shine ya kubutar min da Rayuwar ka da lafiyar ka nagode da baka Yar da ka hada Rayuwar ka data Salifa ba, danayi danasani na har abada da hakan ya faru domin sam batada tarbiya. “Please Momy ki kwanta ki huta ya isa haka. Yafada yana gyara mata kwanciya ya rufeta tareda komawa kan kujera ya zauna, dafa fuskar shi yayi yana shafawa tareda kallon gefen Naziya dake juyi duk tanajin hirar su takasa bacci saboda farin cikin canji da saukin momy.

Ya dauki lokaci kafin ya ja numfashi ya mike ya koma inda take kwance, gefenta ya rab’a tayi dif kamar tana bacci ya kwanta yana kallon saman dakin na tsawon lokaci kafin ya juya ya rungume ta tsam yana Ajiyar zuciya.

Kai khaleel maye ne wallahi tafada a zuciyar ta, wato koda da idon momy dai sai yayi y’an da yakeso, bakin shi ya Dora dai dai kunnen ta cikin rage murya sosai yace “I no you are not sleeping Hajiya, are you happy momy na takamin birki akanki, Hmm duk wayan Amarya dai sai ansha manta don haka ki gama gudun ki zamu hadu. d’an motsawa tayi domin gadon karami ne Wanda ta zungureshi badon taso ba ya Kara manneta yana runtse idanun shi, “kinsan dai baki kyauta min ba ko?  This is the worst punishment for me, gaskiya ina kwaruwa Umm.

Shiru tayi mai Saida taji hannun shi ta saman rigar ta yana kokarin zurawa tayi saurin juyowa domin bashi gargadi da ido, yayi saurin cafke lips dinta, yana kallon kwayar idanun ta, tareda juya mata ido Alamar tayi mai shiru.  Ya dade yana shan bakinta kamar mayun wacin Zaki tana kallon tsantsar jaraba kafin ya cire ya dora bakinshi saman wuyan ta yana lasa tareda mayarda numfashi nadan  lokaci. Tashi yayi ganin hakan bazai taba yimai ba ya dagata tareda cewa ” let go. batason hayaniyar su dashi a gaban momy don haka tabishi tana mai gyara mayafin rigarta, ta dauki wayarta tana dubawa kusan karfe daya na dare.

Cikin Asibitin shiru sai hasken wuta ta ko ina ya bude motar shi ya zaunar da ita kafin ya shiga ya rufe ruf, fuskantar ta yayi tareda janyota zuwa kafar shi ya dora kanshi saman kirjin ta yana Ajiyar zuciya.

 

Ganin bazai ce komai ba tace” please  meye haka wai?  Idanun shi da sukayi ja ya dago tareda kallon ta na d’an lokaci kafin ya sanya hannu ya kwantar da kujerar motar yace ” keep quit my friend, tunda bakisan damuwa ta ba Allow me to sleep OK. Kwanto da ita yayi kan kirjin shi ya rufe idanun shi Alamar baccin zaiyi da gaske. Kafin kace me yayi bacci ta tsaya tareda sauraran Ajiyar zuciyar shi a natse,. Mamaki ya bata batareda ya tabata ba yasha baccin shi har Asuba,  Wanda momy ma batasan fitarsu ba tasamu bacci mai cikeda kwanciyar hankali da kuma saukin da taji a jikin ta,

Ganin Ana kiran salla ga jikinta yayi ciwo domin ya kanan nad’eta ya hanata motsi sam, ta d’an bubbuga shi, ya bude idanun shi, baccin bai ishe shiba tace “Ana kiran salla fa. Mika yayi tareda ita a jikinshi yayi salati tareda karanto Addu’ar tashi daga bacci. “You see is All your foult jiya bansamu bacci ba yau ma bai isheni ba saboda rashin jinki da munje gida nasan zanyi bacci mai dadi.

Batace mai komai ba tafara kokarin sauka a jikin shi, riketa yayi ” wai ke meke faruwa ne?  Kin zama kurma ne da kike bina da idanu ba magana, ko fushin ne da bansan laifina ba haryanzu? “Muje muyi sallah mutane sunfara fitowa. Sakinta yayi saboda lokacin sallah suka koma dakin, har lokacin momy bata tashi ba sabon brush ta bude tayi kafin tayi alwala ta fito. Tasamu baya ciki, domin dole sai yaje gida he can’t pray batareda yayi wanka ba domin yasan ya fitarda Abubuwa duk da bai samu Abinda yake soba.

Sallah tayi ta zauna akan dadduma tayi ta Azkar dinta  har gari yayi haske.

Likita yayi matukar mamakin saukin jikin momy lokacin da ya shigo, yace is a miracle a dare daya ansamu improvement sosai domin duk nauyin jikinta ya sauka saura gefe dayan kawai Wanda yace a hankali shima zai warke idan taci gaba da shan magani. Tayi godiya da kanta.

Karfe takwas Aunty Raliya ta kuma zuwa da basket din Abinci ta ga Naziya da momy suna hira sama sama ta rashin sabo domin Naziya kunyar momy takeji ita kuma so take tajata a jiki sosai.

 

Abun ya matukar farantawa Aunty Raliya rai, ta ko saki jiki da momy sukasha hirar su tanata godiya da sa Albarka, ta sake ta d’an ci Abincin da Raliya ta kawo,zuwa karfe goma Tace zata tafi sai ta kuma dawowa, Naziya ta mike tace zataje tayi wanka ta canja tadawo ta Kira nurse tareda bata umarnin ta kula da momyn kafin tadawo, suka fita tare, momy taso tace ta Kira khaleel mana ya kaita Amma batason ta kuma yi musu katsalandan a rayuwar Auren su tasan komai zai tafi dai dai, Allah dai yabata lafiya.

 

Saida suka fita aunty Raliya tafara yimata fada, meyasa zata ce zata bita? “Aunty ai yasan zan bukaci wankan yatafi batareda niba don haka bazanje gidan ba nidai muje gidanki, ai kayana da na dawo suna can. Shiru tayi kawai kanin mijinta da yakawota ya mayarda su, koda ta tafi tayi wanka ta shirya ta natsu ta karya. bata samu bacci mai dadi ba jiya  saboda nacin khaleel don haka Saida ta kwanta na kusan hour biyu.

 

Khaleel kuwa bayan ya shirya Saida yaje office dinshi yaga meke tafiya domin baisamu sukunin lekawa ba ya d’an dauki lokaci kafin ya dawo Asibitin, Samun momy yayi da Aunty Zarah da tadawo jiya ta samu labari a wurin Aunty Raliya domin duk ta damu bata samun wayar momyn Kwana biyu, fuskar shi ya tamke ya shigo kamar yaga kashi don Allah yagani ya tsani Matar nan shiyasa ya mugun raina ta, hawaye takeyi tana Sannu aunty Allah ya wulakanta sharefa da zuri’ar ta matsiyata. Sallama yayi ciki ciki ya samu gefe daya ya zauna ta juyo cikin fada ” khaleel Amma wallahi kai bakada kishin mahaifiyar ka, yaza ayi ace Suyi ma Aunty irin wannan Abun Amma ka zuba ido ka kyale su?

 

“Zarah kije ke kidauki mataki da kanki dama kece mai babban kaso a duk Abinda yake faruwa a rayuwar gidan mu, don haka karki manta inkin tashi yimusu hukunci ki hada da kanki kema kina bukatar hukuncin.

 

“Kingani ko Aunty wallahi Ibrahim ya mugun raina ni sai kace ba kanwar uwar ka nake ba kayita zuba min magan ganu son ranka,  wallahi zandauki mataki akanka mtsww. “Hope dai badani kike wannan zancen ba da kuma tsakin, domin Zaki iya fuskantar bacin raina fiyeda tunanin ki, girma na kikayi ko kece kika haifeni da zanbaki girma?  Look we don’t need you here just leave, go and fix your life first, don munafunci ina kike lokacin da ita yayar taki ke bukatar taimako?  Were are you? Sai bayan ta samu sauki ki debo dogayen kafafunki kizo kina kawo mana sanabe were are all your relatives, sai lokacin da munafunci ya tashi ku cikawa mutane gida, look am not like Ahmed duk wadda tasan ba zumunci zai kawota gidan muba she is not welcome, kowace ta tsaya gidan tsohon mijinta, especially you Amara.

 

Tuni Aunty Zarah ta hadiye bala’in ta ganin ya hau yana faman surfa mata that means ajiraye yake da ita, momy ce tace ” khaleel that enough OK. Yace “Sorry Momy were is that girl?  “Taje ta yi wanka ta canja tadawo. Dama yasan zatayi hakan wato bazata iya fada mai Abinda take bukata ba sai kawai Tayi Abunda taga dama don taga yana sonta yana lallaba ta, OK zai nuna mata koda yana son mace kuma baya daukar wulakancin ta why take  mai yawo da igiyar Aure any how?  Haushin ta ne ya saukewa Zarah tass tun ma baiji meya faru ba.

Komawa yayi kan kujera yana Danna wayar shi fuskar shi kamar hadari, momy ta kalle shi tace ” khaleel bansan me ke ranka ba, Amma na rokeka haukar da kamun yanzu ta iso kar yarinyar nan tadawo ka rufemin ita dafada.

Shiru kawai yayi domin yakai wuya, zarah kuwa mamaki take ciwon ne ya janyo momy har take damuwa da Naziya haka?

Kallon ta Tayi tareda yin murmushi kawai. Domin ta Riga tadawo hanya sambal bata fatan ta kuma karkacewa,

 

Aunty Raliya  tasa aka dawo da ita bayan ta tashi ta shirya cikin kana nan kayanta ta zura katon hijab saboda shigar domin duk native wears dinta na gidan khaleel, harda socks ta sa baki,

Bayan ta zura after dress a sama saboda koda zata bukaci cire hijabin a Asibiti,

Wata irin uwar kasala takeji da tashin zuciya, da batasan dalilin shiba don haka duk sai jikinta ya mugun mutuwa, koda ta shigo cikin Asibitin zuciyar ta tashi takeyi sosai musamman kamshin pharmacy  dake tashi a Asibitin,

A cikin natsuwa ta shiga dakin bakinta daukeda sallama yana nan zaune a wuri daya, muryar ta da yaji tuni zuciyar shi ta sauka yaja numfashi tareda zuba mata ido, ta matsa tareda gaida momy da Aunty Zarah da ta zuba mata ido itama tana ganin mugun canji da murjewar da Naziyar Tayi,

Ta koma kusa dashi ta gaidashi tana yamutsa fuskar ta domin jitake kamar ta koma saboda tashin zuciya,shikuwa kallon al amarin ta yakeyi yana noticing komai duk Tayi sanyi lakwas, tana zama cikin ta ya mugun murdawa Amai ya taso mata, da gudu Tayi bathroom suka bita da Kallo dukan su kafin ya mike yana mamakin ta ko lafiya?

K’ak’arin  Aman da takeyi yasa momy ta daka mai tsawa ” kabi yarinyar nan  kataimaka mata ka tsaya k’ik’am kamar sabon soja. Jefa wayar shi Aljihu yayi tana rikeda washing hand basin sai kwara Amai takeyi ya karaso tareda dafata yana mata sannu, yitakeyi kamar zata Amaye y’an hanjinta dama tea kawai ta karasha bayan ta tashi baccin,  Saida ya bata ruwa ta wanke bakinta ya fito da ita, momy jitake kamar ta mike ta taimaka mata da kanta, kwantar da ita yayi akan extra bed din tana maida numfashi, ya zare mata hijabin, “ka Kira likita ya dubata ka tsaya nan kana kallon ta banson shirme. Momy ta fada, duk da zuciyar ta tagama fada mata damuwar bataso Tayi farin ciki saita tabbatar, inko cikine da tafi kowa farin ciki. Yana fita Zarah tace “Aunty ai wanna dagani ba tanbaya ciki ne da ita, don ni tun shigowar ta naga yellow din da Tayi nasan juna biyu ne. “Allah ya Y’ar da da zancen nan Zarah. Momy tafada tana shafa hannun ta mai lafiya,

Likita ya biyoshi ya shigo tareda nurse, yafara tsokanar ta ” mai jinya ta koma patient. Jinin ta ya deba yabawa nurse yace taje takai lab ayi  P T test.

Bayan minti talatin ta dawo da result,

Khaleel na zaune ya na mamakin what is wrong with her, ta rufe jikinta da hijabinta ta juya mai baya domin kamshin jikinshi ma is killing her, likitan ne ya shigo fuskar shi a sake, ya mikawa khaleel hannu “congratulations sir, a zuciye ya mike kamar mai jiran a taboshi “my wife is sick and you are congratulating me?  “Relax  Sir Ibrahim,  your wife is pregnant.

