Yar Aikin Karuwai Hausa Novel

Yar Aikin Karuwai Book 1 Complete

Sponsored Links

 

🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼

      LITTAFIN KYAUTA NE

Related Articles

                1-5

Official

By
AsmaBaffa

08061929616 Sabon layina

          BISMILLAH

INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON RUBUTA SABON NOVEL DINA NA KYAUTA SABO DA JIN DADIN MASOYA NA,SANNAN FANS DINA INA BAKU HAKURI A BISA LAYINA NA DA YA SAMU MATSALA DOLE SAI SABO NA CANJA,DUK WACCE KE DA TSOHON LAYINA ZATA IYA GOGE SHI TAYI SAVING DA SABON, SANNAN WANDA SUKA SAN INA WANI GROUP NASU PLEASE KU BA ADMIN LAYINA TAYI ADDING DINA DA SABUWAR NUMBER TA

MASU BIBIYAR NOVELS DINA INA MATUKAR GODIYA MATUKA SANNAN IDAN AN FARA KARANTA NOVEL DIN NAN TO SHARHI NAKE BUKATA BA GODIYA BA,ALLAH YA BAMU IKON AMFANA DA DARASIN DAKE CIKIN LITTAFIN AMEEN.

LITTAFAN DANA RUBUTA SUNE

CIRANIN AMANA
MA’AIKACIYAR GOMNATI
KASUWANCINA
GASKIYA CE
KAMARSU CE DAYA
DUK INDA TA FADI
ME MAGANI
TUBABBIYA
HADIN KAI
JIN DADI SABO
MAFARKIN FARIDA
WARE BAIKO
AUREN MU

NA KUDI SUNE

RASHIN SA’A
TA GYARU
ADDUAR KAWA
YAR KWANGILA
GIDAN GWAURO
DANGIN RABI
DUNIYATA AAMNAH
BABU KAUNA
JIKAR MAGUZAWA

SADAUKARWA GA
DUKKAN YARAN TSUNTUWA

PAGE NAKI NE TAWAN
AIDA MAMAN TASNIM

 

      Cikin dare misalin 1:40am na fito fitsari buta na dauka nabi ta jikin dakin Gwaggo wani uban nishi naji Wanda ban taba ji ba ana ihu washsh…..ahhhhhh……uhhhhhh……Ahhhhh zaka kashe ni….zaka kashe ni…Zan mutu….zaka kashe ni …Ahhhh….wash…uhmmmmmm….zaka kashe ni…zaka kashe ni….zaka kashe ni…..tsoro ne ya kamani na sake kasa kunne tare da manna kaina a jikin kofar naji ihu da zaka kasheni Yana Kara ta’azzara,a fili nace karfa ayi kisan kai Muna nan gaskiya bai kamata ba ya kamata na Kai agaji waye zai kashe Gwaggo haka bazan kyale ba wallahi, kofar dakin na shiga kwankwasawa Shuru ba a bude ba amma Ina Jin Maganar Gwaggo tana zaka kashe ni wayyo….kofar na hau duka da karfin gaske Jin za ayi kisan kai

   Cikin bacin rai aka bude na kutsa kaina ciki da sauri,cikin zafin nama na runtse idona ganin Gwaggo zigidir Babu komai a jikinta tana kokarin daura zaninta cikin sauri,Dagaci ma daga shi sai dankwalin Gwaggo Yana Kare gabansa ashe sex suke ana kwasar love ban sani ba,duk da haka ban gane ba nace au kuyi hakuri dama zuwa nayi na taimakeki Gwaggo naji kina ta cewa zai kashe ki zai kashe ki shine nazo kawo Miki dauki ashe kalau kike, kinci uwarki da ubanki shegiya annamimiya munafuka me labe cewar Gwaggo,Dagaci kasa magana yayi ya mako kofarsa ya kulle Saura kadan ya datse da hannuna, ai ji nayi Gwaggo taci gaba da zaka kashe ni tana nishi,tsayawa nayi a jikin kofar na dora Hannu a kai Ina salati nace shike nan Gwaggo zuwa gobe sai gawarta,kasa jurewa nayi na kai Hannu zan sake kwankwasa musu kofa sai kuma na fasa Kawai Ina jimami na tafi na bar wajen.

          Washe gari kuwa
Shigowa gida nayi Ina rabe rabe a bango cikin wulakantattun kayana Atamfa ce amma kana taba ta zata yage kadan take jira doguwar riga ce,dankwali me santsi Wanda ake Kira da disco shine daure a kaina na zamge goshina sai kyalli yake,tsoro nake ji sabo da nayi laifi an aikeni ban dawo da wuri ba,Gwaggo da Aunty Amarya na samu a zaune gaban murhun gawayi,Dagaci Yana zaune a saman tabarma jikin dakinsa ba Wanda ya kulani Ina rabe rabe idona ya ciko da kwalla a tsorace na mikawa Gwaggo daddawar dana siyo Ina ja da baya Ina kyarmar jiki,ba Wanda ya kulani cikinsu ni sam gwara ma suyi fadan yafi sauki akan wannan shurun da Suka min,salin alin Gwaggo ta karbi sakon bata ce komai ba dole akwai wata a kasa,na gaza Shuru nace Gwaggo baki ce komai ba ko dan zagina kiyi mana,Aunty Amarya na kalla nace Aunty dan Allah ko ashar uku ce dan Allah,cikinsu ba Wanda ya kulani

    Nasan wannan shurun nasu yafi komai bala’i a wajensu na rasa inda Zan saka kaina,gaban Dagaci na karasa tare da tsugunawa idona cike taf da kwalla,nace dan Allah ni kuyi min bala’i,Dagaci sai lokacin yayi magana yace a’a me za ace dake,da sauri na girgiza Masa Kai na furta a’a akwai abin fada dan Allah kuyi min fada,wallahi sai Kun Yi min fada sai kunyi fada aikena fa kuka yi na dade ban dawo ba ko zagina ai ya kamata kuyi shine hankalina zai kwanda,dan Allah Baba kuyi min fada,gaban Aunty Amarya na koma na durkusa na furta dan Allah ki zazzageni ku dakeni dan Allah,Dagaci na sake kallo Muka hada Ido nace ka balla ni dan Allah kayi min dukan kawo wuka, ni nasan da wannan shurun nasu muguntar da zasu min gwara su min dukan tsiya duk ranar da Suka yi wannan shurun to zanji jiki,banza suka min ba Wanda ya kulani,sai da na dame su Dagaci ya fisgo ni na saki ihu ya hau jibgata Kamar wani gardi ya samu sai da ya min lilis sannan Gwaggo ta miko min buhu dauke da masara a ciki tace dauki dan ubanki ki tafi nika ta sake hambareni sai da na Kai kasa sabo da azaba haka na dauki nikan na fice.

        Cikin kauyen mu me suna rinjin tsangaya dake cikin karamar hukumar Ungoggo dake Kano state nake tafiyata cikin nutsuwa yau ma da sanyi na dake ni mace ce me sanyin hali babu sawa ba hanawa haka nake,dauke nake da buhu a kaina na dakko Mana garin tuwo daga wajen nika da kyar nake taka kafata sabo da gajiya gida na dawo na shiga gidanmu madaidaici me dauke da dakuna hudu da wani karamin daki da suke tara tarkace Wanda ke a zauren gidan Kuma shine dakin da nake kwana da Yar tabarma ta a gefe
Saukar duka naji a bayana a firgice na juyo Ina Sosa bayana a inda nake bayan na ajiye garin tuwon na zauna a jikin bango na rakube Ina hutawa, tana zazzaro min idanu Kamar zasu ballako su fado kasa tace tashi tsintacciyar mage maza kije ki karasa aikinki kaf bana son ‘ya’ya na sun gama karatu sun dawo a samu matsala kaf garin nan babu kamarsu,ko akwai Wanda yayi makarantar gaba da secondary idan ba yarana ba munafuka kina kallona da idonki a soye Kamar an watsa waken suya, a hankali nayi kasa da kaina ina me runtse idona a cikin raina nace ya Allah yaushe zan fita daga wannan kangin Allah ka nuna min Iyayena ko dangina idan ma bazan gansu ba Allah ka hadani da Wanda zai rikeni a matsayin ‘ya Kamar kowa,wani saukar azazaben rankwashi naji tace wai dan ubanki bada ke Gwaggo take ba,juyowa nayi naga Aunty Amarya ce a kaina yanzu wanda dazu Gwaggo ce take dukana ganin zasu yi min taron dangi na mike nace yanzu da me zan fara? Da kan uwarki zaki fara cewar Gwaggo dake jawo ruwa a rijiya, Dagacin garin nan ya shugo Wanda muke Kira da Baban Mairo,nidai aikin gyara gidan nakeyi Wanda gidane a kauyen na rufin asiri gidane na bulon siminti ko Ina ya sha siminti cikin dakuna Kuma tiles ne da bandaki   idan ka shiga gidan baza kace a Kauye kake ba sabo da daidai misali Yana da kyau,Baban Mairo Yana kokari wajen kula da iyalinsa kaf garin yaransa ne suka fi kowa ilimi dana addini dana zamani banda ni tunda Ni tsintata akayi iyakata primary na iya karatun hausa da rubutawa  matansa Aunty Amarya da Gwaggo Suka zugashi ya cireni sai Islamiyya Kawai nake zuwa da Yamma gashi har na Kai 21yrs a zaune ni banyi aure ba ni banje school ba sai aikin gida sabo da a garin ma duk kyan da Allah yayi min ba wanda ya taba zuwa wajena kowa cewa yake yi bazai auri marar asali ba babu Wanda ya sani ko yar shege ce ni sabo da mafi yawa Indai yaran halak ne ba a jefar dasu.

    Dagaci dan Asalin garin Argungun ne Wanda tuntuni iyayensa Dake Fulanin tashi ne Suka dawo Kano Ungoggo me yana da kanne biyu Mata Talatu da Hafsa duk a garin suke aure da yaransu maza da Mata,Dagaci Raliya Gwaggo itace ta fari ya Aurota daga garinsu Argugun Haihuwar Farko ta haifo Maryam ana ce Mata Mairo,ta sake haifo Bilkisu ana ce Mata Gaji,sai Namiji Imrana sai Abdullahi ana ce Masa Audu sai lawan da Autansu Sagiru,duk yaran Gwoggo ne.
Duk suna kanana Dagaci ya Karo Auren Kubra ana ce Mata Aunty Amarya a bazawara ya aureta bata haihuwa shi yasa sun dade bata taba haihuwa ba sai dai yaran Gwaggo Kawai ganin Gwaggo yaranta ne Kawai shi yasa basa zaman kishi da Aunty Amarya sun hade kansu duk abinda daya tayi to dai dai ne,basu da Imani Basu da tausayi ko kadan,Dagaci ma haka daga shi sai Yaransa Indai ba yaransa ba to baya son wani da ci gaba ko a kauyen baya son kowa da samu sai iyalinsa.

   Gwaggo ce ta bani labarin Lokacin da ta haifi Bilkisu Gaji kenan da watanni bakwai lokacin Kuma aka tsince ni jaririya a nannade cikin sabon zani cikin jini Wanda ko cibi ba’a gama yanke Mini ba a jikin wani masallaci yarinya ce Fara kyakyawar gaske, ana ta cecekucen waye zai dauka a kauyen kowa yaki karba,kowa yace bazai dauka ba Shima Dagaci yaki karba aka rasa me dauka Jamian tsaro Yan Sanda suna ta roko ko za a samu me dauka Kar a bari a kaini gidan raino amma kowa yaki,Gwaggo tana Jin labari tace yo tunda kowa baya so ni a bani idan na raineta ta girma na samu Yar aiki komai na gidan sai ta dinga yi min na huta idan Allah yayi me kashin arziki ce ta zama kadara na dinga Neman kudi da ita,Gwaggo da sauri ta falfalo tace a bata tana so,Hukuma ta bawa Gwaggo Amana akayi rubuce rubuce aka damka Mata jaririya bada son ran Dagaci ba haka na taso cikin tsangwama da bala’i a gidan tun Ina karama Gwaggo kullum ita da yaranta sai hantarata da zagina haka Dagaci da aka auro Aunty Amarya ma haka Suka dora da ganamin azaba iri iri kaf kauyen da yan uwan Dagaci sun tsaneni basa kaunar ganina haka Dangin Gwaggo dana Amarya bani da inda zanje naji sanyi wahala idan da sabo na saba har Muka girma tare da yaransu suma basa so na har dama dama Mairo ma gashi Allah ya bani kyau da cikar zati,kaf garin bani da masoyi Namiji cewar ni Yar shege ce bani da iyaye ba Wanda yake zuwa wajena zance har gashi Ina 21yrs a kauyen Gaji tana 21yrs Mairo tana 23yrs,Mairo da Gaji suna gama Secondary ya samo musu admission a poly Kaduna sukayi HND yanzu sun gama zasu dawo gida daga Hostel shine ake ta shirye shiryen tarbarsu Kamar zasu dawo daga kasar waje.

     Washe gari da safe Dagaci ne ya kwala min Kira bayan na gama aikina da sauri na saka slifas dina dan Madina naje nace baban Mairo gani na durkusa har kasa kudi ya miko min yace maza jeki cikin garin kano ki siyo min Lemon kwali da ruwan roba ki hau machine saura ki zauna baki dawo da wuri ba ki tsaya karuwancin naki karba nayi bance komai ba na shiga daki na dakko Hijab dina blue na dora a saman doguwar rigata ta kodaddiyar Atamfa ta maroon,Gwaggo na samu tana juya Miya nace Gwaggo na tafi cikin gari,Tsaki taja tace to ko ki dawo lafiya ko Kar ki dawo lafiya Rabi Ina ruwana Rabi kike ko Rabi Kudirar Allah ko? Aunty Amarya dake linke Kaya tace Wai Rabi Miracle haka ake ce Mata a makaranta bakar kinibabba munafuka Yar shege anyi cikin Shege an jefar a bola,inda sabo na saba haka na fice Babu me Napep ko Daya a kauyen dole machine na hau na Shiga cikin garin kano bakin wani katon shago nace ya tsaya a nan,Me machine din ya sanni na sanshi garinmu daya nace dan jirani Musa naje na dawo,yace to ni Kuma na shiga ciki na Fadi abinda nake so aka ebo min na siyo zan fito kenan Naga wata katuwar mota me kyau tayi parking wani mutum kyakyawa baki ya fito daga motar shi baza a kirashi da matashi ba sannan baza a kirashi  da babban mutum ba,tunda ya fito yake kallona kamar maye,da sauri na tafi na dane saman machine din da muka zo tare,da Sauri mutumin yace dan Allah malam me machine tsaya,nace Kai Musa muje,Mutumin yace karka tafi zan baka kudi,Musa ya tsaya cak da machine na bata rai cike da masifa nace Musa muje nace fa,Musa yace Allah ya gani bazan tafi ba kina ji dai yace zai bani kudi haka Kawai ki cuceni ke nawa zaki bani? to ba inda zani,kinga dan Allah ki saurare shi yayi sauri ya barmu mu tafi,baki na turo gaba tare da kallon mutumin nace Ina jinka,Murmushi ya saki yace Kawai kwatancen gidanku zaki bani idan nazo sai na fada Miki dalilina na tsaida ku,Shuru na Masa har ya gaji da tsaiwa yace Ina jinki princess,Harara na watsa masa,Musa zancen ya karbe ya Fara Masa kwatancen gidanmu yace idan kazo kauyen namu kace gidan su Rabi Yar tsuntuwa ko gidan Dagaci,Murmushi mutumin yayi yace nice name sunana Alhaji  Mas’ud amma kowa da Alhaji Kutama ya sanni, baki na tabe Ina kallo ya bawa Musa dubu biyu,Musa sai Murna Yana godiya yace zaku iya tafiya,sai lokacin Musa yaja machine muka tafi Yana murna,nace Wlh Musa kayi asara tirrr da Kai,dariya ya sake yi tare da furta ba komai naji.

   Ina sauka a kofar gidanmu na biya Musa kudinsa na shige gida da sauri,Ina shiga Dagaci ya hauni da masifa da bala’i,Gwaggo tazo ta fisge ledar lemukan tare da dungure min kai tana furta gantalalliya anyi gadon karuwanci,Aunty Amarya tace yo matar da aka tsinta yashe a titi cikin jini ai kinsan bata da uba Yar shege ce ai,bance komai ba sai ga Mairo da Gaji sun fito daga daki ashe fitata suka shugo gida,Gaji ta kalleni tace jaraba ja’iba haihuwar kwararo na tsaneki wlh Gwaggo ban San ya akayi Yar shege take da kyau haka ba,kalli duwawunta Lodi guda Nawa Kuwa sai kace Kullin Sugar gata Fara Ni Kuwa wankan tarwada Mairo ma haka,duk inda tazo ta tsaya Muka tsaya dole ita za a dinga kallo,kalli duwaiwaka sun Bude,Aunty Amarya tace ai sabo da maza ne yasa Kwankwaso ya bude inda Zaki San Yarinyar nan tasan maza matan aure ne kugunsu yake fashewa amma gashi ita tun tana budurwa,Dagaci da shigowarsa kenan yace Allah ya bata sa’a tayi cikin Shege a gidan nan taga yanda ake daddatsa mutum da ransa a gidan nan.

    Ina jinsu ban kulasu ba sai da na gaji nace baiwar Allah ce dai, na ebi ruwa nayi wanka nayi Sallah naje wajen Gwaggo a hankali kamar almajira na duka nace Gwaggo Zan samu abincin? Aunty Amarya da kinibibi ta amshe zancen da furta ke dalla algunguma ba abinda Kika iya sai ci shegen ci kamar Yar Jaka da wata jar Fuska sai kace zabiya na Mura,a hankali nace kuyi hakuri kaddara tace tazo haka da ace akwai Iyayena baza ku ganni a nan b….kafin na karasa duk masifar dauriyata na fashe da kuka me tsuma zuciya na mike Zan tashi Mairo ta fito daga daki sanye cikin Riga da wando damammu sun Mata kyau tace dan Allah Gwaggo ku bata abincin nan ko a huta da jaraba,Gaji Kuma tace ku kyale Yar iska tayi kukan jini yarinya sabo da samun sarari tusar asuba shike nan ana magana sai kuka,Gwaggo lokacin su Audu yara sunci abinci sun jagwalgwala shi ta jawo ragowar ta Kara wani dan kadan akai ta tura min tana furta gashi Nan sarkin ci ciki Kamar zani dauki ki tafi ko na hambareki, Dauka nayi da sauri sabo da tun safe banci komai ba na koma dakina Wanda ba komai sai tabarma sai Ghana must go wacce kayan sawata ne a ciki,Zama nayi na lashe abincin tas na fito da kwanon,Muna yin Sallah Isha na fito nayi wanke wanke nasan ya zama dole da dare ma bana hutawa,Ina kwance a dakina bacci ya Fara daukana Dagaci ya shigo har dakina yace ke tashi na aikeki shago ki siyo min battery Zan saka acocilata wato touchlight,mikewa nayi na duba agogona wani na roba Wanda ake Kira da lado lado karfe goma na dare ga shagon da nisa dama komai dare ni suke aike ba ruwansu da cewar ni macece.

     Haka na tashi Dagaci sai kallona yakeyi Kamar maye,kunya ta kamani,bawan Allah ya Fara lasar labbansa nidai na zurma Hijab na karbi kudi na tafi da sauri a tsorace haka naje na siyo na kawo Masa ya karba tare da shigewa dakinsa.
Dama kwanan Aunty Amarya ne yau Dagaci akwai abinda ya kulla a ransa fada yake so ya takali Amarya, Amarya ta Sha wankanta tana kamshi tazo ta kwanta a bayansa tare da rungumeshi, cike da masifa yace ke mene haka ya naji kina tsami,Amarya ta bude baki kafin tayi magana cikin masifa da bala’i yace tashi ki bar min dakina kazamar banza shi yasa Gwaggo take birgeni,Amarya kishinta ya motsa ranta ya baci ta mike cikin fushi ta fice daga dakin Dagaci ta koma dakinta tare da kwanciya,karfe biyu na dare Dagaci ya fita daga dakinsa nayi nisa a bacci kamar a mafarki haka naji ana shafa min nono tun Ina Jin Kamar ba gaskiya ba sai naji gurnanin mutum Yana ahhhhh…uhhhhhh Yana ci gaba da lagude min Boobs da sauri na farka na bude baki zan tsala ihu naji an rufe min baki da hannu daya shi Kuma Daya hannun ana shafa min kirji,jikina ne ya hau rawa Kamar an jona min shocking,Dagaci yace ke ke ke shiiii kwantar da hankalinki Baban Mairo ne Dagaci yi Shuru ki bani hadin Kai idan ba haka ba sai na koreki daga gidana Kuma kin San baki da wajen zuwa baki da kowa sai ni a duniya Zan iya yankaki Babu Wanda zai ji labari sabo da haka ki yarda dani Kawai ai dama kina bawa mazan banza ga Wanda ya rike ki tun kina tsumma ni sai a barni a banza ai kamata yayi a fara kosar dana gida sai a kaiwa dawa,fisge fisge nakeyi da Shure Shure amma ya rikeni Yana furta zai yankani Ina ji Ina gani zai min fyade ta karfi,Takalmi na jawo da kyar cikin duhu na shiga kwalawa Dagaci a kansa ta ko ina wanda ba shiri ya sake ni, Amma mayen ya sake dawowa ya rikeni   ban San Ina na cafka ba da bakina na gartsa Masa mugun cizon da ba shiri ya sakeni yaja baya azaba tasa ya mike ya bar dakin ganin zan tona Masa asiri.

     Mikewa nayi na sawa dakina sakata na kwanta naci gaba da baccina cike da mamakin Dagaci mutumin da ya rikeni Ina jaririya na girma yanzu zai lalata min rayuwa ban kawo barin gidan ba a Raina sabo da nasan bani da kowa a duniya ban san kowa ba sai su,duk kauyen babbar kawata guda daya ce Saratu Kuma bata gari an turata kudu Lagos Kuma ta koma Anambra can yankin Igbo

    Washe gari da safe sai ga Dagaci ya fito da kumatu bangare daya a kumbure suntum,Gwaggo ce ta tambaya Kai Kuma lafiya Baban Mairo naga Kamar sawun hakora? Dagaci yayi Miki Miki karshe yace daga mafarki wlh, mafarki nayi Ina fada da damusa a kungurmin daji Muna cikin kokawa ta kafta min cizo a kumatuna abin mamaki Ina tashi naji zafi kumatuna ya kumbura suntum,ban san Sanda na washe baki ba dariya ta kamani da kyar na danne, Aunty Amarya dariya tayi tace hakkina ne ai da ganin cizon nan sai dai namun daji ba dai Dan Adam bil Adama ba sai ka nemi maganin mayu, Gaji Yan boko anyi Diploma Mairo ta Gama NCE sai Sannu suke ma Dagaci,Yau ma haka na yini Ina zuba aiki zuwa Yamma na gama komai da aka sani nayi wanka Ina zaune Ina dan hutawa sai ga yaro ya shigo da sallama yace Wai ana sallama da Rabi,wata shewa Gwaggo ta saki tace wanne asararre ne shi kuwa wannan gyartai ne ko me yankan farce ko kuwa me gyaran takalmi nasan Rabi Kam sai dai irinsu,Aunty Amarya tace kema da bata bakinki ai sune ma tashi kije dan ubanki ko ma samu mu aurar dake mu huta da Kaya,nace ni bazan je ba,Gwaggo tace ubanki da yayi cikin shegenki yaci uwatas dole kije aure zamu yi miki,Zaki tashi ki tafi ko sai na makeki shegen wuya duk guru,mikewa nayi dama sanye nake cikin tsohuwar atamfata Leda Riga da skert arsh da zanen black na yafa tsohin mayafina na fice,Ina fita Naga katuwar mota ta gaske Alhaji Kutama ya fito daga cikinta hankalinsa kwance yasha shadda blue Yana kamshi.

    Zaune suke a kasa gaban Mama, Papa, Iyamami,Baffa,sai Mami, suna Musu nasiha akan zaman Aure,Papa yace to   Kai Nawwar zaman aure sai hakuri Alhmdllh ma kaga Yar uwarka Muka zabar maka Kuma gashi ka amshi zabin namu Hannu bibiyu sabo da ka faranta Mana duk Kuwa da cewa kana da kudi domin a halin yanzu yaron Dake da arziki sai dai abi abinda yace amma Kai gashi a matsayinmu na iyaye ka Amince ka auri Yar uwarka Sabreen to ku dai ba Yara bane Nawwar shekarunka sun Kai 30 ke Sabreen kin dade baki aure ba shekarunki sun wuce 29yrs sa’ar Nawwar ce ke shekarunku daya wannan ba shi zaisa ki Raina shi ba dole sai kin yarda shine shugaba a kasansa kike idan kinyi haka sai ki zauna lafiya,karki kalli Kuna da kudi kina samun na kanki kice Zaki raina mijinki kiyi Masa biyayya Sabreen ku zauna lafiya idan da matsala yanzu an waye ba sai an kawo Kara wajen iyaye ba sabo da ko Kun kawo Kara karshe dai hakuri za a baku ku koma ku zauna,idan kina Kai Kara wajen iyaye to baza suga mijinki da kima ba lokacin Kuma ke kin manta Kun koma Kuna zamanku lafiya su Kuma Yan Uwa da iyaye suna Jin haushin mijinki Yana ganawa yarsu azaba,idan Kuma kawaye Kika fadawa to ki sani a banza kawayen zasu na kallonki kowa yasan ba dadin aure kike ji ba,wannan zai bawa kawaye da Yan Uwa damar zugaki su baki shawarar da ba itace ba,Kai Kuma Nawwar Kai Namiji ne sai kayi hakuri nasan kana da nutsuwa da hakuri dan Allah ka Kara wani hakurin,Nawwar zuciyarsa wani zafi take Masa da radadi ya rasa me yasa har yanzu a Nigeria hausawa suke auren dole wa yaransu musamman ga masu kudinmu Kawai sai dai a hadaka da yarinya ko kana so ko baka so,Sabreen Kuwa hawayen bakin ciki takeyi ji take Kamar ta kashe kanta sabo da yanda ita take son wani baturen kasar Italiya inda tayi karatu Suka zuba soyayya an hanata aurensa sabo da ba musulmi bane ita bata San ma Nawwar ba Sam sabo da ba a kasar ta girma ba shi Kuma a UK yayi karatu, gashi ya hadu tako Ina amma shi so daban yake ba ruwansa da haduwa ko kyau.

   Bayan Papa ya gama Nasiharsa Mama tace ku tashi ku tafi gidanku Allah ya muku Albarka,Baffa Kara yayi yace dan Uwansa yayi musu fada shi bazai ce komai ba,Mami tasan danta baya son auren,Sam Sabreen bata dace da shi ba amma anfi karfinta, haka Amarya da Ango Suka Mike Suka fito compound yayinda Nawwar sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda dinkin zamani silver yasha kyau ba kadan ba Yana kamshi da kyar yake taku sabo kafirin girman Kai da Izza,Sabreen itace Kamar namijin ba yanga ba komai tace let’s go kana ta tafiya haka Wai mene hakane ahhh nifa ban Saba ba yawwa a turai mu bama haka kowa normal ne da Namiji da mace duk Daya,baki ya tabe tare motsa dan karamin bakinsa masu dauke da jajayen labba Kamar zaiyi magana ya fasa,Sabreen ce ta saka hannunta cikin nasa ta fisgo shi tace muje bacci nakej…bata karasa ba ta janye hannunta da sauri tace kaiiiii….wannan ai Kaine Softy sai kace mace kaji laushi hannunka ka dinga karfafa jikinka,shi dai baice komai ba sai a hankali yake furta aure Nawwar Ango,ni an min aure da girmana ni za a nemowa Mata wato duk idon da Allah ya min su Papa sun raina halittar Allah ni ban Isa Naga mace tayi min na zaba ba sai sune zasu zabo min duk manyan idanuna ni wato bana ganin Mata bane tunda hakane ai bai kamata naga farjin mace ba ya kamata na nemo Papa ya nuna min Hanya tunda abin hakane zasu ga tsiya.

     Guard ne ya budewa Sabreen bayan wata dalleliyar mota ta Alfarma Fara tas ta shiga Shima Nawwar yazo ya shiga bayan an bude Masa ya hakimce tare da zaro dankareriyar wayarsa Yana latsawa, Driver a hankali yaja Suka tafi zuwa katafaren Mansion dinsu na gani na fada Wai aljannar duniya gate din ma Sai dai a danna remote ya bude ana shiga zai maida Kansa ya rufe iya kudin gate yaci ace anyi katon gida guda,parking space motocin Ogane Dana Sabreen gasu nan,Fitowa tayi shi Kam sai da ya Gama yangarsa ya fito Suka karasa bakin kofa zasu shiga Sabreen ta fada ciki Kawai Shi kuwa Nawwar ka rantse shine Amaryar Addua ya tsaya ya dinga surfawa sannan ya shiga da kafar dama tare da yin Sallama , Sabreen ta kalleshi tare da tabe baki tace Wai dama har yanzu ana wannan abin,bai ce mata kala ba ta juya ta haura sama domin tana ta faman kallon gidan yanda ya tsaru sai Santi takeyi komai yaji an narka dukiya,Dakinta ta zaba dama na Ogan kana ganin part dinsa kasan na musamman ne komai Silver da palonsa na musamman ne,Sabreen wanka ta shiga tayi ta fito ta shirya sosai ta shafa turaruka masu tsadar gaske ta saka rigar bacci maroon me kyau,Sabreen Kyakyawa ce wankan tarwada ga hanci gata Yar tsila ce bata da jiki siririya da ita chas da ita sai dai bata da nono Allah ya halicceta nononta kanana ne karshe domin basu fi girman lemon tsami ba da kadan tafi me irgan dangi sai katon Nipples,a saman bed dinta ta kwanta tana ta Jin yunwa,Nawwar ma wanka yayi ya saka boxers dan guntu dama shi baya bacci da riga sai ya kure ac ya Shige bargo wannan dabi’arsa ce.

     Har ya kwanta yaji shima yunwa yake ji sai ya tuna nasihar iyayensa musamman Baffa mahaifinsa me share Masa hawaye akan ya sauke hakkinsa da Allah ya Dora Masa shine farin cikinsa shi kadai zai masa ya tabbatar da ya dauke shi uba,maminsa  ya tuna yanda take kaunar Sabreen a rayuwa haka ya mike da sauri ya zura Jallabiyya a ransa yace da yayi tunanin sai Papa sunzo sun nuna Masa Hanya amma hakan ai ya musu rashin kunya, Nan take yayiwa driver waya ya lissafa Masa kayan makulashen da zai siyo da Kuma address na inda zai siyo masa,ai kuwa ba afi 20mnt ba ya kawo Leda me kyau cike da kayan ci da sha,Nawwar ya karba sannan ya nufi bedroom din Sabreen, Knocking ya mata dake yunwa ta hanata bacci ta mike da sauri tare da bude kofa,Kallonta yayi sama da kasa yaga ba komai a kirjin sai Yan abu kubul kubul,Idonsa ya dauke ya shiga ciki Sabreen ta turo baki gaba tana cewa me zaka min a daki nifa tsoron maza nake gaskiya,yasan tsagera ce rainon turai karya take Kawai Wai shi za ayiwa kisisina,bai kulata ba tace Nifa bana bukatarka Malam ka tashi ka bar min dakina ba Yar iska bace ni, Murmushi yayi kadan dan baida Wasa ko kadan azabar gadararsa kadai ta isheka,Kamar bai jita ba ya zauna a gefen bed Yana Danna wayarsa Yana cewa a hankali wannan boobs din me zan shafa ,Sabreen tace au dani kake kenan ni kake zagi,yace tsohuwar wakace tasu Sa’adu bori
Ni kinji nace baki da nono gasu nan manya

  Sabreen tace wlh bazan taba yafewa ba kaci min fuska, bai ma kulata ba ya bude namansa yaci abinda zai iya yasha Madara ya koshi,itama bata kulashi ba ta hau ci yanda ta koshi sannan ta tattara sauran ta Kai kitchen tasa a fridge tayi brush ta fito ta fada saman bed,Nawwar ya kalleta yace ya Kika kwanta,me Zan maka Kuma? ta tambaya,yace au baza muyi ba yau? me? Auren mana,wata Yar budurwar dariya ta saki tace dake ni zanzo na afka maka ka dade baka ci ba Kuwa,Baki ya rufe da sauri yace ke kunya babu irin wannan kalamai a first Night,tace to Kuma to kuma to Kuma ni ahhh…ta sake juya baya,baki ya tabe ya zare jallabiyyarsa ya haura saman bed yace karki raina min hankali Papa ne yace ayi shi zai dinga Jin dadin ba Ni ba,dariya ta kwacewa Sabreen tace Allah ko,yace to ni bana so feeling ma ban taba Yi ba,Sabreen ta zaci Wasa yake ko fada yake Kawai dan yaji dadin bakinsa,ai kuwa jikinta ya matsa sosai tare da rungumeta shi dai baiji ya motsa ba Babu abinda ya harba,Bai taba mu’amula da mace ba bare ma ya sani,ya Fara shafata taki juyowa ta juya Masa baya tuni Sabreen ta lumshe Ido tana Jin wani dadi a hankali ya gangaro da hannunsa saman kirjinta yace Allah da baiwa Abu maka maka Haka,Sabreen wani bakin ciki ya cika Mata zuciya cike da masifa tace ae haka Allah ya yini,Nawwar nan take yace Alhmdllh wlh ki dinga godewa Allah kullum ya Miki baiwa  irinku baku da yawa a duniya ku unique ne abu yan cukul haka gwanin birgewa sunansa braziyya huta dan taku bature ya daina kera bra

  Sabreen bacin rai ya sake kasheta amma tana Jin dadi yanda yake bin sassan jikinta da salo,Nishi takeyi kawai shi Kuwa ko motsi abarsa bata yi ba yace a ransa bani da lafiya na tabbata,sai da Sabreen ta gaza hakuri ta juyo ta damki dick dinsa ko kunya sai da ta Fara Masa Wasa da ita sannan yaji ta mike sosai yaji dadi Yana ta godiya ga Allah Kar yaji kunya a gaban yarinya,Suna ta murza juna sosai Sabreen kasan ta Saba dama gashi an bata magungunan gargajiyar Taki Sha tace kazanta baza ta Sha maganin Mata ba ita ai ba son mijin take ba idan ma yaji ba virgin bace shi ya jiyo matsalarsa tafi so ma ya saketa, ai Kuwa Nawwar sosai yake Jin dadinsa suna murza juna amma duk da haka yaki Mata kiss kyankyamin bakinta yake gata neat da tsafta ta gaske Amma dan iyayi Wai bazai yiwa kowa kiss ba sai wacce yake so da kauna Kuma gashi zai shiga Headquarter, harda wani lallabata tana kokarin cafkar bakinsa sai ya wayance ya matsar da Kansa ita Kuma ta gama haukace Masa jira Kawai take ya Fara,ai Kuwa harda cewa ki nutsu Baby a hankali Zan Miki bazan Miki da zafi ba nasan ke virgin ce bazan baki kuka ba kinji,Sabreen ji take Kamar taci babu ta matsu ya Fara ya tsaya Yana wani bazai Mata da zafi ba,
Nawwar dai matarsa virgin harda lallabawa sai kace munafuki idan yayi Kamar zai shiga sai ya fasa Sabreen har dukan jikin bango takeyi sabo da dadi, gashi ta jike sosai da sosai da yaji discharge din yaji wani kyankyami yace a ransa Nan Zan tafi yanzu cikin cabalbali,

   Abinda Sabreen ta kasa fahimta Nawwar bashi da sha’awa da yawa badan ma ta Masa Wasa da yawa ba ko magana bazaiyi ba shi yasa ya kasa mancewa da komai ya kasa susucewa ya zauce ya kasa gaba daya,Yana cikin hankalinsa shi yasa yake ma iya bata lokacin,a hankali yake kokarin shigarta amma yaji sulub ya wuce zurum,dadin da yake ji ne ya hanashi magana sai da kyar ya iya furta ahhhh….da…di….naji…Su…bul…na wuce…..arshshshs…ita kuwa Sabreen gaba daya ihu takeyi tana Kiran Dadi aci gaba,harda cewa ayi Mata da karfi,ai Kuwa Nawwar minti kadan ya kawo Wanda ita Sabreen ko rabin ma Fara Jin Dadi batayi ba bare ta kawo, Jikinsa ya janye da sauri maimakon saka Albarka da I love you Sai tsintar muryarsa tayi Yana furta Allah ya isa…Allah ya Isa…Allah ya Isa Yar iska Karuwa kin bari na shiga kazanta shaddar kasuwa,kinyi disvirgin dina,na dade Ina Kare mutunci na Ina tattalin kaina wa matata ta sunna an hadani dake duk maza sun gama dake Allah ya saka min,Sabreen zatayi magana yaja pillow din Kan bed din ya kwada Mata a kanta da karfi yace Gongoni,abin ya Miki yawa gaki no breast gaki a rarake kina min rashin kunya sai na ballaki ya maida kayansa ya fice daga dakin tare da bugo Mata kofa Kamar zai ballata

   Sabreen ta tsaya sororo tace Kan bala’i kaga mutum ya Gama Jin dadinsa zai Raina min wayo mikewa tayi taje tayi wanka sosai ta dawo tana mugun sha’awar Nawwar ya iya romance amma bai iya dadewa ba Yana sex ita Kam ko Dan haka Indai zaina tabata zata hakura ta zauna mutu ka raba ita taga gidan aure,Nan take ta jawo magani ta balla ta Sha Wanda zai wanke mararta sperm dinsa da ya sa Mata ya fice,Handbag dinta ta Bude ta zaro wata Yar karamar kwalabar giya ta shanye ta jefa kwalabar a jaka,ta dakko wani kullun cocaine ta zuba a saman drower ta jikin bed ta shaka tana ta faman shakar abinta saida ta shaketa tas a hanci nan take idonta ya Kara yayi jajir ta Fara layi da tangadi tana maye ta rufe hanbag din ta fada saman bed sai bacci me nauyi ya kwasheta.
Nawwar kuwa bayan yayi wanka ya tsarkake jikinsa,Nafeela yayi sosai sabo da kasa bacci yayi sabo da bacin rai sai bacci barawo sabo da gajiyar biki a saman Sallaya baccin yayi gaba da shi.