Yafada yana Kara Washe baki, saurin juyowa Tayi idanun ta a waje “pregnant?  Ciki kenan fa?  Ita keda ciki?  Ciki fa??.

Momy dake jingine ta gyara zama kamar ta sakko takeji ta daga Naziya ta goya sai kabbara takeyi, zata samu Karin zuri’a, zataga jikan ta Wayyo dad’i.

Khaleel kuwa d’askarewa yayi kamar Wanda ya suma, bai taba imagining ciki ba a Auren su yanzu bawai don baiso ba no sai don Abubuwan daketa faruwa da shi na farko rashin Ahmed nabiyu rigin gimun momy,

Yakasa koda motsi yanzu shine keda cikin jikin Naziya?  That means he is going to be a Dad?  Allahu Akbar. Yayi sujud shukhur, batareda ya duba inda yake ba. Kafin ya tashi ya rungume likita “likita da gaske am going to be a dad?  Ya juya wurin momy da gudu ya rungume ta “momy  Zaki zama granny. Wasu irin hawayen farin ciki ne suka zubo musu su duka itada khaleel  din,  Aunty Zarah Tayi dariya tace ” congrats Son Allah ya inganta. Sakin momy yayi ya dawo tareda rike hannun Aunty Zarah “Sorry Aunty for all the trouble tank you for your prayers Amen Allah ya inganta min.

“Oh mun shiga uku khaleel bako kunya cikin farko? Koda yake kalli Aunty ma jikan Fari harda hawayen murna lallai zamusha Kallo. Tafada cikeda tsokana, ” eh bakomai kifada duk Abinda zakice.

Naziya kuwa reaction din su ya taba mata zuciya sosai har batasan lokacin da itama hawaye ya zubo mata ba,  ita bata tabaji ko ganin dokin ciki irin nata ba ace har momy na kukan murna wannan ciki ai Alkhairi ne a gareta, Allah sarki Ahmed Ashe bashi bane uban ya’yan ta Allah mai yadda yaso.

Matsowa yayi cikeda farin ciki yaganta tana hawaye. Da mugun sauri jikin shi na rawa ya karaso “Innalillahi baby ya Zaki fara kuka bayan kinada ciki please don’t hurt my baby stop it. Hannun shi akan marar ta yasha yanajin wani irin farin ciki,  ya dago kanshi “baby cikina na nan please ki kulamin dashi kidaina yawo ki natsu basai kinyi komai ba ko wanka zanrika yimiki kinji no need ki wahalar min da yarinya.

Gaba daya ya manta da duk mutanen dake dakin likita kuwa Abun ya matukar burgeshi, don haka bai tafi ba, Saida momy tace “doctor ka sallame ni zanje gida inkarasa warkewa idan akwai Abinda za arika yimin zan rika zuwa checkup.

“Tab bansan Wanda yafi wani doki ba keda khaleel Aunty. “Zarah gwara inkoma gidan tunda kinsan halin d’an naki kar yaje ya hana min ita sakewa yajamun Asara.  “Tofa kaji likita. “Eh ba wani damuwa sai medication dinta kawai dama ba Abinda muke yimata shi irin wannan ciwon warkewar shi gaba daya dama sai a hankali. Amma Hajiya kiyi hakuri har zuwa karshen satin nan. “No likita discharge me. Juyowa khaleel yayi “no momy please kibari ki Kara samun sauki zan kula da ita karki damu.

Shiru Tayi na d’an lokaci Saida likita ya fita tace “khaleel kana ganin zan kuma shiga Rayuwar ku ne domin inkara hanaku zaman lafiya?  So nakeyi inkasance tareda Naziya nasan wahalar laulayi tunda tafara da Amai ga gida bakowa at least ina kusa hankalina zai kwanta.

Gwanin tausayi Naziya ta sakko duk da batajin karfin jikin ta ta matso kusa da MOMY, ” momy ina nan tareda ke Sai kinji sauki ba inda zanje. “Aa Naziya gida Zaki koma ki kula da kanki kinji” nidai  tare zamu tafi. Tafada tana marai raice wa kamar zatayi kuka. Fita kawai yayi yabi likitan yace ” doctor you have to discharge my momy kafin matata ta jamun Asara please, zaku iya hadamu da nurse da zata kulamin da ita kafin ta karasa warwarewa,and inaso ayi mana Ultrasound insan watan cikina da kwanakin shi da kuma lafiyar shi.  ” that’s not a problem dama yakamata hakan, maganar nurse munada kwararru,madam ko yanzu zaka iya kawota muyi ultrasound din.

Godiya yayi ya koma tareda cewa ” get ready Aunty Zarah zamu tafi gida baki daya bari muga doctor da Naziya, let go. Yafada tareda dagata suka fito yana makale da ita kamar gold takun ma ji yake kamar yayi mata shi, nan take akayi mata, cikinta kimanin sati bakwai zuwa takwas.

Abu daya ke takura ta shine kamshin perfumes dinshi, is killing her dauriya kawai takeyi, koda suka shiga mota juyawa tayi gefen window ta danna domin iska ya rika shigowa, kokafin su isa gida duk ta bata jikinta da Amai, da kuma motar shi, sai sannu suke yimata duk ta galabaita, don haka suna isa daukar ta yayi MOMY kuwa wheel chair sabuwa Aunty Zarah ta taimaka mata ta turata zuwa gefen ta, da mai aikinta ta gyare fess, taji dadin ganin masu aikin su duk sundawo, gidanta yadawo dai dai, mai aikin tafara tanbaya ko Salifa na gidan?  Tace koda tadawo basa nan batasan me yafaru ba. “Ai Aunty kinsan halin khaleel kila yayi musu Abinda ya dace, what ever dai tunda basa gidan Alhamdulillahi.

 

Gefen Naziya kuwa daukar ta yayi ya kaita bathroom ya mata wanka tsab yana hadiyar yawu domin Allah yagani ya mugun yin kewar ta, dan komai yakara Masha Allah…. Yana mata wanka yana murzar ta duk ya rikice yana mata sannu, “please ka kaini dakin momy banason wannan pefurmse din naka, gaba daya gidan nan kamshin ka yakeyi zuciya ta na tashi I can’t stay here please kafitar dani kafin in Amayar da y’an hanji na….. 🖊

 

 

 

“Wnn Abu dai bamai sauki bane wurin khaleel akwai rigima kuwa, baruwana, but I understand ur situation Naziya 😞

 

 

 

 

*Matar Soja*

10/26/21, 5:26 PM – Buhainat: 6⃣3⃣&6⃣4⃣

 

 

 

 

……………. Tagumi yayi yana kallon y’an da take saurin zura kayan ta, kafin ma yayi wani Abu ta dauki hijabin ta da wayar ta tayi waje, “what is that?  Yafada yana mikewa, ko kafin ya zura jallabiya ya bita harta kai sashin momy so take tayi nisa da kamshin jikin shi inba haka ba ta fara Amai kenan. Suna zaune a falon Aunty Zarah ta kawo matsa tea a cup tana bata Naziya ta shigo, kanta akasa ta koma gefen su akan doguwar kujera ta kwanta batareda tace komai ba, tsayawa sukayi suna kallon ta kafin zarah tace ” lafiya dai ko akwai matsala ne Naziya? ” Bakomai aunty kawai zan kwanta ne anan. “Keda nakeso ki huta shine kika fara yawo bazamu shirya ba inba zaki natsu wuri daya ba. Juyowa tayi kamar tayi kuka idanun ta rau rau tace ” momy bana son can ne wani irin kamshi yakeyi dake tadamun zuciya. “Ki fada musu kawai bakyason kamshin perfumes dina ne shiyasa kika gudo nan, ko kuma kinayi ne kawai saboda ki wahalar dani?

Dariya Aunty Zarah tasa tareda cewa “eh akwai Kallo da bana komai da nan zan tare ba ruwana da tv, kai baby bakason kamshin dady tab.

Dukar da kai momy tayi tana murmushi cikin wani irin farin ciki, kafin tace toh ka canja ka kumayi kokarin korar na cikin gidan da wani kamshin tunda bataso karta cutu. Kallon y’an da ta juya musu baya yayi ya kama baki yarasa me zaiyi, kafin ya mike ya fita gidan.

Momy tace “Zarah Kira mai aiki ta bata Abinci, me zakici Naziya?  Tace shrimps takeso soyayye da miyar source.

Aunty Zarah ta kyalkyale da dariya ” barewa tayi gudu d’an ta yayi rarrafe?  Lallai wannan d’an tun baizo duniya ba ya gado tsoho. ” inkin gama yiwa surukar taki iya shege ki wuce ki hada mata kinsan mai aiki bazata iya yin yanda zaiyi mata dadi ba, da kafafun na motsi da da kaina zanyi mata. “Bari inje tom. Tafada tana dariya, abun ita kanta ya mugun burgeta y’an da Y’ar uwarta ta dawo kan hanya, dama ita tuni ta tuba bata taba Y’ar da taje wurin wani malami kota aiketa dafe kudin takeyi don tasan intace bazata jeba zasu samu matsala kamar sauran y’an uwan dake fada mata gaskiya.

Don haka ta natsu ta hado mata Abinda takeso, lokacin bacci yafara daukar ta. Momy tace “tashi kici Abinci ina kula dake ba wani Abinci kikeci ba ko a Asibiti. Tashi tayi ta zauna akasa, har wani irin tsinkewa miyanta yakeyi saboda ganin abun da take marmarin ci.

Tafara ci kenan ya shigo da kwali kato, suka zuba mai ido har ya Ajiye tareda kallon y’an da take cin Abincin ta ko dago kai batayi tana wani irin lumshe idanun ta, ya jingina jikin kujera, Abun na matukar burgeshi, Saida ta cinye tas tasha ruwa kafin ta mike ta kai plate din kitchen. Dawowa tayi tana Ajiyar zuciya domin taji ta dam yanzu. “Momy ga shi na sayo Kala Kala ta zaba Wanda takeso inrika Amfani dashi. Yafada yana baje tirarukan masu shegen kamshi da tsada Sunkai kwalba Ashirin,

Ai kuwa da gudu ta tashi tunbai bude ba tayi dakin Ahmed dake part din tana fitar da numfashi dakyar ta samu zuciyar ta ta kwanta.

Binta sukayi da Kallo shima ya ce ” what again momy?  Aunty Zarah ta ce “kagane kamshin ne kawai bataso saika daga mata kafa har zuwa lokacin da komai zai dawo dai dai. “Till when please, nidai gaskiya da sake haba. Ya mike zai bita momy tace “dawo nan karka sata Asarar Abincin da taci yanzu yarinyar nan Ina lura da ita ba wani Abun kirki takeci ba, Amma baka damu ba, duk damuwar ka kawai ka takurata ka hanata sakat, idan ka shiga wurinta ranka zai baci.

Fita gidan yayi cikin fushi, ita kuwa samun gado tayi taci baccin ta hankali kwance.

 

haka y’an dubiya keta zuwa gidan suna duba momy y’an uwan ta kusan kullum suna gidan, yanzu ba wani hayaniya ko fada tsakanin ta dasu sai zumunci, haka kawu modu yanzu shima da iyalin shi suna yawan zuwa gidan  domin kowa yasan Hajiya balkisu ta canja sosai, zumunci takeyi da gidan malam da Inna, sometimes in suna zaune da Naziya zatace “idan naji sauki kafafuna suka samu zan je har gidan inyi godiya inajin dadin Addu’oin da yake aiko min a jikina, Allah dai yasa agama lafiya.

Khaleel kuwa dole badon yaso ba ya hakura da Naziya, don tun yana satar dare ya shiga tana bacci, zata zabura tafara kelaya Amai kamar zata suma ya hakura da zuwa cikin gidan sai dai ya kirata a waya inkuma ya shigo yaganta yana daga nesa zaiyi magana ya juya, duk ya dawo gwanin tausayi, ankwashe kusan sati biyu a haka ita kuwa ta murtuke takara murjewa da cikar d’an yen ciki. Shiyasa bayako son kallon ta.

 

Zaune yake a office ya kasa yin komai, Allah yagani shifa ba karfe bane da zai zauna kusan sati uku ba mace bayan yasaba da ita, rabonsu da kebewa tun a bangkok, marar shi har wani nauyi take yimai, ranar bai tsinana komai ba har lokacin tashin shi yayi ya buga mota yayi gida, wani irin zazzabi zazzabi yakeji ma,

Duk ya sukurkuce,

Ita kuwa ranar taci adon ta domin Shukrah tazo ta zana mata lalle ta Y’ar fa mata kana nan kitso mai kyau, ta cancara ado cikin super wax dinta mai kyau taji dinkin yayi Riga da sket ta murza d’auri,  tayi kyau fiyeda tunani kamar wata sabuwar Amarya, kana ganin ta kaga mace mai d’an yen ciki,

Dawowa tayi falon dauke da kwanon  awarar da tasa Shukrah tayi mata kafin ta tafi, momy dake zaune kan kujera tana duba jarida domin hannun ta daya ya saku saura kafar kawai itama tana janta a hankali yanzu, tace “kici yaji a hankali Naziya karki haifo yaro ya cikamun gida da kuka. Murmushi tayi tana cewa “momy inban sa yaji ba baya mun dadi…..

Shigowa yayi da Sallama kasa kasa, tun shigowar shi ya zuba mata ido yana kallon y’an da tayi kyau sosai, Kirjin ta ya kalla da suka Kara kunbura kamar zasu faso,

Samun kusa da Momy yayi ya zauna tareda yin Ajiyar zuciya idanun shi akanta  ya koma kamar wani maraya ya dora kanshi saman kafadar Momy, yana gai sheta, cikin tausaya wa tace “yadai Ibrahim?  “Momy am sick. “Subuhanallahi. Tafada, itama Naziya da duk ta kasa natsuwa ta yi saurin dago kanta ta kalle shi domin Allah yagani kwanan nan tana mugun kewar shi so take taje gareshi tanajin nauyin momy gashi ya janye gaba daya, ganin y’an da take kallon shi yasa yace ” Momy yaushe zaki Kara yimin wani Aure? Yafada cikeda tsokana. Ture shi tayi a kafadar ta tace ” banson iskanci wane irin Aure Kuma? “Momy nifa kinsan na saba zama da biyu kawai kidawo min da fauziya ko ki karamin wani Aure.

Wasu irin miyan kishi ta hadiye tareda ture plate din awarar ta na mai kallon kurulla, dauke kanshi yayi tareda cewa “momy inkin yanke shawara please kiyi sauri kiyimin nagaji da zaman kadaici, and please kisa mai aiki ta kawomin coffee inaso inkwanta ne anan dakina, agyare yake? ” yes agyare yake ai kasani, kuma kagama mafarkin ka ka farka ba wata mace a gidan nan again kayi hakuri da wadda kakeda banson iya shege.

“Nidai Momy kiyi min ko inkoma China in dakko miki suruka.  Yafada yana juyawa, tayi mugun kunbura saboda kishi yana wucewa dakin shi ta mike tareda d’an gwarar da plate din awarar ta a kasa tayi kitchen. Momy tayi dariya domin tasan wasa yakeyi don ya tsokaneta kuma yayi nasara don gashi tama kasa boye kishin ta, cikin fushi ta hada mai coffee ta nufi dakin nashi lokacin ya kwabe dagashi sai towel ne a jikin shi, yasan kishin ta sosai don haka yayi expecting dinta don haka yanajin anturo kofa yayi biris yana cewa ” come in. Y’an da ta d’an gwara jug din coffee din yasa ya juyo yaga takama kugu idanun ta sun ciko, wani irin maida yawu yayi yana kare mata Kallo da sama har kasa,,ace Matar shi ce wannan amma tana mai kwalelen wainnan kayan, kukan data samai ne yasa yadawo cikin hayyacin shi,

Cikin kwantar da murya yace me yafaru?  batareda ya matso kusa da ita ba.

Da gudu ta matso kusa dashi tareda fadawa kirjinshi  ta kankame shi  gam tasa mai kuka mai karfi, “nidai ban yarda ba. Tafada tana murza fuskar ta a kirjinshi ya yi baya tareda zubewa a gefen gadon yana riketa jikin shi na rawa ” baby why are you punishing me?  Kince bakyason kamshina na hakura na Kyaleki yanzu kinzo kina daukar Alhaki na,yazaki zo kina bugamin wainnan balloons din masu laushi?  “Kayi hakuri karkayi Aure please.  Murmushin karfin hali, yayi “oh saboda zanyi Aure ne yasa kikazo wurina?   Bakya jin kamshin nawa ne yau?  Ko zuciyar ki bata tashi yau ne?

Ai kamshin baya damuna yanzu. “Hmm why to baki koma dakin kiba?  ” kunya nakeji ai. “Ok jekici gaba da zama da Momy ni zanje in Auro wadda zata zauna dani batareda tabarni ina walagigi ba kamar maraya, kinsani baby kinsani this is not easy for me amma kin kyale ni kusan tree weeks marana na ciwo look. Yafada yana zameta tareda zare towel ya nuna mata hajiyar, ” kingani she needs you badly kin gujeta bayan kin saba mata da dumin ki da dadin ki. Yafada yana fitar da nishin sha’awar ta da kuma zakuwa. Hannun ta mai laushi ta saka ta kama kamar tanajin tsoro ta d’an murza kamar mai lallashi tace “Sorr….. Saurin kama bakinta yayi domin gudun karya kurma mata ihu momy tajisu, jikin shi na rawa ya dora hannun shi saman marar ta” Sorry baby I miss your momy badly kasa an horani.

Tsit kakeji na tsawon awanni baka kuma jin duriyar suba nidama na tsere don kar in makance, koda naga ankwashe hour biyu na koma naganta dunkule a cikin bargo, yana makale da ita kamar ya shige jikinta yana rage murya, ” baby last round please please please…. “Um um wayau ne kace last dazu yanzu kuma kace last nidai a’a. “Oh baby wallahi kece kikaja fa how many weeks?  Da wayo yasamu ya shige cikin bargon na kuma guduwa,, domin gwara inyi musu nisa Aunty Aisha ta hanani leken Asiri,

Har dare momy bata kuma jin duriyar suba, tayi dariya tareda wucewa dakin ta da taimakon mai aiki nurse dama zuwa takeyi  kullum ta zo ta dubata ta tafi.

Dadduma ta hau ta yita addu’oin ta na neman kariya tareda yiwa Ahmed Addu’a, sukuma tayi musu Addu’ar Daurewar zaman lafiya.

Zuwa dare kuwa tattarawa sukayi suka gudu gidan su, soyayya ta dawo sabuwa fil, tattali da tarai raya kamar ya mayarda ita ciki,  Washe gari koda ya tashi yayi sallah da kanshi ya hado mata breakfast ya bata yace su koma bacci kafin suje part din Momy, kallon shi tayi ” bazaka je aiki ba?  “Yes am the boss so na dauki hutu saina huta kafin inkoma sai duk kinbiyani bashina da kika dauka. “Nafa biyaka tunjiya. ” waya fada miki ko yanzu kar’i nake nema yafada yana hayewa jikinta tasa Y’ar Kara, “cikina!  Yayi saurin sauka tareda shafa cikin “sorry baby na dady wants more, kasan momyn takace ta mallake ni.

 

Basu suka fitoba sai karfe shabiyu, sunci adon su kamar ka sace su ka gudu saboda haskawa fuskar khaleel shar ya wani murmure tsab kamar bashi bane jiya kalar tausayi, momy na ganin su taji wani farin ciki,  bakin ta kamar ya yage tayi hamdala, suka tsuguna tareda gaishe ta, tace “khaleel ya jikin?  “Jiki kuma momy?  Waye ba lafiya?  Naziya da duk kunya ta gama rufeta ta dukar da kai tana murmushi, “kace jiya bakada lafiya, ka warke ne?  Sosa kai yayi yace ” oh momy kaina ne ke ciwo dama yanzu kuma yadaina saura kadan shiyasa ma bazanje office ba sai man da sati biyu. “Hmmm yayi kyau Allah ya bada lafiya, shikuma maganar Auren fa yasha ruwa kenan?  Tafada tana dariya tareda kallon Naziya, da duk kunya ta rufeta, ” momy ni na isa inkara Aure bayan inada mata am just kidding karkija a hanani sakewa kuma.

Haka sukayita raha a tsakanin su, ta mike ta wuce kitchen domin shirya musu Abinci, momy tace ” karkiyi aikin wahala kibari mai aiki tayi. ” momy zan iya ai. Yana binta da Kallo tareda shafa kanshi yana tuna duk wani moment nashi da ita tareda hamdala.

 

Saida ta wuce momy tace ” khaleel ka kai yarinyar nan gidan su ta gansu tunda tadawo bataje gida ba sai dai su da sukazo duba ni suka ganta. “Zamuje zuwa gobe nasa akawo mata motar ta ma yau zata iso. “Masha Allahu dama yakamata ace Matar ka batada motar kanta, nace cikin motocin Ahmed ka bawa malam daya mana me zakayi da tulin motocin nan daka Tara ka samu wasu kudi ka ware ma ka bada tallafi ga Almajiran da yake koyarwa nasan da Ahmed na nan zai yi hakan. Farin cikin canjin halin momy yakeji sosai yace ” momy duk karshen wata ina ware musu na Abinci, duk wani Almajirin Malam baya bara yanzu ana dafa musu Abinci ana basu suturu da Abubuwan rufa. “Toh Masha Allah Allah ya yi Albarka ya Kara budi ya sauki Naziya lafiya.

 

A ranar kuwa dalleliyar motar ta ta iso sabuwa dal ja mai duhu, tayi farin ciki sosai har momy saida ta lallaba ta fita tagani tareda tayata godiya, tace ” madallah saura kuma koyon tuki. “Momy ai na koya  a can da mukaje bari kigani ta bude ta shiga suna kallon ta, sai murmushi yakeyi yana kallon yanda ta bayyana farin cikin ta a fili, bai taba yin Abinda yajishi ya faranta mai ba kamar y’an da yau yaga fara’ar ta a bayyane, ga Addu’a da take zabgamai da tafi komai dadi a wurin miji, ta tayar tareda d’an tukawa kadan ta kashe tafito tana mai rungume momy saboda farin ciki, yau itace da motar kanta, ” Aa sakeni kije ki rungume Wanda ya siya bani ba. Tafada cikin tsokanar ta, ” kyaleta momy ai tsegumi ne yasa ta tsallakeni ina ware hannu. ” to rasa kunya. Ta juya ta wuce cikin gidan ta tabasu wuri.

Matsowa yayi ya riko hannun ta “let’s go ayimin godiyar a ciki not here yafada yana daga mata gira tareda cirata sama ba ruwan shi da idanun mai gadi, tako sagalo wuyan kayanta tsab, domin ta shirya biya da kudin da ba aganin su……. 🖊

 

 

 

 

 

“Toh a hankali dai munkusa kai karshen wanna labarim da ikon Allah don haka ina fatan Allah yabani Iko tareda juriya kukuma Allah ya Kara muku hakuri masoya yakaro kauna ya Kara budi ya warware wa kowa matsalolin rayuwar shi Allah masu Aure Allah ya karo d’an kon kauna, wainda basuda miji Allah yabasu nagari�.

 

 

 

*Matar Soja*

10/28/21, 4:58 PM – Buhainat: 6⃣3⃣&6⃣4⃣

 

 

 

 

……………. Tagumi yayi yana kallon y’an da take saurin zura kayan ta, kafin ma yayi wani Abu ta dauki hijabin ta da wayar ta tayi waje, “what is that?  Yafada yana mikewa, ko kafin ya zura jallabiya ya bita harta kai sashin momy so take tayi nisa da kamshin jikin shi inba haka ba ta fara Amai kenan. Suna zaune a falon Aunty Zarah ta kawo matsa tea a cup tana bata Naziya ta shigo, kanta akasa ta koma gefen su akan doguwar kujera ta kwanta batareda tace komai ba, tsayawa sukayi suna kallon ta kafin zarah tace ” lafiya dai ko akwai matsala ne Naziya? ” Bakomai aunty kawai zan kwanta ne anan. “Keda nakeso ki huta shine kika fara yawo bazamu shirya ba inba zaki natsu wuri daya ba. Juyowa tayi kamar tayi kuka idanun ta rau rau tace ” momy bana son can ne wani irin kamshi yakeyi dake tadamun zuciya. “Ki fada musu kawai bakyason kamshin perfumes dina ne shiyasa kika gudo nan, ko kuma kinayi ne kawai saboda ki wahalar dani?

Dariya Aunty Zarah tasa tareda cewa “eh akwai Kallo da bana komai da nan zan tare ba ruwana da tv, kai baby bakason kamshin dady tab.

Dukar da kai momy tayi tana murmushi cikin wani irin farin ciki, kafin tace toh ka canja ka kumayi kokarin korar na cikin gidan da wani kamshin tunda bataso karta cutu. Kallon y’an da ta juya musu baya yayi ya kama baki yarasa me zaiyi, kafin ya mike ya fita gidan.

Momy tace “Zarah Kira mai aiki ta bata Abinci, me zakici Naziya?  Tace shrimps takeso soyayye da miyar source.