    Washe gari da safe Ango sai 9am ya farka daga bacci lokacin yaji kamshi kala kala Yana tashi a gidan gana abinci gana room freshner dana turaren wuta irin na shuwa domin Nawwar su Shuwa ne,tashi yayi  a dakinsa ko Ina an gyara an wanke toilet kal kal tana kyalli wanka ya shiga ya Dade kafin ya fito Yana Fitowa ya iske Sabreen tana gyara bed din har ta Gama a ranta tace ba sabo da Kai nakeyi ba Bananarka nake yiwa, bautar Banana zanyi yanzu bata aure ba,tana gamawa tace Ina kwana wani kallon ballagaza ya watsa Mata yaja Tsaki yaci gaba da uzurinsa,a hankali ta karaso gabansa tace Zan iya tayaka tare da dora hannunta a kirjinsa wani saukar mari taji me gigita Dan Adam ta zaci Nawwar wani lakwa lakwa ne,kafin kace me Idonsa yayi ja Yana huci yace duk ranar da Kika Kara gigin tabani wlh na lahira sai ya fiki nishadi banza ballagaza,Sabreen taji ciwo domin tana da aji sosai da Saurayinta Dan kasar Italy Lorenzo  dashi Kawai take sex,haushi taji ta fice Kawai ta koma dakinta ta  ta jawo Kwalabar giyarta Votka highway ta kwankwada ta shaki cocaine dinta,ta kwaso wasu kwayoyi na maye sunfi goma ta watsa a bakinta ta Kora da ruwa ta manta ta Dora girki ta fada saman bed bacci me mugun karfin ya kwasheta,Yana cikin shiri yaji ihun Yan aiki suna wuta wuta girki har ya kone gas ta Kama Wanda gaba Daya kitchen din ya Kama da wuta ta gaske,da gudu ya sakko sanye cikin 3qtr arsh da farar t-shirt waya Kawai yayi sauri ya Kira Yan kwana kwana,kafin suzo ma’aikatan gidan da makwafta an kawo agaji ana ta kokarin kashe wutar,Nan take ya Kira Papa ya sanar masa yaga Sabreen Shuru bata fito ba duk ihun da akeyi dakinta ya koma da sauri ya sameta a saman gado tana ta shakar bacci,mamaki ya kamashi yanzu yanzu ta bar dakinsa amma har tayi baci,ke…ke..ke…ya furta Shuru inda kasan gawa ya sake bubbuga gadon duf Hannu yasa ya dagata Shuru a hankali ta Dan bude idonta ta lumshe ta koma baccinta tashin duniya taki tashi har Yan kwana kwana sunzo ma sun kashe wutar kitchen dai ya kone kurmus,Mama tace Oh Allah ya takaita wahala,Nawwar ya fito yace Mama kuzo kuga Sabreen irin baccin da takeyi ban sani ba ko ta mutu ne,Mama da Papa suka ruga cikin dakinta,Suma yin duniya sunyi ko motsi ko ta Bude Ido sai ta lumshe,Mama cikin mantuwa tace Ni Kam papan Sabreen ko cocaine dinne ta Sha yau,da sauri Nawwar ya kalleta,Papa ya kyaftawa Mama Ido nan take Mama ta canja zancen tana wayancewa ai nufina sai kace me shaye shaye cocaine Naga a turai itace ke sa Haka,Papa yace no Sabreen bata Shan komai Suka canja zancen,Nawwar tunani ya shiga sai Kuma Kawai ya basar bayan komai ya lafa a ranar ya Kira masu aikin gini Suka rushe kitchen din ba garen da yaci wuta akayi sabo cikin kwana uku aka Gama komai aka gyara ka rantse ba ayi gobara ba ko daya,daga ranar Kuma Nawwar ya hana Sabreen girki yasa Mami ta samo Masa dattijuwa Uwale da Ladidi me aiki dama akwai maza masu kula da compound etc,Daya ita zata dinga shara da mopping da duk wani tsafta,Uwale ta kware a girki iri iri itace me abinci Kawai.

    Waye Nawwar da Sabreen.

 

Sabuwar Number ta
08061929616

 

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼

LITTAFIN KYAUTA NE

                6-10

Official

By
AsmaBaffa

08061929616 sabuwar Number ta fans

LITTAFAN DANA RUBUTA SUNE

CIRANIN AMANA
MA’AIKACIYAR GOMNATI
KASUWANCINA
GASKIYA CE
KAMARSU CE DAYA
DUK INDA TA FADI
ME MAGANI
TUBABBIYA
HADIN KAI
JIN DADI SABO
MAFARKIN FARIDA
WARE BAIKO
AUREN MU

    NA KUDI SUNE

RASHIN SA’A
TA GYARU
ADDUAR KAWA
YAR KWANGILA
GIDAN GWAURO
DANGIN RABI
DUNIYATA AMNAH
JIKAR MAGUZAWA
BABU KAUNA.

Page naki ne
MRS CHIEF

    NAWWAR  SULAIMAN RAJ shine cikakken sunansa asalin Shuwa ne,Sulaiman Raj iyayensu   su biyar Suka haifa Sulaiman shine na farko sai kaninsa Yusuf Raj,  Sunusi Raj,Fatima wacce ake Kira da Binta sai Autarsu Rukayya,Allah yasa suna da wadata irin ta da suna da arzikin dabbobi da noma,sun taso cikin gata amma basu Yi ilimin boko ba sai na addini Kawai,sun girma sun Kai shekaru 27 lokacin tuni an aurar da Binta da Rukayya suna auren masu kudin gaske Yan kasuwa a cikin garin maiduguri,mazan Kuma da girmansu Suka koyi karatun hausa da rubutu harda turanci suna dan iya karanta wani abin sabo da Business da sukeyi, gaba daya mazan Rana Daya aka daura musu aure irin na gata Kuma cikin family aka zabo musu matayensu Sulaiman aka hada shi aure da Yar uwarsu Salma Mami kenan wacce ke da yara biyar Nawwar shine na farko,Sultana,Nasira,Hamra sai Autansu Nawaf suna ce Masa Autan Mami, daga baya bayan Nawwar ya gama degree na farko sai ya karo Amaryarsa itama Yar dangi shuwa ce dukkansu jininsu daya Safarau suna ce Ummin Haidar, tana da Yara biyu Haidar dan 8yrs sai Ahmad 5yrs, Yusuf Papa kanin Baffa kuwa aka aura Masa Mariya Mama kenan Wanda yarsu daya tal Sabreen Allah kuma bai sa ya Kara aure ba har Suka manyanta sai Sunusi aka hadashi da matarsa Zuwaira wanda shi baiyi tsawon rai ba Allah ya masa rasuwa wanda matarsa ko haihuwa bata yi ba, daga Baffa sai Papa sai Kuma kannensu da suke gidan Aurensu Binta da Rukayya, gaba Daya sai kasuwanci yasa Sulaiman Baffa ya tattara da matarsa Suka koma can kudu garin Inyamurai da Zama Onitcha inda take bakin ruwa a Anambra state shekara daya matarsa Salma ta haifo danta Najimiji katon gaske kyakyawa na nunawa sabo da su din jinin kyau ne,ranar suna yaro yaci suna Nawwar, Yusuf lokacin matarsa tana da tsohon ciki bayan watanni kadan ta haifo yarta mace zankadediya taci suna Sabreen, Bayan Mahaifinsu ya rasu, ganin haka Sulaiman ya dakko Mahaifiyarsu da suke Kira Iyamami ya dawo da ita gidansa nan Onitcha suna zaman su lafiya.

  Nawwar kuwa tun Yana yaro Baffa ya koya Masa kasuwanci ya dorashi akan harkar sosai har ya tara dunbin dukiya da tarin kadarori.

Bayan an raba gadon Sunusi Wanda ya rasu papa gaba daya ya handame dukiya har ta Kannensa mata yace zai dinga juyawa,shi yasa dukiyar shi sai taki albarka wannan yasa ran Yusuf ya baci bakin ciki ya kamashi ya tura Yan Daba har gida Suka yiwa Baffa fashin milliyoyin kudi babu Wanda ya sani ya ci gaba da bushasharsa,Babarsu tayi bakin ciki amma bata San danta bane yayiwa dan Uwansa turen yan fashi ba,Yusuf sai kukan karya ya samu dukiya ya tattara duka yaci gaba da juyawa Yana samun kudi a ciki yake biyawa Sabreen  kudin makaranta da komai nata bayan Baffa shi ke masa komai ,Iyamami bata San komai ba ganin danta Namiji Daya Yana da kudi na fitar hankali duk da Yusuf shima yana da nasa rufin asirinsa sai tafi tausayin Yusuf ya koma dan gwal a wajenta sai abinda yace,duk abinda yace shine dai dai part dinta guda a gidan,sai Yusuf shima Baffa a gidansa ya warewa dan Uwansa part guda shi da matarsa Mama,Arzikin dai baya ci gaba kullum sai karewa suke,ganin haka tun Sabreen tana primary ya hada milliyoyin kudi ya kaita Italy tare da matarsa Zuwaira Mama ya kaisu can Kan ta kula da Sabreen ta samu Ilimi me kyau zai dinga zuwa musu ziyara,bayan sun tafi shi Kuma Nawwar a nan kasar can maiduguri aka maida shi wajen Rukayya can yayi makarantar secondary sabo da ya samu tarbiyya da ilimin addini tunda arewa ba Kamar kudu ba.

    Har Nawwar ya gama Secondary Sabreen tuni ma a Italy ta dora da degree lokacin Mama ta dawo Nigeria shi Kuma Yusuf ya siyar da wani katon gidan Baffa a Abuja million dari a ciki yake turawa Sabreen kudi na hauka Baffa bai sani ba sam,Sabreen kuwa bata da aiki sai shaye shaye makarantar ma da kyar take zuwa tana gidan Saurayinta Lorenzo sune shekewa.
A wajensa ta koyi shaye shaye,sai club sai wajen Lorenzo tana sonsa shi yasa ta bashi kanta yake lalata da ita.
Shi kuwa Nawwar da bai San komai ba akan Sabreen sai Allah ya dinga hada shi da turawa masu kudi Suka Fara aiki a kamfanunuwa daban daban ya Fara samun mahaukatan kudade na shigo da Kaya da fitarwa ta fannin jirgin ruwa,Yana gamawa ya dora da masters yana Kuma Harkar business Allah ya sa Masa albarka,abokinsa kwaya daya ne dan gidan wani Sanata,guy ne hadadde shima dan masu dashi shima a kudu suke da Zama tare sukayi Secondary Suka tafi Uk tare Kuma amma shi Khaleel  bai dora da masters ba babansa ya sama Masa aiki a NNPC,ya dawo gida Nigeria ya auri matarsa Sufia.

    Alhaji Yusuf sun San komai abinda yarsu ke aikatawa na shaye shaye da bin saurayinta da sauran abubuwa marasa kyau sai Alhaji Yusuf Wanda Nawwar suke Kira da Papa yaje wajen Iyamami tare da matarsa Zuwaira yace tunda kowa yasan Sabreen ta lalace Babu me iya auranta a haka Kawai a hadata aure da dan uwanta Nawwar nasan Nawwar bazai ki jininsa ba,abin yayiwa Kaka Iyamami dadi a ranta tace ka kawo shawara ai tunda ya kusa dawowa sai a fara Shirin aure,Nawwar shi kuwa sai da ya kafu ya Zama me kudi na kirki ya Blbude kamfanunuwansa a nan Nigeria can Onitcha da wasu state sannan ya dawo ba zato Mami da Baffa sai ganinsa suka yi babban abokinsa Khaleel ya dakko shi,abinda ma basu sani ba Nawwar ya mallaki gidaje da abubuwa da dama a nan Nigeria Maminsa da Baffansa sun sani su, sai Murna su Papa sukeyi lokacin Sabreen taki dawowa rabonta da Nawwar tun suna Yara,bayan Nawwar ya cika wata Daya da dawowa ya Fara zuwa Office Yana ta kasuwanci gidansa da ake kera Masa Wanda zai zauna da matarsa idan yayi aure wannan na musamman ne,Papa hankalinsa ya tashi ganin Nawwar ya Zama me kudi shi Kuma Wanda ya handame sun kare ga Baffa dan Uwansa arziki sai abinda yayi gaba duk da kuwa irin zaluntarsa da yake yi yana siyar Masa da kadara ba tare da ya sani ba,sai ya dage da son lallai Sabreen ko tana so ko bata sai ta auri Nawwar ta nan zai samu ya mallake dukiyar Nawwar, Haka ya Kira Sabreen Yana masifa yace wlh idan baki dawo gida Nigeria ba ban yafe Miki ba, Mama zaune take kusa da Papa tace ka dinga binta a hankali ita kadai ce garemu,Papa Yana fada yace to kina ganin ni naki yin arziki gaba daya kamar bakin uwa duk gani a tsiyace kina gani dan uwana Sunusi uwar mu daya u abanmu daya yazo yayi kudi ni kuwa na roka na roka Shuru,akan haka fa ganin lokacin Sunusi har ya kusa fin Sulaiman kudi hakan yasa na tura aka kashe Sunusu ya bar duniya,da Sauri Mama ta rufe masa baki tana furta ka rufa mana asiri Kar wani yaji tunda ba Wanda ya sani to muyi shuru, yace to nayi shuru,Sabreen masifar papa yasa ba shiri ta tattara ta dawo,Papa da Kansa ya dakkota a airport,tana shigowa part din Mami a Palo ta iske Nawwar Yana dining Yana cin abinci
Mami tana ta zuba Masa surutu,dake Allah yayi ba me son magana bane Kuma shi bai fiye fara’a ba ga kafirin Isa da mallaka da son girma sai ya Mata shuru sai jefi jefi yake furta uhm hakane, har Sabreen ta kwala sallama ta shigo ta Sha tsadaddijar gown golden ga takalmi da Haka tayi kyau matuka,Mami ko  murna bata yi da dawowarta ba ,Nawwar ko kallonta baiyi ba yaci gaba da uzurinsa itama bata kulashi ba sai da Mami tace ga yayanki Nawwar ku gaisa,sai lokacin tace Ina yini ta Kara gaba bai ko amsawa.

    Itama sai bayan ta cika sati biyu da dawowa sannan Papa ya kirata ya sanar Mata cewar ya hadata aure da Nawwar ita Kuma Saurayinta Dan Italy take so Lorenzo,Zata Yi Musu papa ya dakatar da ita yace wlh idan baki yarda da auren nan ba sai na tsine Miki muna so muci arziki kina hauka kudi ne fa da shi kina gani arzikina ya Kare shi yake mana komai yanzu ci Sha sutura idan Kika aure shi ai dukiyar ma zai mallaka Mana wata Kuma mun samu damar Shiga jikinsa tunda shi Sulaiman busy ya Masa yawa, Mama tace ana Neman arziki kina hauka idan kika aure shi ai kinyi dace, Sabreen ba yanda ta iya haka ta amince Kawai,sannan Baffa ya samu Nawwar har dakinsa ya zauna yace Nawwar magana nake so muyi Jin haka Nawwar ya gyara zama sabo da shi mutum ne me biyayya, sune Suka kula da shi Suka dauki nauyinsa har ya zama abinda ya zama yanzu,Baffa yace dan Allah na rokeka Nawwar ka auri ‘yata Sabreen sabo da Kaine kadai na yarda zaka riketa da Amana ko bayan ba raina dan Allah karka ce a’a ka amsa min,Murmushi Nawwar yayi yace ni ai bance bana son Sabreen ba na amince Baffa bani da abinda zan biya ku iyayena,sannan na gama gina gidana na gama komai sanda kuka shirya ayi bikin,Yusuf Papa yana gefe a zaune shima ya dinga murna yace an gama dan albarka Allah ya baku zaman lafiya Kamar gaske bayan a ransa yana ta saka tsiyar da zai hadawa Nawwar ya gaje wannan kudin nasa da ya tara.

   Baffa tunda ya auri Amaryarsa Ummin Haidar gaba daya ya tsani uwar gidansa Mami haka su Iyamami ma Suka tsani Mami basa sonta kullum sai zagi da cin mutunci,duk abinda danta yayi to ita zasu Zo su zage tasss bata da iko tayi magana Baffa sai ya sake ta gaba daya igiyar auren Saura daya jal,bai bata kwananta sai dai ranar girkinta tayi girki ta Kai Masa part dinsa amma Kuma Ummin Haidar ce zata kwana da miji,tun Mami na zuwa Yana wulakantata ya koreta har yace ta daina zuwa Masa da dare,a gidan daga ita sai yaranta su Nawwar da su take rayuwa,Abu na gaba gaba ma abinci ya daina zuba Mata a part dinta ganin haka Nawwar ya koma siyen komai a gidan na abinci Watarana ma har bangaren Iyamami da Papa, basa kaunar Mami ko kadan a gidan,Ko bata je wajen Baffa ba idan yaga dama har bangarenta zai Zo ya zazzageta ya fita,tayi kuka har ta Saba ma da rayuwar.

   Bikin su Nawwar wata daya kacal aka saka sabo da gaggawa nan da nan biki yazo ba wani shagali Kawai aure za a daura a Kai Amarya cewar Sabreen tunda ba auren soyayya bane ana gobe daurin aure Yan Uwa da abokan arzuka sun ciga gida, ga kawayen Amarya sai Nawwar Wanda bai kaunar auren Sabreen baya sonta Sam haka suka raba Iv,Hajiya Binta da Rukayya kannen su Papa sun iso da yaransu samari wasu Kamar Nawwar wasu Kuma kasa da haka,akwai ma Mus’ab babban dan Binta ya girmi Nawwar,Washe gari aka daura auren Sabreen Yusuf Raj da Nawwar Sulaiman Raj Kan sadaki dubu dari, kudi dama ya basu da kansu Suka je kazar waje suka hada lefe, bayan Sallar Isha Papa da Mama suka Kira Ango da Amarya,Baffa,Mami,Ummin Haidar suna gefe Papa ya fara Nasiha me shiga jiki kamar gaske har zuciya sannan Suka ce su tashi su tafi shine Suka tafi gidan aurensu yayin da Ango ya dandana Amarya yaji ba kanta.

     Ci Gaban Labari

      Karasawa nayi a nutse Ina zuwa nayi sallama ya amsa,nace Ina yini ya amsa min Yana kallona yana zuba Murmushi ni dai daga haka bance komai ba,da Kansa naji ya fara magana yace Rabi na dago da kaina a hankali na maida kaina kasa Ina Wasa da yatsuna yace ba Wasa ne ya kawo Ni ba,kamar yanda na fada Miki sunana a farko to hakane Ina da mace guda Daya da yarana uku ,da gaske nakeyi wallahi harga Allah sonki nakeyi da aure bada Wasa ba,Amma bance sai kin Soni yanzu ba Sanda Kika ji kina so na sai ayi komai,nace to kawai,yace Ina Harkar shigo da Kaya da zannuwan gado daga kasashen waje Zan dinka  baki bedsheet kamar guda ashirin zuwa sama ki dinga Kara ribarki kina siyarwa Kinga kin samu Sana’a ko tunda naga da shekarunki,Mamakinsa ya kamani na zaci karya ne ashe da gaske yake haka Muka rabu,sati Daya ya sake dawowa Allah bai sa Yan gidanmu sun San me kudine ke zuwa wajena ba har sai da Muka shaku sosai na fada son Alhaji Kutama,muka tsunduma a soyayya daga nan ya Fara min Wasa da kudi a haka ma Ina kin karba,har dai yace zaizo ya gaisa da iyayena,wani zuwa na fadawa Gwaggo Saurayina zaizo ya gaishe su sai dariya suke min tunannsu talaka ne Yana zuwa Gaji ta leka taga irin motarsa ta koma gida tace jama’a kuzo kusha kallon Saurayin Rabi,dukkan matan gidan Suka leka waje abin ya tsorata su Mairo tace tab ko mu da mukayi ilimi bamu samu irin wannan Saurayin ba ko me lifan bamu da shi sai Rabi wlh da sake,Dagaci ya gigice yace Kar Wanda ya damu Kansa Rabi baza ta aure shi ba Amma a kyale shi muyi amfani da damar mu sai mu samu kudi,Haka ya lallaba su Basu nuna min komai ba na Masa iso har ciki Suka gaisa sun Sha Alheri na kudi Dagaci ma dubu dari biyu ya bashi ya bawa su Gwaggo dubu ashirin ashirin,Gaji da Mairo dubu goma goma sannan yace za a kawo kayan abinci, a ranar ya siya min waya me tsada Ranar murna ta cika gida sai basu kulani ba Muka ci gaba da soyayya da Alhj Kutama ya dinga kashe min kudi kamar hauka kayan sawa masu tsada iri iri takalma jakankuna,mayafai etc,Dagaci ne ya kwace iPhone Dina ya siyar ya siya min Tekno keypad Yar dubu bakwai yace baza ki rike babbar waya ba, Haka kayan kwalliya duk su Mairo da Nawa suke amfani da turaruka,gashi ya Fara kawo min yadin gado Ina siyarwa iri iri a garin,Dan ma a Kauye muke ban waye ba tunda ni ba ilimi nayi ba iyakata primary a Jss1 Dagaci ya hanani zuwa,Dagaci ya fada Masa gaskiya cewar Ni Yar tsintuwa ce duk da haka Alhj Kutama yace yaji ya gani yana so, Haka Dagaci yace ya kamata Kutama ya turo da manya,ba Wasa ya turo manya Suka kawo kudin aure aka tsaida aure wata hudu.

    Abu Yana ta karasowa Ni Ina ta Shirin biki Kutama Kuma ya tafi Dubai business dinsa yace bazai dawo da wuri ba sai dai a daura aure baya nan idan an daura zai min visa na bishi kasar waje can Dubai Haka akayi magana da Dagaci.
Haka biki yazo komai ya turo danginsa tunda baida iyaye kanin babansa da sauran Suka Zo da yawa aka taru aka daura Aurena da Kutama akan sadaki dubu dari biyu,ga lefe an hada na gani na fada,to bayan an gama ba wani shagali akayi ba tunda bani da gata ba Wanda ke shiga lamarin auren nawa idan ba Dagaci ba,Ina jira muji me Ango zaice Muna waya kullum har sati daya da biki, Gwaggo tana zaune tare da Dagaci Ina dakina Basu San Ina Jin hirar tasu ba sun manta Ina dakina Kuma a jikin dakin Nawa suke,yace karku damu kanku Gwaggo na Gama daukan mataki malamin yace bazai taba Zama tare da ita ba kwana nan zamu ji labari me Dadi,Gwaggo ta rangada shewa tace Alhmdllh ai nafi so Gaji da Mairo ta suyi auren su Allah dai ya kawo musu Miji me kudi Wanda zamu huta cewar Dagaci, Ni dai bance komai ba Ina zaune a gida Ango Shuru Shuru tun Yana kirana har ya daina kirana idan na kirashi ma bazai daga ba,gashi a gari sai gulmata akeyi Ango yaki zuwa an daura aure har wata guda Shuru,kayan lefen Nawa ma duk su Mairo sun kwashe sai kadan Suka barmin,kullum nayi kuka har na gaji Addua nake Yi ba dare ba rana.

    Ango Nawwar da Amarya gaba suke da juna baya kulata bata kulashi komai na gyaran gidan masu aiki keyi da girki ma tunda ya hanata yi,kullum sai dai taci ta Sha taci uwar gayu tayi shaye shayenta ta kwanta bacci bata free kullum a make take cikin maye,tsabar shaye shaye muryarta har ta koma ta Yan maye a slow take magana tana lumshe idanu tana wani babbasarwa Watarana Kuma ita kadai zaka ga tana ciccijewa shi dai Ango aikinsa yake fita yana uzurinsa ko kararsa bata kaiwa harkarta take yi dama ita bata da kawaye a nan kasar rayuwarta takeyi kawarta guda daya ce Yar gidan wani Minister Jamila suna ce Mata Jamcy tare Suka lalace a Italy tare suka dawo kasar tare suke shaye shayensu asalima Jamcy ita dake bata Yi aure ba ita ke kawowa Sabreen kayan mayen a boye su zauna su Sha hira duk sirrin Sabreen Jamcy ta San komai,har kwanciyar aurensu first night ta bata labari yanda abin ya wakwana,Jamcy tace ashe duk kyan nan nasa da Izzarsa na banza ne ba lafiyayye bane,Sabreen tace dan wofi ma sai iya sarrafa mace da romance baya aiki,ga Banana katuwa tsayi da kauri kin ganta Kuwa Jamcy tab

    Nawwar yau sai bayan yayi Sallar Isha ya shugo gidansa,Sabreen tana zaune a Palo tana kora lemo ta zubawa lemon kwayoyin maye,harda mikewa ta dakko glass cup ta zubawa Nawwar ganin shi take tsiyaya tana Sha bai zaci da kwayoyin maye ba a ciki bai disga ta ba ya karba ya shanye sannan ya haura sama,abinka da ba a saba ba sai yaga dakin ya fara juyawa yana hajijiya da shi,kafin kace me ya fadi tim a kasa ya mike ya sake tangal tangal ya fada saman bed Idonsa ya rufe Kuma shi ba bacci yake ba Kuma ba Idonsa biyu ba bai san a Ina yake ba, a haka ya kwana ya yini idonsa a bude yana magana a hankali yana furta Mami Mamina na mutu ne ko a raye nake? a lahira nake ko a duniya nake ne.

   Sabreen bata ko kalli dakinsa ba kuma tasan bai taba shan komai ba,sai yamma likis taci wanka tare da haurawa sama ta ganshi a kwance shanana kamar gawa kuma idonsa a bude yana magana da kyar yana Kiran Mami,Sabreen ta sheke da dariya tana tafa hannaye,saman gadon ta haura ta samu kumatun Nawwar yana ji Yana gani ta kwada Masa Mari tasan baya hayyacinsa idan ya dawo dai dai bazai San ta mare shi ba,ai duka ta rufe shi da shi sannan ta sake kwada Masa mari,baya ko motsi ko mintsininsa akayi bazai ji ba,kayan jikinsa ta cire masa ta masa zigidir sai da ta gaji sannan tayi ficewarta ta barshi timbur a saman bed Yana sambatu,wayarsa ana ta Kira ba a daga ba

   Mami tana cikin masu kiransa taga danta ta kira kwana daya Shuru ba a daga ba Kuma bai biyota ba Kawai kasa daurewa tayi a daren ta shiga lafiyayyar motarta da kanta tayi driving zuwa gidan Nawwar, Sabreen tana dakinta a kwance tana latsa waya sallamar duniya tana Jin muryar Mami taki amsawa har sai da Mami ta gaji ta bude kofarta ta ganta tana danna waya,Mami ranta a bace tace amma Sabreen kina jina Ina sallama sai kace ba musulma ba,sai lokacin Sabreen tace banji ba Ina yini,sabo da bacin rai Mami bata ma amsa ba tayi gaba zuwa dakin Nawwar, ta kwankwansa Shuru haka ta kutsa ciki sai da ta tsorata ganin danta tsirara a kwance shanana yana surutai da gani kasan ba lafiya,da gudu ta karasa tana Nawwar tana girgiza shi,cikin maye ya furta waye…dan Allah a duniya nake ko na mutu? Mami kuka ta saki ta furta Maminka ce Nawwar me ya sameka? Ita Sabreen din bata da hankali ne? Nawwar dai ba ganewa yake ba tambaya Kawai yake na mutu ne ko Ina Ina duniya,da sauri ta nemo sutura ta saka Masa ta fita ta Kira masu gadi Suka taimaka aka sashi a mota sai asibiti,Sabreen tana ta dariya tana kallo ya window Samanta, ana zuwa asibiti likita yace ai kayan maye ne ko aka bashi ya Sha ko ya Sha bai taba sha ba, Nan take Mami tace Sabreen ce itace take shaye shaye naji labarin,wata Allura likita yayi Masa 15mnt sai ga Nawwar ya dawo hayyacinsa babu abinda ya tuna sai Sanda ya sha lemon da Sabreen ta bashi,sunan Mami ya kira, ta dinga murna tace Sannu Nawwar kalli kumatunka yayi ja Kamar an mareka dama gashi fari,yace ni ban sani ba muje gida salloli zanyi Naga kamar tunda na Sha lemon Sabreen banyi Sallah ba,Mami tace Allah ya saka maka ranar aka basu sallama.

   Yau Kuwa ya Sha bacci harda makara sai washe gari 12pm sannan ya iya bude Idonsa a hakan ma ya dade kafin ya fara ganin daidai ya mike yaje yayi wanka da Alwala ya fito Sallar asuba yayi da tsakar rana ya hada da azahar sannan ya fito Neman abinci,Sabreen tana kallonsa dariya ta kwace Mata, bai ko kulata ba yasan tabbas a lemo ta saka Masa wani abu abincinsa yaci ya koshi Ladidi me aiki tace ranka ya dade Ina yini yace yawwa barka da asuba an tashi lafiya,Ladidi tace ai Yamma tayi karfe daya na rana ma ta wuce,sai lokacin ya tuna.

    Sabo da baya shiga harkarta komai ma ta daina Yi a gidan in Banda bacci ba abinda tasa gaba, shima harkarsa yake Yi da Kansa yake gyara dakinsa, ganin shi yaki kulata har tsawon wata guda ta gaji ta Kira Mama,Mama daga Wayar tayi tana dagawa ta fashe da kuka,Mama gigicewa tayi ta saki Salati tare da furta na Shiga Uku Ni Zuwaira Sabreen lafiya dukanki yake? Sabreen cikin kuka tace Mama wlh bashi da lafiya baya iya saduwar aure sai ta Kara da sharri tace ai kullum Mama sai dai yayi min da yatsansa yanzu gashi dalilin haka na hadu da ciwon Mara kullum sai ciwon Mara,Mama ta dafe kirji tace kardai bata tashi? Sabreen tace inda kisan an jika Tsumma a ruwa Mama,firgita Mama tayi tace da sake,katon saurayi Kamar Nawwar ko ta babanki da yake dattijo ai tana aiki, to ya batun kudi baiyi yunkurin baki ajiyar takardun gidajensa da filaye ba ko wasu kadaran? Sabreen tace tab ai komi nasa na takardu babu a gidan nan mutumin nan a shirye yake,kin San Papa yace nayi kokari na binciko Masa takardun filaye da gidaje amma wallahi dakinsa ba komai sai takardun Office dinsa sabo da Haka tunda aka kawoni nake gyara Masa dakin sabo da na samo takardun Amma ko Daya,Mama tace bar shege dan iska idan nan gaba ba a samu komai ba sai kiyi Masa abinda zai sakeki mu huta,Sabreen tace an Gama Mama amma kuyi Maganar da Papa aji me zai ce a haka suka rabu.
Mama Kuwa Papa yana dawowa ko hutawa baiyi ba ta same shi da labarin yace tayi hakuri taci gaba da Zama haka Muga abinda Allah zaiyi ko za a samu takardun domin yanzu bani da komai a kasa kudadena babu kadarata Saura kadan.

   Mama yarta ta sake Kira a Karo na biyu,Sabreen tana dagawa tace yawwa munyi Maganar yace ki Kara hakuri dai a gani, sannan ni Wai baya ajiye makudan kudade ne a gidan? Sabreen tace Yana ajiyewa har da daloli ma kuwa,Amma Sabreen anyi sakarai Baki Fara dan ebowa a ciki ba ai bazai gane ba,mutumin nan Mama bashi da mutunci kullum Fuska a murtuke Kar nazo ya kamani Ni kaina Ina son daukan kudin amma Ina tsoro wlh,ke dalla shashasha sakarai in Zaki bude idonki ki bude idan kin ebo ai ko fili ma mallaka ni da ke karki fadawa Papa wannan daga Ni sai ke, Papa shi ta takardu yake yi muma muyi kokari mu samu rabon mu,Sabreen tace to dama kadan take jira tana so ta dinga kashe kudi tana siyen kayan mayenta masu tsada kudinta sun Kare kaf ga Papa complain yake Mata baida kudi,fada da cikawa suna gama Wayar ta mike tare da lallabawa sadaf sadaf har bedroom dinsa dama baya gida tana zuwa ta bude inda kayan sawarsa suke tasan a gefe guda akwai inda yake zube kudi,tana budewa ta gansu wannan karon da yawa bai Kai bank ba, rapa daya ta dauka na dollars ta duba a kudin Naira na Nigeria ta kwashe dubu dari uku lokaci guda ta fice da abinta tana Fitowa Mayafi ta yafa ta dauki key din motarta ta fice daga gidan ba tare da ya sani ba,banki ta wuce a direct ta Kai kudin nan harda zuba dalolin a dollar account dinta ta fito da dubu dari data rage,waya ta sake yi da kawarta cikin kankanin lokaci ta kawo Mata yar mitsilar cocaine da kayan mayensu masu karfi ta biya kudin Suka shiga shopping mall ta siyo giyarta ta fito.