Aunty Zarah ta kyalkyale da dariya ” barewa tayi gudu d’an ta yayi rarrafe?  Lallai wannan d’an tun baizo duniya ba ya gado tsoho. ” inkin gama yiwa surukar taki iya shege ki wuce ki hada mata kinsan mai aiki bazata iya yin yanda zaiyi mata dadi ba, da kafafun na motsi da da kaina zanyi mata. “Bari inje tom. Tafada tana dariya, abun ita kanta ya mugun burgeta y’an da Y’ar uwarta ta dawo kan hanya, dama ita tuni ta tuba bata taba Y’ar da taje wurin wani malami kota aiketa dafe kudin takeyi don tasan intace bazata jeba zasu samu matsala kamar sauran y’an uwan dake fada mata gaskiya.

Don haka ta natsu ta hado mata Abinda takeso, lokacin bacci yafara daukar ta. Momy tace “tashi kici Abinci ina kula dake ba wani Abinci kikeci ba ko a Asibiti. Tashi tayi ta zauna akasa, har wani irin tsinkewa miyanta yakeyi saboda ganin abun da take marmarin ci.

Tafara ci kenan ya shigo da kwali kato, suka zuba mai ido har ya Ajiye tareda kallon y’an da take cin Abincin ta ko dago kai batayi tana wani irin lumshe idanun ta, ya jingina jikin kujera, Abun na matukar burgeshi, Saida ta cinye tas tasha ruwa kafin ta mike ta kai plate din kitchen. Dawowa tayi tana Ajiyar zuciya domin taji ta dam yanzu. “Momy ga shi na sayo Kala Kala ta zaba Wanda takeso inrika Amfani dashi. Yafada yana baje tirarukan masu shegen kamshi da tsada Sunkai kwalba Ashirin,

Ai kuwa da gudu ta tashi tunbai bude ba tayi dakin Ahmed dake part din tana fitar da numfashi dakyar ta samu zuciyar ta ta kwanta.

Binta sukayi da Kallo shima ya ce ” what again momy?  Aunty Zarah ta ce “kagane kamshin ne kawai bataso saika daga mata kafa har zuwa lokacin da komai zai dawo dai dai. “Till when please, nidai gaskiya da sake haba. Ya mike zai bita momy tace “dawo nan karka sata Asarar Abincin da taci yanzu yarinyar nan Ina lura da ita ba wani Abun kirki takeci ba, Amma baka damu ba, duk damuwar ka kawai ka takurata ka hanata sakat, idan ka shiga wurinta ranka zai baci.

Fita gidan yayi cikin fushi, ita kuwa samun gado tayi taci baccin ta hankali kwance.

 

haka y’an dubiya keta zuwa gidan suna duba momy y’an uwan ta kusan kullum suna gidan, yanzu ba wani hayaniya ko fada tsakanin ta dasu sai zumunci, haka kawu modu yanzu shima da iyalin shi suna yawan zuwa gidan  domin kowa yasan Hajiya balkisu ta canja sosai, zumunci takeyi da gidan malam da Inna, sometimes in suna zaune da Naziya zatace “idan naji sauki kafafuna suka samu zan je har gidan inyi godiya inajin dadin Addu’oin da yake aiko min a jikina, Allah dai yasa agama lafiya.

Khaleel kuwa dole badon yaso ba ya hakura da Naziya, don tun yana satar dare ya shiga tana bacci, zata zabura tafara kelaya Amai kamar zata suma ya hakura da zuwa cikin gidan sai dai ya kirata a waya inkuma ya shigo yaganta yana daga nesa zaiyi magana ya juya, duk ya dawo gwanin tausayi, ankwashe kusan sati biyu a haka ita kuwa ta murtuke takara murjewa da cikar d’an yen ciki. Shiyasa bayako son kallon ta.

 

Zaune yake a office ya kasa yin komai, Allah yagani shifa ba karfe bane da zai zauna kusan sati uku ba mace bayan yasaba da ita, rabonsu da kebewa tun a bangkok, marar shi har wani nauyi take yimai, ranar bai tsinana komai ba har lokacin tashin shi yayi ya buga mota yayi gida, wani irin zazzabi zazzabi yakeji ma,

Duk ya sukurkuce,

Ita kuwa ranar taci adon ta domin Shukrah tazo ta zana mata lalle ta Y’ar fa mata kana nan kitso mai kyau, ta cancara ado cikin super wax dinta mai kyau taji dinkin yayi Riga da sket ta murza d’auri,  tayi kyau fiyeda tunani kamar wata sabuwar Amarya, kana ganin ta kaga mace mai d’an yen ciki,

Dawowa tayi falon dauke da kwanon  awarar da tasa Shukrah tayi mata kafin ta tafi, momy dake zaune kan kujera tana duba jarida domin hannun ta daya ya saku saura kafar kawai itama tana janta a hankali yanzu, tace “kici yaji a hankali Naziya karki haifo yaro ya cikamun gida da kuka. Murmushi tayi tana cewa “momy inban sa yaji ba baya mun dadi…..

Shigowa yayi da Sallama kasa kasa, tun shigowar shi ya zuba mata ido yana kallon y’an da tayi kyau sosai, Kirjin ta ya kalla da suka Kara kunbura kamar zasu faso,

Samun kusa da Momy yayi ya zauna tareda yin Ajiyar zuciya idanun shi akanta  ya koma kamar wani maraya ya dora kanshi saman kafadar Momy, yana gai sheta, cikin tausaya wa tace “yadai Ibrahim?  “Momy am sick. “Subuhanallahi. Tafada, itama Naziya da duk ta kasa natsuwa ta yi saurin dago kanta ta kalle shi domin Allah yagani kwanan nan tana mugun kewar shi so take taje gareshi tanajin nauyin momy gashi ya janye gaba daya, ganin y’an da take kallon shi yasa yace ” Momy yaushe zaki Kara yimin wani Aure? Yafada cikeda tsokana. Ture shi tayi a kafadar ta tace ” banson iskanci wane irin Aure Kuma? “Momy nifa kinsan na saba zama da biyu kawai kidawo min da fauziya ko ki karamin wani Aure.

Wasu irin miyan kishi ta hadiye tareda ture plate din awarar ta na mai kallon kurulla, dauke kanshi yayi tareda cewa “momy inkin yanke shawara please kiyi sauri kiyimin nagaji da zaman kadaici, and please kisa mai aiki ta kawomin coffee inaso inkwanta ne anan dakina, agyare yake? ” yes agyare yake ai kasani, kuma kagama mafarkin ka ka farka ba wata mace a gidan nan again kayi hakuri da wadda kakeda banson iya shege.

“Nidai Momy kiyi min ko inkoma China in dakko miki suruka.  Yafada yana juyawa, tayi mugun kunbura saboda kishi yana wucewa dakin shi ta mike tareda d’an gwarar da plate din awarar ta a kasa tayi kitchen. Momy tayi dariya domin tasan wasa yakeyi don ya tsokaneta kuma yayi nasara don gashi tama kasa boye kishin ta, cikin fushi ta hada mai coffee ta nufi dakin nashi lokacin ya kwabe dagashi sai towel ne a jikin shi, yasan kishin ta sosai don haka yayi expecting dinta don haka yanajin anturo kofa yayi biris yana cewa ” come in. Y’an da ta d’an gwara jug din coffee din yasa ya juyo yaga takama kugu idanun ta sun ciko, wani irin maida yawu yayi yana kare mata Kallo da sama har kasa,,ace Matar shi ce wannan amma tana mai kwalelen wainnan kayan, kukan data samai ne yasa yadawo cikin hayyacin shi,

Cikin kwantar da murya yace me yafaru?  batareda ya matso kusa da ita ba.

Da gudu ta matso kusa dashi tareda fadawa kirjinshi  ta kankame shi  gam tasa mai kuka mai karfi, “nidai ban yarda ba. Tafada tana murza fuskar ta a kirjinshi ya yi baya tareda zubewa a gefen gadon yana riketa jikin shi na rawa ” baby why are you punishing me?  Kince bakyason kamshina na hakura na Kyaleki yanzu kinzo kina daukar Alhaki na,yazaki zo kina bugamin wainnan balloons din masu laushi?  “Kayi hakuri karkayi Aure please.  Murmushin karfin hali, yayi “oh saboda zanyi Aure ne yasa kikazo wurina?   Bakya jin kamshin nawa ne yau?  Ko zuciyar ki bata tashi yau ne?

Ai kamshin baya damuna yanzu. “Hmm why to baki koma dakin kiba?  ” kunya nakeji ai. “Ok jekici gaba da zama da Momy ni zanje in Auro wadda zata zauna dani batareda tabarni ina walagigi ba kamar maraya, kinsani baby kinsani this is not easy for me amma kin kyale ni kusan tree weeks marana na ciwo look. Yafada yana zameta tareda zare towel ya nuna mata hajiyar, ” kingani she needs you badly kin gujeta bayan kin saba mata da dumin ki da dadin ki. Yafada yana fitar da nishin sha’awar ta da kuma zakuwa. Hannun ta mai laushi ta saka ta kama kamar tanajin tsoro ta d’an murza kamar mai lallashi tace “Sorr….. Saurin kama bakinta yayi domin gudun karya kurma mata ihu momy tajisu, jikin shi na rawa ya dora hannun shi saman marar ta” Sorry baby I miss your momy badly kasa an horani.

Tsit kakeji na tsawon awanni baka kuma jin duriyar suba nidama na tsere don kar in makance, koda naga ankwashe hour biyu na koma naganta dunkule a cikin bargo, yana makale da ita kamar ya shige jikinta yana rage murya, ” baby last round please please please…. “Um um wayau ne kace last dazu yanzu kuma kace last nidai a’a. “Oh baby wallahi kece kikaja fa how many weeks?  Da wayo yasamu ya shige cikin bargon na kuma guduwa,, domin gwara inyi musu nisa Aunty Aisha ta hanani leken Asiri,

Har dare momy bata kuma jin duriyar suba, tayi dariya tareda wucewa dakin ta da taimakon mai aiki nurse dama zuwa takeyi  kullum ta zo ta dubata ta tafi.

Dadduma ta hau ta yita addu’oin ta na neman kariya tareda yiwa Ahmed Addu’a, sukuma tayi musu Addu’ar Daurewar zaman lafiya.

Zuwa dare kuwa tattarawa sukayi suka gudu gidan su, soyayya ta dawo sabuwa fil, tattali da tarai raya kamar ya mayarda ita ciki,  Washe gari koda ya tashi yayi sallah da kanshi ya hado mata breakfast ya bata yace su koma bacci kafin suje part din Momy, kallon shi tayi ” bazaka je aiki ba?  “Yes am the boss so na dauki hutu saina huta kafin inkoma sai duk kinbiyani bashina da kika dauka. “Nafa biyaka tunjiya. ” waya fada miki ko yanzu kar’i nake nema yafada yana hayewa jikinta tasa Y’ar Kara, “cikina!  Yayi saurin sauka tareda shafa cikin “sorry baby na dady wants more, kasan momyn takace ta mallake ni.

 

Basu suka fitoba sai karfe shabiyu, sunci adon su kamar ka sace su ka gudu saboda haskawa fuskar khaleel shar ya wani murmure tsab kamar bashi bane jiya kalar tausayi, momy na ganin su taji wani farin ciki,  bakin ta kamar ya yage tayi hamdala, suka tsuguna tareda gaishe ta, tace “khaleel ya jikin?  “Jiki kuma momy?  Waye ba lafiya?  Naziya da duk kunya ta gama rufeta ta dukar da kai tana murmushi, “kace jiya bakada lafiya, ka warke ne?  Sosa kai yayi yace ” oh momy kaina ne ke ciwo dama yanzu kuma yadaina saura kadan shiyasa ma bazanje office ba sai man da sati biyu. “Hmmm yayi kyau Allah ya bada lafiya, shikuma maganar Auren fa yasha ruwa kenan?  Tafada tana dariya tareda kallon Naziya, da duk kunya ta rufeta, ” momy ni na isa inkara Aure bayan inada mata am just kidding karkija a hanani sakewa kuma.

Haka sukayita raha a tsakanin su, ta mike ta wuce kitchen domin shirya musu Abinci, momy tace ” karkiyi aikin wahala kibari mai aiki tayi. ” momy zan iya ai. Yana binta da Kallo tareda shafa kanshi yana tuna duk wani moment nashi da ita tareda hamdala.

 

Saida ta wuce momy tace ” khaleel ka kai yarinyar nan gidan su ta gansu tunda tadawo bataje gida ba sai dai su da sukazo duba ni suka ganta. “Zamuje zuwa gobe nasa akawo mata motar ta ma yau zata iso. “Masha Allahu dama yakamata ace Matar ka batada motar kanta, nace cikin motocin Ahmed ka bawa malam daya mana me zakayi da tulin motocin nan daka Tara ka samu wasu kudi ka ware ma ka bada tallafi ga Almajiran da yake koyarwa nasan da Ahmed na nan zai yi hakan. Farin cikin canjin halin momy yakeji sosai yace ” momy duk karshen wata ina ware musu na Abinci, duk wani Almajirin Malam baya bara yanzu ana dafa musu Abinci ana basu suturu da Abubuwan rufa. “Toh Masha Allah Allah ya yi Albarka ya Kara budi ya sauki Naziya lafiya.

 

A ranar kuwa dalleliyar motar ta ta iso sabuwa dal ja mai duhu, tayi farin ciki sosai har momy saida ta lallaba ta fita tagani tareda tayata godiya, tace ” madallah saura kuma koyon tuki. “Momy ai na koya  a can da mukaje bari kigani ta bude ta shiga suna kallon ta, sai murmushi yakeyi yana kallon yanda ta bayyana farin cikin ta a fili, bai taba yin Abinda yajishi ya faranta mai ba kamar y’an da yau yaga fara’ar ta a bayyane, ga Addu’a da take zabgamai da tafi komai dadi a wurin miji, ta tayar tareda d’an tukawa kadan ta kashe tafito tana mai rungume momy saboda farin ciki, yau itace da motar kanta, ” Aa sakeni kije ki rungume Wanda ya siya bani ba. Tafada cikin tsokanar ta, ” kyaleta momy ai tsegumi ne yasa ta tsallakeni ina ware hannu. ” to rasa kunya. Ta juya ta wuce cikin gidan ta tabasu wuri.

Matsowa yayi ya riko hannun ta “let’s go ayimin godiyar a ciki not here yafada yana daga mata gira tareda cirata sama ba ruwan shi da idanun mai gadi, tako sagalo wuyan kayanta tsab, domin ta shirya biya da kudin da ba aganin su……. 🖊

 

 

 

 

 

“Toh a hankali dai munkusa kai karshen wanna labarim da ikon Allah don haka ina fatan Allah yabani Iko tareda juriya kukuma Allah ya Kara muku hakuri masoya yakaro kauna ya Kara budi ya warware wa kowa matsalolin rayuwar shi Allah masu Aure Allah ya karo d’an kon kauna, wainda basuda miji Allah yabasu nagari�.

 

 

 

*Matar Soja*

11/3/21, 1:14 PM – Buhainat: 6⃣5⃣ &6⃣6⃣

 

 

 

 

 

………….. Alhamdulillah Rayuwar tayi dai dai a wurin wainnan ma’aurata khaleel a kullum cigaba yake samu cikin Naziya ya girma sosai ta shiga wata na tara khaleel kullum cikin shopping din baby yake har online yaga sababbi sai yayi oder  daki guda ya ware ya shirya kayan harda painting dakin anyi shi irin na dakin yara gadaje hudu different design itadai tace Abubuwan sunyi yawa momy tace ba ruwan ta tabarshi yayi idan taga wani Abu ma ita ke tunamai ya siya,  tace “Momy toh ni ko kyalle bai siyamin ba sai baby.  “Dole ne wannan kwantar da hankalin ki.  Saidai momyn ta siya miki ina zaki kai kaya wasu ma fa ko kalarsu bazaki iya tunawa ba a cikin akwatin ki madam. “Kaifa akwai Wanda yakai ka tara tsumma ko bazaka saka ba,wainnan na Aure ne ka shirya zaka hada akwatunan haihuwa yaro. “Kai lallai zan hado set biyu kuwa harda na Amarya. Yafada ya gudu domin tsokana don yasan ta tsani kalmar Amaryar nan, “ba ason kayan tom. “Ke dalla har yau baki gano halin shi ba ya gane kina nuna kishin kine shiyasa yake tsokanar ki share shi Amarya sai dai yajira ta Aljannah. , momy kafa ta warke tsab zumunci tsakanin ta dasu inna Abun ba’acewa komai, yanzu ta Ajiye aiki tunda tayi jinya, don haka takan ware lokaci kawai domin fita ziyarar y’an uwan ta, ta dunke sosai da gidan kanin mijinta nata wato Alhaji Muhammadu,  Rayuwa ta koya mata darasi mai zurfi harta haddace, da kanta idan taga mai bukatar taimako tana taimaka mai, har gidan su Fauziya taje tabawa iyayen ta hakuri sosai suka ce bakomai ai haka Allah ya tsara, Fauziya na nan na aikin ta tasamu wani Alhaji mai mata daya zasuyi Aure abinsu, don haka Rayuwar ta natafiya y’an da Allah ya tsara mata, ta hakura da Khaleel domin tasan baya ta ita, in akwai mace guda a rayuwar shi to itace Naziya, baya ganin wata mace a suffar mata sai Naziyan shi,

 

Cikin gidan na koma tana zaune  a tsakiyar falon ta, tayi kiba sosai ta bude ga kyau da shekinta na nan sai ma kar’i,  da tayi, cikinta yayi katoto dashi kafafun ta sun kunbura, rigar less ce a jikinta fubu domin yanzu sune suturar ta, sukawai take iya jin dadin su, madara da milo ta kwaba wuri daya tana d’an gwala,

Momy ce ta shigo dauke da plate din tuwo da miyar shuwaka, tana jin sallamar ta tafara kokarin boye d’an cup din madarar ta, “turus tayi tace ” fito da Abinda kike sha ingani. d’an tura baki tayi tace ” kai momy bafa komai bane madara ce. ” wato bazaki rufawa kanki Asiriba Naziya, anfada miki nauyin babyn nan ya wuce misali ki rage ciye ciyen nan bakyaji. matsowa tayi ta Ajiye tuwon tace ” mikon nan dama nasan tunda najiki shiru anan akwai Abinda kikeyi to nagano ki ai.

Sallamar shi ne yasa momy tayi shiru tareda juyawa gefen shi ” jinan Ibrahim yarinyar nan zata koma gefe na harta haihu tunda bazaka daina bata Abinda na hanaka ba yazaka rika biye mata kalli y’an da take Kara kunbura kullum.

“Wallahi ba ruwana momy ni ba Abinda nake bata impact nakwashe duk madarar dake gidan nan nima na hakurada shan shayin. ” ina ta samu wannan tom. Ta nuna mai wadda ke cikeda cup. Murmushi yayi mai kyau ya matso kusada ita ta dunguri kanta ” look baby karkija momy ta rabamu akan wannan Abubuwan da kike yi kinga yanda kika zama kuwa kinkusa biyuna fa, please ayi hakuri da madarar nan. Yafada kamar mai lallashin Y’ar yaye, ” wallahi inban shaba jinake kamar numfashi na zai fita don Allah kubari inrika shan kadan bada yawaba. Kallon momy yayi da fuskar tausayi ” momy ki taimaka mana kinji.

Tsaki tayi ta tura mata kwanon tuwon “sakko ki mike kafafu kici Wanda zai wanke miki yaro da nono tunkafin ki haihu maza. Tana tura baki ta sakko kasa,

Ta wuce kitchen din ta domin kawo mata ruwa, yayi saurin zama, ” baby lokacin tashi office baiyi ba fa nadawo. Dago sexy eyes dinta tayi bayan tasa lomar tuwon ta tace ” why?  Duk da tasan me ya dawo dashi. “Oh don’t pretend like you don’t know, kwana nawa rabon da kibarni in huta, nakasa hakurine nadawo. Ganin momy yayi shiru, ” kai matsa mata taci abincin ta tunda kai baka lurada taci bataci ba. “Momy nima fa bawanda yadamu da damuwa ta me nadawo yi meke damuna ba Wanda yadamu nazama maraya tun yanzu, toh inta haihu ba mai komawa kaina ma gaba daya. “Ka shirya ma gida zataje wanka tunda ni kun raina ni nafadawa Kulu harma nafara yimata shiri tana haihuwa daga Asibiti sai gidansu sai tayi Arba’in zata dawo.

Dariya yayi harda jingina a jikin kafadar Naziya kafin ya kalli momy da duk sun zuba mai ido suna kallon dariyar rainin wayan shi, “Amma dai momy wannan story ne kawai ba gaskiya bane?  “Tatsuniya ce kaji, zaka gani in lokaci yayi. “Gwara ta zamo ta tsuniya kuwa don bazai yuwuba, ina ban Y’ar da ba wallahi, yaron nawa yazo duniya baza akawomin shi gidan ubanshi ba afaramin yawo dashi ina.  Tuwon ta takeci tana kallon y’an da ya hakikance yana zuba rashin kunya akan d’an da baizo duniya ba. Saida taci dayawa momy ta kwashi kwanonin tafita ta kyalesu, yana ganin ta fita ya mike zunbur ya dagata sama daga ita har katon cikinta, yayi cikin dakin su na bacci.

Tsayar da ita yayi ya na kallon katon cikinta abun na burgeshi sosai, wayar shi ya ciro yafara daukar ta hoto, yasaba yanzu kusan kullum sai ya mata hotuna saboda gani yake ba macen da ta taba burgeshi da ciki sai Naziya cikin yakara mata kyau da cikar haiba, tazamo hamshakiya. “Nidai kadaina daukata haka bayan nayi muni wannan cikin yasa duk nazama wata giwa. “Keke waya fada miki?  Ai bazaki gane y’an da kike burgeni bane badon na matsu inga baby naba da nace kiyita zama ahaka ina more Idona, look at my wife, ba raini kinga duk Wanda ya ganki yasan yes bakya tareda lauzy man nacika ki ta ko Ina. Yafada yana wani bubbudawa.

Rigar ta tube domin zafin dake taso mata duk da iskar Ac dake hura ko ina a cikin dakin, tarage daga ita sai under wear da bra, ” nima ai ba raguwa bace kasani nima nayi kiwon ka look at you harda wani tunbi ka Ajiye fa, ka kwashe min farin fata ma. ” I agree wallahi, domin bakaramar madara nake kwankwada ba, dole aga canji a jikina baby kedin ba ta wasa bace shiyasa kike juyani yadda kikeso, to yazanyi dole in lallaba  ki. Yafada yana shigewa jikinta cikin dabara da wayau, tace ” banson wayau fa da dadin baki. ” Allah ba wayau sai gaskiya, nidai a samma Almajiri yana bara don Allah. Yafada yana mai dora hannun shi saman kirjin ta tareda hade bakin su wuri daya.

Na janyo y’an kafafuna na gudu domin banason ayi aika aika ina wurin,

Sai bayan hour biyu suka fito cikin wani adon yana faman tarai rayar ta,

Ta lafe a Kirjin shi tana nishi ” nidai kajamun bayana na ciwo har wani budewa naji yanayi. “Sorry sorry kinga ki wartsake kafin momyn ki ta hauni yanzu da fada, guduwa ma zanyi office inada aiki da yawa, muje in rakaki wurinta in wuce.

Daga Kofar gidan ya juya ta shiga tana yatsunar fuska, momy na zaune tana kallon labarai a Aljazera tayi sallama.

 

Can karshen kujera takoma ta zauna dakyar, momy ta kare mata Kallo tace ” kai zamani yazo ya wahalar da ita da tsohon ciki abanza, kai khaleel ai dama ina ganin d’an banzan yaron nan nasan me yadawo dashi gida. A zuciyar ta take surutun ta saida taga ta zamo kasa tareda janyo trow pillow ta kwanta akasa, tace ” ina shi Ibrahim din?  ” ya koma office yanzu. “Hmmm. Taci gaba da kallon ta saida taga juyin yaki karewa tace ” ke meke faruwa ne?  “Bakomai momy. ” idan da akwai matsala kifada muje Asibiti yanzu kinji. “Aa babu komai momy.

“To tashi a kasa ki shiga cikin daki ki kwanta kinji kar jikin ki yayi ciwo. Dakin momy ta wuce taje ta haye gadon ta ta kwanta da kyar, maganar gaskiya khaleel yaja mata domin jin bayan ta takeyi kamar zai cire,   sai can taji ya tsagaita ta d’an yi Ajiyar zuciya ta gyara kwanciya, tana tunanin halin khaleel, kamar magnet haka ya koma mata gashi baya taba fushi indai akan hakan wannan Abun ne sai yasan y’an da yayi ya mata wayau ya more, All this months bayan dawowar su daga bangkok yaki Y’ar da yaje ko nan da can saboda ita duk da yanada appointment dayawa bai Y’ar da ya   tafi ba sai dai yayita wakilta manager dinshi, domin yaso yaje da ita momy ta hana, saboda cikin tace ba inda zaije yakai mata yarinya da ciki sai ta haihu.