    Jamila tace ya kamata kawata ki nemi Sana’a ki fara Kinga Zama haka bazai kaiki ba karki dogara da miji ki nemi aikin gomnati ko company,Kallonta Sabreen tayi tare da furta Jamcy kenan ni business nake so na Fara nasan zanyi ciniki idan na Fara siyar da su Coccaine,wiwi,kwayoyi,su codeine da sauransu,Jamcy tace wlh da Kuwa kin samu kudi kinga Yan wannan da nake siyarwa kalli katon mansion dina Dana kera,ki Fara wlh zaki samu kudi idan Kika Yi karfi sai mu Fara shigo da dawar nan Yar Cameroon wacce ake yin giya da ita kamfanin giya da tsada suke siyarwa Zaki hadu da manyan masu kudi,yanzu fa wannan shigo da dawar giyar ita masu kudinmu suke shiga Dan danan zaki ga mutum da tarin milliyoyin kudi to ya Fara mu’amula da kamfanin giya dare Daya ake kudi Kamar na yankan Kai,tafawa sukayi Sabreen tace Haka za ayi Zan sa mijina ya bani jari,Ae ko million Daya ya Baki ya Isa ki Fara da kadan Sabreen motarta tayiwa key tace bari na wuce gida Kar ya dawo bana gida,kowacce motarta ta ja ta Kama gabanta,ko da ta koma gida Ogan bai dawo ba.

     Bayan watanni ni Rabi Ina gida Alhj Kutama ya Aiko Yaronsa ya kawo min takarda, gabana ya fadi Ina shigowa gida na bude na karanta Kawai naga ya rubuta min Saki har uku lokaci guda,hawaye Suka zubo min na fashe da kuka na mike Ina Jan kafa da kyar na kaiwa Dagaci,yana karba ya duba sai naga Murmushi ya subuce masa sai Kuma ya hade rai yace haka Allah ya tsara sai ayi hakuri Allah ya kawo wani ko me yasar masai ne,kallon Dagaci nayi Kawai wasu hawayen masu dumi suka gangaro min na fita na koma dakina naci kuka na koshi,tun Ina damuwa har na hakura ba’a dade ba na hadu da wani manager na gidan Mai me kudi Yana mugun sona Amma ni Sam ba shi nake so ba nafi son Kutama,su Gwaggo bakin ciki Kamar su mutu sai masu kudine suke zuwa wajena su Kuwa yaransu talakawan ma basu zuwa..

   Yau Juma’a Ina gida sanye cikin vest da skert dina dan kanti brown me digon fari nayi kyau sai ga babbar Aminiyata Saratu taci wanka na gaske ta Zama gogaggiyar Yar gayu Yar birni sanye cikin rantsatsiyar Shadda Maroon jaka da takalmi komai me tsadar gaske,da murna na tashi na tareta nace Saratu kece Wai dan Allah? Gwaggo da sauran yan gida suka saki baki galala suna kallon Saratu  ta cakare,Gaji ce ta dawo daga kasuwa tace Wai Saratu ba dai kece da mota ba haka? Saratu tace wlh Allah ya nufa na siyi kwano,ke Kuwa wanne aiki Kika samu a kudu? tace ai kin San Onitcha bakin ruwa ne akwai business ba karya da naje can na Fara dan zamarwa wata Nkeci a restaurant Ina Mata wanke wanke da idona ya bude na gane yanda ake kasuwanci sai na Fara sana’a inje a bani takalma da jakankuna masu araha akan sari sai na dora ribata idan na siyar na Kai kudi na karbi wasu ana haka na Fara samun jarin kaina Ina Sara da kudina Allah ya sa min Albarka nazo na bude katon restaurant na zuba yara…Gwaggo ce ta katseta tace ke ki bari Dan Allah kice kinyi kudi,Saratu taci gaba da cewa gefe daya Kuma Ina ta kasuwancina a Haka yanzu na siyi katon gida na gani na fada ga mota na siya,Mairo tace cab kekam kin tsallake,Ina murna nace sai naji kamar na biki ki bani aiki a restaurant dinki ko nima ki min hanya,Saratu tace tashi muje dakinki mu zanta,su Gwaggo suka tabe baki,muna Shiga dakina Saratu tace bari na baki Address dina idan Zaki kawo min ziyara Watarana idan Kika je tashar da ake hawa motar Anambra zaki samu masu zuwa Onitcha ma idan kinje ki hau Napep ko taxi kice Odimgbe Street kina zuwa wajen ko wa Kika gani kice gidan Seraline za’a nuna Miki nice Seraline a can a haka ake kirana,nace uhmmm to zanzo Watarana na shakata Kinga yanda Kika hadu Kuwa Masha Allah haka Muka Sha hira na fita tare Muka dinga yawo a Kauye Muna ta labari cike da nishadi,tunda kaf garin sai kallon Saratu akeyi ana sha’awarta,dama Bata da uba ya rasu tun tana karama daga ita sai babarta sai kanin Babanta Wanda ke daukan nauyinsu ita Kuma babarta bata da kowa sai sai wata Yar uwarta da suke zaune tare,Saratu tana zama budurwa Kanin mahaifinta Kawu ya Mata wayo idan ya kaita dakinsa sai bata kwayoyi a cikin lemo ya bata ta shanye hankalinta ya fita daga jikinta sai yayi amfani da ita,Kuma idan ta dawo hayyacinta sai yace Indai ta fadawa wani sai ya kashe ta,kullum Yana mata haka wata da watanni ba Wanda ya sani Sai Katsam ciki ya bayyana a jikin Saratu,da Innarta ta matsa Mata da duka ta fada Mata abinda Kawunta ke Mata,Kawu Yana Jin asirinsa ya tonu ya hada kayansa ya gudu ya bar garin har yau ba a San inda yake ba,matarsa tana gidansu da yaranta hudu,Inna ganin ana ta cakaki a kauyen sai ta tura Saratu Lagos wajen wata Yar uwarsu Hajiya Kattime,a can Kuma sai waya Saratu ta bugowa Inna Wai cikinta ya zube shine sanadin barin kauyen Saratu.

  Yanzu Saratu itace take ci da mahaifiyarta tana turo musu da kudade,sanadin zuwan Saratu Onitcha daga tafiya Lagos wajen Yar uwarsu shikenan akaji ta koma Anambra ta samu aiki a can,Maman Saratu tana Jin dadi sosai komai tana turo da kudi ana bata shi yasa kullum cikin sawa Saratu Albarka take.
Washe gari cikin dare na sake fitowa wajen da muke Alwala jikin dakin Dagaci ne ina tsugune Ina Alwala naji Aunty Amarya tana sheka ihu kasancewar Dagaci yau a dakinta yake,tana furta….Zan mutu…kana haukatani….Ido na zaro na mike tsaye a fili na furta a’a wai me yake musu ne wannan wacce irin mugunta ce kullum sai ya zalunci matansa,ihu naji Aunty Amarya ta saki …Dagaci naji yace karki haihu kinfi min a haka…baki bude na harari dakin Dagaci nace sabo da Kai azzalumi ne akan bata haihuwa kake Mata mugunta gashi tana ta cewa zata mutu

    Muryar Aunty Amarya tana tashi ta sake yin wani nishi tana zaka halakani….ka barni haka…na tuba….zan mutu….wani gurnani naji tayi Wanda na gaza hakuri nayi Sauri na hau dukan kofar Ina cewa kayi hakuri Baba dan Allah ka kyaleta karka kasheta duk da cewar naga Gwaggo ranar nan bata mutu ba Watarana tun kana dukansu suna tashi to wataran mutuwar zasuyi,kofar na shiga duka da karfi Ina cewa wayyo jama’a ku fito ku kawo agaji wayyo zai kashe Aunty….Gwaggo ce kawai ta fito sauran yaran bacci yayi nisa,Gwaggo tana Fitowa tace laaaaa yanzu yau ma laben kike yi musu wannan wacce jarabar ‘ya ce ta dakko tabarya,butar dake hannuna na saki na gudu dakina na kulle sannan naji Dagaci da Aunty Amarya sun fito suna ta zage zage,Ni Kuwa tausayinsu nake ji a raina Dagaci zai kashe su kasancewar bani da kawaye a garin basa barina na shiga cikin jama’a bare nasan wani Abu na rayuwa.
Washe gari da safe Dagaci ya fito na dinga zuba Masa harara Ina Masa kallon azzalumi me dukan matansa Yana musu mugunta zai kashe su,ranar yini nayi Ina hararar Dagaci.

    Satin Saratu daya a Kauye ta koma,Ni Kuwa Ina zaune sai samari nakeyi masu kudi ban taba saurayi talaka ba,Gwaggo hakan Yana bakanta Mata rai har daki ta samu Aunty Amarya tace Amarya ki bani shawara mu San yanda zamuyi da Yarinyar Nan Rabi Nifa har ga Allah na gaji kina ga ta Hana yarana samun samari masu kudi kowa yazo Rabi Matukar Yarinyar nan bata bar gidan nan ba mu da ganin ci gaba sai dai in Muna Saduwar aure da Dagaci,Rabi ta sheke da dariya tace ai da kin dauki shawarata da tuni shegiyar ta bar gidan nan tunda dagaci shima ba kaunarta yake ba,Gwaggo tace Wai shawarar da Kika bani kwanaki? Kwarai kuwa,shewa sukayi tare da tafawa Gwaggo tace an gama,Shuru Shuru ni dai Ina ta Shan wahala ta iri iri a gidan har aka kwashe wata biyu yau Gwaggo girki ta sani ban sani ba Gaji ta faki idona bana kusa ta watsa min gishiri me mugun yawa a Miya sai da na gama an zubawa dagaci nasa ya baje ya balla ya Kai loma Daya bakinsa ai a gigice ya tofo tuwon waje yace wacece take so ta halaka ni a gidan nan? jikina ya hau rawa nan take na fara karkarwa Ina rabewa a bango,Gwaggo ta dandana miyar ihu ta saki da karfi,Aunty Amarya ta lasa itama tace Ashe da babbar makiyar mu muke zaune Zaki kashe mu

    Tuni na Fara kuka nace wallahi Allah gishirina dai dai na zub…saukar mari naji Dagaci ya hau jibgata Aunty Amarya ta Miko Masa wata Sanda ya dinga makamin tun Ina tsaye har na zube a kasa,Ina kuka har na daina motsi ma na kasa sai da ya gaji Dan Kansa sannan ya rabu dani,azaba tasa na kasa tashi a nan yashe tsakar gida har Suka Dora wani girkin ban tashi ba babu Kuma Wanda ya kulani sai da na samu sauki sannan na iya yunkurawa na tashi da kyar Ina daura zanina Daya kwance Ina sheshekar kuka na fada dakina zazzabi da ciwon Kai Suka lullubeni haka na kwana ko lekowa ban iya ba sabo da azabar zazzabi da ciwon kai, Sallah ma Sai da Isha tayi na lallaba na fito da rarrafe na dafa jikin banko naje nayi wanka da sabulun wanki dama Ni a gidan ba’a barina nayi wanka da sabulun me kamshi sai dai sabulun wanki ko omo ake bani a wulakance tunda na taso a haka na taso a hakan ma idan na tambaya sai an zageni anyi min gori sannan Dagaci ya bani da kyar.

    Bayan na fito nayi brush da Alwala duk da zazzabin Yana jikina haka na canja Kaya wankanku sabo da Ina da tsafta ni,Sallolina na rama a zaune sannan na fita wajen Gwaggo dake zaune a dakinta sallama nayi tasa yaranta gaba suna ta hira sun baje tsire suna ta ci itama Aunty Amarya ita da Dagaci suna cin nasu a dakinsa yau ita ke da girki,Gaji tace to mayya anji kamshi anzo dan a sammiki,Ko ma mene wannan tsiren haramiyarta ko barbade shegiya mayya haihuwar kwararo Yar shege cewar Gwaggo,Mairo tace dan Allah ku kyaleta haka ke dalla marar zuciya me za a baki? Na kalli Mairo a haka itace me sauki,nace abinci za a bani yunwa nake ji,Audu da Imrana Suka ce anzo gidan ubanmu sai cinye Mana abinci akeyi ki tafi gidan ubanki Mana ko uwarki data haifeki ta jefar ta baki,Ido na runtse sabo da bacin rai ga zazzabi na cina,Tsaki gaji ta ja tace muje ni na zuba Miki,Gwaggo tace ki kula a cikin miyar akwai nama karki manta ki sa Mata nama ko yanka daya,mikewa nayi bayan Gaji ta zuba min tuwon Dan kadan da Miya ta bani a wulakance ko almajiri baza ayi Masa haka ba,na saba da haka shi yasa na karba Kawai na koma dakina na cinye na Sha ruwa sannan na koma na kwanta bani da kudin siyen magani ko kwandala babu inda zanje Kuma a bani,haka Wasa Wasa na kwashe kwana hudu Ina zazzabi kullum a kwance nake yini,Ina wannan hali naji Gwaggo da Amarya sun leko dakin Gwaggo ta fasa ihu da kururuwa ta Fara wayyo jama’a ku kawo Mana a gaji,jama’a kuzo bala’i ya same mu mun shiga Uku yau ya zamuyi,mamaki ya kamani na bude idona da kyar kafin kace me Dagaci ya fado dakin mutane makwafta sun cika damkan a gidan ana tambaya lafiya,Aunty Amarya ma tace shike nan ta tona Mana asiri ta gama damu dama ance tsintacciyar mage bata mage,Dan tsuntuwa kwai masifa,Dagaci yace menene Wai tace Gwaggo dakko takarda ayi a gaban kowa ya gani, Gani mukayi Rabi kullum tana ta zazzabi da amai gashi duk ta  dashe tayi fari tas sai tofar da yawu takeyi,shine Gwaggo tace ita tana zargin ko Rabi cikine da ita Muka tafi chemist din garin nan muka Kira Tijjani Dafta yazo da abin gwaji Yana gwada fitsarinta yace ciki ne da Rabi nan take nace ban yarda ba yarinya kamila,sai ya zuki jininta a sirinji ya hau machine da wuri ya Kai asibitinsu na garin nan aka gwada har sau uku ciki ne da ita har na wata biyu,Gwaggo ta zaro takarda tare da mikawa Dagaci tace dazu Tijjani ya kawo idan Baku yarda ba a Kira Tijjani zaiyi bayani,Dagaci ya duba yaga tabbas Rabi Muhammad,makwafta sai aka Fara salati abinka da Kauye kinyi asara Rabi kin bata wayonki,kin cuci kanki wallahi baki kalli maraicinki ba sam Allah ya shirye ki,wasu na zagina haka Suka gama Suka tafi mamaki ya kasheni gaba daya na nemi zazzabin na rasa babu,Dagaci ne ya dakko wuka na mike tsaye da sauri abinka da me cuta Nan na kasa tsaiwa na zube kasa sharaf, Yace Dan ubanki wa ya Miki ciki? kuka na saki me tsuma zuciya nace wal..wal..hi bani… d..da ci…Mari ya hau kwada min ta ko Ina,yasa kafa yayi ball dani na bugu da jikin bangon dakinmu na fasa ihu me tsanani yaci gaba da dukana yace baza ki fada min wa ya Miki ba,na dage akan gaskiyata ni ban san kowa ba,sai da ya gaji da dukana sannan  yace na Baki sati ko ki fadi Wanda ya Miki ciki ko ki bar min gidana shegiya tsinanniya tambadaddiya,wacce Allah ya kwashe Mata Albarka azzaluma,Yar iska fasika,Ni dai kuka nake wiwi har ya gama ya fita a dakin,su gaji Suka shugo Suka duddugure min Kai,Gwaggo murna suke Kamar zasu kashe kansu ita da Aunty Amarya.

     Gani nayi Zan mutu a daki na lallaba Ina kuka na fice na nufi chemist din Bala banje ma Chemist din Tijjani ba,Bala ya ganni Ina kuka jikina duk rauni Yana jini,yace Rabi lafiya Kamar kinyi hatsari na sake rushewa da kuka na bawa Bala labarin komai Bala ya jinjina Kai yace Allah zai saka Miki Rabi kiyi hakuri kinji haka Allah ya kaddara Miki Haka ya wanke min raunin ya bani magunguna na dawo gida na balla na Sha,abinci ma Dagaci yace Kar a sake bani dole nake Shiga gari inda muke mutunci Ina rokon abinci a taimaka min,to gashi zance ya baza gari nayi cikin Shege duk inda na zaga sai zagina akeyi ana ci min mutunci,abincin ma kafin a bani sai an ci min mutunci a haka har sati ya zagayo,Ina idar da Sallar asuba lokacin na warke ma naji bugun kofa kamar za a ballata,Ina Budewa Dagaci yana min magana kasa kasa dan Allah Rabi nima ki yarda dani ki bani hadin Kai naji dadi,ko kina da cikin ba komai zanyi haka Indai zanji dadi, gida bai koshi ba a kaiwa dawa,harda lallabani sabo da Allah Rabi gani a gida ai gwara ni mu dinga Yi a boye sai na kaiki asibiti a zubar da cikin ki zauna a gidana kinji Rabi,idan ta Kama ma Sai na aure ki,Kallonsa nayi shekeke kawai,nace wlh baka Isa ba babu ni ba kai Allah ya kiyaye ni Kuma bani da ciki ehe,bazan taba yarda ba babu Wanda ya taba min wajen Iskanci na Kuma bazan yarda wani ya taba min wajen Iskanci na ba.

  Fusata Dagaci yayi yaji haushi naki yarda da shi sai ya dawo da masifarsa dan uwarki fada min waye yayi cikin eyeeee waye yayi cikin? nace wallahi kaji na rantse ban taba sanin wani da Namiji ba wallahi Allah ko Qur’ani ka bani zanyi Alwala na dafa ko Kuma ka kaini asibiti da kanka ka gani,Dagaci yace karya kike munafuka akanki kwandala bazan kashe ba wajen gwaji,maza kwaso kayanki ki bar min gida,hankalina ya tashi na durkusa har kasa Ina kuka nace dan Allah kayi hakuri idan na tafi Ina zanje bani da kowa ku kadai na sani Dan Allah…..tashi nace tun kafin na karyaki,kuka nake wiwi amma babu Wanda ya kulani ma,ganin baza su hakura ba na dakko ledar Yan tsummokara na,Ina Fitowa Gwaggo tace yo kya tafi tsaya a Sanmiki koko ki kurba ta gama dama koko yana tiriri tana min dariyar wulakanci ta Miko min a kofi karba nayi na kalli kokon na kalli Gwaggo na juye Mata kokon a kirjin gaba daya,ta kwalla uwar Kara ta Fadi tana birgima sabo da zafin Kokon nasan sai ya kone Mata kirji na fice da gudu,Yan gidan Suka Yi Kan Gwaggo ni kuwa Ina tafiya gudu gudu sauri sauri Allah yasa garin ba kowa kasancewar sassafe ne,Bala me chemist ne ya ganni ya fito yace Kudirar Allah Ina zuwa haka? nace ai ya koreni,Bala yace wannan wanne irin azzalumi ne yanzu to Ina Zaki je? nace Ina da kawa a Kudu can wajenta zanje,kina da kudin mota ne? Kai na girgiza Masa Ina goge kwallata nace bara zanyi a hanya,yace Allah sarki ya zaro dubu daya yace ga wannan ko ruwa kya Sha,Hannu biyu nasa na karba Ina ta godiya,yace ki tsare mutuncinki kinji Rabi karki bari a lalata Miki rayuwa Allah ya baki Miji na gari me share Miki hawaye.

   Idona ya kawo sabon hawaye muryata tana rawa nace Ameen ba komai Mahaifiyata ce ta jawo min da bata jefar dani ba da babu me wulakantani Ina fadar haka kuka me karfi ya kwace min Malam bala yace kiyi hakuri kinji ai kina da waya bani number dinki idan da wata matsala ki nemi layina kinji zan iya bakin kokarina bani da inda Zan ajiyeki Rabi Amma da kin zauna a gidana amma kin San gidana daki dayane ma,nace ba komai na karbi number Bala na shigar a karamar wayata shima na sa Masa tawa na juya da sauri na bar garin na shiga motar cikin birnin Kano inda zanyi bara na samu kudin zuwa wajen kawata Saratu dake Anambra Onitcha, ita Kuwa Gwaggo tana ta kururuwa Dagaci ya samo Zuma ya shafa Mata a kirjinta inda kokon ya kone Mata,tace da gani Rabi daga tsatson yahudawan larabawa ta fito Wanda basu da Imani.

SADAUKARWA NE GA DUK YARAN TSUNTUWA

A dinga sharhi please

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               11-15

Official

By
AsmaBaffa
08061929616

SADAUKARWA ZUWA GA DUK YARAN TSUNTUWA

 

Page naki ne
MARYAM T BALIYA

        Nawwar a gurguje ya fito cikin shiri yasha wankan wani danyen yadi milk shara shara,gashinsa yaci gyara na gogaggun matasa kamar wani bature Yana zuba kamshi,agogonsa me azabar tsada yake daurawa yana sakkowa daga steps wani Yaronsa ne ya fito Masa da Yar karamar jakarsa wacce ya shirya kayansa da sauran abin bukata ya wuce Masa da ita ya saka a boot din mota,Sabreen tana dining tana breakfast sanye cikin kayan bacci tana ganinsa ta dauke Kai Wai ita me aji, kallo ma bata isheshi ba,har yanzu bai duba inda ya ajiye kudinsa ba bare yasan ta ebi wasu ba,Zama yayi ya hadawa Kansa tea yana Sha Yana cin chips sai da ya koshi sannan ya dauki wayarsa yace na wuce Kano Ina da meeting a can har na 2weeks,shekeke ta kalleshi ko a dawo lafiya babu tace to Kawai ta mike tare da haurawa sama,baki Nawwar ya tabe ya daga Kiran wani abokinsa Khaleel suna waya Yana fada Masa ya tafi kano,fita yayi ya shiga mota ya kame a baya securities a mota uku suna take Masa baya,gidansu ya fara zuwa tare da yiwa Maminsa sallama sai yaje ya samu Papa Yana gida har dakinsa ya shiga bayan sun gaisa Mama tace kaga dana ga iya wanka ga kyau,Murmushi Nawwar yayi ba shiri,Papa yace ai Yar mu ta dace,Sumarsa Nawwar ya shafa sannan yace Papa dama Kano zanje Ina da meeting da wasu turawa sunzo daga Finland akan business dinmu zanyi sati biyu,Papa yace a’a to Allah ya bada sa’a ubangiji ya ida nufi,Mama ta furta Allah ya tsare hanya yace ameen ya mike yace na tafi sabo da jirgi ya musu sallama ya fito direct part din Iyamami ya nufa kakarsa kenan,zaune ya isketa a kujera ta tasa katuwar tv gaba tana kallo tana tauna goro,Dan Nema sai yau aka ga damar zuwar min dama nasan ni ba kaunata kake Yi ba sai kayi sati ban ganka ba auren ma bana Yi na sake ka,Murmushi Nawwar ya saki yace dama ni me zanyi da tsohuwa ga matata sabon jini dama sallama nazo na Miki zanje Kano Ina da wani meeting, Iyamami tace aikin kenan to Allah ya tsare na zaci da matarka zaka tafi ma,ai ba dadewa zanyi ba,to Allah ya bada abinda ake Nema yace ameen tare da zaro kudi da yawa ya bata yace ga kudin cefanenki tunda na bawa Amarya karki ce na zalunce ki,dariya ta dinga Yi tayi godiya ya wuce Suka wuce airport.

     Bangaren su Mama Kuwa Yana tafiya Papa yace bar shege ya gama tara Mana mu gaje dukiyar,wani ma yaji cewar Mama.
Nawwar yana zuwa Kano wani Yaronsa yazo da mota ya kaishi green palace hotel inda aka sauki turawan kuma a nan hotel din zasuyi meeting din kullum har a Gama,bai ko zauna ba kayansa Kawai ya ajiye yaje inda zasuyi meeting din dama shi ake jira,Yana zuwa suka Fara basu gama ba sai bayan Sallar Isha,wanka yayi da Sallah sannan ya zari motar da aka bar Masa ya fita dan zaga gari sanye cikin farar jallabiya me tsada.

   Rabi ina sauka a Kano ban San inda nake ba haka na samu wani lungu na fito da yagaggen Hijab dina ja,ya gama fatattakewa haka na saka nace Neman Sadaka yo ai sai anyi Kalar tausayi sosai a kasar nan basa ba da Sadaka sai anga mutum ya kusa mutuwa sabo da wahala,ni Rabi ina maganganuna ina canja kamanni nace gani jajir ai dole na Zama Yar dukununu na nemo gawayi a hanya da kyar na samu na dandaka da dutse na dan shafa kadan a fuskata Kamar me shafa powder nayi wani duhu,hakorana ma duk na goga musu bakin sukayi Kamar sunyi tsatsa in ka kalli Rabi Kamar ba ni ba,tafiya nayi me uban nisa ga rana tayi sosai sai da na samo wata makaranta wacce babu gate ta gomnati ce na shiga na samu saman baranda na ajiye kayana a nan sannan na fito gefen titi tare da shanye hannuna Daya ya dawo Kamar me shanyayyen hannu ina tafiya ina cewa a taimaka min sabo da annabi a taimakeni na samu abinci, na koma dai dai wajen danger inda motoci ke tsayawa jiran a basu hannu su wuce ina bi ta tsakiyar motoci ina a taimakeni sabo da Annabi,dan me Mana ruwa da iska abinci ya gagare mu,wani ya sauke glass zai siyi charger naje wajen ina Alhaji adubi girman Allah Allah ya kaika gida lafiya canjin ishiri ya mika min ni Rabi na karbe ina Allah shi Albarka,matarsa dake Gaban mota tace na tsani almajiran Nan duk su damu mutane wasu ma sunfi ka kudi da gatansu sabo da mutuwar zuciya sai su fito bara,mijin yace ai baka San wa zaka taimakawa ba a haka wasu ne Suka bata wasu,wasu da kike gani dole ce ta sasu bara baki San mene dalili ba.

    Na hada uwar zufa sosai amma daga goma sai biyar sai ishirin yinin ranar gaba daya kudin abinci naci dasu zuwa Yamma na koma makarantar inda kayana suke naci sa’a Kuwa lokacin Yan makaranta suna hutu sai na fito wasu gidaje dake kusa da makarantar na lallaba na leka wani gida na talakawa sosai ai Kuwa a zaure na iske wani dan baho karami na dauke shi na gudu tare da komawa makarantar na ebi ruwa a tuka tuka din na duba jakar kayana na dakko sabulun wankina na zaga bayan aji tunda ajujuwan a rufe suke me gadi ma ya tafi hutu abinsa a can a tsorace nayi wanka na canja Kaya sannan na Kara Nemo gawayi na mulke Fuska ta na kwanta a barandar Ina hutawa bacci ya sace ni sai bayan Sallar Isha na farka,a gurguje nayi Alwala tare da Sallah sannan na sake Fitowa cikin dare ko zan dace,ko da na fito ban iya bara ba sai yawo Ina ta kallon birni ko Ina haske Kamar Rana Yan Mata da samari da Yan gayu ana ta lailaya Kan mota gaba Daya kallo ya dauke min hankali Ina ta yawona har nazo bakin wani hamshakin Hotel na tsaya Kawai Ina kallon haduwa motoci sai parking suke wasu a ciki wasu a waje,Yan Mata Kuwa Subhannallahi ana ta shiga dasu da manyan Alhazawa wasu ana sauke su a napep,wasu sunyi gayu suna zaga wajen masu so suna samu suna Shiga dasu ciki,sai zare Ido nakeyi Ina kallo.

    Ina nan tsaye wani kamshi ya daki hancina Wanda ban taba Jin irinsa a duniya ba,kafin nayi motsi wani azababben matashi ya wuce ta gefena,Nawwar kenan hannunsa dauke da ledojin take away,wayarsa ce tayi Kara ya Fara lalubota ya zaro Wayar ya daga tare da shigewa cikin Hotel din, Wallet dinsa ce ta Fadi bai kula ba sabo da ga waya ga ledoji a hannunsa har ta Fadi bai sani ba,Ina kallo da sauri na karasa kanta na dauka tare da budewa ATM card ne kala sun Kai biyar a ciki sai wasu kudin Amurka dollars amma dake ni Yar Kauye ce ban San Mene ba sai na tabe baki nace aikin banza babu abin arziki a ciki ma bari na jira ko zai fito ya amshi abarsa,waje na samu nesa da wurin na zauna a jikin wata bishiya,shi Kam bai San ma ya jefar da wallet dinsa ba wanka yayi ya kwanta bacci abinsa,Ni Kam a jikin bishiyar bacci ya kwashe ni sai farkawa nayi Naga rana a kaina,tashi nayi da sauri na koma makarantar da masaukina yake Alwala nayi nayi Sallah wallet din tana wajena,itacen bishiya na balla na zauna na goge bakina tas na kuskure da ruwa,Fitowa nayi Ina dubawa har naje wajen da mutane suke sosai da manyan shaguna ga me kosai a wajen na siyo cikin kudin barata na jiya,na siyo bredi da shayina ba Madara aka zuba min a Leda na dawo makarantar na zauna naci na koshi,na sake shafa bakina a Fuska duk nayi Mata dabbara dabbara da bakin gawayi na saka yagaggun kayana na bara na fito rike da wallet a hannuna

    Ina tafiya Ina kalle kalle Ina zare idanuwa wani ne ya tare ni a hanya ganin Kamar ko zararriya ce ni,yace ke…a gabansa na tsaya Ina kalle kalle,gashina na sosa na kasa tsayawa kyam,kana ganinsa kaga kamili yace Ina Zaki je? nace ai Almajira ce ni,kai ya jinjina yace kina zuwa makaranta Kuwa? Murmushi na saki nace tab ai ni Jahila ce bani da ilimin komai yanzu ma littafi da karatu bazai Shiga kaina ba,galala ya kalleni yace kina so ki iya? da sauri nace ae,yace Okay da zaki iya zuwa dakina da na koya Miki dole sai karatu ya shigeki da yatsansa ya nuna kirjina yace idan bai shiga ta kanki ba dole zai shiga ta nan idan bai shiga ta nan ba to Dole zai shiga ta nan ya nuna gabana da yatsa,nace har ta nan karatu Yana shiga kaji karya,to Malam Iskanci aka ce ana yi da wajen,Kai baka sani ba Iskanci fa akeyi da wajen ba ruwana wajen Iskanci ne,na ja tsaki na juya nayi tafiya ta abina Ina masifa ya dauka bani da wayo zai taba min wajen Iskanci na Allah ya kiyaye.

   Direct hotel din nan na koma ko zanga mutumin jiya gashi bazan ma ganeshi a Fuska ba sai dai ko idan naji kamshinsa na dade Banga alamar shi ba na bar wajen na tafi barata yau ma iya kudin abinci na tara, Wasa Wasa kullum Ina zuwa Hotel har da dare ban sake Jin me irin kamshinsa ba har na kwashe kwana biyar,shi Kuma Nawwar bai ma duba wallet dinsa bata nan ba,yau da dare na sake komawa nace wallahi daga yau Matukar ban ji me kamshinsa ba bani sake zuwa, ranar Kuma Nawwar ya nemi wallet dinsa ya rasa musamman atm card dinsa sune Suka dame shi, Fitowa yayi ko zai iya gani a cikin motarsa Nan ma ya gama dubawa babu, Fitowa yayi dake da duhu a wajen ko fuskarsa ban gane ba nidai naga hadadde ya wuce,Yana wucewa wani kamshi ya dakeni naji Kamar irin kamshin Wanda ya jefar da wallet dinsa jiya,Ina juyawa Naga ya Dan min nisa da karfi nace Malam….tsayawa yayi ba tare da ya juyo ba da gudu na fyalla naci wawan birki a gabansa Ina haki na zaro wallet din tare da Mika Masa nace t…taka..ce? Yau sati guda kenan ka jefar da ita na ganta kullum sai nazo ko zan ganka,kasan irin hatsarin da na Shiga a hanya sabo da zan kawo maka abarka ai Saura kadan wani ya taba min wajen Iskancina,wai dan Allah karatu ai baya Shiga ta wajen,Nawwar bai gane me nake nufi ba ko saurarar zancen nawa baiyi ba, farin ciki ya Kama Nawwar cikin muryarsa me dadin saurare yace ta ya Kika ganeni? Nace kamshinka yasa kawai danni ko yanzu in za a kasheni bazan ce ga fuskarka ba sabo da duhu,karbar wallet din yayi Ina kallo ya duba komai nasa Yana ciki inda suke ya fito da dalolin masu yawa ya irga ko wacce dala dari dari ce a ciki ya zaro guda Uku yace gashi na gode

  Baki na turo nace Hmmm uhm jam ni me zanci da wannan takardar ai gwara ka bani dari biyar,dariya ta kamashi yace kudine fa idan Kika canja sunfi dubu dari nace wallahi bana so kaji mutum dama can baka yi Niyyar kyautata min ba in hakane ka bani dubu daya mana,Nawwar ya buga buga nace wlh bana so,yace to jirani a nan Ina tsaye a wajen ya koma cikin hotel din sai gashi da kudi Yan dubu dubu ya Mika min Yace gashi dubu talatin Kika samu ba cash a hannuna da yawa,da sauri na karba nace Allah ya shi Albarka za kaga daidai a rayuwarka bukatunka sai sun biya da iznin Allah na juya na take da gudu,yace jita Kamar yarinya da bakar Fuska kamar bayan tukunya Kai wannan da baki take,ni kuwa ko gane fuskarsa banyi ba nasan dai fari ne sosai dan dogo haka ,baki ya tabe ya juya ya koma ciki Yana cewa Kai amma tana da Amana a Zamanin nan.

    Ni Kuwa cike da murna na kwana da sassafe Ina idar da Sallar Asuba wanka nayi da ragowar sabulun wankina na wanke fuskata tas duk da na dan canja sabo da yawon bara a rana,kayana dana jiya na wanke su tas jakata na dauka Yar wayata na Kira   Saratu kawata tana shiga Kiran duniya ba a daga ba,nace ya zanyi haka Zan tafi Kawai,sai dana jira 8am tayi na samu na karya sannan na tambayi wani me Napep inda ake shiga motar su Anambra ya kaini Kuwa har can irin inda ake shiga mota haka Ina zuwa aka saka ni a motar Onitcha direct duk haka Ina ta Kiran Wayar Saratu amma taki dagawa Kuma tasan number ta haka mota ta ja Muka tafi,mun biya kudin mota tuni harda Yar ragowar kudina na adana abina cikin aljihun doguwar rigata domin sanye nake cikin doguwar rigar wani material orange rigar harda aljihu shine a kayana me Dan dama dama Yana min kyau,na yafa dan karamin mayafina,tunda muke kwarara tafiya nake uban bacci na farka na koma cike nake da nishadi Kamar ba gobe, sai tsakar dare Muka Isa Wanda mafi yawa a tasha muka kwana,in Banda turanci da Kuma pidgen English sai yaren Igbo shi Kawai ke tashi,gaba daya a tsorace nake,na matsu na ga Saratu nace yanzu Saratu dan masifa ta iya Zama a garin nan ko tsoro bata ji Kar fadan arna da musulmi ya barke a halakasu, gashi bana Jin turanci,Fitowa nayi daga tashar ba Wanda ya saurareni kowa Harkar gabansa yake yi, Napep na gani na tare iya sunan street din na iya fada masa yace you be Hausa? Yana cewa Hausa na washe baki na daga Kai sama kamar naga Dan uwana bahaushe,shiga nayi ya Fara tafiya Naga haduwar birni gidaje na gani na fada Muna tafiya Ina ta farin ciki,a fili nace yanzu nasan nazo birni, Birni na shigo,Yan Kudu gani sunana Rabi ae Rabi me zamani dariya na saki hahahaha kamar sabon kamu,nace wuhuhu kuturun dosan uwa ana bala’i a kudu, na nuna wasu Yan Mata da yatsa nace kalli cinyoyi Kai cinya a waje haka da Dan wando gajere wasu da mini sun Sha takalma masu tsini,na saki ihu nace yehoho ana tsiya nayi tafi da hannayena nace naga waje.