Har bacci mai dadi ya dauketa ta zabura tareda tashi zaune domin wani irin amsawa bayanta yayi da ma marar ta bana wasa ba, tuni ta sakko tsaye tafara kai kawo, momy dake falo duk hankalin ta nakan ta tataso ta shigo, y’an da taganta ne yasa tace ” ke nakuda kikeyi, kinga y’an da kike gumi, ina kayan haihuwar taku ko baku hada ba ne?  Tace an hada suna side din mu Amma momy ai EDD na bai kaiba.

“Banson shirme nidai ina zuwa  ta wuce  Abinta cikin sauri ta dakko  Karamar akwatin ta fita da ita ta. Driver ta Kira tace ya gyara mota zasuje Asibiti,

. koda ta koma abun fa da gaske ne duk ta gigijce tayi saurin saka mata hijabin ta ta rikota suka fito tana yimata sannu,

 

Ba bata lokaci suka karbeta lokacin tanajin kamar marar ta zata fashe saboda azaba, sai salati takeyi tana Addu’a , Sukace ai Abun yazo gadan gadan don haka sai labour Room, saboda sauri ko wayar su bata kwaso ba, bare ta Kira khaleel din, shikuwa y’an da yaga Tanayi  yasa yayi ta Kiran ta bayan fitar shi, wayar kuma na gefen ta,  bata dakko ba don tayi ta ringing shiru. Haka ya daure yaci gaba da aikin dake gaban shi domin bayaso ya kuma barin office sai ya gama, can ya kasa daurewa ya Kira layin momy shima shiru lokacin tana Asibiti itama tata na gida.

Bai kawo komai ba ya ci gaba da aikin shi,

Bayan minti talatin ba tareda  doguwar nakuda ba ta sunkuto katoton d’an ta kyakkyawan gaske mai farin fatar ta da fuskar ubanshi,.

 

Nurses sai santi sukeyi suka shirya su duka uwar da d’an, aka fitowa da Momy da sunkucecen miji, ta karba jikinta na rawa tace “Ahmed dina ya dawo kalle shi sak Ahmed saboda fatar shi da idanun shi, taganshi sak d’an ta mai hakuri, wasu irin hawaye suka zubo mata a fuskar ta, ta fara tofeshi da Addu’a tana Allah ya sa ka gado hakurin mai sunan ka. Momy da karfin hali tuni ita ta lakaba mai suna.  Saida aka fito da Naziya dakin hutawa ta tuna da ita taga miji jiki na rawa bakinta har kunne sai lokacin ta tuna da zancen waya, tace ” kinga saboda rudu ban dakko wayata ba. Saida ta shiga sadin da aka kwantar da ita ta shinfida yaron kusa da ita tace “Sannu Naziya kinji Allah ya miki Albarka kinga Abinda Allah ya Azurta mu dashi, bari insa driver ya dakko min waya ta a gida nabarta kema taki na can kar khaleel yakira bai san halin da ake ciki ba.

Ta fito tafadawa driver wayar ta na falon ta yasa mai aiki ta bashi ya kawo.

Yana shiga harabar gidan misalin karfe hudu khaleel na shigowa da motar shi, badon ya gama ba yadawo sai don yakirasu basu dauka ba, fitowa yayi cikin sauri ya gaida khaleel din yace “ranka ya dade su Hajiya na Asibiti yanzu ma wayarta tace indakko mata.

“What Asibiti?  Meyasa tunda ka kaisu baka kirani kafada min ba?  Come on bani hanya ya koma motar ya yi reverse ya fita aguje, kardai ya bantalo aiki ne gashi lokacin haihuwar bai gama cikaba sai nan da sati biyu,  don haka a  high speed ya isa Asibitin, ko wani rufe motar bai tsaya yiba ya  wuce da sauri, ganin momy tsaye tana leken hanya ya karasa da gudun shi ” Me ke faruwa momy ina babyn take meke damunta ne?  Duk ya rude jikinshi har rawa yakeyi karyayiwa kanshi asara,  daure fuskar ta tayi kamar mai fushi tace “kai meye haka tana ciki ga dakin can. Ko jira baiyi ba ya tafi a sittin tabi bayan shi tana dariyar rudewar shi,

Tunda ya tura dakin yayi turus domin ganin jariri kwance a gefen ta yana motsa hannu yana cilla kafafu yana kuka tareda tande baki saboda yunwa.

Idanun shi a waje na mamaki yakasa koda motsi saida momy tace ” ko in shafa maka ruwa ka suma ne?  Cikin tsokana, ” momy baby…..  my baby…. Da gudu ya karasa ya na kokarin sunkutar yaron ya kasa, “tsaya malam inbaka, kallon Naziya yayi data runtse idanun ta saboda marar ta dake ciwo kadan kadan, karbar shi yayi bakin shi har kunne saboda murna da farin ciki ya zauna gefen ta “baby look at our baby yafada yana kallon kyakkyawan yaron  shi tareda riko hannun Naziya daya ya naji kamar ya mayarda su ciki, kukan da yaron yakeyi ne yasa ya ce “momy ko yunwa yakeji ne kinga y’an yake bude baki yana kuka. Yafada yana kallon jan bakin yaron d’an mitsili dashi,

“Ai wannan Yaro zaiyi ci tun da yafito yake wannan tande baki, ga uwar na fama yabari ta d’an huta sai a wanke nonon yasha. “Sai an wanke me za awanke they are clean momy tabashi kawai. Yafada yana kokarin kwantar da yaron, momy tabishi da kallon bakada ta ido, shi ko a kwalar shi, “kai bari ta huta kawoshi inbashi ruwan zam zam da Zuma.

Ta bude kayansu ta ciro wani d’an mitsilin cup da spoon ta fita ta dauraye ta dawo ta bude zam zam da kwalbar Zuma mai kyau ta diga ta zauna tareda cewa “mikon shi saika tashi ka Sanar wa su kulu da gidan kawun ku dasu zarah.

Cikin doki ya mike ya fara kiran number Malam  suka fara gaisawa tace mikon nan don tasan baida kunya sai yanzu yayi Abinda zai sata a kunya ita, ta karba tace “Sannu malam ya kokari’ to dai kayi Aboki kafadawa kulu tasamu miji na kwace. Yayi hamdala tareda godewa Allah yace toh Masha Allahu Allah ya barmana ya raya bari in shiga infada musu.

Kafin kace me kowa yaji wannan haihuwar kafin wani lokaci Asibitin ya cika makil da d’an gi saida momy ta koreshi, su Shukrah Aunty Aisha Aunty Raliya su Zarah sai hira akeyi, ganin yaron na d’an gine Asibitin na cika likita yace zasu iya tafiya ai komai normal ne daga, d’an har uwar don haka zuwa magrib sun gama hada kayan su ta kirashi bayan ya idar da sallah tace yazo ya kwashi Naziya yakai gidan malam an sallame su. Ta kashe waya, Aunty Zarah dake Rungume da yaron tace ” tab Aunty bakiso zaman  lafiya Khaleel din ne zai bari atafi da Naziya wani wankan gida y’an da yake wannan rawar kafar.

“Yoh biyemai zamuyi, kinsan y’an da nake fama dashi ne ni zanso taje tayi wankan ta mai kyau a gida cikin natsuwa. “ai momy tunda kina nan da kinbarta malam bazai bari ba ma don bayason wannan al Adar. Inji Raliya,  ai kuwa malam ya Kira yakai karar Momy yace ” ai baza ayi haka ba Ibrahim bana bin wannan Al Ada, dakinta zatayi wanka kaji karka damu.

Yayi Ajiyar zuciya ya buga mota yayi gidan shi saboda yasan yayi tsiya, suna jin shiru momy tasa zarah ta Kira driver ya kwashe su, tace wato saboda nace yazo ya kai ta gidan shiyasa ya gudu ko?  Toh tun baizo duniya ba nake hawa mota d’an ubanshi, su Aunty sai dariya sukeyi itadai tayi tsit tana jiran karon su dashi,  don ita tagama murna zata je wurin Inna, don wannan ce kawai damar ta idan ta wuce shikenan sai dai ziyara aje adawo gashi idan taje gida baya barin ta ta dade ya rika damun  ta kenan ta dawo gidan shi kamar zata gudu,

 

 

Suna shiga harabar gidan sukaga motar shi momy tace su wuce nata gidan da Naziyar zataga tsiya, haka aka kaita har gadon momy Aunty Zarah ta shirya ruwan zafi tareda na jariri, Momy tace” Raliya  taimaka wa Naziya tayi wankan bari inyiwa yaron. “Toh tace ta taimaka mata tayi wankan tsab ta gyara jikinta su Aunty Aisha suka gyare gadon tareda baza turare ko Ina na baza kamshi,  Aunty Zarah ta shiga kitchen ta samu mai aikin ta shirya farfesun  naman kaza da yayi lugub ta hado mata da tuwon shinkafa da miyar Agushi,  tana fitowa ta shirya, momy tace su Aunty Raliya suje su kwaso mata duk Abinda zata bukata itada yaron su kawo nan kafin su wuce domin dare nayi.

 

Oga khaleel na can yana tunanin ta inda zai bullowa Al amarin yaji sallamar su Shukrah, tashi yayi cikin jin kunya dama a shirye yake kawai yana tunanin rigimar da zai tarar yagansu, “Aunty yaushe kukazo?  Yafara kame kame ” ai mundade da dawowa kayan Naziya zamu kai gefen momy tana can itama……….. 🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

11/3/21, 1:14 PM – Buhainat: 6⃣7⃣&6⃣8⃣

 

 

 

 

……………….Fita yayi zuwa cikin gidan fuskar shi a turbune, yasamu momy na magana da Aunty Zarah tana ganin shi tace “here he comes, ni na shiga daga ciki. Aunty Zarah tace ” ka taro march khaleel. “Aunty wai me kuke nufi dani ne da zaku ajiyemin ita anan. “Ka gode Allah da  ta tsaya ma a nan din kai dai ka lallaba Aunty kafin KO dakin ta hanaka shiga wannan ciccin magana da hura hanci kasan badamuwar tabane better come down. “Aunty mutum da iyalin shi sai anyi tajamai rai?  “Ni kaga sauri nake inyi gidana ka gyarota baruwa na. Zama yayi a falon ya dora daya kan daya yana latsa wayar shi saida yaga su Aunty sun gama shigo da kayan suna kaiwa dakin momy Aunty Zarah tace “ku muje Raliya in sauke su Aisha mu muyi gidan mu. “Kutafi kubar mana Shukrah nayiwa malam magana, gobe driver yaje ya kaiki ki kwaso kayanki  mu na nan zaki taya mu reno, ga dakin Ahmed can ki je kiyi wanka ki huta kinji.

Toh kawai tace ta wuce, su Aunty suka dauki jakun kunan su suka wuce, saida ya musu sallama ya dawo zai shige dakin momy tace “dakata malam bacci zatayi tagaji karkaje ka damesu. Sanin fushi want  solve his problem, yace “Ayya Am momy gaisawa kawai zanyi infito kinji please, gaba tayi jin kukan yaron ya take mata baya, ” tashi Naziya daure ki gwada bashi Mama mugani tunda yaki yin shiru.

Dago kanta tayi suka hada ido ya mata kuri tareda kallon kirjin, he is eager to watch her feeding his baby, kashe mata ido yayi momy ta fita da feeding bottle din yaron tace bari inyi boiling kan indawo bashi kinji. “Zantaya ta momy don’t worry. Yafada yana matsowa, ta harare shi tayi gaba kawai, saida yaga ta fita yayi saurin kulle Kofar yadawo da gudu tareda zama gefen ta ya rungume ta itada babyn dake kan kafarta, ” I love you hayati, tank you so much Allah yayi miki Albarka keda yarona,  ya bata fake a kunci tareda manna mai shima  yace “meyafi wannan farin ciki a Rayuwa?  I have everything best wife and now this, best blessing in the world, sune ya’ya baby we are blessed Alhamdulillah, and Allah ya horemin Abinda zan wadataku insha Allahu batareda kun rasa komai ba a Rayuwa in ina numfashi you want lack anything,  kinga am ready next year ki suburbudo min twins or triplets. Harar shi tayi tareda cewa “eh mana tunda haihuwar ba wahala badole kafada haka ba. “Hhhh oh come on baby keda daga fita ina dawowa sai naji good news, tell me how, ya akayi ne? ” ai bazaka san ya akayiba tunda kaine ka takalo min nakudar tunfitar ka bayana bai daina ba. Tafada mai komai ya rungume ta gam yana dariya “wow kice akwai wani sirri dake kawo saukin labour amma kike min rowa,  OK next time bazan daga kafa ba duk rakin ki. “Nice ma mai rakin?  ” no ni na isa infada matata jarumace tunda ta sunkuto min wannan katon babyn.   karbar shi yayi ya ciro dabino ya mai huduba tareda diga mai ruwan abaki ya fara lashe bakin shi soo cute, yana kallon shi itama tana kallon baiwar da Allah yayi musu, tana godiya ga Allah a cikin zuciyar ta, saida ya kammala ya dora mata shi saman cinyar ta yace “bashi nono ingani kafin momy ta dawo, yasa hannu yana kokarin zage mata zip, ta rike hannun shi tace “wait basai ka cire ba zan daga rigar. ” no salon ki danne mai hanci remove the shirt, bai saurareta ba ya zage tareda cire rigar, yaja Numfashi tareda cewa “Hmmm sun Kara kunbura baby. Tana runtse idanun ta taciro nonon a bra ta daga kan yaron ya taimaka mata ta manna bakin shi a kai, kamar yana jira ya cafke yafara ja kamar ankoya mai, tayi Y’ar Kara saboda zafin y’an da yakeja, “yadai?  “Zafiiii. ” oh meyasa ni idan na kama bakya yin karar?  Bude idanun ta tayi tace ” naka ai bazanji ba. Tafada tana kashe mai ido. Kuri ya mata na d’an lokaci kafin yace ” look you just born karki dauki Alhakina kinga KO yanzu bakisan wane irin hali nashiga ba seeing my son sucking this. Yafada yana dan matsawa, idanun shi na wani lumshewa, ta buge mai hannu tace “zai kware fa. Saida yaron yayi bacci ta zare bakinshi nonon ya biyo domin yariga yakawo, d’an karamin hanky ta dauka zata goge mai baki ya, yayi saurin karba ya saka bakinshi ya sude nonon tas daya zubo, tana kallon shi, kafin ya duka ya lashe d’an mutsilin bakin d’anshi,

“Ruwan nonon kakesha?  Fuskar ta a yamutse, dagowa yayi ya daga mata gira Alamar what?  No be my property. “Na shanye ruwan…. Bare wannan mai dadin,  wow baby zan rika taya yarona shan wannan sweet milk din, meyasa ni da nakesha ba ruwa sai yaro yazo ruwan kezuwa?  Hmm bazan taba bari ruwan ya koma ba zaki dauki ciki ki haihu.

“Da gaske kakeyi ko wasa?  “What?  ” shan nonon. Tafada tana kallon shi cikeda son gano gaskiyar zuciyar shi, “of course am serious, in naga dama ma ma ba fura zansiyo ina gutsira inashan nonon ba.

Kyalkyale wa tayi da dariya y’an da yake magana da zuciyar shi daya, kwankwasa Kofar momy yasa ya zabura ” good night momyn ki zata fara fada na rufe mata kofa. “Zakazo ka bude ko sai ranka ya baci. Tafada da karfi cikin fada. Yayi saurin budewa ta tureshi ta shigo “bani hanya uwar me kakeyi harda rufe kofa don iya shege kabarni waje yarinya ta haihu yau ma bazaka daga mata kafa ta kwanta ta huta ba. “Haba momy biki fa takeyi mezanyi mata. “Fita don ubanka mara kunya. Tafada tana kokarin kaimai jifa saboda ya fassara ta, dariya yasa yana cewa “Allah ya barmin ke momy natafi nabarki da Ahmed da momyn shi, nayiwa d’an ki takwara. Fuskar ta ta Washe “Allah  yayi Albarka ya raya Ahmed. Tana share hawaye da suke kokarin zubo mata. Naziya ma saida taji jikin ta yayi sanyi ta kalli yaron a zuciyar ta tace “Allah yasa kayi halin mai sunan.

 

 

Cikin kwanakin ba karamin gata da kulawa take samu a wurin Momy ba, harma da d’an gi, har malam yazo yaga Abokin shi Inna dai taki zuwa saboda Kara momy tayi tayi tace mezan zo inyi da wani miji bana bukata nabar miki Hajiya balkisu, tace toh nagode nikam ina son Abuna, su Aunty Raliya kullum sai sunzo zuwa yamma su tafi, angon k’arni baida sakat Yanzu saboda taron mutane a kullum, saidai yasa Shukrah ta kawo mai shi yaganshi uwar tayi tsadar gani,

Har zuwa ranar taron suna daya tara d’an gi da y’an uwa da Abokan Arziki, Wanda khaleel ya gwangwaje su da shatara ta Arziki Abin ba acewa komai sai sanbarka, momy ma bakaramin kudi ta ke kashewa little Ahmed ba Wanda sukewa lakani da Nur, domin shidin hasken zuciyar sune baki daya,  harda sabuwar mota ya d’an karo mata, ranar suna, Ana tsaka da taron aka kawo mai ita, sai lokacin ya shigo cikin gidan duk da taron mutanen ya Kira Aunty Zarah yace ” please ku Aramin mai jegon minti biyu, momy ta fito da fada, ” kai wai baka ganin taron mutanen nan ka ratso kana wani neman ta mezata yimaka?

Dai dai tafito cikin Adon wani d’an kareren leshi mai shegen kyau da tsada tana walwali tasha kunshi kafafu da hannu ga wani head da aka nada mata ya zauna kamar wata sabuwar Amarya ba mai jego ba, kowa idanun shi ya koma kanta, harda uban gayyar, wani irin narkewa yaji zuciyar shi nayi ganin  ta, zai iya rantsuwa ba wata mace kamar Matar shi a duniya, tuni aka fara kashe mata hotuna, kallon ta takeyi da wani irin sirri Wanda tuni ya fahimci itama tana kewar shi don haka bai damu da idanun mutane ba yafara takawa cikeda kasaita dajin yafi kowa sa’a ya matsa kusa da ita tareda rikota, ya ciro dalleliyar wayar shi ya mikawa Aunty yace “snap us Aunty. Akasa shewa domin bakaramin daceew sukayi da juna ba, ga shaddar jikin shi tayi Kala da tata, yaci hula tangaran, ita kanta tasan tasamu miji, yes she can shout out loud and say this is my husband, kowa yaji, ya mugun yimata kyau kullum Kara murjewa yakeyi, she really admire him, har wani kishi taji yana d’an tabata don akwai y’an mata na family dayawa a gidan datasan wata zata iya k’yasa mata  miji, don haka ta rike Abinta kam,

D’an dukowa yayi a kunnen ta ” let go out side I have a surprise. Yajata suka fita ana binsu da guda tuni momy ta kauce tana farin ciki, duk da harabar gidan akwai motoci birjik bai hanata hango wannan farar motar sabuwa dal ba taji flowers da balloons a gabanta an manna sticker katuwa mai daukeda “For you my wife.

Kafin ta ce wani Abu ya d’an ka mata key din “tank mom nur. Tareda dora mata kiss a bakinta, wasu irin hawaye na farin ciki suka fara gangarowa a fuskar ta, takasa cewa komai domin bakaramin kaya ya d’an karo masu ba, harda gwala gwalai na kece raini da batasan ta ina zata fara sakasu ba, Rungume shi tayi tareda cewa ” ina kakeso insaka kaina saboda farin ciki this  is too much my love.

Kara rungume ta yayi yana murmushi mai cikeda farin cikin my love data kirashi, ” kin biya ni yanzu yanzu for calling me your love baby, I want you to love me more only me, ki nuna min so ki tarai raye ni ki maidani d’an lelenki that’s all what I want from you.

“I love you dadyn Nur,zan nuna maka duniya ma zata shaida hakan because I really do love you, you are the best husband the best father and the best son, am very proud of you Allah yakara Arziki da budi yakuma tsaremin kai.

Dagata yayi cak yana juyi da ita duk da mutane na yawo a wurin ko ajikin shi, ” Wayyo dadi kice inrika kawo miki surprise domin insamu Addu’a da wainnan sweet sweet words din. “Kai son irin wannan Abu a idanun jama’a?  “Kai Aunty wallahi keda momy kunason hana ruwa gudu, sauka tayi cikin jin kunyar Aunty Zarah tace “Aunty nayi sabuwar mota. Tasa guda tareda cewa Masha Allahu Allah yasa Albarka, gaba yayi yabarsu ganin duk Anfito ana tayata murna, tabi bayan shi da Kallo, she feels like following him ganin ya shige gidan su,

Yanzu take blaming kanta na kin bashi kulawa sosai duk da suna gida daya batasan wane irin hali yake ciki ba, tasan momy na kulada cikin shi, Amma tasan halin shi ta gefen rashin hakuri ta wani wurin gashi bai samu damar complain ba,

Haka taron sunan ya ci gaba anci ansha sun samu sha tara ta Arziki, har zuwa lokacin da kowa ya watse yarage daga momy sai Shukrah domin har naman sunan ma da rana aka soyeshi aka rabe Abunka da manya, nidai nasamu naci hanji domin a cikin naman suna ba Abinda yakai hanji dadi, don haka ni acan na makale.

Tun karfe tara momy tace Shukrah ta koma dakin ta wurin Naziya tanaso tasha magani ta kwanta tagaji da yawa yau. Naziya tace “gaskiya momy kije ki huta tunda akayi haihuwar nan bakya wani hutawa. “Toh miji fa nayi badole ba, nasa sun kai muku duk kayan da kuka samu gidanku kafin sutafi. “Toh Allah yakara girma momy da lafiya. “Amen. Ta yiwa Nur Addu’a ta Kara rufeshi ta fita, tana fita Naziya ta mike tace “Shukrah zanje wurin Baban shi don Allah karkiyi bacci ya farka yayita kuka, har momy tagano bani. “Hhhhh ba ruwana idan nayi bacci yayita bare baki. “Don Allah karkiyi zandawo zuwa karfe goma nan da thirty minutes kinji. “Toh kiyi sauri. Matsawa tayi ta gyara jikinta da kyau tareda feshe jikinta da kamshi ta zunbula katon hijab ta sudada ta fice.

 

 

A zaune yake yana kallon hotunan su na dazu yana murmushi, kallon bangon falon yayi inda ya jera hotunan su a bango daya na farko nashi na tsakiya Nur sai nata a gefe, tunda aka haifeshi yamai wannan hoton yasa A gidan, bata ma sani ba,

“Allah ya jikan takwarar ka, yaya Ahmed banda kamar ka duk duniya kayimin komai kana raye katafi kabarmin Abinda zantuna dakai a kullum, Naziya itace kyautar da tafi komai da kayimin a duniya, look at your name sake he is just like you. Yafada yana danna hoton Nur ya bawa wayar kiss “I love you my family, I miss your mother soo much my son har bana iya bacci saboda kewarta. Yaji anturo kofa, a hankali yayi saurin juyawa, zabura yayi tsaye “baby!!!!, ist really you?  Hijabin ta tacire tareda ratayawa a jikin hanger ta fara takowa cikin y’anga domin Kara siyemai zuciya. “Yeah nice ko sai na nemi izinin ina son ganin mijina?  Jikin shi na rawa saboda tsananin farin ciki Da murna ya karaso da gudu ya rungume ta. “Wow my baby am very happy for this special visit, were is my son?  ” nabar shi da Shukrah nace bari inzo in shayar da dadyn shi shima tunda shi ya koshi. Saurin dagowa yayi ya zuba mata ido domin kalmar ta tasa yaji tsigar jikin shi na wani irin mikewa da yin zillo, yafara kallon rigar bacci dake jikin ta baka ta lafe saboda silk, kirjin nan dake cike sun wani irin tsone mai ido saboda kunburi, cikin wani irin rawar murya yace “da gaske baby you are going to feed me your special milk? “Yes if you really want t….. “Ofcos I love too ya sunkuceta sai kuryar dakin, sai samata Albarka yakeyi, sanin yayi matukar kewar ta ta dage tabashi taimako sosai har yasamu natsuwa, yana lafe a jikinta sai kissing dinta yakeyi ta ko Ina yace ” tank you baby, ina momy kika zo nan?  Kara rungume shi tayi tace “tayi bacci da wuri kasan tagaji dayawa, nabar wa Shukrah na gudo nan. “Naji dadi sosai baby ta damu dani sosai. “Bari in koma kar ya tashi yafara kuka Asiri na ya tonu. Tashi yayi ya zauna tareda kallon y’an take kokarin mayarda rigar ta, “kiyi wanka mana. “Sai naje can banda pad inna cire anan. “Wai yaushe wannan abun zai dauke ne yaufa sati daya. “Kai ance sai mutum yayi Arba’in fa. “What da sake fourty?   “Bakowa bane fa ni bansan nawa kwana nawa zaiyi ba, “please idan ya tafi kifadamin I can’t wait, kinga yanzu kinki bari ko gogawa inyi kadan am missing it “you are shameless. Tafada tana direwa a gadon da gudu, yabita…..  🖊

 

 

 

 

*Matar Soja*

11/3/21, 1:14 PM – Buhainat: 6⃣9⃣&7⃣0⃣….. 🔚

 

 

*bazan rufe wannan lbr ba batareda godiya a gareku ba y’an uwa marubuta, kun nuna min kauna ta gaskiya kunbani goyon bayan da bazan taba mancewa ba*

Gareki my writer SA’ADATU BINT ABDULLAH,

tareda ke AUTAR MANYA, karamcin ki bamai faduwa bane Allahu yabar kauna da soyaya.