     Munzo wucewa ta wata GRA nace wuhuhu Kai Saratu lallai kinci gaba haka Zan zauna a katon gidanki,bani ba Arewa dole sai nayi kudi inzo inyi ta aikina in tara kudi ba inda zanje naga waje,Kai Rabi kin dace Ina magana da karfi Ina dariya Ina zazzare Ido Ina nunawa da yatsa Ina ta kallo,Me Napep bai San me nake cewa ba, tafiya mukeyi kamar zamu bar gari tafiya taki karewa tun Ina nishadi har na gaji nace Allah dai yasa yasan unguwar da nace,tafiya akeyi na gaji ma tun Ina magana har na gaji nayi shuru ga yunwa na cina,cikin birnin naga mun bari munzo wasu unguwanni Ghetto area unguwar talakawa da Yan jagwal badan ginin bulo bane da yawa sai nace kauyenmu yafi nan komai da komai.

     Sai da muka zo daidai wani lalataccen gida yayi parking Yana min alama da na fito,Ina mamaki na fito dauke da jakata a Hannu nace ya za ayi ka kawoni kauye ni da nace birni dan mugunta sai da ka wuce duk wurare masu kyau sanna ka kawo ni lalataccen wuri ni nasan wacce nazo wajenta baza ta zauna a nan ba Yar gayu ce me kudi tace Mansion ta gina a birni wata ce ta karaso wajen tana Jin hausa da alama ma bahaushiya ce itace ta tambaye shi da turanci meke faruwa? Yace shi bai San me nake cewa ba,tace ke meke faruwa? Ina masifa nace Odimgbe Street nace ya kawoni shine ya kawoni kauye Kuma wajen kawata nazo Saratu Amma kamar ana kiranta da Seraline,nan take matar ta sheke da dariya tace nan ne Abeg dauki jaka ki Shiga ciki kice a nuna Miki dakinta ki jirata, Ni dai nace Yar gayu ce fa me kudi ce kawata matar ta sake shekewa da dariya tace bawa me Napep kudi dalla malama kinzo mansion din Sera,Ina mamaki duk na hada zufa na biya me Napep kudi na Shiga ciki,matar ta rakani wani dan daudu ya shigo Yana karairaya yace wannan fa daga Ina haka? key zaka bata na dakin Sera zata jira ta bakuwarta ce,shewa Dan daudun yayi tare da furta ahayye daga Kauye amma wannan za’a kwashi gara,nidai mamaki nakeyi Dan yanda Naga Saratu ta hadu bazan taba yarda a irin wannan gidan take ba, gidane baida Fadi sai tsayi zururu daki daki sunfi ashirin ko wacce kofa na facing wata kofar dakin,tsakar gidan siminti duk gidan Kuma bandaki guda daya ne tal dakunan Kuma harda Yan daudu mutum uku a gidan,duka layin unguwar Haka gidajen suke unguwa ce ta karuwai arna da musulmai da duk wani yare a kwai a unguwar, kidane iri iri ke tashi Mata ta ko Ina gasu Nan da kyawawa da munana duk da shigar banza wasu sabo da kyau sai kace mene ma ya fito dasu amma haka aka bude min dakinta na shiga.

   Dakin nake karewa kallo da tiles dinsa sai katuwar katifarta da fanka irin ta kasa sai akwatunan kayanta a gefe,can barin Kuma Gas ce karama da duk wani kayan girki na bukata akwai shi,Babu wutar nepa Sanda na shiga sai zafi kamar zai kashe ni na jike da zufa haka na zauna na buga tagumi Ina kallon hoton wani katon gida me kyau manne a bangon dakinta,Daya barin Kuma katuwar poster ce ta batsa Namiji ya rungume mace babu Kaya a jikinsu ni dai kunyar hoton ya kamani na daina kalla na sadda kaina kasa,gajiya nayi da Zama na fito waje na samu a tsakar gidan wasu suna shan giya,wasu sunyi group kayan maye suke sha,wasu suna ta busa wiwi,wasu Kuma suna ta buga chacha sai bina suke da kallo suna kus kus gasu duk matane sai Yan daudu a cikinsu da wasu tambadaddun mazan,Ina juyawa wani yace Kai ji Duwawu dan Allah bakuwar Sera ce,wata inyamura ta kalleni tace Ohh Jesus see her back nidai fita nayi daga gidan da ko kofa babu bare a rufe a jikin wata bishiya na tsaya Ina kallo yanda karuwai ke hada hada wasu suna rawa kamshin girki sai tashi yake,inda nake tsaye Me POS ne wani tattirin dan duniya hancinsa ya saka barima har waje uku,kitso ne a kansa kana ganinsa kasan ya gogu da bariki,yace ke ya sunanka? Yana Jin hausa amma ba sosai ba dake Wai ya zauna a Jos,na kalle shi nace sunana Rabi,ahaa yace yaci gaba da harkarsa,Ina tsaye wata karuwa tazo ta bada dubu dari ya tura Mata a accnt, yace oh lallai Lili jiya an daki harka har dubu dari ko da Alhaji Kika hadu? Tsaki Lili ta ja tace Munafuki Abeg send  my money,aikin banza tana tauna chewgum, sai Suka Fara fada,me POS yace see your head mango head,with your toothpick hand idiot,suna ta cece kuce Ina tsaye Ina jinsu sai ga wata mota hadaddiya tayi parking Saratu ce ta fito daga motar taci uwar kananan kaya wani bumshort ne a jikinta sai yar riga bingila komai nata a waje ga takalmi me shegen tsini da jaka ta rataya komai da ta saka blue and white ne sun Mata masifar kyau.

     Tana ganina ta saki Murmushi naje da gudu Ina murna na rungume ta tace kawata kece nace ai tun dazu nazo Ina jiranki dariya tayi tace Ina can wajen aiki muje ciki muka tafi cikin dakinta sai kallonmu akeyi anyi sabuwar bakuwa, muna shiga na hau Saratu da fada nace Saratu Wai Ina hadadden gidan naki ne Dan Allah mu bar nan gidan na tsane shi mu koma can,Saratu Tsaki ta ja tace karki sa min ciwon Kai idan zaki zauna ki zauna nan ne gidana gidan da nake fada Miki ban gama gina shi ba,ihu na saki tare da dafe kirji nace Saratu la’ilahaillahu ashe haka kika iya karya kalli gidan da kike a waje marar kyau kalli dakinki sai zafi yanzu a nan kike rayuwa wlh gidan Dagaci yafi wannan sau dubu ke kauyenmu yafi nan layin naku kyau,gidanku ma yafi nan tsari haba Saratu ashe duk karya Kika je Kika yi Mana a kauye na gama ganowa yanzu dama karya ce motar ma naki da ita Kika je Mana data aro,Kinga Rabi idan Zaki zauna ki zauna idan baza ki zauna ba ki koma kauye,badan wlh ke bace baki Isa ki tsaya a gabana ki dinga fada min magana ba,Hannu na shiga tafawa Ina karewa Saratu Kallo nace kalli cinyoyinki kalli duwawukan ki cibi a waje ashe a nan tsirara kike yawo Saratu,tsaki Saratu ta ja tace wai Kinga me ma ya kawoki ne kike fada min magana haka? haka nayi shuru,zama mukayi na bawa Saratu labarin komai na gidan Dagaci,Saratu ta tausaya min tace Yar uwa nasan wasu wahalar da Kika Sha tun Muna yara me yasa baki kai Kara hukuma ba tunda sai da aka cike Miki takardu da komai sannan aka damkawa Dagaci ke tunda yace Yana so ai hukuma bata bashi Kawai dan ya zalunceki ba,nace da a baya Ina karama kin San hukumar gidan raino suna zuwa duba ni Dagaci ya dinga tsarasu ya fada musu karya Kuma suna ganina shar shi yasa ma tunda na girma Suka daina zuwa,idan na Kai Kara ya fini power ta ya za a kwato min hakkina a kasar nan tamu da zukatan mu sun gurbace,sannan ki duba fa Allah ne ya kwace ni Saura kadan ya fasa ni ya lalata min rayuwa Allah ne ya tsare,Saratu tace yanzu uba mahaifi ma neman yarsa yake a Zamanin nan bare ke Yar tsintuwa Allah ya kyauta yanzu kafin nayi girki kinsha wahala bari na bayar a siyo mana abinci me zaki ci? nace ah Ina kudu ai a kawo min Sakwara da miyar Agushi ,Saratu tana yanga ita a dole wayayya ta bawa wani dandaudu kudi ya tafi siyo Mana abinci Muka ci Muka koshi daga nan hirar Kauye ta barke muna ta labari,tace ya labarin saurayinki Kutama? nace Allah sarki Alhaji Kutama ,baki Saratu ta tabe tace ke dalla manta da shi ki fara sabuwar rayuwa,rayuwar yanci rayuwa me dadi ki samu aikinyi Wanda Zaki dogara da kanki,Farin ciki ya kamani nace yawwa Saratu dan Allah ki samamin aikin Yi kinji,karki damu Zaki samu aiki amma sai kin canja suna,Ido na zaro nace na canja suna Wanda aka yanka min rago aka rada min Rabiatu sai na canja suna,Kinga kamar ni Seraline ake ce min ki samu sweet name na Yan gayu irin su cutie,princess,sweet pussy etc,Ido na zaro nace ah Saratu bazan iya ba Ina laifin ma a kirani da Miracle din Kawai, Okay Miracle din ma yayi ai cewar Saratu,duk tunanina wani aiki ne babba.

    Ban fahimci inda aikin nasu ya nufa ba sai da dare yayi naga kowacce har mazan suna ta faman daukan wanka ko wacce ta sa Kaya matsiyata Wanda tsirara Kawai suke,naga wasu matan Wanda zasu kwana da wani me kudin sun shirya anzo an dauke su a manyan motoci wasu Kuma sun shiga Napep sun tafi,Wanda Basu da wani Kuma suna shiri zasu fita gefen kwalta me son kwana da karuwa ya dauka ya biya,na kalli Saratu nace Saratu badai wannan sana’ar itace aikin da Kika ce kina yi ba? Ba kunya tace shine Ashawo work aikin siyar da Pussy kasuwancinmu kenan ka biya ka ci,baki na bude a tsorace nace Saratu kiji tsoron Allah kin cuci iyayenki tunaninsu Kuna tare da Yar uwarku aikin restaurant,ba kyau Saratu ke a karuwancin ma mafi Muni kike yi na kwalta haba Saratu karki biyewa arna akan abin duniya ki tuna addinin mu,tsawa Saratu ta buga min tana duba mudubi sanye take cikin Yar ficikar gown bata fi rabin cinya ba Blueblack ta sa hular gashi me tsada,tace karki dameni idan baza kiyi ba ki kyaleni bana son wa’azi aikin banza local girl,dan bakina na turo gaba nace ni dai bazan yi ba,Ina kallo Saratu ta Sha takalmi me tsini ta fice,sai da safe Suka dinga dawowa,a Haka na kwashe sati biyu har na Saba da kowa da mutanen layin kowa ya sanni Muna mutunci har idona ya fara budewa nima na fara dan zama tsagera sabo da Zama da madaukin kanwa shike kawo farin kai,Ina daki a zaune bani da ko sisi Saratu tace

   Rabi ki bude kunnenki kiji zaman da kikeyi a karkashina ya Kare zan hakura mu zauna daki Daya dake amma fa ba kyauta ba dole ki dinga kawo kudin haya rabi Nima na kawo rabi mu hada mu biya,sannan daga yau na gama ciyar dake da kudina sai kema ki fara neman kudi ki dauki nauyin kanki da kanki sabo da haka na baki nan da wata guda ki kawo kudi dubu hamsim nima na kawo mu biya kudin haya,sai abinci ki nemawa kanki daga yau,na rasa me zance ma gashi bani da wajen zuwa,nace to a nan gidan Kinga ni dai bazan iya siyar da gabana ba bazan yi karuwanci ba idan akwai masu daukana aiki zan dinga musu shara da wanke wanke,Saratu tace akwai ‘yarzabil kaf layin nan tafi kowa kudi,akwai wise itama tana da kudi ta Dade tana Neman Yar aiki a gidan nan, ga Star itama duk nasan zasu yarda ki musu girki,wanke wanke da shara da mopping,idan duty na wanke bandaki yayi na kowacce ke Zaki wanke musu haka sharar compound kaf gidan nan kullum da duty kowa so Zan musu magana,nace to ai suna da kirki ma ki fada musu Kinga na samu aiki idan na samu miji me sona nayi aure na,Saratu baki ta bude tace aure lallai Zaki kashe kanki yarinya tab, amma rayuwarki ce.

    Nace Saratu karki dameni da iyayi na sanki kin sanni me zaki boye min,yawwa idan na samu Miji aure zanyi yawwa ehe yanzu tsadar rayuwa tayi yawa ga tsadar abinci sabo fa da tsadar abinci yanzu Mata masu ciki sun daina Amai,Saratu ta kwashe da dariya tace ke makaryaciya inji uban wa? nace baki da labari ke? Dariya Muka dinga yi Saratu tace to bari na baki shawara tunda ke soyayya kike so kiyi aure idan zaki fara soyayya ki tabbatar kinyi photocopy na zuciyarki ki ajiye Original din a gida Kinga idan an samu matsala dama zuciyar taki photocopy Kika bayar sai ki dawo gida ki dauki Original din,dariya nayi sosai muka tafa nace kawata har yanzu baki bani shawara ba fa akan yanda zan kula da budurcina a gidan nan naku na karuwai.
Saratu zama ta gyara tace karki yarda da Namiji ko waye musamman idan Kika ji Yana kiranki da Sexy Nan gaba zai iya cire Y din yayi Sex dake daga karshe ya cire S din ya kiraki a Ex-girl friend ki Zama wise Kar wata ta Miki wayo ta hadaki da Namiji ta samu kudi tunda ke kin zabi aure no problem,mun dade Muna hira.

   Washe gari dake da asuba na fito nayi wanka da Alwala,na fito Kawai naga Mata da maza sun kafa layi kamar layin banki ashe Wai toilet za a Shiga ake wannan uban layi,kowa yazo sai ya hau layi,da sauri na koma ciki nace Saratu yanzu akan za ayi kashi aka kafa uban layi haka? shi yasa nace ai ke tunda kina Sallah ki tashi kafin ayi Sallah Kuma fatan kin wanke bayin kafin kiyi amfani da shi? nace sosai ma ai baki ga na dauki Hypo ba,tace to ta juya taci gaba da baccinta babu Sallah ba salati,ni na gyara Mana dakin na Mana abin kari, bayan kwanaki sosai na kara sabawa da gidan kowa ya sanni nasan kowa, mutum uku Seraline ta hadani da su Suka daukeni aiki a gidan zasu na biyana duk wata ‘Yar Zabil ta dauke ni,Wise sai Star tun kafin ma na Fara aiki suka jibgo min kwancen Kayan sawa kana nan Kaya da namu na hausawa masu kyau da tsada,harda takalma Suka bani abubuwa na ras,a ranar na fara musu aikinsu kullum ba fashi sai abinda suka ce,gashi duk canji in ya ragu bar min sukeyi,Muna haka kullum idona sai budewa yake Ina Kara gogewa sannan bakina ya bude yanzu surutun masifa gareni Kamar naci aku,kana taba ni ba mutunci ga fada dana koya,ga rashin kunya Nima Jin Iskanci da kalamai na batsa yasa na iya wasu nima bana Jin kunyar fadar magana duk girmanta,Nima su rawa da su whot game da ni akeyi a gidan idan ba caca akeyi ba,Ina cikinsu na koyi saka shegun Kaya baza kace na hada Hanya da muslunci ba Kawai abinda ban taba shine fita titi neman customer Ina nan a virgin dina ban taba Iskanci ba sai dai Kawai nasan mazan gidan da Yan daudu mun Zama kawaye kuma kusan duk arna ne Muna rungume juna da su Kamar kawaye mata,gashi pidgin English Ina ta koya a hankali yanzu na Fara iyawa ba laifi gashi abin haushin kudin idan na samu a cikina nake cinyewa sai kudin haya da sauransu babu kudin da zan iya tarawa ma sam sabo da basu da yawa,Amma sutura da komai a gidan duk su Wise sunfi mutum ashirin bani Kaya suke har na kwashe watanni shida.

    Yau Star ce ta sani girki da yamma likis Ina girkina a dakinta itama komai akwai a dakin na more rayuwa nata dakin ba irin na Saratu ba harda ac ya hadu itama Yar zabil haka da wise su suna samun customers sosai, ina ta juya stew sai ga Star ta shigo a gajiye ta fada saman katifarta tana wash,na kalleta nace hala jiya customer ya baki wuta? Star tace ke dai bari mutumin hariji ne baya gajiya sai da ya more kudinsa kaf guy din ya daki harka yayi ta front, back da center babu ta Inda baiyi ba,nayi tsuru Ina kallonta Ina mamaki bada kansu da suke yi nace wai Star ni kuwa abin nan da Dadi? Star tace wa ya fada Miki karuwa na enjoying sex ai karuwai irinmu badan Dadi muke ba sai kana son mutum ko Yana birgeka kake jin Dadi ai Kawai mu bude maka zamuyi ka daki harka yanda kake so ka bamu kudi,in Kinga yanda muke dagewa Muna sarrafa maza zaki mamaki Kuma mafi akasiri ba Jin dadin muke ba sabo da Kawai muja hankalinsa ya Zama babu wacce yake so yayi sex da ita sai mu,shi yasa muke kwacewa Mata mazajensu wasu sun tsaya kunya da shirme mu Kuwa zamu yi maka yanda baka ma tunani dole a nace mana,nace ah gwara da Kika fada min idan nayi aure kice na dage? Star tace ki dage sosai ki fahimci mijinki me yafi so yarinya ki gyara kanki karki Wasa da gyara ki kashewa jikinki kudi,Kinga dai irin magungunan da muke siya masu mugun tsada,da ace zaki samu Wanda kike so ki gwada kiji dadi, sai naji Ina so Nima nayi sex din yanda kullum a wajen karuwan ke kwadaita min dadin shi, so suke su rinjayeni na fada harkar nima amma naki,Auzubillahi na dinga ja Ina Neman tsari a raina,dama kullum bana Wasa da addinina ga Karatun Qur’ani kullum Ina yi Allah ya tsareni,Ina ta girki Muna hira daga ita sai pant da bra a haka wani katon Arne Igbo yazo ya sameta da gani kasan ba karya akwai kudi a kugunsa,Yana shiga dakinta ya fada kanta a haka Suka fara kissing a gabana inda sabo na saba gani ko a jikina Ina jinsu suna ta fama har ya rabata da kayan jikinta tsirara take shima daga shi sai sai boxers ta cire Masa Kaya,Condom ta saka Masa da kanta nishinsu na dadi Kawai nake ji,Allah yasa na gama gas na kashe da sauri na bar dakin suna ta masha’a dinsu,Ina Fitowa Wise ta dau wanka zata unguwa da karamar akwatinta me kyau tace Miracle zo ki rakani gidan saurayina,dakinmu na shiga na saka Yar riga doguwa me siririn hannu Kamar hannun best daga sama ta dan tsuke kasa ta bude yar kanti ce brown me adon golden cikin kayan da suke bani.

     Mayafina karami nayi rolling brown nasa flat shoe dina brown na Fara gogewa fa gani kyakyawa ajin karshe Fara sol dani ko Ina sai ayi ta kallona, Jakarta na dauka Muka shiga napep,Wise duk tafi yanga da wulakanci ni kaina bana Mata wasa sabo da halinta gata kyakyawa da ita,wani katafaren gida Muka Isa,knocking tayi gate man ya leko Yana ganinta da alama ya Santa ya bude Yana washe baki,kallona yayi yace small madam how far?Fuska na bata nabi Bayan wise tun kafin mu shiga ciki ya leko wani fari Igbo kyakyawa ne amma katon arne ne,glass cup ne dauke da juice a ciki yaci wanka cikin kana nan kaya yan ubansu gashi matashi,yana zuwa ya kalleni nace good afternoon sir, yace Good day Yana Murmushi tare da rungume Wise,tana shafa sajensa tace Baby I miss you,yace miss you more,let’s go upstairs and have fun,hannayensa ya maida saman kugunta Suka haura sama ta juyo tace ya bani kudi na koma gida,ai Kuwa 5k ya bani sai Murna nakeyi na karba Ina godiya na wuce gida nace daga rakiya 5k guda yau akwai zazu,Ina komawa gida Seraline tana gida yau hutawa takeyi tana Jin kida Ina shiga na dinga cashewa Ina karkada Mata 5k sabo da yanzu duk na fetsare ban taba rawa ba sai a nan gidan duk na koya kullum sai nayi rawa tun Ina hauka har na fara gogewa.

   Saratu dariya takeyi tace akan 5k kike wannan rawar da ace aiki nake fita rana daya Zan iya samun dubu dari ma,na kalli Sera nace ba shegen da zai shigar min local government ku dai da kuke ashawo Kobo kobo 2thausand Kuna rabawa kyauta kuje ayi ta ketara muku local government ni duk shegen da ya shiga local government dina to dole yayi loosing Election,Baki ga Dagaci ba tuni sun rasani,dariya Seraline tayi.

   Su Gwaggo tunda na tafi ko a jikinsu Kawai murna sukeyi suna Jin Dadi Gwaggo tace yanzu sai mu zauna mu taru akan yaranmu su samu mazaje masu kudi suyi aure,Aunty Amarya tace yau wajen wata shida da barin Yar banza gida har gidanmu yayi dadi duk ta tare Mana waje,Dagaci ne ya shigo da abincin kajinsa dakin dana bari kaji masu kwai ya zuba Yana kiwo a ciki duk da ta bangaren aikin gida sun rasa me yi sai dai suyi da kansu gashi Gaji da Mairo basa aikin gida kazamai ne sai dai Iyayen suyi,ana haka Katsam Gaji ta hadu da wani me kudi a kasuwa ya biyota har gida Yana da kudi Alhaji Kabiru Danbinni murna wajen Gwaggo da Dagaci ba’a magana sai abinda Alhaji Kabiru yace, sai da ya bari sun Saba sosai Yana kashe musu mahaukatan kudi sai ya fara fita da Gaji yawo yana siyo Mata kayayyaki, yau Sunday zance yazo yayi parking da arniyar motarsa Gaji taci gayu ta Sha kyau ta fito tana taku dai dai Farin ciki ya Kama Alhaji Kabiru tun kafin ta karaso ya fito a motar ya tsaya Yana Kare Mata kallo sanye take cikin Material Maroon Wanda shi ya dinka Mata ba karya tayi kyau ta ko Ina dama su Gaji anyi school a waye suke,Yana kallon Gaji yace sai naji kamar na rungume ki,Murmushi ta saki yace Allah dama ace yanzu tare zamu kwana da zan more, Gaji Ido ta rufe sabo maganganun Alhajin nata,yace ki daina kunya yara kanana ma yanzu Jin dadin rayuwarsu suke yi bare ke da girmanki,ki bari na dan motsaki ki Dan kawo yau kiyi bacci me dadi kin tsaya Kamar Yar Kauye haba Gajina,wallahi da ace kin yarda dani Kawai romance ba sex ba babu abinda bazan baki ba,komai zan siya Miki Zan Miki komai,I will take care of you

    Gaji tace ni dai bana son Sex sai munyi aure,wayancewa yayi haba ya za ayi na lalata Miki rayuwa ai bazan ma iya ba Kawai romance amma ya kamata ace munje inda yake da privacy waje me sirri inda zamu saki jiki sosai muji dadi ai romance dinma yafi Sex,Ni mota ma zan siya Miki kwana nan in kin yarda,Gaji taji mota tace to muje amma dan Kaine yace ko kefa ai yanzu rayuwa sai ana Jin dadi ana dan motsawa amma duk kin bari kinyi mugun tsatsa,dariya tayi tace tsatsa Kuma yace yes kinyi tsatsa,gida ta Shiga tace Gwaggo Alhaji yace naje zai kaini na siyo Kaya,Gwaggo tace sai kin dawo tunda ai mijin aure ne ba damuwa ai aure zakuyi nan kusa a dawo lafiya Dagaci Yana ji yace mutumin kirki kenan Alhaji Kabiru Danbinni ba abinda zamu ce Masa,Gaji dai ta fice ta shiga gaban mota ya ja sai cikin birni tunda Suka taho yake Mata maganganu na batsa,yace da alama zakiyi ni’ima,zakiyi dadi,sannan Wanda ya sameki ya dace zaki dade ana sex dake baki gajiya ba,gaki da alama jarababbiya ce ke kina da karfin sha’awa,Gaji tace ta ya ka sani? Yace af baki san wani littafi ba me suna Surah inda aka siffanta dukkan kalolin Mata to ke me surarki haka aka ce a littafin,ai ya kamata muje na sha dadi ko ya kika ce.

    Zaune muke a tsakar gida Muna game din whot ban wani iya sosai ba sai cinye ni akeyi,Munfi mu shida Sera,Wise,Star,Yarzabil, Mandula,Manduwa sai dan daudu Santana,Star tana yi tana bulbula sigari,Seraline itama kunnawa tata wuta tayi tana sha,Wise kuwa bata Shan komai na hayaki sai kwaya ita, sai yarzabil yar Syrup ce ita Kuma,Mandula Kuwa ba abinda bata sha,duk na goge nima har yanzu kallon baki waye ba suke min,Muna fama sai nishadi mukeyi,Santana ya kalleni yace Miracle ki taimakawa kanki ki nemi kudi Ina baki shawara kin zauna kina ta talauci shegen pussy din ai ba gutsira za ayi ba kin zauna Wai ke aure a nan gidan zaki samu mijin aure ko balagaggen dan bariki zaki aura a nan,kin San dai kaf layin nan yan Iska ne,Nima da Zan samu Wanda zai aureni ai da naji dadi,dariya ta kamani nace kalleka ko kunya baka ji kana Namiji ka maida kanka dan daudu Wai da zaka samu Wanda zai aureka Namiji fa kenan stupid karka isheni me suffar Condom,dariya su Wise Suka dinga yi, Yar aikin Karuwai lallai kinci abinci cewar Yar Zabil dama yawanci duk gidan Yar aikin Karuwai suke ce min.
Anjima fa akwai gala a gidan nan,dama unguwar kullum sai anyi gala iri iri mawaka suna zuwa suyi show Yan gala,akwai bangaren gala a unguwar  yau can zasu kusan kwana,da dare da ni aka tafi can wajen Yan solo duk munyi gayunmu,Su Wise suka dinga lika musu kudade ranar Karuwai sun zubar da Naira,Nima mawakin ya birgeni mawakin hausa ne Wanda ke tashe kudin dake hannuna dubu uku da na riko a hannuna na hau step naje na lika Masa su,na dawo kida na kwasata na ranci dubu biyar wajen Seraline naje na Kuma lika masa,mu indai Harkar banza zakayi a gidan babu me hanaka sai dai ma a goya maka baya.

 

Sharhi fans

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

16-20

Official

By
AsmaBaffa
08061929616

SADAUKARWA NE GA
DUK YARAN TSUNTUWA

 

Page naku ne

UMMU LATEEFAH
SADIYA MUHAMMAD
ZAKIYYA BELLO
FATEEMAH FAROUK
ALINA
MMN NASRIN
GIMBIYA DIYAR KATIBI
AUNTY NURSE ZARIA

Jinjina gareki
HAUWA S ZARIA
ME KARANTA AUDIO NA BOOKS DINA

 

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

        Gaji wani katafaren gida taga ya kaita me gadi ya bude,Alhaji Kabiru Danbinni yace nan ne gidanki nan zaki zauna idan munyi aure,farin ciki ya Kama Gaji duk ta rude haka suka fito,hannunta ya rike Suka Shiga ciki duk ta rude taga gida me kyau sai da ya nuna Mata ko Ina sannan ya shiga kitchen ya kawo Mata lemo da ruwa ta sha ya fito musu da kayan makulashe Suka ci sannan ya jata bedroom dinsa yace muje kiga dakina ai bamuje ba,suna shiga taga ya hadu sosai daukanta yayi cak tare da daurata saman gadon shima ya haye,hannunta ya rike yana murza yatsunta a hankali kasa Masa musu tayi sabo da kudinsa,wuyanta ya Fara shafawa a hankali ya hade bakinsu waje daya,cikin salo ya zare Mata rigarta bra dinma ya balleta gata da dukiyar Fulani nan ya Fara sarrafasu ta wani lumshe Ido tana jinsa Yana gurnani kamar wani rago,Murzata yake yanda yaga dama duk ya rude bai san sanda yake cewa muyi sex ba,Gaji tace a’a gaskiya Jin zata botse Masa yace to shikenan romance tsaya…tsaya…tace nidai banda Sex,yace to naji dakata wait…tsaya Yana ci gaba da murzata tare da furta zan mallaka Miki komai Allah ya Miki baiwa,skert dinta ya zare daga ita sai wando tight iya gwiwa,hannunsa ya tura ciki, ta rike hannunsa shi Kuma ya shiga furta tsaya ba komai…ba komai tsaya duk ya zauce, wani ihu daya kurma sai da Gaji ta firgita tace Kai Kuwa sai kace ana Jan rago za a kaishi kasuwa kabi a hankali mana,Alhaji da katon tumbinsa yace zakiyi dadi kinji ruwa,Gaji tace nifa zaka ji min ciwo a hankali sai fingering yake Mata tana Jin dadi itama  ,haka yasa Gaji shima tana ta faman murza shi Yana gurnani,Gaji tace ni zaka kashe min dodon kunne haka ake Jin dadin sai kace kana sex idan kana sex yo ai sai dai kukan Saniya zata haihu jajirinta ya sawo Kai,haba sai kace Kan jaririn Saniya zai fito,Alhaji Yana jinta Yana cewa na baki kaina Gaji da sauri tace yo tsakani da Allah me zanyi da kanka duk girmansa ni kaga ban san wajen siyar da kawuna ba bare na Kai a siya rike abinka kayi sauri Kawai kaji dadinka,a cinyar Gaji yasa abar tasa a haka ya kawo yana wani Jin dadi ya rungumeta sannan ya Kama Gaji ya Fara Mata sucking dadi ya kwashi Gaji tace ajalina yazo ni Gaji,taji dadi sosai sai da Suka gama lalacewa sannan tayi wanka ta fito ta shirya shima yayi nasa Suka fito Yana ta Jin Dadi suna zuwa gida dubu goma kacal ya bawa Gaji bayan siyayya Daya dan mata wacce bata taka Kara ta karya ba,tayi godiya Itama ta tafi tana tuna irin dadin da taji tace dama haka abin yake masu aure Kun ci uwaku da bakwa fada Mana gaskiya sai kowacce kinibabba tayi mukus a gidan mijinta sai da ta gama haukarta sannan ta shige gida, su Gwaggo harda guda yarsu tayi goshi,Aunty Amarya tace ke Kam Yar nan kinyi goshi Gaji tace rankwalele ma Kuwa goshi Kato sai kyalli suna ta dariya Mairo tace Sis Ina tayaki murna,Gaji tana murna ta furta don’t worry sister verysoon Zaki samu naki kema,Mairo tace Allah yasa.

    Nawwar ne zaune a dakinsa yana tunani yace Oh God karfa na Shiga hakkin yarinya ni bani da cikakkiyar lafiya gaskiya nayi magani har na gaji, yace dole na hakura da ita haka naci gaba da neman magani,kudin da ya ajiye bai kai bank ba da dadewa ya tuna wajen ya Bude kudi yace daukeni inda ka ganni sisi babu a ciki,Sabreen duk ta sace su a hankali wasu ta bawa mama wasu Kuma tayi shaye shaye da su,Kira ya kwala mata tana jinsa tana Palo tana latsa wayarta yar aiki tana Mata tausa a kafafu tace banza,me aikin tace Auzubillahi wallahi a Zamanin nan ana kuskure da yawa matan yanzu koya miji ya bata musu sai ta dinga zaginsa wasu a gaban kawaye idan an hadu ana zancen halin maza,wasu idan sunje gida wajen Yan uwansu ko a gaban iyayensu su dinga zagin miji sabo da ya musu laifi wlh ba kyau Mata ku gyara,tsawa Sabreen ta bugawa dattijuwar da ta haife ta tace wallahi Zan koreki a aiki banza munafuka Ina ruwanki ko kanin ubanki ne dan an zage shi to na zage shi na Kara taja tsaki ta mike tana kutuntuma ashar ta haura sama a gaban Nawwar Kuwa mukus tayi ta tsaya tare da furta gani,yace baki ga kudin Dana ajiye ba ko kin canja musu wajen ajiya? Direct tace nayi amfani dasu nayi uzurin rayuwa da su,Ido ya zaro tare da furta for real? tace ae Ina bukatar kudade Kawai na kwashe,kin San nawa ne Kuwa? Oho maka,cikin tsananin Fushi ya furta are you out of your mind?   baki ta tabe tare da gyara dan guntun wandon da ta saka tace nifa kaga ka daina min tsawa akan wasu chicken change me yasa ka fiye takur….Mari taji ta ko ina yace kudin ubanki ne ya nemo min Ina tunanin baki da hankali ke karamar Yar iska ce bari na nuna Miki na fiki Iskanci waya ya jawo tace Allah ya Isa shege ai Kuwa ya hau tafkarta sai da ya fasa Mata jiki ta gudu da kanta tana kuka wiwi,kayanta ta shiga hadawa ya fito zai fita sanye cikin 3qtr da riga me gajeren Hannu yayi kyau,ganinta yayi ta saka akwatinta a motarta taja ta bar gidan a fusace yace tafi nono fari Ina tunanin faranta Miki kina min shirme yaja tsaki ya shiga motarsa rantsatsiya ya bar gidan zuwa gidan babban abokinsa Wanda shi Yana da mace da yaransa biyu Khaleel kenan.

    Sabreen da kuka ta shiga gida Mama ta tare ta tana tambayar lafiya? tace wannan Dan burar…Dan kutmar….tsinanne azzalumi mugu shine ya dakeni akan kudin nan, Mama tace Yar tamu guda lallai Nawwar baida mutunci bari Papanki ya dawo a sanarwa kakarku Iyamami ita zata dauki mataki tunda ita ta haifi ubansa,suna zaune Papa ya shugo da murna ya samu wata kwangila zai samu kudade ya iske Sabreen ya tambaya lafiya? Mama ce ta fada Masa komai harda cewa bazan yarda ba a kashe min yarinya ta tilo,Papa yace akan wasu Yan milliyan biyu zai kashe min ya lallai yaron nan Wasa yake dani wlh Naga dama sai na hanashi sakewa a rayuwa,bari naje ai Iyamami ce maganinsa Kuma duk abinda nace ta zauna daram.

    Bai ko zauna ba ya nufi part din Iyamami inda Yar aiki ke Mata gyare gyare tana ganin Dan nata tasan ba lafiya, tace lafiya Yusufa? Ya kwashe zance ya fada Mata harda cewa yanzu Sabreen ba Yar uwarsa bace ai shi me bata kudi ne bare gata matarsa,Iyamami tace itama bata kyauta ba da ta satar masa shi Kuma Dan ubansa sai ya dake ta,dama na fahimci yaron nan yanda yake jiji da Kai magana ma aikine a wajensa ni gaskiya ki yiwa ubansa da uwarsa magana,Iyamami wayarta ta jawo tace kamo min number dinsa,Lokacin Nawwar suna ta labarin kwallon kafa da abokansa yaga Kiran Iyamami,Tsaki ya dan ja yasan zancen Khaleel Yana kallonsa ya daga Iyamami ko jira batayi yayi magana ba tace Dan ubanka kazo Ina neman ka,to yace Kawai ya kashe wayarsa,Khaleel ya kalle shi yace lafiya dai? yace hmm Kai dai bari wannan Yarinyar Sabreen Mana tunda na aureta wlh Banga amfaninta ba a wajena daga bacci sai sata,sata kuma? Ae sata fa dama Ina ganin ana sace min kananun kudi to yanzu har million biyu ta kwashe ban sani ba,gata bata da kunya bata da respect zata iya cin mutuncin kowa Dan iskan baccin nan nata na rasa na mene mace ta kwana ta yini tana uban bacci,kasan Ina ta Shirin ci gaba da magani akan rashin feeling dina sabo da na dinga bata hakkinta amma Yarinyar nan harda zagi,Khaleel yana tausayin abokinsa yace eyya sorry kaji sai hakuri kaci gaba da hakuri,yace bari naje sabo da Iyamami itace ta haifi Baffa Ina girmama su sannan Mami zasu ciwa mutunci idan Baffa yana gari bazai so na wulakanta Masa uwa ba shi yasa nake Mata biyayya su Kuma gani sukeyi Kamar isarsu ce ta sa,shima Papa Ina ganin girmansa shi yasa nake zaune da yarinyar,Khaleel rokonshi yayi yace ka Kara hakuri kaji yace Inshaallah ya wuce gida.