Hazika mai yayi fasihiya NIMCY LOVE jin jinar bangirma.

Hakurin ki abun kwatance ne my Aunty, BINTA UMAR ABBALE.

ina maganar hakuri karamci bazan manta dakeba MAMAN NURUL HUDA.

Addu’a tareda jinjinar bangirma mai rubutu da ilimi da hangen nesa HASSANA D’AN LARABAWA.

… GARKUWAR MARUBUTA uwa maba da’ mama Allah yasa ki gama labrin tubali lafiya,

Kunada matukar yawa bazaku fadi dukaba sai dai kusani duk kuna zuciya ta Allah yasadamu da Alkharin sa Ameen.

Sakon ta Aziya garemu baki daya na marubuta biyu da muka rasa kwanan nan Allah muma yasa mu cika da kyau da Imani,  ina kewar ki Zinariya Allah ya Albarkaci Abinda kika bari. Amen Amen

 

 

…………..shiya rakata har cikin dakin Shukrah nata baccin ta, Nur yafarka tareda saka hannu yana wulwula kafafun shi na shirin yin kuka, da saurin shi yana dariya ya daukeshi tareda fita ya na mata ido ta biyoshi, dakin shi suka tafi ya shinfide shi a gadon shi ya na mai wasa, saida ta shige tayi wanka tafito takarbeshi yana kallon su ta bashi nono ya cafke yana sha, matsowa khaleel yayi tareda hadasu ya Rungume, “my boy na maka wayau nasha nima. A wannan daren baiyi wani baccin kirki ba yana nan makale da iyalin shi, harta ti bacci haka ya zuba musu ido yana godiya ga Ubangiji,

Tsabar gajiyar da tayi batasan gari ya waye ba, haryayi wanka ya shirya ya dauki yaron shi yafito falon dai dai momy na tanbayar Shukrah ina Y’ar uwar ki take?  Bata kaiga bada amsa ba tayi wuki wuki domin ba Naziya ba har Nur batasan inda yake ba itama tayi baccin gajiya, “ga jikan ki nan Momy. Suka juya tareda zuba mai ido yana wani irin sheki da daukar ido, “kai ina uwar shi take?  “Bacci takeyi Momy kinsan gajiyar taro. Kallon Shukrah tayi tace jeki nemi breakfast kinji, kai kuma mara kunya bani shi inyi mai wanka, Allah ya shirye ka, don iya shege don nayi bacci ka lallabo kazo ka takure yarinya bayan tagaji, kaga kabi yarinyar nan a hankali tana biki karkasa ta kwainuka. “Meye haka kuma momy?  Ubanka modu ne. “Momy ba ruwana ita tabiyo ni dakanta fa narakota shine muka kwana anan. “Allah sarkin y’an sharri?  “Oh yanzu baki Y’ar da ba Momy?  ” get away. Ta wuce Abinta. Yayi dariya tareda cewa “sai kin shafa kinga takoma gidan ta zaki gane itama tana kewa ta.

 

A haka sukaci gaba da jegon su cikin gata da kulawar momy Shukrah dai sati biyu tayi dakyar inna tace abata Y’ar ta haka, momy tace ai mungode ma ko a hakan kulu. Shukrah ansaka ranar ta da Almajirin malam sadiq, tuni anfara shirye shirye, Wanda khaleel ya biyawa malam da Inna Ummara harma da Shukrah, yace su hajji zasuje bana shida Naziya in Allah yakaimu, sunyi murna sunyi farin ciki sunyi Addu’a tareda sa Albarka.

Momy ce ta tsaya tsayin daka ta hadawa Shukrah kayan daki dana kitchen kafin su Inna sudawo Ummara, Wanda koda suka dawo suka tarar da Abin Arziki, malam Yayi ta fada yace abun Yayi yawa, momy tace Shukrah Y’ar tace da Ace tanada wani d’an ma shi zata bawa ta hada su biyu a gidan ta, domin ba Wanda yaki irin Arziki a gidan shi,   suna dawowa aka fara shirye shirye, Nur nada wata biyu, Yayi bulbul, kullum suna hanyar gidan malam a cikin motocin ta sai wadda taga damar hawa, wani lokaci harma ta khaleel tukawa takeyi, kowa yaganta yasan yes tana cikin lokacin ta a gidan mijin ta, tazamo Y’ar gata gidan miji da cikin d’an gi,su suka dage suka gyara kanwar su wadda itama tabi tana gyara kanta domin tasani tana tareda gwarzon miji, da baya gajiya da ita.

 

A haka sukayi Auren Shukrah cikin girma da farin ciki kowa ya koma gidan shi ya tsuguna, Wanda saboda karamci malam yabawa kawu modu wakilcin uban Amarya shi yayi na ango Wanda ya mugun farantawa kawu dasu khaleel rai, harma da momy tayi farin ciki Wanda wannan dalilin yakara musu Y’ar da da shakuwa a tsakanin su.

 

Ina labarin su Salifa?  Tuni momy ta roki khaleel tareda sa bakin Naziya yasa aka kyalesu, sunyi matukar nadama domin sunga jarabawa don Salifa tuni tafara wani irin ciwo duk ta rame ta fita hayyacin ta Wanda koda aka kaita Asibiti gwajin farko aka gano ta daukeda ciwon zamani, tayi kuka momyn ta harda suma saboda tashin hankali haka ta zauna jinyar ta gata itama kwankwason ta sai a hankali tun buguwar da tayi,  fadin halin da suka shiga ma bata lokaci ne, don haka Allah yasa muyi kyakkyawan karshe a rayuwar mu.

 

Bayan wata shida da haihuwar Nur, a zaune take tana share hawaye yana faman lallashin ta, kallon pregnancy test strip din takeyi tana share hanci, dariya yake hadiyewa ya kalli d’an shi dake zaune yana wasa da kayan wasan shi yayi kamar d’an larabawa saboda sha’awa, “what is your problem Momyn Nur? ” kaine matsala ta nafada maka tunfarko muyi planing kaki now look yarona six months ace inada cikin wata biyu, gaskiya kasan y’an da zakayi dashi.   Hade fuskar shi yayi for the first time a rayuwar Auren su dayaji ta mugun batamai rai, ya mike zunbur ya fita sai gidan Momy yana huci.

Zaune take sanye da eye glass tana karatun jarida ya shigo a fusace ya zauna tareda dafe goshi. “Kai lafiya ka shigomin gida bako sallama?

“Please yarinyar nan ce fa momy zambata mata rai?  “Wace yarinyar ka keda ko ka Haifa a gidan nan inji? ” Momy Naziya, wai… She is crying because she is two months pregnant, tundazu take kuka ina lallashin ta, can you imagine she have the gut  tace incire cikina momy my baby. Yafada yana nuna kanshi, Ajiye jaridar tayi tareda zuba mai ido nadan lokaci kafin tace “now tell me how you react to her, kayi mata hauka ko?  Jinan kar inji kar ingani wai ka hau Y’ar nan da fada, yoh badole tayi kukaba yaro d’an wata shida ace ciki wata biyu.  “Ni bance komai ba kawai nafito ne. “Better.

Mikewa tayi taje gidan tareda barin shi anan,   tana ganin Momy ta goge hawayen ta, matsowa tayi tareda zama kusa da ita Nur nata washe mata baki tareda mika hannu ta daukeshi tana mai wasa kafin ta koma kan Uwar.

“Naziya. “Na am momy. “Ina ilimin ki yaje?  Ina hankalin ki ya shiga, bakin ciki kikeyi saboda Allah ya miki baiwa,?  Kinsan cewa yaran nan biyu dana Haifa ba a son raina bane, naso in tara yara Allah yagani sai ya kasance tundaga Ahmed da Khaleel ban kuma samun haihuwa ba, kinsan me, ina matukar farin ciki kuma ina son duk Abinda zaku taramin koda dubu ne inda rai da lafiya zanrike muku su, kika sani ko biyun sune rabonki?  Karki kuma fadar a cire miki ciki koda daga Arba’in kika samu wani kinji ni.? ” toh Momy kiyi hakuri. “No mijin ki zakibawa hakuri bani ba. Ta mike da Nur ta fita daga gidan dai dai yana shigowa, “ka Kara lallabata yarinya ce Ibrahim, ta wuce.

Yana shigowa ta tashi tareda nufar shi ta rungume shi gam, “Am sorry Abban Nur, bazan karaba kaji forgive me. “No problem karki damu am ready to take care of you and my child, cikin minti kadan sun gyaro Al amarin su tareda taimakon Uwa tagari a yanzu.

 

Alhamdulillah, cikin shekara biyar Naziya ta Ajiye yara Hudu bayan Nur, tayi twins maza sai Karamar su yanzu da take goyo balkisu wato Ummul khair, gaba daya batasan wahalar raino ba kakarsu ta dauke musu komai, haka take bin mijin ta duk inda zaije hankali kwance sun yawata kasashe a wannan shekarun, idanun ta sun bude sosai ta Kara wayewa tareda Aji, taso taci gaba da karatu Amma ganin khaleel bai so kuma ya bude mata hanyoyin samun kudi da yawa business center nata nakanta Wanda tafi karfin hidima tundaga dubu daya zuwa dari biyar har million, y’an uwan ta ma sun shaida ita din mai sa’ace.

Kudi na musamman tasa khaleel ya ware tareda gina wata babbar makaranta mai suna Ahmed foundation, wadda take taimakawa marayu da basuda karfi suke samun kulawa sosai batareda ko sisin suba,

Momy ta Ajiye aikin ta tuni bata zuwa sai kula da y’an jikokin ta, haka zata zuba Abinta a mota suje ziyara gidajen y’an uwa, har gidan malam sai suje su wuni susha hirar su sai sun ishi inna da barna tace “Hajiya balkisu ki kwashi mazajenki sun isheni da barna suna fama da jajayen kunnuwa. Haka zasuyi ta raha a tsakanin su, haka take zuwa gidan kanin mijin ta ma, ta canja sosai kamar ba itaba,

A cikin wannan satin su Naziya suka shirya fita bangkok kamar duk kowane karshen shekara yanzu saboda kasuwancin shi.  A dai dai lokacin Ummul khair nada wata takwas kuma tagano tana daukeda wani cikin don haka ba wani dogon bayani ta cireta tareda Ajiye wa takwarar ta tabi mijinta domin su hole, tuni ta gano cewa Matar so ke gwarne don haka ta daina damun kanta domin duk cikin dazatayi khaleel na farin ciki, toh meye damuwar ta Sai muce Allah ya karo Arziki da   zaman lafiya a tsakanin wainnan ma Aurata…… Pen’s 🖊

Alhamdulillah nagode wa ubangiji da ya nufeni da ganin karshen wannan littafin

Dubun godiya gareku masoya aduk inda kuke, my Real fan’s wato AUREN GADO paid grp one and two, domin kune real fan’s dina domin kun nunamin kauna da soyayya ta hanyar rububin siyan wannan labarin, fatan Alkhairi agareku bazan taba mantawa da Alkharin ku da hakurin ku gareni ba,

Ina rokon Afuwa saboda yanayi na jinkiri da aka samu akan wannan labari, ba son raina bane kana naka Allah na nashi, this is the though time for me saboda situation dina, am sorry duk Wanda na batawa rai a wannan tafiyar, saboda ajizanci na d’an Adam, ku yafemin don girman Allah.

Darasin da na ke son y’an uwa su dauka a wanna lbr shine, kaso mutum don Allah,mucire hassada son zuciya handama mugodewa ubangiji da duk Abinda yabamu a Rayuwa, sannan kuma Muna fatan muyi kyakkyawan karshe irin na momy Allah ka nufemu da gyara kura kuranmu kafin mutuwa.  Ayi Amfani da Abinda zai amfane mu a wannan lbr sannan mu watsar da duk Wanda baida Amfani kuskuren da ke ciki Allah ya gafarta min Alkharin dake ciki Allah yasa Al umma su anfana dashi,

Dubun godiya gareku masoya da nake bawa a pc kunada yawa, lallai soyayyar ku babbace a wannan labr da kuma gareni Nafisa na yinku over Allah ya karo Arziki ya kareku daga dukkan sharri.

 

*TAMMAT BIHAMDILLAH*

Leave a Reply

Back to top button