    Yana zuwa Iyamami ta hau bala’i harda kuka tana cewa inama ubanka zai dawo yau ko gobe daga kasar waje ya gani yanda kake wulakanta jininsa wallahi kabi duniya a sannu Yarinyar tace baka kwana da ita,Nawwar idan baka da lafiya ka fada na tafi Kauye na hado maka magani,Shi dai Yana jinsu har ta gama yace bani da lafiya Iyamami abar bata tashi,a gaban kowa ya fada ko kunya,Iyamami tace Sannu Allah sarki za’a Nemo maka magani dan Allah kayi hakuri ku zauna lafiya da Sabreen, Sabreen tana daki aka kirata ta fito idonta duk ya kumbura,Mama tana Fushi tace ke koma ki huta gobe na maidata da kaina ko nace idan ta warke,Iyamami tace to kaji,yace ba damuwa,Iyamami tace gobe Zan tafi Kauye kaji,yace to,Papa yace Dan Allah Nawwar Dana karka sake kaji kaida Yar uwarka itama munyi Mata fada baza ta sake ba,Nawwar dai yace to Suka gama ya wuce gida ,Mama da Papa suka sa Sabreen a daki suna fada Mata lallai Yana warkewa ta saki jiki ta haihu da shi idan ta haihu da shi to sun gama mallakar dukiyarsa da komai sai yanda Suka yi,haka suka zugata sosai ita Kuma Iyamami an tafi Kauye karbo magani,kwana daya tsakani sai gata ta dawo da tarin magungunan gargajiyar ciki harda rubutu har gida ta samu Nawwar ta karanta Masa yanda zaiyi amfani da magunguna,wani dan itace ta Mika Masa tace rike idan abar ta harba ko ta mike ka fada min,Nawwar ya karba ya rike Shuru ko motsi tace,yana rikewa ta furta to ya? yace ai ko motsi bata yi ba ko na nuna Miki? Iyamami tace gidanku fitsararre dariya yayi sosai hakoransa kyawawa Suka bayyana,Iyamami tace ji yanda kayi kyau kana Murmushi ashe mijin nawa dai yana dariya,yace idan magani yayi aiki sai a fara ta kanki dukansa tayi ta mike tace marar kunya ba ta tafi abinta,shi dai bai zaci magani zaiyi ba a banza yake kallonsa sabo da yayi masu tsada ma baiyi ba har na asibiti Shuru sai wannan garin ganyen bishiyar haka yana tabe baki yana wani kyankyami a haka ya fara amfani da magunguna.

    Miracle…Miracle….Fitowa nayi da gudu naji muryar Yar zabil Ina Fitowa tace wanke wanken fa waye zai miki? nace kiyi hakuri na tafi nayi Mata na gama dakinmu na koma na samu Seraline ta kalleni tace Rabi ki daina zubar da mutuncinki a gidan nan duk layin nan babu me kyawunki Rabi kin tsaya a wanke wanke da shara wasu banzaye suna wahalar dake Wanda da zaki Fara sana’ar nan nasan sai kinfi kowa customers,yanzu kudin da kike samu basu isarki ci da sha da biyan haya bare kiyi saving ki fara gaki yanzu kin waye kin goge kin Zama tsagera wata Maganar da kike fada ko ni Watarana sai na daure zan iya furtawa,nace sana’ar ku bazan iya ba Ina tsoron Allah duk iskancina a baki ne wlh,to naji Kinga yanzu dare ya kusa zamu je aiki ki shirya muje dake kiga yanda ake harkar ki bawa idonki abinci ko banza kyayi kallo Zaki ga yanda ake aikin sai ki dawo gida nace wannan dai zan iya,to ai bani da Kaya masu kyau na fita,Sera cikin kayanta ta zabo min wata gown silver and black me tsadar gaske amma bata fi rabin cinya ba,ta fito min da dankunne da agogo me kyau da takalmi me dan tudu sai hular gashi dogo me tsada tace shirya,kayan na kalla nace a haka Zan fita tsirara haba Sera Allah Yana kallonmu fa,tace Kinga idan zaki sa kisa malama tana min masifa haka ta tayani na shirya,wani mahaukacin kyau da nayi itace ta min make up me kyau sama sama,duwawukana Kamar zasu fado ita kanta Sera sai data tsaya tana kallona tana yaba surata,Fitowa mukayi matan gidan duk sun shirya wasu ma tuni suna can gefen kwalta titin da ake zuwa me kyau inda yake kusa da layin masu Hannu da shuni,yan daudu na gani sun cakare Suma sun tsaya a titin Mata masu kudi suna zuwa suna daukansu wasu Kuma maza yan luwadi suke daukansu abin ya bani mamaki ga haske kamar rana wani nishadi nake ji,duk motar data wuce su Sera suna binta suna furta customer,suna nuna musu jiki suna tura musu duwawu,Idan me mota Daya ya tsaya sai su yanyame motar Kamar zasu afkawa Namiji ya fito ya zabi wacce ta masa,Ina kallon ikon Allah sai dariya nake yi.

Wata mota ce me tsada ta tsaya Suka tafi da gudu tare da yanyameta sai Kuwa Suka ga mace Yar gayu babbar mace ta fito ta duba cikin Yan daudun ta zabi Wanda ake Kira da Santana ya balle Mata botin rigarsa Yana karairaya taga ya Mata ta jashi Suka Shige mota,ihu na saki Ina Dariya nace wayyo ana tallan duwawu,ba shegen da zai bi ta local government dina my GRA wlh lala babu me shiga GRA na,juyawa nayi Ina tafiya dagwas dagwas na koma gida abina Ina Allah wadai da wannan sana’a Wanda Hausawa musulmai Suka Fara tsunduma kansu cikin irinta su hada jaka su tafi street Ashawo.

    Washe gari ma haka na cakare cikin kayan Seraline Muka je Nasha kallo tun abin baya birgeni har naga suna ta tara kudi ni ana ta barni a baya sai tura kudi sukeyi gida ana siya musu gida da filaye da kudin ashawo duk sun tara kudi a tunanina fa,ni kuwa kowa sai kallon banza suke min,sannan ba mutunci kwandala babu me baka kyauta,bayan satikai haka kawai Katsam ba abinda nake so nima sai Karuwanci yau dai na sa a raina zan fara Karuwancin nan nima na samu kudi amma me tsada zan yi sai idan namijin yayi min sannan sai idan da kudi da yawa,Shigowa nayi dakinmu da dare na samu Seraline tana shirin fita nace Kawata na sa Raina yanzu Kam Zan Fara Ashawo work dinan ki ci gaba da bani aron kayanki kafin na samu customers na siyi nawa,Saratu taji dadi tace ko kefa maza shirya baki da matsalar kayan sawa Kinga yanzu 10pm Kar mu makara,da sauri na Fara shiri na dau wanka cikin dogon wando tight da Yar riga karama nayi kyau matuka Muka tafi,gefen titin Muka tsaya tunda naje motoci ke tsayawa daukana amma kowa yazo sai nace Million daya daga nan me motar zai dauki wata ya barni nan tunda wasu gasu nan 2k 5k ma daukansu akeyi idan customers basu zo da yawa ba,Haka yau ma na koma gida ba kowa,washe gari aka sake fitowa dani nan ma nace sai Million daya kowa sai ya min kallon banda hankali, wani bahaushe ne yazo a Yar karamar motarsa ya tsaya tare da Fitowa Yana Kare mana kallo ya kalli mandula yace juya na gani ta juya sosai ya barta nan ya karaso wajena baki na tabe,yace juya na gani na juya a gabansa ya jinjina Kai yace kinyi muje ko nace kaje da wa? You dey craze? Kasan kudina Kuwa? Nawa to ya furta Yana kallona nace million daya zuwa sama,Ido ya zaro yace ke Kuwa sai kace matan gidan Aljanna zunubi ne fa ga tarin zunubi sannan ga tsada haka,kaga ja kayi gaba ko yanzu na tarwatsa maka kwakwalwa wlh bani da mutunci da kake gani na ja tsaki, wuyana ya shafo kafin ya zare hannunsa na kwashe shi da Marin da yasa ya gigice sauran karuwan Suka goya min baya gamu da hadin Kai kafin kace me mun kashe titi da fada da kyar ya kwaci Kansa ya bar wajen a guje cikin motarsa muna binsa da zagi nace shege ko maza  sun Kare me zanyi da Kai na ja tsaki Ina gyara gashina sannan Ina tauna chewgum kas kas kas…

    Nawwar magungunan Iyamami ya raina su ganin yayi masu tsadar gaske ma amma me sai yaji idan yaci ya koshi ba abinda yake bukata sai mace,sai da Sabreen tayi 3days sannan aka dawo da ita gidansa bata canja zani ba sai ma rashin mutunci data karo,Yan aikin ta fara ci musu mutunci dama hakuri suke yi da ita idan Coccaine dinta ta motsa haka take daddana musu ashar bata da respect,Daya Yar aikin ta hada kayanta ta gudu Sabo da zagi da cin mutunci sannan bata basu abincin kirki a dafa ayi komai amma ta hana su,Ladidi me girki ce ta rage sai maza masu aiki su dama yawanci kudi yake basu suci abinda suke su sunfi son ma a Basu kudin har canji suke samu kullum,Ladadi ce ta fito Kawar Sabreen tazo Jamcy ta kawo Mata lemo,Sabreen tace ke tsohuwa wannan Kawai zaki kawo shine kadai a gidan? Ladidi tace Zan kawo ai Hajiya ban gama abinci bane,Wai ke wacce irin dabba ce ne,Ladidi da mamaki ta kalli Sabreen domin tayi kusan jika da ita ma,tace dani kike Hajiya? No da uwarki nake dalla wuce ki kawo Mana snacks,Ladidi tace ko ba komai Sabreen ai naci darajar furfurata sannan ni nasan nayi jika dake amma ki iya kallona ki zageni, Sabreen daga Jin haka sai haukar kwaya ta motsa ta zabgawa Ladidi Mari,kumatu Ladidi ta dafe hawaye ya shiga sintiri a kumatunta juyawa Kawai tayi ta shiga bangarensu ta hado kayanta tana hawaye ta fito zata tafi,Jamcy tace wannan shine dai dai banzayen Yan aikin nan sai su dinga hada kansu da me gida, Sabreen ko a jikinta tace kina jina dan iskan mijin nan nawa Watarana Yana birgeni da baya shiga safgata inyi shaye shaye na lafiya lau dariya Suka Yi tare da tafawa dukkan sirrin Sabreen ba abinda Jamcy bata sani ba ko hannu Nawwar ya rike Mata to sai Jamcy taji labarin ita kuma Jamcy wayo gareta bata fadawa Sabreen sirrinta sai dai dai, Motar Nawwar ce ta kunno Kai cikin gidan cikin jerin motocinsa yayi parking sannan ya fito ya samu Ladidi da kayanta tana kuka zata tafi,da sauri ya fito ya tareta Yana Tambayarta lafiya tace matarkar ce ta zazzageni sannan ta mareni,Nawwar zuciyarsa ta harzuko tsohuwa haka, muje Baba Ladidi tabi bayansa tana cewa ni gida zan koma na zauna gaban yarana har abada na daina aiki a gidan masu kudi Ina da gata na,suna shiga palon a tsawace yace ke har kina da damar Marin Baba Ladidi ubanki ta miki ya karasa Gaban Sabreen tace dan Iskanci na….Saukar Mari taji ba daya ba ta ko Ina,Ladidi tace na gode Alhaji ka rama min, Wayar tv ya fisgo ya tsulawa Jamcy itama ya haukace musu,Jamcy ta mike ta fice da gudu ta bar gidan Sabreen ma taga zai Mata illa ta buya a kitchen ta saka key, Kudade masu yawa ya bawa Ladidi tana ta godiya ranta fes an rama Mata ta tafi gida.

    Gidan ya zama babu me girki Kuma Babu me gyara ciki Sabreen tace itama ba baiwa bace baza tayi ba,Dakinsa ma da Kansa yake gyarawa,kullum ita Kuma sai baccin asara,Yana gama shanye maganin Iyamami sha’awa Kamar ta kashe shi kullum da kyar yake bacci,haka ya gaji zai Kai Kansa wajen Sabreen,yau 10pm a Palo ya sameta tana kallo sanye cikin rigar baccinta, karasawa yayi sanye cikin kayan baccinsa masu kyau silk milk, Yana zuba kamshi da mamakinta sai ta ganshi ya zauna a gefenta yana kallonta a hankali yace nazo karbar hakkina yau,ban gane hakki ba? yace Sex I need you,a ranta tayi dariya tace dan iska akace baka mikewa an fada maka ni ta Wasa ce ai dole ayi Mana biyayya dole na ja Masa aji sai yayi kuka ya tsuguna a gabana dan iska,a fili kuwa tace bana bukatarka ni Kam,kallonta yayi ya saki wata Yar budurwar dariya yace sabo da na kawo kaina hakkinki zaki sauke Nima na sauke nawa Kuma Ina bukata ko na taba hanaki wani hakkinki? banda wannan Kuma shima kin San banda lafiya yanzu lafiya ta samu,wani kallo ta Masa na baka Isa ba ta mike tace bani bukata ta haura sama tare da shigewa dakinta ta fada saman bed tana uban dariya tace zaka ci ubanka sai ka durkusa min, tana tunanin zai biyota sai taji Shuru har tayi bacci,Shi kuwa wani bacin rai ne ya mamaye shi Wai kamarsa mace tayiwa haka in banda kaddara ma me zaici da Sabreen tsaki ya ja tare da komawa dakinsa da kyar ya samu yayi bacci ranar.

     Washe gari haka ya gaza hakuri da asuba ya nufi dakinta ya shiga ya sameta tana baccin kwayarta tashin duniya ko motsi haka ya shirya ya tafi wajen aiki,Wanda suke karkashinsa yau ransa a bace Suka ganshi sai masifa yake musu da bala’i Wanda ba haka suka sanshi ba.
Yau ma da dare da wuri ta sheki kayan mayenta ta fada saman gadonta tana ta bacci indomie ta dafawa kanta shi kuwa sai dai yaci abinci a waje yanzu bai son hayaniya,sha’awa ta hana shi sukuni kamar ya mutu haka yake ji Amma Yana zuwa tana uban baccinta haka ya dawo,Wasa wasa har ya kwashe kusan sati ji yayi zai mutu idan bai samu mace ba,mararsa har ciwo take Masa kawai ya samu ya kawo ko sau daya ne, baya cikin hayyacinsa ya fito daga bedroom dinsa 10pm tana Palo tana kallo a hankali ya karasa inda take cikin takunsa na isa,baki ta tabe tare da daure fuska yace Wai me kike nufi ne ni bazan iya Miki ta karfi ba amma ki sani Allah yana kallonki Kuma kina cikin fushin Allah dan wlh bazan yafe Miki ba Matukar baki bani hakkina ba sabo da ke ba kanwar uwata bace, nace bana bukatarka dole ne Wai ta mike ta nufi dakinta tana karkada kugu Wai dan ya bita ta raina Masa wayo,shi kuwa ji yayi kamar zai mutu sabo da tsananin bukata tsaki yaja ya koma dakinsa yace matarka halaliyarka tana maka haka ga Mata can har gefen kwalta idan da kudinka sai abinda kake so wanka ya shiga a gurguje ya shirya cikin farin wando cif cif shi ya saka Riga arsh wata Yar dai dai shi daga baya tayi tsayi gaba Kuma ta dage designers ne,ya Sha takalminsa fari me kyau da tsada ya daura agogo Suma taci gyara Yana uban kamshin wani sabon turare me tsada sabon shigowa ba irin turaren da yake sawa bane a baya Wanda na sani yama daina saka wancen Yana yawan canja turare, Kamar a sace shi ya fito Yana takunsa na birgewa,wata motarsa ya zaba arsh katuwar gaske kana gani kasan akwai Naira ba karya,shiga yayi ya bar gidan,ita kuwa Sabreen Shaye shayenta tayi tare da kwanciy saman bed sai bacci.

    Kamar yanda na Saba fita har yau ban taba bin wani ba zabi nake yi Wanda har yanzu ba Wanda ya birgeni sannan ba Wanda yace zai iya biyan kudin da na saka,Wani guntun wandon ne a jikina Bumshort dark green me adon brown harda aljihunansa ko Ina da rigarsa irinsu daya Yar ficika da kadan ta wuce cikina me gajeren hannu da dan takalmina Snickers me kyau brown da Yar jakata me doguwar sarka brown,sai hular gashina baka me dogon gashi har baya sai kace baturiya haka na fito,Ina tsaye sai fitsara nake zubawa a kwalta ana ta kwashe Matan karuwan amma banda ni, dandaudu Wanda ake Kira da Santana wata mace Hajiya tayi parking tazo ta zabe shi harda balle Masa riga itama ta  shafa kirjinsa tace wow tana lashe baki tare da Jan hannunsa Suka shiga mota shima yayi kasuwa na tsaya Ina dariya yan daudu sai kasuwa suke,Nawwar a nutse yake driving shedan yana Kara ingiza shi,Yana tafiya Yana kallon gefen titi ai Kuwa ya karaso inda muke a saitina yayi parking karuwan suka taho kowacce tana jujjuyawa tana furta customer….bai bude motar ba har suka Gaji Suka ruga da gudu wajen wata motar, kallona yayi kadan tunaninsa ma arniya ce ni,Glass ya sauke kadan sai yaji na daga waya Ina gaiswa da Bala a kauyenmu Ina hausa,mamaki ya kamashi ashe bahaushiya ce musulma tunda yaji na furta ya Salam,Ina gama wayar na karasa jikin motarsa na juya tare da karkada Masa kugu,muryarsa naji yace ke….ai na kalleshi da sauri na zaci dan kasar waje ne ashe bahaushe ne a Raina na furta cab amma ya hadu sai kace zan suma,a fili kuwa nace customer ya akayi akwai fa GRA harda Grass carpet tsakani da Allah banyi aski ba yau satina uku ba aski kasan ba kowa ke son a salsale Local government ba idan baka so sai ka siyi shaver a aske yawwa, Shuru yayi Yana mamakin fitsarata,Jin yayi Shuru nace kalleni Alhaji yo Maliya ma haka ta ganni ta kyale na cika kogi ya Kai ya kawo,kirjina na girza nace full chest ba cuwa cuwa ko fulawa me kwabo albarka a laushi,yace let’s go kina bata min lokaci,nace wait muyi tsada kasan Ina da tsada sabo da ba cucuwa zan baka front and back harda Center ka daki harka,dan Tsaki yaja tare da furta ko nawa kike so zan baki,nace alright wooo karka yi Wasa dani akan balance Dina Zan iya maka rashin mutunci ko nawa na fada sai ka bani Ina gama fadar haka na bude gaban motar na Shiga sanyi da kamshi Yana ratsa min zuciya haka yaja motar Muka nufi wata GRA wani katafaren gida,sai naga kamar na sanshi amma ban iya tunawa, muna Isa me gadi ya wangale kofa ya shiga da motarsa duk na Zama Yar Kauye sai kalle kalle nake yi, na kalle shi tare da tambayarsa wannan gidanka ne? Kai ya daga min kawai Yana gaba Ina baya har cikin hadadden palon in banda kamshi da sanyi ba abinda ke tashi na sake kallonsa Karo na biyu nace Wai da gaske duk wannan gidanka ne ga motoci su ma naka ne? Ae yace a takaice,nace wow dan yaronka da kai ka tara arziki haka,wani bedroom naga ya wuce tare da bugo min kofar sai da ya tsoratani.

   Yana tafiya na mike tare da dira tsalle nace farkon farawa Kai Ina da nasibi gaskiya karuwanci yayi a rayuwa idan ba karuwanci ba ta Ina Zan hadu da Handsome haka Kuma na shigo irin gidan nan ai sai karuwanci ewoo Karuwanci yanzu na Fara ba fashi irin wannan arziki haka,maryarsa naji yace zo Ina jiranki,mikewa nayi da jakata a hannu na shiga bedroom din da ya shiga,ganin irin dakin sai da numfashina ya dauke sabo da tsaruwarsa komai kamar Palo Golden color,sanye yake da Jallabiya Fara Kal ta Masa kyau,yace make yourself comfortable nace kasan fa ba wani turanci na iya ba ka rage wannan big big grammar din naka,toilet na Shiga Naga sabon brush na dauka nayi brush tare da yin wanka na fito daure cikin guntun towel,zaune yake saman Sofa ya hakimce Yana latsa waya  nace Sir kana so ne a shafa turare a GRA din kasan ba kowa ke so ba sabo da karka tsotso turare a bakinka,yace duk yanda kika yi a ransa ya furta Karuwa sai abinda kace take yi amma matarka ta sunna baka Isa da ita ba, body spray na fesa nace sai aron rigarka idan Kuma haka kake so mu kwanta no wahala,ma’adanar Kaya ya nuna min na zabo T-shirt dinsa na saka ta min yawa tsayinta har cinya ta kawo min sai na barshi haka na adana kayana dana cire na maida towel din toilet na fito Ina kallonsa bai kulani ba sai na tuna yanda Saratu ta koya min yanda tace ana yiwa Namiji me aji,gabansa na karasa na tsaya sai naji kunyarsa abinka da baka taba ba

    Daurewa nayi nace Sir na Zama ready muyi abinda ya kawoni bana son dogon labari akan kudina yawwa,Wayarsa ya ajiye a gefe Yana kallona yace ke na Miki Kama da Mazinaci? Kallonsa nayi nace Kai Nifa Malam wlh dole sai munyi iskancin nan Kawai baza ta yuwu ka hanani kudina ba tafiya nayi na zauna saman cinyarsa sosai Muna facing juna,kokarin hade bakinmu nake yi ya kau da Kansa da sauri yace fyade zaki min ni da kudina nace ai wlh sai dai idan wandon karfe zaka saka,Kankame shi nayi yasa hannayensa Yana kokarin janyeni a jikinsa naki yarda,dama acikin yanayi yake kadan yake jira wannan kokawar da mukeyi itace tasa ya kawo Ina zaune daram akan Hajiya Babba,gani nayi Yana makyarkyata Yana tsuma Kamar mazari yayi sauri ya rungumeni Kamar zai fasa min Kashi yana huci amma a haka ya firtadagani da kyar yake magana da…d…dag…dagani..nace ni dai kudina wlh baka Isa ba sai munyi,Yana Gama releasing dinsa ya zubar da abinda ke damunsa a haka tureni yayi da karfi sai da na saki ihu sabo da azaba duk ya hada zufa,ban gane kawowa yayi ba ma na zaci kokawar da mukayi ce ta jawo, toilet ya shiga ya rufe kofa ya dafe kirji sai yayiwa Kansa yar dariya ganin irin ambaliyar da yayi yace shegiya karuwa amma Sabreen sai na dade bana Jin komai,wanka yayi tare da tsarkake jikinsa ya cire gajeren wandonsa da ya baci ya wanke tas ya shanya sai gani nayi ya fito sanye da jallabiyyarsa da gani wanka yayi,nace idan zafi kake ji ka Karo ac mana yanzu fa kayi wanka Kuma ka sake wani,Tsaki yaja tare da gasa min harara,kwarjininsa yasa nayi shuru na haura saman bed din na kwanta abina,Kaya ya dauka tare da ficewa ya canja, ya fice sai karar tashin mota naji bai dade ba naji ya dawo dauke da ledojin take away dauke da kaji da Madara etc, a gaban bed din ya zube min,na washe baki nace sai kace Amarya an gode na sakko Ina tsaye Yana zaune a saman Sofa Yana canja channel ya Kai channel din kidan Yan Nija Yana tashi kasa kasa Yana niyar canja channel yaga na Fara cashewa,baki ya bude a ransa yace kwararriyar karuwa ce, wai wannan wace ne? fitsararta tayi yawa dole naji wace ita, juyawa nayi Ina kada Masa mazaunai idonsa ya rufe da sauri da tafukan hannayensa kamar wani abu ya fada Masa a ido,dariya nayi na zauna na bude ledojin na dauki kaza guda a gashe Babu batun a balla da kadan Ina Sam da hannu biyu na rike Ina yaga,gashina na sosa dama tuni na cire hular gashi sai dogon gashina da yasha calaba,Ina ci Ina Kora lemo na Yana satar kallona mamaki fal ransa Ina gama ci na tashi na wanko hannu na  da baki na kwanta saman bed nan take bacci ya kwashe ni ban sani ba,dakin ya bar min ya koma wani dakin a can yayi baccinsa.

A dinga sharhi
Ina godiya fans

AsmaBaffa
🌼YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                21-25

Official

By
AsmaBaffa
08061929616

SADAUKARWA NE GA
DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Najida Aliyu Bicca
Zakiyya Bello
Mrs Mukhtar
Fulani Gal
~Fatima
Mama Gee
Ummu Muh’d Graphics Design
Maman Dr
Aunty Nurse Zaria

Jinjina gareku
Fancy Honey tawa
Ummin Sadeeq
Nice girl

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

 

       Washe da Asuba na tashi Alwala nayi sai nayi Sallah tare da azkhar na koma baccina abina sai 9am na farka a hankali na fara bude idona a saman Sofa na hangoshi yasha wanka cikin wasu kana nan kayan ya sani a gaba ya tsura min ido,da sauri na dago kaina nace lafiya? Kaga kazo kayi abin nan gashi har safiya tayi kazo kayi sabo da bana son sabon labari cewar ai baka yi komai ba baza ka biyani kudina ba bana son matsala,kallona yayi Muka hada Ido yace cikin izza Kamar bazai magana ba tashi muyi magana,mikewa nayi zaune a saman tsakiyar bed din Ina turo dan bakina gaba me kyau nace Ina jinka,ya kalleni yace ya sunanki? Cike da masifa nace Malam aiki nazo ka biya ni kudina Kar na tashi tafiya naji ba kudi wallahi sai na nuna maka inda mutunci yake ma ban nufa ba,bani da mutunci bani da kunya bana kunyar uban kowa karuwa ce ni yawwa Kar ma mu samu matsala ni imanina kudi ne,abinda nafi so a duniya na farko kudi,na biyu kudi na uku ma kudi,calm down Zan biyaki nawa ne kudinki ya tambaya, nace tunda naga kana da mutunci zan iya daga maka cinya a dubu dari biyu,Kika ce million daya? Nace Wasa nake ai sabo da yan rainin hankali nake cewa haka haba duk da cewa ni GRA gareni da ac da komai a cikin wajen ga grass carpet komai neat ai bazan wuce dubu dari biyu ba,yace zan biyaki double tsaya ki nutsu muyi magana,Ina jinka,ya sunanki cike da shagwaba nace sunana miracle,yace ba wannan ba na gaskiya Wanda iyayenki suka yanka Miki rago,nace sunana Rabiat,shine Kika canja na bariki da miracle? nace ai dama tun a kauyen mu ana ce min miracle sama sama Amma dai yanzu sunana na karuwanci miracle,yace Alright akwai kitchen idan Zaki ci wani abu,nace oh bari nayi wanka ko zamuyi tare? Fuska ya murtuke na mike na shige toilet wanka da brush nayi,fita yayi ya siyo breakfast lafiyayye yana dawowa ya iske har na shirya tsaf yanda nazo amma lipgloss na shafa Kawai sai powder da turare na fito palo,abincin ya Mika min na zauna a gurguje naci na koshi na mike nace zan tafi a zahiri ban koshi da Naman da ya siyo da chips ba ga jakata Yar karama ba dama na sace,sama ya haura yace min Ina zuwa nace to,na saci ledar Naman da chips din Ina boyewa a bayana ya fito ya kamani Ina boyewa a bayana,lekawa yayi da sauri da Ina Ina nace da..dama..c..ci zanyi Kuma yanzu ma na fasa bana son ci yanzu na maida da sauri inda na dauka na ajiye,Dollar ta kasar amurka ya irga ya bani,sai naji kamar na sanshi har muryar kamar na sanshi amma na manta Ina na sanshi,baki na bude yanzu nasan kudi sosai na karba baki hangame nace me nake gani kamar Queen Elizabeth? Wow dala wallahi,da dollar ka biyani baka taba ni bafa? Matsawa nayi jikinsa nace ga Nono shaba shaba ka taba ko na dubu biyar ne a cikin kudinka,yayi sakato yana mamaki ni kuwa dariyar farin ciki na saki na daga kafa na Sara Masa yanda sojoji ke yi nace yesss sir sai abinda kace daga yau,baya naja na nuna shi da yatsa nace Kai mutumin kirki ne,dole kaga daidai a rayuwarka,Sir Allah ya maka Albarka Allah ya biyaka,ubangiji ya tsare ka na daka tsalle na rungume shi sosai ina sheka dariya bai kulani ba ya tsaya kamar gunki nace zan tafi ko yaushe kaji kana bukatata ai Dole na baka ko ma kaga dama Ka fatattaka ni ,dariyarsa ya danne na juya nace na tafi har na fita na sake bude kofa na dawo da sauri na tsaya a gabansa nace zan nuna maka halacci duk Sanda ka nuna kana so na baka service zan maka abinda baka zata zan baka wuta Oga zan gama da Kai na kasheka da dadi bye na furta tare da daga Masa hannu na fice na bar gidan ina ta farin ciki.

    Ina fita ya saki dariya sosai yace Allah me iko dama haka karuwai suke wannan karuwanci baiyi ba a rayuwa Allah ka tsare mu ka tsare zuriar mu da dukkan musulmai,sai lokacin bayan ya karya ya fita ya koma gida Wanda har yau Sabreen baccin asara take fama ko Sallah bata yi ba.
Ni kuwa yau da murna da farin ciki na dawo gida,Ina sauka a napep na fito da dalolin Ina karkadawa Ina taku dai dai Ina tauna chewgum a Haka na shiga ciki sauran karuwai sai kallona sukeyi nace ya kuka gani na fara da kafar dama ni bana rabawa a 5k 2k me tsada ce,Yan daudun nan Suka fito Santana yace inyeee wannan waye haka gaskiya kinyi dace suna ta zuwa suna min murna,wise ta kalleni tace Yar Aikin karuwai Ido ya bude,Star ma ta karba ta irga tace a’a Yar Aikinmu tayi goshi taci gaba,Ina gadara nace da nace bazan yi sana’ar nan ba ashe aiki ne me kyau yanzu da na sa raina zanyi to na fara da zuciya daya zanyi harkar sai Kun tabbatar dalibar taku tafi malaman daukan darasi,shewa sukayi ana tafawa ana ihu,na shige dakinmu can na iske Seraline tana bulbula sigari hannunta Kuma cup ne na giya tana korawa,nace caji kike Yi kenan duk gidan nan Kuna shaye shaye ni dai bazan taba yin shaye shaye ba,baki Sera ta tabe tace karuwancin ma haka kika ce gashi Kuma kin fara,kallonta nayi nace kawata ya yau Naga kina cikin fushi ne? Sera tace ke dai bari wani banza ne shege ya daukeni ya nuna min me kudi ne ashe ba motarsa bace baida sisi motar ogansa ya aro ya bari na saki jiki da shi a gidan karki ga yanda yayi min kaca kaca ba style din da baiyi ba Ina tunanin na Zama big girl ashe me gadi ne a gidan me gidan yazo ya kore mu ya wulakanta mu in fada Miki sisi dai ban samo ba,dariya nayi na kwanta a gadon nace ke ya akayi haka Sera kece fa Kika koya min Harkar nan Kika ce Kar na sake nayi sex da Namiji sai munyi tsada ya bani kudina cash sannan na yarda da shi karki damu na samo kudi zan iya baki ko dala dari ce kya rage zafi na zaro dalolin a jakata nace Kinga wani me dabban kudi na hadu da shi in fada Miki ko tabani baiyi ba ya bani kudi haka,Nan take Seraline wani kishi ya kamata yarinya tazo a bayanta ta samu kudin da ita tunda take bata samu ba a duniya,ita dare daya ta samu haka Kuma ko taba ta ba ayi ba su kuwa sai sunci sa’a ake samun me biyansu 10k ma Watarana Kuma har 50k sukan samu, wani bakin ciki da hassada ya Kama Seraline itace fa ta koyawa Rabi Harkar amma tazo dare daya ta fita.

   Ni dai naga ranta ya Kara baci na nuna Mata dala dari dari nace kin gani yanzu zanje na canja a min transfer accnt dina ga dala dari in Kika canja ta Kai wajen dubu saba’in,Wata tsawa Saratu ta buga min tace bana son kudinki an fada Miki talaka ce ni,nace kyauta na Miki fa,to bana so ko dole ne ta ja tsaki,baki na tabe nace shike nan kinwa kanki na tashi na fita naje a layinmu dake wajen bariki ne komai akwai a nan na canja aka min tsansfer na cire dubu dari biyu naje shopping na siyo kayan sawa masu kyau kana kana iri iri harda Atamfa da leshi da material irin dinkakkun nan,na siyo takalma da jakankuna dai karfina ba masu tsada can ba amma suna da kyau.
Tunda na samu kudina washe gari hutawa nayi a gida ba inda naje,sai a kwana na biyu na fita yau ma ban samu Wanda ya min ba haka na koma gida abina.
Washe gari Kuwa na dauki wanka cikin legins fari da rigata blue na rataya jakata da takalmina me igiya flat me kyau na sa hular gashi brown color, Ina tsaye sai ga motar Nawwar ta tsaya Ina hangoshi ta glass zuwa nayi nace ni kazo dauka? Kai ya daga min ai Kuwa na bude gaban mota na shiga Ina girmamashi shegu kudi wani kwarjini da tsoronsa nake ji.

   Gidan da muka je Rannan shi ya sake kaini Muna shiga katuwar tv din a kunne take kidan turawa na tashi ban San Sanda na Fara bi da bakina ba Ina girgiza Kai tsabar rashin kunya da lalacewa wanda ta hadu ta min yawa,dama ance a kiyayi irinmu na Allah idan Muka tashi lalacewa abin ba kyau, Kamar me shaye shaye ko Sabreen uwar Yan Coccaine baza tayi abinda nake ba,remote ya dauka ya canja channel ya Kai news, saman kujera na fada na zauna Ina Sosa Kai kunyarsa ta kamani sabo da baida Wasa Kuma ya tsare mutuncinsa ga uwa uba kudinsa tsoronsa nake ji,Shuru nayi na nutsu Ina Wasa da yatsuna,kallona yayi ya jefo min tambaya yace me yasa baza ki daina karuwanci ba baidace dake ba,gaki kin Kai mace Kuma musulma hausa Fulani ace kin maida kanki Yar kwalta mene dalili ai gwara kiyi aure,nace aure fa kace? Ni nayi aure tab ai ni ba ta gari bace Kuma bani da asali ba ruwana bazan dorawa kaina ba azo a dameni ana ce min karuwa marar asali ba ruwana Kai nifa bata gari bace da har Zan samu Miji nayi aure ni Kam baruwana,sana’ata Kuma Ina sonta akwai nishadi ga yanci inci gashin kaina,yace ba kudi kike so ba? Nace sosai ai ni bani da Kamar kudi a duniya,to Zan na biyanki Albashi duk wata ki zauna a nan gidan ki daina karuwanci,kallonsa nayi nace idan kasan zaka biyani kudi yanda ya kamata Zan iya gwada Zama amma idan na gaji Naga bazan iya ba Zan koma inda na fito,yace Zan dinga biyanki da tsada ki zauna a nan,Nifa bazan zauna ni kadai ba ko ma mene sai dai in kana gidan nan sabo da ni na Saba da surutu idan ba kowa da wa zanyi Hira sai kace Ina prison,yace Alright Zan zauna Indai Zaki daina Zama a titi ana daukanki ana sex dake uban kowa bakya Jin kazanta ko wanne Namiji ya jaki wannan kazanta ce,baki na bude nace ahhh Antaina ai tayi a rayuwa Mene abin kazanta Kai…..shut up ya furta a fusace,Shuru nayi

    Shuru mukayi yace Ina Neman Alfarma a wajenki tunani sex zai ce muyi yanda ya kyautata min da sauri na mike na fada jikinsa tare da cewa gani an gama muyi, yace no ba wannan ba,na sake cewa gani kayi ko Mene,yace ba shi nake nufi ba,komawa nayi na zauna tare da furta okay Ina jinka,yace Ina da aure Kinga dole Zan dinga kwana a wajen matata ba kullum zan na kwana a gidan nan ba,nace ba damuwa Indai zaka biya ai an gama,yanzu Naga gidan nan da kayan abinci komai akwai sai kudin siyen nama da kayan Miya tunda Zan na girki,yace Ina sane Zan baki gobe da rana sai ki fara nace to,canja min channel Nigerian film nake so,haka ya kamomin tashar yace gashi wannan ce me sa latest film kullum,okay na furta Ina murmushi, mikewa yayi zai fita,da sauri nace Ina zaka je? Wajen matata,ka gaishe ta,inji wa zance ya furta ko Murmushi babu a fuskarsa,inji Karuwarka zaka ce,hmm Kawai yace ya fice Yana fita nace ban zo da Kaya ba sai dai na dinga saka naka Amma ba kyau saka kayan maza to ya zanyi tashi nayi tare da yin wanka na linke kayana na zaro gajeren wandonsa na saka har gwiwa ya kawo min Yana da Fadi na zurma rigarsa wata me santsi milk me dogon hannun,hannun gaba daya hannayena sun kule a ciki, Ina Fitowa na zaga gidan na Sha kallo sannan na dawo wajen me gadi na kalle shi shima kallona yake yi sanye da kayan ogansa yace Sannu Hajiya,Murmushi nayi tare da tambaya ya sunanka? yace Ilu sunana Yana zaune saman wani dogon bench nace Ilu dan matsa gefe na zauna,Ilu ya matsa gefe na zauna a gefensa dama matashi ne,nace Ilu Kai Dan wanne state ne? Ilu yace Hajiya ai ni dan Kano ne a garin albasu cirani nazo Allah ya hadani da Ogana,nace ashe garinmu daya,yace yanzu a haka ke bahaushiya ce Yar Kano ma musulma Kuma? Nace kwarai kuwa kasan karuwa ce ni  amma karma ka fara tunanin zaka kulani ko da wasa kazo sai na fasa maka Kai da kwalaba bana yi da irinku sai me kudi ko da kudinka sai da rabonka,idan ka kawo min raini Sai na sake Yi maka sabuwar kaciya da girmanka, ka ganni paradise kenan ta duniy ..horn Muka ji Ilu ya tashi ya bude gate Yana dariyar maganata shi ya Isa ya kula matar da ogansa ya kula,Nawwar ya shigo da wata jar mota ba irin wacce ya fita da ita ba,Ilu dawowa yayi ya zauna Muka ci gaba da labarin mu sai ga Nawwar ya fito ya hade rai tsoro naji Zumbur na mike nabi bayansa da sauri,ledojin hannunsa na karba Ina cewa Sannu da zuwa Oga, muna shiga Palo ya dinga balbala min masifa bana son rashin kamun Kai,me gadin zaki fita a haka kalli kaurinki duk a waje surarki ta fito a cikin kayana zaki fita harda Zama a gefensa bana so respect your self,dan bakina na turo gaba Ina Kunkuni Ina tsoron fada Masa magana nace ni sabo da Allah shike nan bani da yanci ka takura min a cikin gida,shut up….ya furta a tsawace,Shuru nayi Ina doka kafafu tare da kukan shagwaba nace ni na takur…quite ya min tsawa nace Hmmm ummmm ahhhhh uhmmm….harara ya watsa min nasa hannuna tare da toshe bakina na tsaya gefe tare da yin kasa da kaina,waye yace ki saka min kayana da wannan kazamin jikin naki duk maza sun gama da shi,Murmushi na saki nace neman kudi ne kaima in kana so kazo naka sai yafi na kowa na karaso gaf da shi,hannunsa na riko ya fisge abinsa ke bakya tunanin shedan ko Ina so na rabaki da masifa kina sake jefa kanki,to Ni kadai ce ga wasu can Ashawon ka raba wata da karuwanci mana dole sai ni,kalleki bakya kunyar kanki,bakya tausayin iyayenki,bakya tunanin ayiwa Yan uwanki abinda Kika yi ko kannenki, da karfi nace hehe ai bani da kowa Yar shege ce ni,bani da kanne bare yayye bani da kowa kaga ni kadai ta shafa Kuma ba aure zanyi ba bare ayiwa yarana, abinda Iyayena sukayi suka haifeni shi nake yi,Yan Uwa ma banda kowa a duniya ni kadai ce a duniya sai kuwa na fara hawaye ban San Sanda na Fara zubar da hawaye ba kuka ne ya kwace min sosai na Shiga yinsa a tsaye,baki ya saki Yana kallona,na kalleshi idona jage jage da hawaye na karasa gabansa nasan idan yasan Zan rungume shi bazai yarda ba sai nayi wuf na fada jikinsa Ina goge hawayena kamshinsa yasa har wani lumshe Ido nake nace please ka lalata ni,dan Allah muyi iskanci,tureni yayi da karfi na fada saman kujera yace look bana son Iskanci Ina Wasa dake ne? Zan daina zuwa gidan nan Kuma wallahi zan kulleki a gidan nan babu ta inda Zaki fita ki koma hankalinki ni ba Dan Iska bane,duk lalacewar da Kika yi wacce kike so kiyi Kuma,Shuru nayi ya Gama sababinsa ya haura sama abinsa,baki na tabe nace ai dama na sani da ganinsa nasan Dan love ne da alama ya iya soyayya matarsa tana Jin dadi.

     Tashi nayi na haura sama nima dakinsa na kwankwasa yace shigo,shiga nayi Ina Sanda Ina tsoronsa Yana min kwarjini nace ya sunan matarka? yace Sabreen Kai na jinjina nace tayi sa’a tana kula da Kai ba ruwanka da karuwa, wani mugun kallo ya min nace na janye maganata bata kula da kai,amma kaje can wajenta Mana zan iya zama ni kadai kaje ka bata kulawa,ko kulani baiyi ba yana latsa wayarsa abinsa na gaji na fice,abinci naje na ci abina na koma dakina na kwanta sai bacci me dadi.
Cikin dare ya bar gidan ya koma gidansa Yana zuwa gida Sabreen ya iske a Palo yau bata bacci anci kwalliya sallama yayi ta amsa Kawai,gani yayi yau ta gyara gidan ko Ina fes yasan da wata a kasa,ai Kuwa yayi Shirin kwanciya sai gata cikin kayan baccinta wata munafukar riga maroon,ko kulata baiyi ba yayi kwanciyarsa zuwa tayi ta kwanta a bayansa tana faman tattaba Masa kunnuwa karshe taga ko kallo bata isheshi ba ta rungume shi tana so ta motsa Masa sha’awa hannunta ya janye daga jikinta yace ba nason naci fa bana bukatarki karki dameni,kankame shi ta sake yi tana rokonsa please harda kuka tace yanzu idan banzo wajenka waye zai biya min bukatata ko so kake Yi na Fara bin mazan banza yau nafi wata hudu sau daya ka taba sex dani, karki bata min rai Sanda na dinga binki wanne wulakanci ne baki min ba karki bata min rai wlh sai na tashi na Miki dukan tsiya gwara ma ki kyaleni,kuka ta fashe Masa tana shike nan tunda so kake na Fara bin maza da aure na,tashi yayi zaune ta bashi tausayi ko ba komai macece tana da rauni,yace badan halinki ba dai gani kiyi,au ba Kai ma zaka min ba Kinga idan kina so a haka to ki Fara idan baki so ki Kara gaba,ba yanda ta iya haka ta zare Masa riga ta shiga sarrafashi amma ba wani zaucewa da yayi yaji dai dadi tunda ya Zama dole,gani yayi ta wahala sosai ya fara sarrafata amma ba sosai ba duk ta susuce harda cewa i love you abinda babu Wanda ya taba fadawa wani a cikinsu

   Shigarta yayi sabo da shegen baccin kwaya bata gyara kanta tana nan a wangale sai kace kofar gari,haka ya dinga Mata aiki ta Fara kawowa tana Jin zai kawo Kawai ta zare jikinta cikin zafin nama tana Sosa Kai tace bana so na haihu yanzu,wani bakin ciki ya Kama Nawwar a waje ya zubar da abinsa,ya kalleta ransa a bace yace karki ce ban fada Miki ba bazan sake kwanciya dake ba,tunowa tayi da hudubar Papa Kan tayi sauri ta samu ciki,hakuri ta shiga bashi tace Dan Allah kayi hakuri wlh Zan haihu ka yafe min,Tsaki yaja ya Shige toilet yayi wanka tare da tsarkake jikinsa Yana Fitowa Jallabiya ya saka a daren taga ya dauki key din mota ya fice, baki ta tabe tace cikin ma sabo da Papa Zan yarda nayi kafi ruwa gudu ta mike ta koma dakinta yau bata Sha komai ba bacci ya kwashe ta.

    Gidan da ya kaini ya dawo lokacin nayi baccina na farka na fito palo Ina kallon wani hadadden American film adventure ne a MBC2,shigowa yayi ransa a bace sai da naji tsoro,remote din dake hannuna na ajiye nace Sannu da zuwa,Hannu Kawai ya daga min,nace lafiya Oga? Tsaki yaja tare da furta ba komai,mikewa nayi na shiga kitchen na zubo Masa fruits salat din Dana hada lafiyayye yayi sanyi a daren nayi, Mika Masa nayi ya tsaya Yana kallon glass cup din nace ko na baka a baki, karba yayi yasha yaji yayi dadi sosai yaci gaba da kurba har ya shanye,nace fada min me ya faru? Waye ya taba min Oga?  Ido ya lumshe na matsa kusa dashi nace ga fuskarsa ta nuna ogana yana da damuwa ,yace ba huruminki bane abinda ya shafeni,Ni ai ka dauke ni sister dinka ka fada min ko zan iya baka shawara kasan mu karuwai mun san ta duniya,kallona yayi yana tabe baki yace fada mukayi da matata,nace dama nasan itace ai tunda naga ka dawo nasan da matsala,shine abin damuwa kana bata ranka akan mace,mace me rauni sai hakuri,ka dinga hakuri,ya kalleni yace kina wa’azi karuwa dake,a kula da fadar Malam Kar a kula da aikinsa na furta,yace ban San me yasa ba wasu dangina basa Sona,nace to sai me yanzu dan wani baya sonka sai ka tsaya kana batawa kanka lokaci,tunda kana kaunar kanka Allah Yana sonka ai ka gama,ko kowa baya sonka ai Allah yana sonka ko to mene na damuwa ai Kawai kayi komai ba komai kafadarsa na dafa nace kayi nishadinka Master kowa yaci kutmar….na dirko ashar,dariya na bashi yanda nake magana kamar Ina yi da duniyar gaba daya duk na tashi hankalina.

    Dariya yayi sosai na tsaya Ina kallon irin kyan da yayi nace zaka ci indomie? Yace a yanzu Zaki dafa? Wai bakya bacci ne? Mu da bama bacci sabo da Aikinmu da muke fita sai mu Kai 5am bamu yi bacci ba sai da rana muke bacci,kitchen na Shiga sharp sharp na dafa indomie taji hadi da kwai na zubo Mana a plate daya da fruits salat din na kawo na zauna a saman center carpet nace sakko mu ci,yace bana zama a kasa ni,Kuma bazan ci dake ba ki bani tawa daban,Haka na koma na rabata biyu na zuba Masa tasa  daban komawa nayi saman kujera na jawo center table gaban mu na bashi fork spoon daya Nima na rike daya nina Fara cin tawa sannan yaci tasa yaji dadi sosai bai taba cin idomie me dadinta ba,Yana cinyewa ya haura sama dakinsa ya kwanta bacci ya gama da shi,Ni Kuwa a palon na bingire sai da asuba na koma dakina bayan nayi Sallah bacci na koma,shi kuwa masallaci yaje daga can gidansa ya koma.

    Saurayin Gaji Alhaji Kabiru Danbinni duk wata yaudara da ya so yayi wa Gaji ya samu yayi sex da ita amma taki dake zaman aji ba karya,gashi Yana mugun sha’awarta Kawai sai yace zai aureta zai turo manya,Dagaci ba wani bincike Kawai yace a kawo kudi sai Murna suke Gaji har rawa kafa ake Yi an samu Alhajin birni gashi katon gaske ga kiba ga tsayi babban mutum suna kawo kudi aka yanke ranar aure wata biyu masu zuwa,Aunty Amarya tace to da ace shegiyar Yar tsuntuwar tana nan da Kinga Yasin Alhaji Kabiru Danbinni ita zaice Yana so ba Gaji ba,Gwaggo tana yanka Kubewa tace kyale aljana kyawunta suke bi amma Wai duk Yan kauyen nan talakawa basu cewa suna sonta sai Yan birni masu kudi matsiyaciya yanzu wa ya sani ma ko ta shiga karuwanci,Dama ai karuwanci zata shiga me zata Yi idan ba shi ba ana can ana bin maza cewar Aunty Amarya,Mairo tace nidai Ina Jin tausayinta wlh Allah yasa baza ta lalace ba Kar ta samu cuta ta mutu,Gaji tace to ke Ina ruwanki ni zancen Yarinyar nan idan Ina kauna Allah ya konani,hirar aka canja suna ta Shirin bikin Gaji abinsu.

    Papa ne a zaune yayi tagumi,Mama ce ta fito tare da tambayarsa lafiya? yace Wai Sabreen me take yi ne har yanzu bata samo min ko takarda Daya ta fili ba kin San ance kadarorinsa kusan gaba Daya a Arewa suke Kinga anjima kije gidan nan kiji ya ake ciki ne ki sake koya Mata dabarun mallakar kayan miji,nisawa Mama tayi tare da furta Yarinyar ce bata ganewa kasan shaye shayenta bazai Bari ta tsinana komai ba amma zanje gidan yau,yawwa kije dan Allah yaron nan naji ance sake bunkasa yake Kuma Ina gani a jikinsa tunda kusan kullum sai ya zo gaishe mu sai kafirin wayo da son kudin tsiya baya Wasa da dukiyarsa,Mama baki ta tabe tace ni ai bai taba bani sama da dubu ashirin ba sabo da Kar nayi arziki da shi,ke dai Bari idan abin yaki dole sai na hada da malamai anyi min aiki a kansa,yafi maka cewar Mama.

      Jamcy a hankali sanadin yawan zuwanta gidan Sabreen tana ganin Nawwar gaba daya ta fada kaunar Nawwar mijin kawarta,kwance take a dakinta saman makeken gadonta tunani takeyi yanda zata bullowa abin har ta samu ta auri Nawwar ta Shige gidan ta zauna ta kula da shi tunda tasan sirrin kawarta ta kasa zaman auren ta rike mijinta sai shaye shaye,a fili ta furta babu Abu me saukin samu irin kwacewa Sabreen miji tunda ta sake shi sakaka lallai Sabreen zata ci ubanta sai tayi danasani watarana,nan take ta jawo wayarta ta Kira Sabreen bugu daya Sabreen ta daga tana cewa kawata ta kaina,Jamcy tace ya gida ya aiki Ina tausaya miki ga kula da gida ga kula da miji aiki ai Kuna shanshi masu aure,Sabreen tace wa? Kema kin San banda ni tsinke bana dauka a gidan nan abinda Naga dama nakeyi,dama ni kin San fita yawo bai dameni ba nafi so na Sha kayan aiki nayi bacci,Jamcy tace gaskiya kina hutawa ai auren irin Nawwar yayi ba takura kayi abinda kake so,Sabreen tace hmm jiya ne kadai na zage na gyara ko Ina sabo da Ina da bukatarsa naje na lallabashi ya dan sassakeni naji dadina shike nan na Kama gaba na yanzu Kuma sai wani jikon,dariya Suka kwashe Jamcy tace amma shima yaji dadin ko na sanki da mugunta Ina fada Miki na rigashi kawowa yazo zai kawo kin San a duniya maza nan wajen kawowa shine Jin dadinsu da komai ai jikina na zare sai a waje ya zubar yaji haushi har yanzu yaki hakura da abinda na Masa,zanso kiga fuskarsa,Jamcy tausayin Nawwar taji tace baki kyauta ba wlh ya kamata ki haihu da shi fa kar gado ya wuceki,Sabreen tace ai shi yasa na bashi hakuri so nake nan gaba idan mun sake ya kawo a ciki na samu cikin,yafi Miki dai ni jibi zanzo miki cewar Jamcy,Allah ya kawoki tace ameen tare da katse Wayar.

    Ni Kuwa da safe da wuri baccina ya Kare domin mu bamu Saba bacci mu dade a kwance ba munfi Yi da rana sabo da wajen karuwai ne ba a hutawa Kuma mun Saba karyawa da wuri,lokacin Ina Yar aiki ma da asuba bana komawa bacci nake dafawa masu dawowa da safe abinci sabo da haka tuni 8am na tashi na gyara gidan nan ko Ina sama da kasa, compound Kuma me gadi ne ke gyarawa bedroom dinsa na Shiga na kwashe kayan da ya cire jiya duka na wanke su a injin wanki na shanya su,nabude ma’adanar kayansa  Naga kudade daloli da Yan dubu dubu bundles da yawa na maida na rufe Masa ban taba ba na gama gyarawa na saka turarukan daki na kamshi ko Ina ya dau kamshi na kulle na kunna ac sannan na fito tare da kunna tv na shiga kitchen,tunani na farayi na dafa da shi ko na barshi a raina nace Kar Kuma yazo ta nan nace Kai idan ma baizo ba na bawa mabukata,na fara soye soye na Yan gayu me dadin gaske Zama da Yan duniya yasa na goge da girkin zamani,sai da na gama na dafa tea da kayan shayi dana gani na zuba a flask na shirya komai a dining na kawo komai na ajiye na mutum biyu,wani Kuma na dauka na fita na kwalawa Ilu Kira Wanda Ilu a waje yake cin abinci yaga breakfast lafiyayye ya dinga murna yace Madam na gode nace ba komai, wanka naje nayi a dakinsa Kawai Naga body lotion da tarkacen turaruka nasa lotion din na maza na shafa na dakko wata jallabiyyarsa brown na saka har kasa take ja da na saka komai ya min yawa haka na burmata na saka hular gashina na fito kenan Naga an bude kofa an shigo shine ya dau wanka yayi kyau matuka,na kalleshi nayi Murmushi tare da cewa Sannu da zuwa,bai kulani ba ya koma kujera ya zauna har gabansa na karasa na durkusa na furta Ina kwana ka tashi lafiya? Lfy Alhmdllh yace da dan sakin fuska, nace Office zaka je ne? ae yace min kawai,nace ga breakfast ko kaci a gida? yace sauri nakeyi ko a gida ban tsaya naci ba bare a nan, nace dan Allah kaci to ko kadan ne ya min yawa na Riga nayi da kai,nace kiyi girki dani to na rigada nayi dan Allah taso na rike hannunsa tare da jawoshi taso please, hannunsa ya fisge yace ke ki shiga hankalinki fa ba dan iska bane ni,nace Ni ai itace Yar iska ce karuwa tashi dan Allah,a ransa yace Allah me iko matata bata bani abinci ga karuwa na rokona naci abinci Sabreen Ina hankalinki yake ne ya furta a ransa,mikewa yayi tare da Kai hannu zai gyara rigarsa data nannade na rigashi Kai hannu jikinsa ina gyara Masa nace ka gani zaka yamutse baka je Office din ba,shi dai sai Ido Kawai ya sa min kujerar dining na ja Masa ya zauna sannan na bude Masa duka abinda na dafa kamshi na tashi nace me zaka iya ci a ciki? duka ya furta,nayi serving nasa nace tea da Madara? Yace ae na hada Masa na juya na dandana tare da furta sugar yaji na tura Masa gabansa nima na hada nawa ina ta cin abina shima yana cin nasa gaba daya na cinye komai dana kawo Banda nasa yace ke haka kike da cin tsiya? Nace ae ai ni rikona sai Gomnati sai mutum ya shirya,yaci ya koshi ya rage na dauke na cinye tas na Kai kwanikan kitchen na wanke su na fito na gyara dining din Yana kallona,yaje duka gidan sai da ya duba ko Ina yasha gyara ya fito yace kece du Kika gyara? Nace ae,yace to a samo Miki miji Mana kiyi aure Kawai duk kin iya wannan wai kika zauna bariki,Nace bariki ita na iya ni bata gari bace me zanyi da aure,ai kowa ance ka samowa yaranka uwa ta gari mace ta samowa yaranta uba na gari ni bana cikinsu taya zan cuci yara nayi aure na haife su suje su gajeni a bariki,ya kaga yanda nake Karuwar nan na haifo mace ta fada bariki na kyalkyale da dariya nace da na shiga Uku Kawai haka rami zanyi na binne kaina,dariya ya saki ba shiri yanda nake Abu kamar yarinya Ina tsaye Ina tsalle tsalle Ina zuba zance,nace kayi kyau in kana dariya kana kyau nace kaga Kai zaka Yi dadi fa da gani hariji ne kai ka dace Dani Allah muyi karuwancinmu daga Kano sai Kaduna Mene a ciki

   Fuska ya bata yace Kinga bana son zancen nan,nace to kowa ya siyi rariya ai yasan zata zub da ruwa in ka gaji ka maidani inda ka dakko ni mana,dama har ga Allah na gaji ji nake kamar Ina kurkuku ya ajiyeni waje Daya mu mun Saba yawo bama Zama a gida so nake ya gaji dani ya barni na tafi shi yasa nake Masa haka,tashi yayi zai tafi Office nabi bayansa har mota na rakashi sabo da duk na koyi yanda ake wa Namiji wajen su Yarzabil sabo da kudi sukeyi Kuma haka Saratu kawata ta koya min,kudi ya Miko min tare da furta karki sake ki fita a gidan nan ko me kike son siya ga Ilu nan ki rubuta Masa zai siyo Miki,kunnena ya Kama da karfi sai da nayi Kara yace kin jini ko? nace ae washshsh…..sakar min kunne yayi yace sai Yamma zanzo ki shirya Zan kaiki shopping a siyo Kaya na mutunci ki daina saka min kayana okay nace tare da daga Masa hannu Bye na koma ciki,direct bedroom na fada na kwanta na dinga sheka uban bacci.

    2pm na tashi Ina yin Sallah na koma bacci na sai 4pm na tashi Ina Sallah na fada kitchen nayi white rice taji su green beans na shirya miyar jajjage ta Sha kifi na hada couslow, Me gadi na zubawa nasa Yana ta Jin dadi ya karba Yana godiya,wanka nayi na dakko wata jallabiyar milk me hula na wanke wacce na cire na zauna naci abinci na koshi sannan na gyara wajen da kitchen,kayan da na wanke na tattara na goge Masa sun bushe tuni ma,  na adana a inda yake ajiye kaya,Ina daki Ina murza powder sai gashi ya shigo sallamarsa naji,da sauri na fito palo ya kalleni yace ki daina saka min Kaya na fada Miki,gabansa na koma Ina murmushi nace to wanne zan saka? Shuru ya min nace abinci fa? kaci kafin mu fita mana,hannunsa na rike me mugun laushi,tsigar jikinsa ce ta tashi yaji wani yarrrrr ko Ina a jikinsa hannunsa yayi kokarin janyewa,nace da shagwaba sai fa kaci abincina rungume shi nayi wani Tsaki da yaja da sauri na matsa gefe daga jikinsa harara ya watsa min tare da Jan kwafa,sorry na furta kaina a kasa,dining ya nufa nayi serving nasa yaci yaji wani shegen dadi ai sai da yaci da yawa ya koshi yana Shan lemon dana hada, let’s go ya furta Yana Shan ruwa tare da kuskure bakinsa da ruwa ya hadiye,na rataya jakata babu ko dankwali sai hular gashina babu mayafi a gidan haka Muka tafi ko a jikina.

    Gaban mota na bude na shiga shi Kuma ya zauna a mazaunin driver Yana tashin motar na kunna Mana kida ya kalleni yace malamar kida horn yayi me gadi ya bude gate muka fice zuwa katafariyar shipping mall.

     Parking yayi ya fito Nima na bude na fito Muka jera da jallabiyata yace Dora hular rigar taki a kanki yanda yace nayi na saka hannuna cikin nasa Muka shiga a haka Yana ta so ya kwace hannunsa amma naki yarda a hankali yace ba kyau fa, kukan shagwaba na fara masa, yace zaki tara min jama’a fa naji muje,Shuru nayi muka tafi a haka.

    Dogayen rigunan ya siyamin ready-made masu tsadar gaske wasu Yan Egyft,wasu Turkish,wasu Yan Saudi sai namu irin materials kala kala da ake musu digayen riguna masu kyau buba gasu nan dai,takalma da jakankuna ya siya min iri iri da mayafai irin na Yan Mata inner wears gasu nan da yawa iri iri,kayan bacci sai kayan makeup Suma na zaba,Muka koma layin sarka da Yan kunne,ribons etc,ya kashe kudade sosai muka kwaso kayan ya kwaso wasu nima na kwaso wasu Muna zubawa a bayan mota sai ga abokinsa Khaleel,yayi mamakin ganinsa da wata da bai sani ba amma ya share ya karaso inda muke

     Khaleel sallama yayi Muka amsa ya kalleni ya kalli abokinsa yace Nawwar daga Ina haka? Nawwar gabansa ya Fadi baya so kowa ya sani ya ganshi tare da ni,Ni dai nace da Khaleel Ina yini ya amsa Yana min wani kallo, Kawai yaci gaba da magana da abokinsa suna hirar Office,gajiya nayi na dafa kafadar Nawwar nace na gaji mu tafi gida,wani harara ya zabbaga min na tona Masa asiri Wai,Khaleel yace akwai magana kuje kawai yayi gaba,muma mota Muka shiga Yana min fada wai sai kin tona min asiri a ko ina,nace nifa kaga karka dameni in ka gaji ka rabu dani na koma inda na fito baza ka takura min ba,shut up baza a barki ki tafi ba din,Shuru nayi naji tsoro baki na turo masa tare da dora kaina a kafadarsa yace daga min jiki bana so babu kyau fa Kuma ke musulma ce Allah yana kallonki, to sai hakuri ka hadu da balagaggiya,sabo da ya gaji yace nafi karfinsa ya barni na tafi nace na tara ruwa dan Allah yau ka dan nausa cikin ae…na kalleshi na daga Masa gira, a ransa yace na shiga Uku da kaddararriya yarinya ta isheni da Iskanci a fili kuwa ko kulani baiyi ba,na sake cewa dai dai da Kai ce ni Allah Harija ce ni zaka ji dadi,Ina da Mata fa yarinya nace ni Ina ruwana da matarka mu babu abinda ya damemu,a ransa yace ni ya zanyi da ita karfa jarabarta tasa taje wajen wani ya biya Mata bukata to yau dole na kawo securities gidan nan suyi gadinta.

    Ina jinsa Yana waya da securities yace Yana son mutum biyar, Muna komawa gida ya tayani Muka kwashe kayan tas har dakina na zube naje nayi Alwala yaga na dakko wani hijab dan madaidaici na saka,yace dama kina da hijab Amma Kika ce ba komai da zaki sa Muka fita a Haka? Nace na Sallah ne duk inda naje idan zani aiki da shi nake tafiya sabo da Sallah,mamaki ya kashe shi yace kina Sallah? Nace sosai ai Sallah bata wuceni,yace to ba a karba da ana karba da baza ki lalace haka ba,me yasa Kika lalace da yawa haka? kallonsa nayi nace burina nane tare da tada sallah,na tafi sai da safe ya furta abinsa ya wuce.

Securities ya kawo gidan yace Kar a sake a barni na leka ko bakin gate Suka ce an gama ya tafi,suna ta tsaron gida ai Kuwa yau na ayyana zanje can gidanmu na sanarwa Kawata Seraline Ina gidan saurayina dan Ni tuni ma na sa Masa suna saurayina,na saka kananan kayana da nazo dasu jiya na fito Zan tafi naga sojoji a gidan mamaki Ina takowa tsakar gida Suka daka min uwar tsawa,na kalle su sojoji ne ba raini salin alin ban sake gigin lekowa ba,haushi da Takaici ya kamani.

   Dagaci Yana zaune suna hira da Aunty Amarya Suka sako zancen Rabi,Dagaci yace shegiya tana can karki fadawa kowa bakinki kanin kafarki tunda na koreta da wata shida na kasa hakura sabo da karma ta hadu dana gari ko me kudi sai na koma gidan malamina Malam ya’u nace ya sake cillata Kar tazo garin nan ko da wasa sai ya bani shawara ko a sa ta fada duniya lallai ta koma bariki duk inda taje kawai ta zama yar duniya karuwa zata je a sa Mata son karuwanci lallai ta fada cikinsa tsundum ai Kuwa nan take na yarda ba karamin kudi na kashe ba kafin ayi aikin,ni Sam bana kauna Yarinyar nan ta nuna ta Sanni ma,Yar tsuntuwa yo ai Yar shege ce gwara ma daka Kara cilla shegiya bariki cewar Amarya, Dagaci Yana dariya Yana Jin dadi,Shi a duniya haka yake da hassada a garin kowa ya sanshi,Hassada ce tayi Masa yawa yafiso Kawai ace daga shi sai Yaransa sune zasu ci gaba a rayuwa kaf garin haka yake wa mutane hassada Indai Allah ya daukaka ka baya kauna,idan talaka ne Wanda yake cikin wahala to Inshaallah shine abokinsa,Amma da ka samu kudi to ya daina kulaka wannan har yaransa da matansa haka suke a kauyen kowa taka tsantsan yake dasu.

AsmaBaffa🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                  31-35

SADAUKARWA NE GA DUK YARAN TSUNTUWA

 

Official

By
AsmaBaffa

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

Page naki ne
AUTARESS

       A wajen ta zauna ta bude tana ci tana Santi duk ta gigice sabo da dadin naman harda cewa dan Allah a Ina ka siyo? Sunan wajen ya fada Mata,bata San Yan bariki da sanin waje iri iri ba ko Ina sun sani komai na manyan Yara sun San da zamansa sabo da gantalinsu, sai data gama ci sannan yaci nasa ya koshi ya koma dakinsa yayi Shirin bacci yana kwanciya ta shigo dakin cikin matsiyatan kayan baccinta yasan me tazo nema dama ya gaji da kulata suna hayaniya tana kwanciya ta Fara murza shi biye mata yayi Kawai sabo da ya bata hakkinta haka ta samu abinda take so wannan karon a ciki ta bari ya zuba Mata sperm dinsa ciki take so ta samu, shi bai sani ba yana saduwa da ita yajita a wangale ba gyara Kuma yasan farko ma haka ya ji ta,dannewa yayi kawai ya zaiyi da kaddara tunda ta same shi,badan Yana tsoron Allah ba da tuni ya fada neman Mata sosai, Yana wannan tunanin bacci ya dauke shi yau itama a jikinsa ta kwana bata Sha komai ba, sai da safe tana yin wanka ta tsarkake jikinta taje ta dafa zallan ruwan zafi empty ta zuba a cup ta hada Madara da Milo ta Sha tea dinta da bread da ragowar naman jiya,sai da ya fito Sunday ba aiki zai fita sanye cikin 3qrt da riga me gajeren Hannu marasa nauyi ne sosai,Wai a tunaninta ta bashi abinci tace ga ruwan zafi kazo ka hada tea in zaka Sha,ko kulata baiyi ba ya fice daga gidan,Yana fita tace kai kaga duhu tana gamawa ta maida kwanikan kitchen anci sa’a ta dan gyara gidan sama sama gashi nan dai ta koma dakinta ta Fara shaye shaye ta fada saman bed tana shakar hanci idonta nan take yayi jajir da shi Ido ta lumshe Kamar zata Yi bacci sai ga su Sultana kannen znawwar sun zo gidan su ukun,Sultana,Nasira da Hamra sallamar duniya gidan Shuru ba kowa,ita Kuwa ko motsi ta kasa tana jinsu sama sama har bacci ya kwashe ta,dakinta Sultana ta leka ta dawo tace Kai kuzo mu koma yau ma baccin asara take fa,baki suka tabe suna kallon gidan Suka fice driver ya maida su gida suna ta bawa Mami labarin gidan,Mami tace oh wannan yaro Yana hakuri Allah ya bashi mace ta gari an hadashi da kaddara Ni dama tun farko hadin nan bai min ba amma ba yanda zanyi sai hakuri.

    Yau ni kuwa na gama karyawa na bar Masa nasa a dining na gyara ko Ina kwanciya a kujera da Niyyar hutawa bacci ya kwasheni har yazo ya karya a gidan ban sani ba baccina nake yi,bai tasheni ba ya fice ya tafi gidan abokinsa Khaleel,Yana zuwa ya sameshi zaune tare da matarsa da yaransa biyu,,matar Khaleel Sufia tace na Sabreen Ina kwana ya amsa Yana cewa ya kamata na Miki kyautar kirarin nan,dan Khaleel ya dauka yana Masa Wasa sannan ya ajiye shi Suka koma part din Khaleel suna palonsa,Khaleel yace Wai Dan Allah wace wacce na ganka da ita? Nasan abinda ya dameka kenan dan sa Ido labarin Rabi ya bawa Khaleel bai boye Masa ba,Khaleel yana gama ji yace haba Ina ganinta nasan ban santa ba, ba yar uwarku bace,Amma fa tana da kyau ba karya inda kasan itace tayi kanta,sai dai bata da kunya ashe karuwa ce Kuma bata yi kala da karuwan ba,ita Kuwa karuwancin bai nunata ba ashe Yar kwalta ce,amma Kai tunda harka bata yuwu ba Allah ya tsareka Ina ruwanka da ita ka rabu da ita Mana,Nawwar yace ni so nake ta daina ta koma gaban iyayenta,Yarinyar ta lalace da yawa yarinya karama tausayi ta bani so nake ta shiryu,dariya Khaleel ya dinga shekawa yace ko dai sonta kake Yi? Haba Khaleel amma baka kaunata wlh me zanyi da karuwa,Khaleel yace kaga Wanda ya kangare sai Allah shi yake shirya bawansa a Sanda yaso kaga tun bata jawo maka masifa ba iyayenka sun gano ka rabu da ita,kasan Baffanka baida hakuri tam Kai Ina Kai Ina Yar bariki,Nawwar yace tab ai ka fada a banza ma Sai ta shiryu Inshaallah gidana ma Zan kaita ta zauna a can sabo da gudun shedan Kar ya shiga tsakani,Ashe zaka hada yaki,ai a matsayin Yar aiki Zan kaita ko me na ce zata yi bata da matsala ita Indai zaka biyata kudi,Khaleel yace bana goyon baya wlh Kuma duk abinda ya faru Ka kuka da kanka,ae naji cewar Nawwar ya canja zancen ma don Kar Khaleel ya dame shi.

    Haka naci gaba da Zama a gidan Nawwar Kamar wata matar aure na gaji ji na nake Kamar a kurkuku yau da yamma ya kwana biyu bai zo ba,sai na gudu daga gidan tare da kashe wayata tunda yanzu Yana da number ta  Kar ma ya sameni na gaji yanci nake so,Saratu ta ganni katsam bayan Sallar Isha ta dinga min dariya,nace na gaji wlh bazan iya ba,Kinga bari nayi Sallar Isha mu fita yau Zan fita titi abina bazai hanani yanci ba,Sera tace har yau fa ke kina Sallah nace sosai ma,Ina yin Sallah na dakko wata sabuwar gown dita da kadan ta haura duwawu na saka na saka takalmi me tsini naci kwalliya tare da saka hular gashi wata sabuwa me kitson twisting Wanda tsayinsa ya wuce duwawu Muka gama shiryawa Muka fice titi inda muke tsaiwa, a daren Nawwar yazo gidan amma ya samu bana nan,Ilu ya tambaya Ina Rabiah fa? yace ai ta fita gaf da Sallar Isha,da fada yace me yasa baza ka fada min ba ka barta ta fice,ai ni ganin bata fita shi yasa kuma tace abu zata siyo a chemist,Tsaki ya ja ya shige mota hankalinsa tashe ya duba bai ganni ba direct gidanmu ya wuce na karuwai,motar yayi parking ya fito ransa a bace Kamar zaiyi duka ba kowa a gidan sai wani Dandaudu,yace Miracle fa tana gida? Dandaudu shewa yayi Yana tafa Hannu yace karuwai dama suna Zama da dare ne? Ehehe ai baka sani ba ai karuwai basa bacci da dare sun fita aiki zauna nan kana jira baza ka gansu ba sai da safe ai suna street nima yau hutawa nake shi yasa ka ganni a gida ni kaga nayi nan yayi tafiyarsa,Shuru yayi ya tsaya Kamar gunki sai da ya gaji ya shiga motarsa ya fito daga layi ya nufi inda yasan muna tsayawa,tun kafin ya karasa ya hangoni da tsinannun Kaya a tsaye, a gabanmu yayi parking ya bude mota ya fito,ina ganinsa haushi ya kamani na zumburo Masa baki.

    Tsawa ya buga min Shiga mota muje,harara na watsa Masa Ina dire diren kafafu nace ni Allah bana so na gaji kamar Ina prison ni ko kudin ne bana so ka barni nayi rayuwata kaje kayi taka,mota nace ki Shiga ya furta Kamar zai dakeni sauran karuwan suna kallonmu baki bude, hannuna ya fisga ya jani na tirje ni ka kyaleni bazan je ba,Ina tirjewa harna zube a kasa Ina ta burburwa Ina Shure shure,Tsaki ya ja ya sakar min hannu,sai ya daukeni cak Ina wutsil wutsil ya bude gaban mota tare da jefa ni ciki ya rufe ya Shiga mota yaja muka wuce gidan dai da ya ajiyeni,Yana yin parking ya fito na fito Zan sake guduwa tsawa ya buga min na tsaya cak tare da juyowa yace come karasawa nayi gabansa Ina Kunkuni mari ya kwada min na dafe kumatuna da sauri na kalle shi cikin karaji yace Ina alkawarin da Kika min Zaki zauna? Mene a cikin karuwanci,karuwancin ma na titi ke bakya Jin kunya musulma dake hausa Fulani mene birgewa a karuwanci,bance Miki Zan biyaki kudi ba,har albashi na saka Miki duk wata,nace Zan maidaki school dan Kawai na inganta rayuwarki ba sonki nake yi ba karki Raina min hankali wallahi Kika sake barin gidan nan ba izinina sai Kinga abinda zan Miki useless girl baki San ciwon kanki ba kina yamace kalleki karuwanci bai dace dake ba,kuka zanyi Masa nace ai ni Kawai so nake nayi Ina so ne sai naji Ina son Karuwancin,shut up ya buga min tsawa shashasha wacce bata San darajar kanta ba wuce ciki,tsayawa nayi ya buga min tsawa shiga nace ya furta a tsawace, da gudu na fada ciki,Yana shigowa ya matso kusa dani ihun tsoro na saki na ja baya Kar ya dukeni, yace karki sake karki sake, kika sake zaki ga ba daidai ba yaja tsaki ya koma wajen me gadi yace idan ka sake barinta ta fita a bakin aikinka,Ilu yace Zan kiyaye, ciki ya koma Yana shiga yace tashi ki canja Kaya wannan yan iskan kayan sai na Kona su mijinki Kawai Zaki sakawa,tashi nayi Sadaf Sadaf na koma na canja silk material marar nauyi na fito,Ina Fitowa Kamar ba nice ya gama zazzagawa ba nace abinci fa a dafa,shi da Kansa a ransa yace bata da zuciya ya tabbata da wata ce ranar ko kulashi baza ta sake Yi ba ko matarsa ai sai suyi watanni tana gaba da shi,yace kin bani ne abincin,sum sum na Shiga kitchen na Masa jullof din taliya ta Sha kifi da kayan lambu, kawo Masa nayi har gabansa nayi serving dinsa Nima na zuba tawa Muna ci muna kallo,yace baza ki fada min wace ke ba I mean tarihinki,Ina cin abincina Ina bashi labarina komai ban boye Masa ba,yaji tausayina da yaji bani da kowa a duniya Yar tsuntuwa ce Ni,yace Kuma shine baza kiwa maraicinki gata ba ki Zama ta gari sai ki lalace,Shuru nayi Ina jinsa yana ta min fada ni dai bance komai ba, yace gobe ki shirya gidana Zan maidaki, kallonsa nayi nace matarka fa ni kasan bani da kunya Kar nayi abinda zata ji haushi  in ta min ba kyaleta zanyi ba kasan halinmu,ai yar aiki Zaki zama aiki Zan daukeki tunda kince ke baza ki aure ba baza ki makaranta ba Mene amfaninki Kawai na kaiki can kiyi aiki ki gyara gida kiyi girki,nace yanzu Yar aiki zan koma haka gaskiya tace? Cutar dani zaka yi,ko baza ki abinda nace ba? Kamar zanyi kuka nace zanyi,Kuma kina kwalliya zata ce kwace Mata miji Zaki Yi ta Miki dukan tsiya,Nace wlh sai dai na daketa Kai kasan karfina kuwa hmm amma tunda kace nayi zanyi ai zaka biyani ko? Yace kudi ma Zan Kara miki, ihu na saki nace wane ni nace bazan Yi ba ai ya Zama dole,yace Good girl Kinga mun huta da tsoron shedan,ka huta dai Amma Ni kaina ai shedaniyace me zaman kanta na furta,yace to babu kyau dai kebewa mace da Namiji shi yasa Zan maidaki a matsayin Yar aiki sabo da dangina da iyayena da matata ce za a dameni amma idan a Yar Aiki Kika je sai kiyi zamanki a haka dama aikinki kenan aikin gida da girki,nace rashin yanci dai ya Kara tabbata a kaina ka bari sai jibi to na Kara hutawa,yace Allah ya kaimu.

    Washe gari a gidan ya kwana Sai ga su Sera su bakwai sunzo gidan da kyar Suka gane gidan sabo da na taba fadawa Sera address,da masifa Suka shigo suna kwala min Kira, miracle…Miracle.. na fito Suka hauni da masifa Zaki tafi baza ki dinga fada Mana ba sai mu dinga tunanin saceki akayi,Nawwar ne shima ya fito a tsaya a gefena tare da harde hannayensa a kirjinsa, ni Kuwa nace yarinya ce ni da zan bata kunzo Kuna min ihu a gida,Nawwar sanye cikin kayan baccinsa Yana jinsu suna cewa Kai karfa ka rabamu da yarinya abin ya isheka haka,da sauri nace Sera zanyi diban albarka a nan wlh ki tsaya haka, Kar wacce ta zagi saurayina yarinya ce ni da zaku zo Kuna min ihu,wannan ba Kalar Yan iskanku bane ku Shiga hankalinku,Au haka Kika ce? Nace ae kuje gida idan na gaji zanzo ai Kun ganni kalau nake,Sabo da haushi juyawa sukayi Suka tafi suna masifa, suna tafiya ni Kuma na juya Muna facing juna Ilu dai tana kallo,nace karka damu dasu kayi hakuri ko me kake so zanyi Kai mutumin kirki ne,Shuru ya min na shafa gemunsa nace inya…. inya… inya….dariya yayi ba shiri nace muje ciki na ja hannunsa muka shige ciki,Muna shiga na rungume shi nace kayi hakuri kaji,jikinsa ya janye da sauri yace naji na hakura ki daina tabani nace fa bakya ji, kasan me na furta Ina gabansa a tsaye muna facing juna nace kana da kyau,idanuwa ya lumshe tare da furta ba kya ji,dariya nayi Ina kida baki na shima dariya abin ya bashi yace kin haukace maybe.
Yau ma da dare cewa nayi sai mun fita haka na dau wanka Muka fita wajen Shan ice cream Muka je nan ma ya kashe kudi,daga nan muka wuce wani wajen na shakatawa.

   Sabreen ce ta Kira Jamcy tace har yanzu fa bai dawo ba dan Allah ki Dan duba wuraren shakatawa ko Zaki ganshi da wata,Jamcy tana Dariya a ranta tace to,yau dai ta shirya a motar mamanta ta fito tana bi duk wajen joint tana zuwa Wanda Nawwar muke Kawai ta hango shi tare dani mun fito da ledoji ga wani ice cream din a hannuna Ina Sha Muka shiga mota,Jamcy ta saki ashar tace cab Sabreen Kinga ta kanki amma sai ta bugawa Sabreen waya,tana dagawa tace kin ganshi Jamcy? Jamcy tace ke dalla banza kin cika zargi to na ganshi yanzu ma Yana ma unguwar taku Yana masallaci makarantar da magidanta ke daukan darasi Yana ciki karatu yake a can makarantar Malam maikudi, Sabreen tace dama nayi tunanin haka ai shi akwai addini,Jamcy tace ke dai bari tsaurin addininsa da tsoron Allah dinsa har tsoro yake bani kin ganshi rike da Fiqhu, Sabreen hankalinta ya kwanta abinta mijinta karatu yake dauka a masallaci.

  Washe gari Kuwa Maminsa ya fadawa ya samo sabuwar Yar aiki me hankali,yaje ya fadawa Maman Sabreen,Mama tace ai Sabreen ta huta dama aikin ya Mata yawa har tausayi take bani Kamar ba me kudi take aure ba,itama Sabreen din yace Mata Maminsa ta samo Masa Yar aiki sabo da Kar ta zargi komai ma,tace sai ta zo tunda ita bauta ta zaba tazo tayi,ya kalleta yace dan Allah karki wulakantata ki zauna da ita lafiya,bata ce komai ba,ni kuwa tunda yace a yar aiki zai kaini gidansa sai na zabi wata Atamfa wacce ya dinka min dinkin ba wani na kuzo ku gani bane,na dauki wata atamfar sai Rigar material kayana kala biyu na hada da komai na bukata na zuba a jaka,makwaftanmu na shiga na samu wata me aikinsu budurwa na roketa akan ta bani kayanta kala uku ga sababbi nawa masu kyau,da gudu ta bani ta karbi nawa masu kyau ta bani wata kodaddiyar Atamfa Riga da zani dinkin kauye,sai wani tsohon leshi doguwar Riga da dankwali Wanda ake cewa disco tsoho,sai wata Atamfa ta ji jiki sosai Riga da katon skert marar fasali,sake wanke su nayi na goge washe gari ranar da zan koma can na shirya cikin rigar da zanin na tsohuwar atamfata sauran kala biyun Kuma na zuba a Leda Viva da sauran tarkacen bukata,dankwalin Disco na daura a kaina nan take na dinga yiwa kaina dariya irin watsewar kayan danma ni Fara da bazan ganu ba,Yana shigowa ya kalleni dariya ta kamashi yace gaskiya kina da kwakwalwa muje,na dauki ledar kayana Muka fita na Shiga gaban mota sai gidansa

   A hanya sai dariya yake min wai yayi winning bai taba zaton zan yarda naje gidansa a Yar Aiki ba,bai san duk abinda yace zanyi ba bai san yanda nake ganin girmansa ba,juyowa yayi kadan ya kalleni Yana Murmushi yace a Ina Kika samo kayan nan? baki na turo gaba tare da dora kaina a kafadarsa sannan na furta a wajen wata Yar aiki a makwaftanmu na bata masu kyau cikin nawa,Okay ya furta banda fitina da fada a gidana Kawai kiyi aikinki Zan biyaki ko nawa ne,yanzu nawa ma zan baki? kallonsa nayi lokacin ya juyo Muka hada Ido nace kana tunanin kudinka zasu sa na Zama yar aiki a gidanka? Karuwa ce ni fa kasan abinda muke siyarwa mu samu kudi wlh badan kudinka na yarda ba Kawai Ina ganin girmanka ne Ina Jin kunyarka Ina girmamaka shi yasa,Murmushi ya saki tare da furta a haka kina Jin kunyata Hannu na tafa Ina Dariya nace kasan Kuwa nifa ba karamar cikakkiyar Yar duniya bace,Yar duniya ce ni ta gaske ai nan daka ganni na Kama mutunci na ne ba karamin hakuri nake Yi ba,Allah? ya tambaya nace hmm yanda nake jina ko Namiji Zan iya Masa fyade,dariya yake sosai yace ya baki min ba ni? ai da kin sani kin min,karka cika baki Zan baka kunya a gaban matarka,karki Fara ya furta zamu bata bana so,daga min kafada,kafada ta na noke Wai naki,kyaleni yayi har Muka je katafaren gidansa na aure,sai Naga duk haduwar guess house dinsa da nake ciki ashe ba gida bane Yar Kauye na dawo sabo da tsabar tsaruwar gidan,Fitowa nayi da kayana a leda yace behave yourself,na nutsu tare da sadda kaina kasa Ina Wasa da yatsu na,dariya ce ta kule shi yau farin ciki ya isheshi yayi winning,Fuska na shagwabe,tun daga kofa Muka ji kida na tashi a hankali na furta zanyi loosing control rawa na kirana,yace dan Allah karki yi Yana rokata,nace wannan shine gidan Zama ai nan yafi mim dadi Matukar da wannan kida haka ai akwai nishadi,ciki Muka shiga Yana gaba Ina baya,Kannensa ne Ashe a gidan Suka kunna kida suna ta rawa gidan Suka zo Suka gyara ko Ina har dakinsa,Matar gidan Sabreen sanye take cikin kana nan Kaya tana zaune tana wani bata rai kannen Miji sun Zo Mata gida,suna ganinsa Suka kashe kidan tare da zuwa suka rungume shi dukansu suna Yaya Oyoyo tun dazu muke jiranka.

    Yace sannunku Hamra ce idonta ya Kai kaina Dana shigo Ina tafiya salo salo ta furta wow kaga wata me kyau Suka juyo gaba daya yace me aikin da aka samo min ne sunanta Rabi,Suka ce Masha Allah suna cewa ai gwara daka samo Yar aikin, Sabreen sai lokacin ta juyo ta min wani kallon wulakanci da kaskanci tare da cewa baki iya gaisuwa bane ko ba a koya Miki ba a gidanku,nan take raina ya baci na harzuka Nawwar ya girgiza min kai,labbana na cije na daure nace Ina kwana tace yanzu ne kwanan Kuma haka ake gaida masu gida,Please karki fara bana so kina takurawa Yan aikina dukkansu Yan Adam ne kamarki,tashi Sabreen tayi ta wuce abinta,Raina a mugun bace Sultana tace kiyi hakuri Zama da ita sai hakuri muje na nuna Miki dakinki, yace bafa bangaren masu aiki Zaki kaita ba a nan zata zauna ga room a kasa wancan ki kaita can,Sultana ta kaini hadadden daki ne harda nuna min yanda ake amfani da toilet din ta fito dani ta nuna min komai na kitchen da store sannan ta zuba min abincin da Suka dafa nace Mata yanzu na koshi anjima na ci,tace okay,Ina jinsu Suka ce zasu tafi gida Suka Mana sallama ya basu kudi suka tafi,dakina na shiga Raina a bace da abinda matarsa ta min,shigowa yayi dakin Ina zaune a bakin bed yace kiyi hakuri kinji,nace ba komai amma kasan inda ka dakko ni ko wlh in bata Yi Wasa ba sai na canja Mata kamanni gwara ka tsawatar mata,yace naji to mene na fushin zamana kike fa ke Ina ruwanki da ita,Murmushi nayi nace Okay wooo…. karka damu ya furta good girl,bani kudi ni yau kifi zanci ko kaje ka siyo min,yace a siyo Miki dai ai baza ki Fara fita yanzu ba,Kinga dai nan yafi safe sabo da gudun shedan amma idan kina nan ba wata matsala ai bai dace mu dinga kebewa waje daya ba,naji Ustaz Kar dai ta shigo ta ganka,yace to mene ne nifa bana tsoron kowa da Kika ganni nasan Allah Yana tare da me gaskiya akan me Zan tsorata,karka cika min baki ai Ina gidan nan Zan gani watarana,fita yayi Kawai Yana Fitowa ya haura sama,Sabreen tana jinsa ta share ta fito Palo ta zauna tare da hakimcewa ta kwala min Kira Rabi kike ko wa zo fito dan burar…ta duro min ashar,na fito nace gani Hajiya,tace wacce tarkacece ke? Nace tarkace Kuma Kamar ya? Wacece ke to daga wanne kauyen aka fito? nace Kano kauyen Zaria,tace shi yasa na ganki wata shawaragi, na daure na danne tace Shiga kitchen ki min girki sauri,nace Allah sarki ai ba kawoni akayi nayiwa wata katuwa girki ba ko uwarki nafi karfin na Mata girki,a gigice ta juyo ta kalleni nace ba zamanki nake Yi ba ke baki Isa kisani aiki ba sai abinda Naga dama sai Kuma abinda Ogana me gidan nan yace shegiya me kafar agwagwa,zata bude baki nace Kinga baki San wace ni ba Zan iya sassaba Miki kamanni ba abinda ya dameni bane sai na nada miki mugun duka wlh Zan iya canja ki yanzu,ke kin San wace ni kuwa na nuna kaina nace kin ganni kina tabani bala’i sai ya sauka a gidan nan yau,dariya tayi tace Allah Sannu waliyya,nace yawwa ki kiyayeni ba baiwarki bace ni baki Sanni ba tantiriyar takadariyar yar iska ce ni bani da mutunci Sanda aka Yi rabon mutunci Ina bacci digo ban samu ba Ina bala’i harda zufa Ina nunata da yatsa Tsaki na ja na juya dakina,Wata ashar ta dura tace tab ai Kuwa sai Yarinyar nan tabar gidan nan Kamar yanda na kori wancan, Yar aiki a gidana idan ta sa min Ido ta gano Ina shaye shaye ta fadawa Nawwar fa shi yasa fa nake korar duk wasu Yan aiki a gidan nan.

    Nawwar Yana Jin hayaniyar mu bai leko ba yace Sabreen ta samu dai dai ita ke baza ki gyara gida ba Kuma kin Hana masu aikin ma da ake kawowa suyi…kafin ya rufe baki Sabreen ta banko Masa cikin daki tace wannan Yar aikin ta bar gidan nan bana sonta Ni a canja min wata idan ba jaka ba kuwa za ayi yaki,ransa a bace yace ba inda zata je aiki Kuma sai abinda na sata ba Yar aikinki bace tawa ce ta gyara min gida ta min girki na ci ke kiyi naki yawwa,daga nan ka aurota Mana ai Kuwa da balbalin bala’i a gidan nan Kai da zaman lafiya ya Kare,ya Kare Miki dai ni kullum lafiya Zan zauna,Haka kace to wallahi na baka sati ta bar gidan nan idan ba Haka ba Baffanka da Iyamami sai sunji yace kije ki fada musu ki gani,Fitowa tayi fuuuu ta koma dakinta ta kwanta tana cewa wlh baza ta yuwu ba Ina sam Yan aiki munafukai Ina siyen kwayoyina a sirri Insha a sirri yanzu a kawo wata ta sa min Ido dole ta bar gidan nan.
Sabreen ko ta samu ciki ba Zama zaiyi ba sabo da shaye shaye ita Kuma baza ta iya hakuri ba Dole sai ta Sha yabi jininta,kusan ko yaushe Yana biya Mata bukatarta ta aure yanzu baya danne Mata hakki itace ma Watarana duk Sanda take son shaye shaye to baza ayi ba ko Yana so baza ma ta kwana a dakinsa ba,yayi bincike ya kasa gane dalilin baccin nan nata na masifa.

   Yau banyi aikin komai ba sai washe gari na tashi da wuri na gyara ko Ina a gidan banda dakinta da nasa,breakfast na shirya na ebi nawa na ja gefe na karya sai gashi ya fito da Shirin Office,nace Ina kwana ya amsa ya zauna nayi serving nasa asararriya tana can tana bacci, sai da ya gama karyawa zai fita nace Banda pad Kuma maybe anjima zan Fara period ba kunya na fada,sannan yace kije ki siyo Mana ya zaro dubu biyu ya bani na karba nace na gode ya fice abinsa na kwashe kwanikan ragowar abincin ma na tattara na bawa masu aiki maza na wanke komai na gyara kitchen na koma dakina nayi karatun Qur’ani sannan na saka katon hijab har kasa na fita na siyo pad dita na dawo gida Shuru Shuru bata tashi ba tana bacci har na dawo palo Ina kallo 11:30 am ta fito sanye da rigar baccinta ko wanka bata Yi ba,Ina kallonta na Gane tana shaye shaye Indai kasan me Shan kayan maye to zaka iya ganewa, ke me Kika dafa ta furta nayi shuru,tace dan ubanki ba dake nake ba shegiya mayya,waka ma na Fara na bawa banza ajiyarta,kwafa ta ja ta Shige kitchen ta dafa indomie ta fito ta wuce dakinta Ina kallonta.

     Tunda ya kawoni gidan bana ganinsa baya dawowa da wuri sannan kafin na tashi ma ya fita da sassafe aikine ya Sha Kansa har wurin sati guda itama Sabreen ta gaji bata kulani bana kulata ganin mijinta baya ko saurarena sai hankalinta ya kwanta,ni kuwa na shiga tsananin takura da damuwar rashin ganinsa sabo dan shi nake zaune ban San me yasa ba idan na ganshi sai naji sanyi a Raina naji nishadi marar misaltuwa,idan Ina ganinsa duniyar tana min dadi,gaba daya kewarsa nake yi so nake na ganshi Sam gidan bai min dadi,har Fitowa nakeyi da wuri ko zamu hadu amma bana ganinsa ganin haka Raina ya baci Banga amfanin zamana ba Kawai na saci jiki cikin dare da ledar kayana na fece sai unguwar mu ta Yan bariki, Ina komawa Allah yasa duk sun tafi ashawo nayi sauri na canja kayana masu kyau na kwanta a saman gadonmu sai bacci dake dama tana da key din dakin Nima Ina da key a hannuna duk wacce tazo zata bude Kawai.
Kwanciya nayi da Niyyar bacci amma na kasa sai tunanin Nawwar nakeyi a haka har bacci ya kwashe ni.

    Washe gari Sabreen Bata ji kamshin girkina ba Kuma ko motsina bata ji ba,gidan ta hau dubawa ko Ina bani babu kayana,Sunday yau Nawwar bazai fita ba hutawa zaiyi,Sabreen ta Shiga dakinsa Yana bacci tana ta kwasar dariya,dariyarta ce ta tashe shi ya bude kyawawan idanunsa a hankali ya kalleta yace kina lafiya Kuwa? tace ahayee dama an fada maka Yan aiki ba Yan goyo bane Yar aikin taka ta gudu tuni bata gidan nan tun jiya banji motsinta ba babu ita ba kayant…wata uwar zabura da yayi sai da Sabreen ta firgita Kamar ance uwarsa ta bace,ya dirgo daga saman bed dinsa,Jallabiya ya zura ko wanka ya figi key din mota ya fito,sai da ya duba ko Ina bana nan sannan ya shiga mota ya nufi unguwar mu,wayata ma bata shiga, yana zuwa ya hadu da star Suka gaisa yace Miracle fa? tace dazu na ganta ta fito tayi wanka ma maybe tana dakinsu,Dan Allah Kira min ita,star ta juya ta tafi dakinmu,tana zuwa ta samu bacci na koma duk da nayi wanka na sanye nake da vest peach sai dan wando gajere fari, Saratu ce ta fito daga dakin Wise ta hango Nawwar a tsaye,wajensa ta karasa Suka gaisa yace Rabiah fa?bacci ta koma ka shigo Mana dakin,Star ce ta dawo tace Masa tace baza ta zo ba,okay ya furta yabi bayan Saratu ta nuna Masa dakin ya shiga ita Sera tayi wani wajen ta tafi gantalinta

      Baccina nakeyi ba bata lokaci ya Shiga tashina ke ke….ko jinsa nayi,jikina yabi da kallo ya Dan ja tsaki tare da aza hannunsa Kan kafata ya rike tare da girgiza kafar na farka a hankali na Shiga bude idona Ina kallon mutum sama sama yana tsaye yayi folding hannayensa a kirjinsa mukullin mota na hannunsa tar na saka idona cikin nasa,idanuwansa masu Matukar tasiri ya lumshe tare da danne lip dinsa na kasa da hakoransa kadan,Naga fa lallai shine a zabure na mike zaune nace yaushe kazo? bai kulani ba yace tashi mu tafi,nace nidai na shiga Uku ka takura min ka damu rayuwa ka kyaleni nayi rayuwata kayi taka,me kake nufi Dani wai kayi rayuwarka na by force,ke bari kiji dole ki daina bariki ya Zama Dole ki daina ko kina so ko ba kya so sai kin bar gidan nan which kind nonsense be this,tashi karki bata min lokaci ya furta a Matukar hasale cikin tsananin fadan da sai da na tsorata kina wasting time dina get up,me yasa kike sa min ciwon kaine har waje Yan gidan suna Jin bala’in da yake zazzaga min,Star ta rike baki suna gulma lallai Miracle ta dakko ruwan dafa kanta,Har Kara labewa sukeyi suna manna kansu a jikin kofar dakinmu sabo da suji me ake cewa,Ni bazan koma gidanka ba bana so matarka ta dinga min masifa tana min kallon banza ba dama mu hadu sai ta dinga hararata,ba sai ki rama ba kema,to idan na rama ba Kaine zaka ce bani da hakuri na furta Ina share hawaye,Murmushi ya saki yasan yanda na dinga cin uban Sabreen a gidan sai da Sabreen ta gaji ta daina kulani amma yanzu nace itace take min,yace bana son dogon surutu tashi mu tafi,bazan je ba,Ina magana kina min musu Zan iya janki fa har mota,Ni dai bazan je ba,na daina sa kayan Yan aiki ba daga yau,Mamana da kannena fa idan Suka ganni,to su gani mana basai su rabaka da ni ba ka kyaleni,Tsaki ya ja ya shiga karewa dakin kallo ya hango kayan aikin Dana watsar a daki ya kwaso su harda ledar kayan ya zuba a ciki ya jawo wani Kato hijab yace saka mu tafi,Ina so in Masa musu amma bazan iya ba ya tsareni da Ido kwarjininsa ya min yawa,sai naki sakawa Kuma nayi shuru,durkusawa yayi yace abinda Ina da Hannu ya dauki hijab dina tare da saka min da Kansa yace tashi,kin tashi nayi na Fara kuka,daukana yayi cak ya sabani a kafada da ledar a hannunsa ya tafi duk Yan barikin wajen suna kallo mu bama Jin kunya suma a wajensu wannan Abu ne karami bai Kai a kalla ba ma,a mota ya jefani ya zaga ya shiga shima tare da tuka motar Muka bar layin.

     Tunda Muka tafi nake sharbar kuka bai ko kulani ba,ya wuce dani gidan da na Fara Zama a ciki ya kalleni kadan tare da maida hankalinsa Kan tuki yace gidana ne bakya so? Ina shesheka nace ae,a ransa Yana so ya kaita wajen Maminsa Amma bata da kunya zata iya kunyata shi a gaban Mami ko taje tayi wani shirmen,ko ta dinga guduwa irin wannan za a San da matsala bai so Kuma a San me take yi,shi Kuma baya son kebewa da ita waje daya ita Kuma taki gane nufinsa dole ya koma wajen Khaleel ko zai samu shawarar ya zaiyi da ita.

    Yana parking a gidan na fice na shiga ciki Ina Jin Dadi bana son gidansa,Zama yayi a kujera tare da dafe kansa da hannu yayi Shuru Yana tunani,gefensa na karasa na zauna gaf da shi nace meke faruwa? hannuna na sakalo ta wuyansa yace Kinga abinda bana so Kinga abinda kike Yi bana so shi yasa nake kaucewa kebewa dake,dariya nayi na cire hannun nace Ustazu,hijab dina na cire surata ta bayyana yace kinwa kanki wlh sai kin koma gidana baza ki sani a gaba ki dinga Iskanci ba tashi ya fisgi hannuna ya min tsawa sa hijab jikina na rawa na dauka na saka ya fincikeni har sai da na Fadi amma hakan bai sa ya sake ni ba Kawai jana yaci gaba da Yi a kasa kiiiiiiiii ……na mike da kyar a haka ya sake jefani a mota ya wullo min ledar kayana saka kayan aikinki,na zaro Ina rawar Hannu na saka Riga na saka skert akan kayana na maida hijab din jikina ya ja mota Yana uban Tsaki.

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼

     LITTAFIN KYAUTA NE

               26-30

SADAUKARWA NE GA DUK YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Bellomaryam581
Maryammkhalid2
Dr Suhailat Hussein Armai
Mrs Idris
Ummy M
Oumm Yasmin
Hafsa Abdullahi
Aesha
Hauwa Kasim
Momyy Hibbah
Hadizahamidu369gmail.com.

Masu Sharhi Ina godiya ko da wasu zasu Yi suga banyi reply ba suyi min afwa ban gani bane ban kula ba.

         Washe gari bayan na gama gyara ko Ina na gidan na karya yau bai zo  ba har Yamma sai magriba Ina ta kallon film yinin ranar gaba daya, da Magriba ya shigo bayan ya dawo daga masallaci,Ina ganinsa na fashe da kuka nace Allah ni tafiya zanyi gida na gaji da nan bana so ka ajiyeni a prison ni gidanmu Zan tafi Ina can cikin nishadi ka ajiyeni a nan ni bazan iya ba na nuna doguwar rigar da nasa me tsada cikin kayan da ya siya min tayi min mugun kyau nace kalli Riga har kasa gashi ni rigar ta dameni bana so,sai da na gama Ina tsaye a gabansa yace wannan aikin da kike ikirari kina fita Wai Dan me kike Yi? nace kudi yace to biyanki zanyi ba kyauta nace ki zauna ba,Ina goge hawayena na koma na zauna tare da turo baki gaba,kudi ya zaro dala dari dari guda uku ya Mika min Yace gashi,kallonsa nayi nace wata fa bai cika ba kace Kuma sai wata yace ae baki nayi ki Kara hakuri ya furta tare da Zama,mikewa nayi da murna na kasa magana ma nace wannan Kawai na roko ne akan na zauna Kuma idan wata yayi zaka bani albashi? Yace ae,nace yau ana burar….na dura ashar nace la’ilahaillahu Wai Kai to me kake amfana dani,baka taba ko nono na Kawai ka ajiyeni ka dinga biyana kudi every time money ehhhhheheh nayi wata mahaukaciyar dariya Ina tafa hannaye nace bafa ka amfanuwa da ni a Zamanin nan,na nuna kaina nace ni Kuma banza Rabi wai ni ka bawa Elizabeth, nace yehoho kai Nawwar zan iya maka bauta,Kai mutumin kirki ne Kawai gani ka bautar dani kayi abinda kaga dama dani,ko wuta ka fada Zan iya binka nima na wulla ciki,ah’ah ikon Allah,kallona yakeyi Yana ta dariya yanda na haukace akan kudi,gabansa na durkusa nace Alhaji dama dazu ban gaisheka ba Ina yini ya iyalin? ya kwashe da dariyar da ban taba ganin yayita ba,nace Dan Allah kunyarka nake ji kana ta min kyauta baka tabani bana Jin dadi wlh uhm Sana’a nake uhm haba dan Allah yanzu ko Yan nono baza ka taba ba,yace ae nace dan Allah da girmansu wlh Allah ya bani akwai auki hiiim suke,yace na gode,mikewa nayi nace shike nan Allah yasa dai matarka tana baka nata,a ransa yace ko ta bani ma Yan karamaye ne ko saurararsu banyi a fili yace Ina samun halak dina nace ai Kuwa  ta kyauta amma idan ta maka hauka Kawai ka fada min naje naci babbar burar….,Wai karuwai ma irinmu muke badawa bare mace da mijinta mene amfaninta idan ba a ragargajeta ba shi yasa fa nayi hips kugu na ya bude to yau da gobe taki Wasa ana ta iban harka,yace Wai ke in tambayeki,nace Ina jinka na nutsu sosai yace bakya Jin kunyata? Kai na daga masa nace ae bana ji,sabo da me? ta gudu ai ni bani da kunya na gantalar a titi bana Jin kunyar uban kowa yau da gobe taki wasa,numfashi ya ja yace to idan nazo ki dinga kokarin Adana kalamanki na banza bana so ki daina Yi a gabana bana so tunda kince duk abinda nace kiyi zakiyi bana son kalaman banza,nace to zanyi Inshaallah na daina, better ya furta nace to mu koma karatu Mana,yace me Kika sani a addini da kina da ilimin addini ai da baki abinda kike ba sabo da a wani Hadisi Manzon Allah (SAW) yan acewa

  kullu ummati yadkulunar jannata….kafin ya rufe baki na karbe Hadisin naci gaba da karanta Masa Ina fassarawa nace wato ka gane annabi (SAW) yace dukkan alummata zasu shiga aljana,sai yace illa man aba sai dai Wanda yaki kaga irin mu kenan munki mu tunda Muna karuwanci to Allah ya shirye mu,sai sahabbai Suka ce kalu ya rasulillahi,Suka ce ya ma’aikin Allah wa yam aba?waye zai ki? Sai ya basu amsa Wa man asani Wanda ya Saba mini faqat aba hakika yaki,Allah ya shirye mu na furta yace ameen,nace na kusa fa sauka nan daka ganni da ilimina ko a karatun Qur’ani baza ka kureni ba sannan Ina da littafa da dama a kaina sabo da Ina zuwa Islamiyya a kauye Kuma na dage a lokacin.

    Wato kin sani kike take sani nace mu bar zancen kaga Ina so na sanarwa Kawata Seraline ta San Ina nan Kar tazo hankalinta ya tashi bata ganni ba har kwana biyu yace ki kirata a waya Mana ga wayarki nan, wayata na jawo na Kira Seraline tana dagawa tace Ina ta kiranki wayarki a kashe Ina Kika shiga duk mun damu su Wise sai gwada wayarki ake bata shiga? nace sorry dama Kira nayi na fada Miki Ina gidan Saurayin nan nawa da ya bani daloli to shine yace na zauna a gidan zai biyani na Dan tayashi kwana na wani lokaci shine nace bari na fada Miki ki fadawa mutanenmu kafin na dawo, Seraline ta Yi dariya tace kice kin Zama Yar Hannu nace ae Kawai Muka danyi surutun mu na Yan duniya sannan na kashe Wayar, nace ko Watarana baza kayi sex dani ba? ganin na dameshi sai yace sai Watarana Kawai Sanda naga dama zan iya ki kwantar da hankalinki ko yaushe Zan iya,ya tashi zai fita nace Ina zakaje daga shigowa zaka fita ni baza ka bani lokacina ba wai ni Allah Zan gudu gida na koma inda na fito,karamin Tsaki ya ja ya dawo ya zauna na kamo Mana Nigeria film Muna kaiwa suna saka sabo Muka ci gaba da kalla tare Muna sharhi a kai,cikin Raina Kuwa tunani nake Yi yace ko yaushe zai iya sex dani gashi ni ba taba Yi nayi ba,na dai Saba da maza arna da Yan daudu zamu rungume juna Babu batun mace ko Namiji har zama muke a cinyar Namiji Kamar mace Yar uwarka,a raina nace idan yazo ko yaushe banyi gyaran jiki bafa yazo ya jini ba Dadi ai dole na Kira Sera ya Zama idan bani ya kusanta ba bazai ji Dadi ba tunda dai nasa ran Zan Fara Ashawo work idan ma zai na biyana ko yaushe ai ba matsala sai na dinga Yi da shi Kawai mutum daya,Ina ta sake sake a raina har ya Fara Jin bacci a nan yayi Sallah ya mike yace matata tana jirana,nace to Goodnight,rakoshi nayi har mota securities suna nan suna gadina,da kaina na bude masa motar ya Shige mota na rufe Masa glass ya sauke yace sai gobe nace Allah ya kaika lafiya ka kula da tuki na juya Ina cewa banda ganganci matarka zaka yiwa asara ni ba ruwana,Murmushi yayi kawai ya murza Kan motarsa ya bar gidan.

    Ina komawa na Kira Seraline na fayyace Mata komai dake bama boyewa juna sirri,Sera tace to ai Kuwa zai iya zuwa bakatatan ya nemeki Kuma Kinga dai yanda muke kashewa Gomnatinmu kudi Kinga yanda muke Shan gyara uban kowa ya dandanaka bai iya barinka sai ya dawo,kina da kudi ki kawo a fara kashe dubu dari biyu haka a tsumaki karuwai basa Wasa da gyara Kai kusan kudinmu a gyaran jiki ke tafiya da haka muke samun riba jari muke zubawa ki kawo kudi a zubawa jikinki jari,in kana da kyau ka Kara da wanka karki kalli kina da kyau Wai kice baza ki Kara da wanka ba,nace ai shine na gani nima gobe Zan rokeshi ya barni nazo sai muje Sera ta kwashe da dariya naji dariyar su Wise ma a Wayar hahaha Sera tace kin gammu dukanmu yau Muna gida Hira akeyi suna jinki munce kin dakkowa kanki masifa,Star ce ta kwace Wayar tace Yar wanke wanken karuwai haka Kika jefa kanki a masifa sai kace mijinki zai wani hanaki fita baki da yanci ma wato sai ma ya baki izini zaki fito mene amfanin barikin da Kika shigo daga farawa shike nan sai ki tsaya kina bin Maganar katon banza,nace Kinga star ba katon banza bane karki sake zagar min saurayi,harkarki daban tawa daban kiyi naki inyi tawa,abinda naga dama shi zanyi ko ke kike daukan nauyina,hehehe Suka furta gaba dayansu lallai namijin bariki zaki biyewa zai kaiki ya baro,nace ae naji ke Sera sai nazo tace to suna ta min dariya Ina jinsu…

    Duk da haka zugar tasu ta danyi tasiri a zuciyata amma na danne  washe gari da Yamma yazo 5pm,na shirya cikin wata doguwar rigar nayi rolling da mayafinta na fito a gabansa na durkusa nace dan Allah ka barni naje na dawo wlh bazan dade ba wajen Sera zanje matsala ce ta taso a dakin da Muka Kama karya na sharara Masa,yace hour nawa Zan baki? Nace 3hrs ma yace karki wuce 9pm Baki dawo ba nace to Ina murna na fita ya kwanta Yana jirana,Ina fita na shiga taxi,a ciki na cire Abayata kana nan kayana da nazo dasu gidan Suka bayyana na saka hular gashi na Kar ma su Sera su ganni da manyan Kaya suyi min Dariya,a cikin jaka na saka su,suka ganni nazo Sera tace ya barki kenan nace ae tare da kwanciya a saman gadon nace tsakani da Allah na gaji da mutumin nan Sera,ya takurani ya hanani lekawa ko kofar gida gashi dole sai na sa manyan Kaya na rufe jikina,Kinga takura komai nayi zai ce ba kyau,musulunci kaza kaza gashi mugun tsoronsa nake ji Yana da wani kwarjini kyansa kadai ya Isa ya rudaka gashi baya dariya sosai inda kisan ubana haka ya takura min na karashe da Tsaki,Sera ta dinga dariya tace ke Kika ga Zaki iya ta jawo sigarinta ta kunna Mata wuta,Ina mita nace gida ba nishadi ba kida ba shanawa Ina cikin wahala ai wlh kwana nan na kusa gudowa barikina bazan iya ba,Sera tace maybe sonki fa yake dama kina son aure sai kiyi abinki,nace wa ai da ne nace Ina son aure yanzu Kam rabani da wahala bazan iya ba aure baya tsarina a dinga takura min bada ni ba amma daga ganin mutumin zai iya love,zabura nayi nace tashi mu tafi 3hours ya bani idan na wuce ba mutunci,Sera dariya Kamar ta kasheta tace maganinki kenan yanzu gwara ki hada kanki zo mu tafi gidan Hajiya Mazarkwaila,dariyar sunan ya kamani nace hala itama tsohuwar karuwa ce domin daga Jin sunan bana kirki bane,Sera tace ai muguwar tsohuwar karuwa ce har yanzu ma Kuma yanzu ta koma kawalci manyan masu kudi take kaiwa Mata gata uwar karuwai kayan maye ba Wanda bata siyarwa ta tara arziki da bariki attajira ce ta gaske Kuma tana gyaran jiki na Mata gyaran skin gyaran Gomnati in and out amma akwai kashe kudi amma fa ba karya da kayan kasar waje take amfani idan Namiji ya dandanaki wlh ko a gaban uwarsa in zai ganki sai hankalinsa ya tashi bai iya kusantar wata yaji nutsuwa sai ke,nace iceko ba shirka bace? Tsaki taja tace ance Miki maganin kasar waje na gargajiya kina shirme,kin San karuwai muma ba tsafin da bamayi idan Muka hadu da me kudin gaske wlh in Muka Masa wani tsafin shi da iyalinsa har abada kullum Yana bariki wajenmu, jira nake Allah ya hadani da wani gagararren me kudin uwarsa ma Sai ya juya Mata baya,baki na saki nace nidai ba ruwana wallahi bazan je ko gun Malam ba bare shirka Allah ka tsareni,Sera tace ameen karki isheni Karuwar banza Karuwar wofi,dariya nayi nace karuwai dai Sera har yau dadin sex din nan ban ji ba ban taba yi ba Ina ta ikararin karuwanci amma Abu ya gagareni,ganin dama Kika Yi kin biyewa Dan iskan farkanki Muna tafiya muna hira Muka shiga napep nace Sera nifa yanzu kin San me? tace Ina jinki nace sha’awa ce ta dameni kullum da ita nake kwana nake tashi,to kin cuci kanki kin zauna a gidan dan banza babu me dan saitaki ba dole ba Kuma kina bariki kullum dare da rana a maganganun batsa muke dole a dinga taso Miki da sha’awa Kar aje ayi gyaran jiki Kuma abin yayi Miki yawa Kawai a hakura da gyaran a siya Miki na infection da Wanda zai dai dan dawwamar Miki da niima Kar kizo ki afkawa maza,dariya nayi nace ai Kuwa da ce Masa zanyi idan yasan baya son sex to ya dinga saka wandon karfe dama naji Yana cewa kwanan nan da wandon karfe zai dinga zuwa gidan,dariya mukayi har Muka je gidan Mazarkwaila,gidane na gagara gidanta abin kallo ne Muka shiga tana Palo ita kadai tana kallo kana ganinta ba sai an fada maka ba kasan shedan ya gama fitsare Mata Kai muguwar Yar duniya ce.

    Da murna da karramawa ta karbe mu me aiki ta kawo Mana Kayan ci da sha Muka ci Kuwa Muka Sha sannan Sera ta mata bayani tace amma yanzu yace bazai Yi sex da ita ba sai Watarana Kuma tana cikin wani hali Kar a bata Wanda zata gaza hakuri, Mazarkwaila tace karki sake Kiran kanki da karuwa Kuwa Indai hakane ke Kuwa me ya kaiki wahalar da kanki haka ki zage kiji dadi mene a duniyar dole sai ana hutawa Kinga Ina da Wanda zasu iya baki million biyar ma lokaci guda idan sun sameki gaki Kalar da suke nema ce ni kin San ba kowa nake kaiwa Mata ba sai ka cika me kudi,ke Kuma irinki suke nema akwai arziki a tare dake za a samu alheri dake sosai,nace nidai a’a tsoronsa nake ji ba ruwana Kawai ki bani magani mu tafi yace idan na wuce 3hours akwai matsala Kinga gashi har lokaci ya kusa ni dai yau na shiga Uku wayyo Allah na 8:30pm yanzu kafin naje gida ma 9 ta wuce,Sera da Mazarkwaila Suka bude baki ta mike ta kawo min magungunan infection masu mugun kyau da tsada, ta bani kayan gyaran skin ta gwada min yanda Zan dinga Yi kafin na shiga wanka Dana shafawa, ta bani wasu kayan kamshi tace Kinga wannan karki Wasa da su duk inda kika je sai kin bar kamshi a wajen bazai so ya dinga nisa dake ba sabo da kamshin da kike yi na musamman ne daga Dubai nazo da su,na karba nayi godiya na biya dubu dari da ashirin a iya Yan kayan kala kadan,a gidan na bar Sera na shiga taxi da sauri Ina shiga na maida abayata nayi rolling Kamar yanda na bar gida,9:40pm na shiga gidan da gudu na fada Palo Ina haki,Yana Palo sai da ya tsorata,sake fita nayi na dawo na Masa sallama ya amsa sannan na shiga ransa a bace yace Ina Kika zauna? Ina haki nace bamu gama da wuri bane Kuma mun hadu munyi hira kayi hakuri na furta tare da turo Dan bakina gaba Ina Kunkuni nace ni duk anbi an takura min sai kace babana,yace magana kike? Nace no Ina satar kallonsa na mike na shiga bedroom na boye tarkacena sannan na dawo palo,kinci abinci? ya tambaya nace ae,a ina? a can mana Seraline ce ta bani,baza ki girki ba kenan? Yunwa yake ji bazai iya cewa na dafa Masa ba,nace na koshi ni sai dai in dafa maka naka,me zaki dafa min? abinci mana ba kana cin komai ba sai nayi tunani na dafa, alright tunana naji, tunani na Shiga yi daga baya nace yawwa na dafa maka sakwara da miyar kwai Muna da garin sakwara na gani kaga ba wahalar daka da Zan sha,yace ai girkin ya Miki wahala da yawa da dare haka, tab ai ni bana Jin wahalar girki da aiki ma na Saba mufa ba Hutu Muka zo duniya ba bare ma Kaine mene bazan maka ba sai in baka so, Murmushi yayi kadan yace to zanci Ina so kiyi a nutse a nan gidan Zan kwana yau,yeeeeee na furta Ina ihun murna nace shi yasa naga securities sun tafi,cewa zaka Yi yau kwananki ne Miracle,ka Fara raba Mana kwana kenan,Fuska ya bata,nace sorry wlh yau Ina farin ciki,mamaki yayi yanda yaga Ina ta murna Kamar Zan tashi sama,matarsa Kuwa tab banza wofi ne shi a wajenta.

     Kitchen na Shiga na tsara miyar kwai taji nama sannan na tuka sakwarata lafiyayya,na gama na gyara kitchen din na kawo dining yace kawo min nan ban iya tashi na kawo gabansa na jera nayi serving nasa na zuba Masa juice sannan nace Ina zuwa naje na zubawa Ilu me gadi na fito yace Ina zakije? Nace Ilu Zan kaiwa nasa yace oh har shi kike bawa? Nace ae ai tunda na Fara girki Ina kaiwa Ilu,yace da kayanki fitsararru kike zuwa Gaban Ilu ki Kai Masa abinci? nace ah mene a ciki Allah na tuba ko da bra da pant Zan iya zage garin nan kaf bare zuwa wani Gaban Ilu da damammun Kaya Sanda ka dakkoni farko baka ga a yanda ka dakkoni bane to ai wannan shigar mutunci nayi,yace jeki dan Allah karki sa na mareki,gaskiya na fada maka ni dai na fice na kaiwa Ilu na dawo,yace daga yau ko compound Zaki leka sai da mayafi,takurar da yake min ta min yawa abin ya isheni Kawai nace to idona ya ciko da hawaye akan Kawai ance na saka mayafi,yace kuka zakiyi? Kaina na sadda kasa Ina girgiza kaina Ina bude baki da Niyyar cewa a’a sai kuka yazo min na Fara shesheka Ina kuka sosai nace k…ka…k..ka..sh..shiga…hakkina…k…ka…takura..min…bana..ba..bana…bana…jin..dadi…ba..bana son..wannan rayuwar taka….ka…kyaleni na tafi….kallona yayi yace baki San ciwon kanki ba Rabiah ki daina karuwanci ki daina ba kyau,mace kyakyawa kamarki musulma mene abin so a bariki,Ina amfanin irin wannan rayuwar kiyi aure ki bautawa Allah ki samu lada ki huta mijinki zai Miki komai,sex idan kunyi lada Zaki samu mene a wannan rayuwa,nace ni bana son aure bazan yi ba karuwanci zanyi ni karuwa ce bani da asali gadon Iyayena zanyi,Tsaki yaja yace okay fine Zan saki a school ki koma makaranta ki samu Ilimi,Ido na zaro nace no bana so da girmana godai godai Primary Kawai nayi ta Kauye shekaruna ashirin da biyu ba wata makaranta da zani,ba a girma da karatu Rabi Ilimi ilimi ne ko wanne irine,to ni dakikiya ce nan daka ganni kasurgumar jahila ce ni bana ganewa katuwar jahila ce ni ba uwar da na sani ilimin addini ma Dan na dage ne amma ba abinda da Zan sani,Kai baka ga alama ba jahila ce ni shi yasa nace maka ni abinda zakayi ka birgeni Kawai ka kwanta dani dan Allah ka….wata mahaukaciyar tsawa ya buga min yace baza a kwanta dake ba din karki sake min zancen nan bana son ji sai na tashi na bar Miki gidan bana son zancen banza bana so kinji na fada Miki watch your tongue Inshaallah bazan kwanta dake ba Kuma sai dai na ci abinci badai ke ba,dariya ya mugun bani nace to naji yi hakuri ci abincin ni na hakura ba sai ka c…bakina na rufe yace yanzu kiyi kuka yanzu sai aga kina dariya ke haka kike ne?nace ae Mana ai dan Kaine na koma kusa dashi na zauna yace ki kyaleni naci abincina in Peace dan Allah,na kyaleka ci abincinka in peace not in pieces,dariyarsa ya danne ya kyaleni Yana ci,Hannu nasa a ciki tunda naga da hannu yake ci,nama na dauka nace baka cin naman bude bakin na saka maka ha bakin haaaaa….dariya yayi ba shiri na saka Masa da sauri ya rufe bakin da katon nama a ciki,Murmushi nayi na dauka daya naci Nima na tashi tare da haurawa sama na sake karkade Masa bed din na gyara bed din sosai duk da ba abinda yayi,kayan bacci na zabo Masa na ajiye a gefen gadon na fito

   Har ya gama cin abincinsa Ina Fitowa na iskeshi Yana kallon ball ya lankwashe kafafunsa a Kan kujerar kwanciya nayi na dora kaina a cinyarsa tsokanarsa nayi amma yasan maitata da naci sai ya rabu dani,dagowa nayi Muka hada Ido yace mene kike kallona? baka yi fada ba ya zanyi dake to tunda kin zama mayyata ba kya Jin magana,ki bani tarihinki kinki fada min nayi nayi kinki da nayi magana zaki fara min kuka shike nan gobe bazan dawo ba ai sai nayi kwana biyar baki ganni ba,kayi hakuri Zan fada maka ai nan gaba,Allah ya kaimu yace na koma na kwanta nayi matashi da cinyarsa ban ma San nayi bacci ba,Ina yin bacci ya zame kafarsa ya barni nan ya tashi tsam ya koma dakinsa,Shirin bacci ya Fara Yana Fitowa daga wanka yaga kayan baccin akan gadon da guntuwar takarda a Kai,takardar ya dauka ya karanta WANNAN KAYAN ZAKA SA, SU NA ZABO MAKA ZASU MAKA KYAU, PLEASE KARKA SA WASU IN BA WANNAN BA
DAGA KARUWARKA, .
dariya ta bashi Wai karuwarsa tana so ta dinga ikirarin ita karuwa ce kayan ya saka data zabo Masa ya kwanta abinsa adduar bacci yayi ya kwanta sai bacci.

    Dagaci Katsam shugabannin gidan marayu Suka zo duba yarsu yar tsuntuwa Rabi, tsoro ya kamashi sabo da dama Indai gomnati tasan ka karbi dan tsuntuwa to Dole sai da shedu da kotu da hukumar marayu,sai ka cike takaddu sosai anyi a rubuce sannan jefi jefi sukan leko duba yaransu a ka’ida, ai Kuwa rabon da suzo tun Rabi tana karama sai yau, Dagaci karya yayi yace ai ta tafi Hutu gidan kanwarsa dake Abuja,Suka ce ba damuwa suna ganinsa babban mutum Kuma Dagaci shugaba a kauyen sai basu damu  ba Suka tafi abinsu, Dagaci Yana Jin dadi gashi Rabi ta tafi sun huta za ayi auren yarinya ya zauna a dakin Gwaggo ya fashe da dariya yace Kinga Yan Iska na musu karya sun tafi,Gwaggo ta sheke da dariya tace Ina tsoro fa Kar Yarinyar nan taje ta kaiwa hukuma Kara watarana kasan suna da gata a gomnati,dariya ya saki yace tun yaushe na Gama da shafinta ai wajen malamina na koma nace tunda ta tafi to duk inda take ta fada Neman maza,dabara bata fado min ba sai data yi wata biyar da barin gida na garzaya nace a sata tafiya Neman maza ta kangare ta zama fitsararriya duk inda taje Kar tayi kunya shike nan Kinga ta fada duniya ta gaji iyayenta da Suka jefar da ita ai na bawa Amarya labarin komai,Gwaggo ta sheke da dariya tace muyi Shuru da bakin mu Kar Wanda ya sani bye bye Rabi zaki ga Kudurar Allah.
Gaji Shirin biki Kawai suke babu Kama hannun yaro.

    Sabreen ce ta fuskanci Nawwar baya kwana a gida watarana,yau ma taje har dakinsa ta duba ba kowa har 3am tace kut wato dama mutumin nan dan bariki ne ai Kuwa wallahi sai ubansa da uwarsa sun sani zai gane kurensa Kuma Iyamami sai taji tasa danta ya dauki mataki,Tsaki taja tace ta tabbata Yana can tare da karuwarsa dole na saka Jamcy ta fara bibiyar min shi sai anga Ina yake zuwa zai sani ta mike ta koma dakinta ta kora barasarta me karfi ta kwanta abinta,washe gari da sassafe ta kira Jamcy tana fada Mata mijina fa baya kwana a gida yanzu aiki ya sameki kawata ki Fara bibiyar min shi,Jamcy farin ciki ya kamata a ranta tace Allah ya Kara a fili tace to yanzu duk Sanda Kika ga zai fita da dare sai ki min waya na fito Nima kin gane,ae ba damuwa Zan fada Miki dan Allah ki gano min Ina yake zuwa cewar Sabreen,Karki damu kawata an gama jamcy ta kashe wayar tace Zaki ga aiki Ina nan a kwance yayi abinda ma zaiyi ke Kika ja Mata baki San ma me mijinki ke ciki ba sai shaye shaye taja Tsaki ta kwanta.

     Washe gari kamshin girkina ne ya tashe shi bayan yaje masallaci bacci ya koma,Ni Kuwa tunda nasan Yana gidan Dana koma baccin ma banyi na kirki ba na Fara gyara gida Ina girki kuma a haka na gama komai da komai nawa dakinsa ne ban gyara ba,wanka nayi na shirya cikin wata buba doguwar riga ta material pink dama ni ba kwalliya nake a Fuska ba iyakaci powder da lipgloss pink na shafa na haura sama na nufi dakinsa da kayan gyara dakin, knocking na Masa Shuru na bude na shiga ba kowa karar ruwa naji nasan wanka yake yi ai Kuwa na fara gyarawa kenan ya fito,Yana ganina ya koma ciki tare da zuro Hannu ta cikin toilet din ya ja kofar hannunsa ne Kawai a waje yace bani Kaya da lotion dina,kayansa na bude duk kusan Jallabiya ne a nan gidan baida Kaya a nan,yace banda Kaya a nan na kirki duk suna gidan matata Miko min Jallabiya Kawai,na zabo Masa gajeren wando na fito da wata Jallabiya ruwan zuma na Mika masa,ya karba na Mika masa lotion din ya karasa rufe kofarsa,sai da ya shirya tsaf a ciki sannan ya fito,Yana Fitowa ya iske na gyara ko Ina room freshner nake fesawa yace sarkin Aiki sannu ya furta yana kallona yanda nayi kyau,Murmushi nayi na shiga toilet na wanke komai Kal Kal sannan na fito na karasa komai,a dining na sameshi yana Danna wayarsa cike da nishadi.

    Ina kwana nace yace da ban kwana ba kya ganni,nace ka tashi lafiya to? Lafiya Alhmdllh ya furta,serving dinsa nayi yaga wani Kalar soye soyen ba irin na jiya ba Kuma ba tea nayi ba kunun gyada nayi me kyau ya zauna yaci ya cika cikinsa nima haka,nace da yau ka kainmu joint tunda naga Saturday ne ba aiki,ke da wa da zaki ce na fita da ku? Kawayena mana sai na fada musu a waya da time su zabi inda zamu hadu kowacce taje kawai sai mu samesu a can,yace anya Kuwa? please Kamar zanyi kuka Ina rokonsa,yace to ba damuwa,nayi murna nace mutum biyar Wanda Muka fi mutunci ko? Yace yanda Kika gani, wayata na dauka na Kira Seraline nace ku shirya keda star,wise,yarzabil,sai Santana zamu hadu saurayina yace zamu je outing,Ihu Seraline tayi da murna nan take ta fitar da wani joint na cin nama da shawarma Yana da tsada tace nan za a kaisu,nace karki damu saurayina akwai kudi karku ci komai anjima zamu hadu 6pm Kawai kuje can zamu Zo mu same ku tace an gama,tana kashe waya ta fadawa sauran Suma sai Murna.

    Yace sai Yamma ya mike ya fice tashin motarsa naji,Yana fita gidansu ya nufa ya samu Maminsa a zaune a palonta tayi tagumi,tagumim ya cire da hannayensa,juyowa tayi ta kalle shi tace yaushe ka shigo? Yace Ina ta sallama baki ji ba Mami lafiya dai ko? lafiya tace Kawai yasan ba lafiya ba Kawai baza ta fada Masa bane,yace Mami ki Kara hakuri kinji,tace Inshaallah tana Murmushi,Ina yaran?
Sultana tana gidan Kanwata Rahma,Nasira da Hamra suna Islamiyya,shi kuwa sarakin buga ball Nawaf ya tafi Wai yau suna da ball tsakanin su Yan Jss 3 da Yan Ss1 shine ya tafi,shi ba zaije islamiyyar ba sai ball,yaune Kawai kayi hakuri karka taba min yaro nasan halinka,Ina Sabreen din tana lafiya ko? Lafiya take…sallama Sultana tayi ta shigo tana cewa laaaa Yaya Sannu da zuwa yace yawwa sarkin yawo haka ake Yi daga yin candy shike nan Islamiyyar ma an daina,Ina zuwa wlh Yaya Aunty ce tace naje bata da lafiya,Mami tace ya jikinta nata tunda nasan laulayi take,Nawwar yace ciki fa ita Ina zata Kai Yara ya har bakwai,to Allah ya bata sai taki,Ina Baffanmu? Ya fita tare da Yar gwal din tasa,Murmushi Nawwar yayi yace Allah ya kyauta komai zai wuce Mami na,tace ga abinci fa,yace naci a gida ya mike tare da furta na tafi sai zuwa Yamma watakil,tace Allah ya kaimu a gaishe ta,Yana tafiya Sultana tace wlh in Allah ya yarda Yaya sai ya Kara aure wlh Kinga irin abinda matarsa take Yi a gidan hmm Yaya wahala Kawai yake Yi,Mami tace na San komai ai Rannan na gani da idona Dana je gidan sai hakuri,ke Mami komai kice hakuri ni wlh Rannan ma naso na nadawa shegiya duka Kinga wani wulakanci data Mana da kawayena,ku dinga hakuri Yar uwarku ce dai ato kije kiyi Sallah,tace to ta mike ta haura sama.

     Nawwar gidansa ya shiga ya iske shi kaca kaca ba gyara tsallakewa yayi dakinsa ma gashi nan duk sai yaji ya kasa samun nutsuwa babu tsabta sam, Fitowa yayi ya leka ko Ina matar tasa bata nan,dakinta ya leka ya isketa tana shara uban bacci tayi shaye shaye har munshari take zabgawa kwarrrr…kwarrr…sisi….fi..fifi…ya juya a gidan ya yini sai 5pm ta farka ba Sallah ba salati sai da ta tashi ta hada azahar da la’asar tayi a gurguje ba nutsuwa mayen bai gama sakinta ba ta fito kitchen ta dan tafasa indomie ta cinye abarta tana Shan ruwa ya fito cikin shirinsa ya hade cikin wata farar shadda dinkin zamani na zaratan matasa yayi mugun kyau Kamar a sace shi, ta ganshi ba zato yace kin tashi,yanzu baza kiwa kanki fada ba wannan wanne irin bacci ne ko dai shaye shaye kike ne ban sani ba? kame kame ta Fara tace jiyane na raba dare Ina kallon film,yace uhm ai ko ba kallo haka kike yi,bacci bacci hakkina ma bakya bani ba abinda ya dameki da ci na da Sha na,gyaran gidan,kiyi kwalliya duk ba ruwanki komai na zaman aurenki zero,a Haka Zaki samu ciki ki Haifa min yara, Ina ta baki chance kinki gyarawa Wai me yasa ke bakya ganin yanda yaran zamani masu aure ke kula da mazajensu ba,inda karuwan nan Suka Yi yawa a duniya da karuwan gida dana waje ga Yan kwalta suna ta kwacewa Mata mazaje ke ko a jikinki,ai Sabreen kuka ta saki tace Allah ya kamaka Allah ya Isa dama cin amanata kake yi kana can kana bin karuwai ai dama yanzu baka kwana a gida kullum kana bariki,ya Bude baki yace dama zargina kike yi? to naji Ina zuwa bariki ki gyara halinki ki kwato mijinki,harara ta watsa Masa ta juya ta Shige dakinta ta gyara iya dakinta kal kal Yana shining tayi wanka abinta tayi kwalliyarta sannan ta fito ta Kira shi a waya lokacin ya shiga wata bakar motarsa me arnen tsada ya rubuta wifey ya daga yace ya dai madam ko na dawo ne akwai harka? Wai haushi ya bata ta kashe wayarta ma ta fasa tambayar unguwar Kun San me Shan Coccaine sai a hankali daga yace haka sai haushi ya kamata ta yafa mayafinta a saman atamfarta me tsada ta fito ta Shige motarta ta fisga abinta ta fice ba izininsa tace to shima fita yake baya Zama Nima me zanyi masa.

    Ni Kuwa na gama cakarewa cikin wata English fitted gown ta wani silver din material nayi kyau gashina na Tara a tsakiya na dan Dora siririn mayafina black na saka takalmi Baki da jakata baka,har maroon jambaki na dan shafa sama sama nayi kyau na karshe ana ganina an San wayayyiya ce,Ina shafa turaren da Muka siyo a wajen Mazarkwaila kamshinsa ya Isa gashi da saukar da nutsuwa,shigowa yayi ya min knocking,Fitowa nayi jakata a hannuna tsayawa yayi Yana kallona yanda na Zama wata Queen na diga ruwan kyau dama gani kyakyawa dani, a ransa yace a haka fa maza duk sun gama da ita zancen ya kautar yace let’s go,nace bakace nayi kyau ba,kinyi kyau mana Murmushi nayi nabi shi Muka jera Muna fita yasawa palon key,motar na bude masa da sauri ya shiga na rufe nima na zaga na shiga gefe,nace na iya driving fa,yace ai dama Yar bariki idan bata iya mota ba waye zai iya,nace wlh kuwa.

    Muna Hanya Sera ta min waya suna can jiranmu suke Yi kawai,Muna zuwa yayi parking muka fito hannunsa na rike Muka shiga ciki,sai kallonmu akeyi munyi kyau sosai arna sai yabawa suke,Su Saratu ma abin ya birgesu sosai kana ganinsa ba karya akwai Naira hutu da wanka yabi jiki,kujeru suka Kara Mana mu bakwai Muka zauna mamaki ya Kama Nawwar ganin Santana Dan daudu Namiji ya tira sumarsa ta koma red,Suka ce good Afternoon sir ya jinjina musu Kai kawai yau sunga Isa da gadara a wajensa, mu Kuwa dama bama yanga abinmu,Santana Yana karairaya ya furta su Saratu anga banza ta Fadi anzo kwasar gara,Star tace yo Saratu Ina taga saurayi ai karuwanci ya shiga jikinta sosai,Wise tana ji tace abeg a kawo mana nama da shawarma,kafadar Nawwar na dafa Ina gefensa dama nace kuci kome kuke so wannan Saurayin nawa Dan Albarka ne akwai kudi komai zai biya karku daga kafa Enjoy your life,Saratu da karfi ta kwalawa masu bada abincin tace Juice please tana daga hannu kowacce cikinsu sanye take da matsiyatan Kaya kusan tsirara suke,aka Fara kawo musu gasashen nama,aka kawo shawarma,ga Ice cream,ga lemo,ga wani farfesun kifi a gefe da chips,suna ta ci suna Santi,Yar zabil ta dauki nama ta jefa a baki ihu ta kurma tace heee sweet oooo…Kai yau Ina Jin dadin rayuwata Wise ta furta suna ta ci Nima Ina ci Ina cewa muji dadinmu Karuwai mun samu me kudi,na kalli Nawwar da baya cin komai shi nace ka shiga Uku ka fada hannun karuwai taka ta kare,Murmushi Kawai yake suna bashi dariya,kifin na Fara ci nace ga inda dadi yake, Santana ya furta water Yana yiwa masu wajen magana aka kawo,Saratu ko magana ta daina sai aikin duri Kawai take yi, nace a gama kowa yayi take away abinda yake so,Star sai ihu da wata mahaukaciyar dariya tace yau Muna gwangwajewa,Dan daudu yace ba abinda zamu ce sai muce Allah ya barku tare ke Kuma ki dinga bashi dadi sosai a sakar Masa jiki banda rowa,Yar zabil tace fada Mata dai ko tafi ji irin wannan ba a musu rowa,Wise kallon Saratu tayi tace ke baki da saurayi me kudi Wanda zai kashe Miki kudi haka sai shegen ci duk kinfi kowa ci sai kace saurayinki ne ya siya,Nace ku kyaleta taci sai a Karo karku damu akwai kudi me kudi ne karku tausaya Masa,Saratu tace karku isheni Jin dadina nake yau,karuwanci yabi jini cewar Star,Kai Karuwai Muna shanawa Karuwanci yayi a rayuwa a buga bariki kunji ta daga juice tana korawa tace Muna cin darajar karuwanci,Ke dai bari cewar Santana Dan daudu,shi dai Nawwar saidai yayi Murmushi Kawai Yana kallon ikon Allah na wani tale kafafu Kamar yanda su Seraline Suka zauna Suma kowacce Kamar tana palon uwarta bama Jin kunya duk abinda Muka ga dama fada muke Muna ta shewa ga wajen kida masu Dadi suna tashi,Star tana koshi ta mike a wajen tayi Mika ta koma ta zauna,mikewa nayi Nima Nawwar ya fisgoni na zauna da sauri na kalle shi nace mika zanyi,wani kallo ya min nayi shuru,Saratu ita dama bata da kiriniya akwai dan aji kadan,sai da Muka koshi Kamar cikinmu zai fashe Suka Yi take away ya biya komai sannan Muka fito farkan Yarzabil yazo da katuwar mota ya dauke su Suka tafi Muka fita muma dauke da take away dinsa bai ci a wajen ba,Muna mota yace hankalinki ya kwanta yanzu? Nace ae yace sai me nace gida akwai film din da zasu haska yau Zan kalla,gida ya kawoni Ina fita yaja motarsa ya koma gidansa ya samu ba kowa ya tambayi me gadi yace ai Sabreen ta fita bayan fitarsa, yasan Bata yawo ta tafi ba baza ta wuce gidansu ba,waya ya kirata tace gani ma Zan shigo gidan,Yana kashewa ta ja tsaki tana cewa shi Papa ya matsu nayi ciki bari na lallaba shi dai na samu cikin,tana shigowa gidan Yana Palo a zaune rungume shi tayi ta baya tace na dawo,ledar take away din ya Mika Mata ta karba tana murna Kamar kasan yunwa nake ji

Masu bukatar sauraren Audio na wasu books dina kuje S ZARIA TV

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               36-40

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

Page naku ne

Ruky
Kukuwa
Maman Khadija Abj
SummynDaddy
Fatimalawan600
Maman Twins
Ammey laylah
Umminnas
Serdieycute
Wuta(Golda)
Hafsat I Atiku
Khairiyya Ahmad
Darlin Queen
~Umme

Gingina ga
BINTA UMAR ABBALE
UMMIN SADDIQ
MHIZ AWWAL

        Sabreen tana Jin Dadi na gudu da kaina sai ganinmu tayi ya dawo dani tace wlh baka Isa ba bazan zauna da Yar iska ba ni da kaina zanyi maganinta,ban kulata ba shima bai kulata ba ya shirya ya bar gidan ya wuce gidan Khaleel,Ina zaune zuwa yamma ban San komai ba wasu kartai su biyu Suka fado min daki,hannayensu dauke da manyan bulalai,Sabreen ce ta shigo tace Na’alhaji ku cika Mata aiki yanda nace kudi Zan biya,Ina zaune Ina kallon ikon Allah,mikewa nayi tsaye,Sabreen tace ke ba Yar iska ba wlh baza ki zauna min a gida ba ai ba gidan ubanki bane,Cikin kartin nan Daya ya kamani da igiya a hannunsa Muna kokawa Ina cewa ka sake ni zanci uwarku shegu tsinannu Allah ya Isa a Haka Suka daureni da igiya Kamar goro kowanne a cikinsu da bulala Suka Fara zubaba min ita Kamar daga sama aka basu umarni,Ina ihu amma Sabreen cewa take ku karawa shegiya sai ta daina motsi gobe ai baza tazo gidan wata ba,tunda Naga zasu cuceni yanda tace sai na daina motsi ai Ina Jin haka da Suka sake tsula min uku sai nayi suman karya na daina ko motsi tare da dauke numfashi na, Sabreen ta tuntsire da dariya tare da cewa ku barta haka ta Suma muje na biyaku,Suka juya Suka fice sannan na saki numfashi na amma dukansu dukane bana Wasa ba gadon bayana yayi rudu rudu ya farfashe,na fashe da kuka nace wlh sai na rama,Ita Kuwa biyansu tayi Suka tafi Ina nan kwance a kasa sun daureni sun tafi,inda Allah ya taimakeni na dinga ihu ban daina ba cewa nake wayyo Allah azo a taimakeni har Nawwar ya dawo yaji ihuna a daki da gudu ya shigo ya ganni a daddaure da igiya,na saki kuka me karfi,yace waye ya Miki haka nace Sabreen cikin kuka,reza ya dakko ya yayyanke igiyar na tashi zaune da kyar nace kalli bayana na zuge Masa zip yaga yanda bayana yayi rudu rudu bulala Uku kawai wani wajen har da jini abinka da Fara dama,waiyazubillah ya furta ya fita a fusace,Ni Kuwa wayata na jawo na Kira Seraline tana dagawa na fashe da kuka nace ku taho za a kashe ni matar saurayina tasa Yan Iska sun min dukan tsiya sun fasa min jiki kuzo gidan na fada Mata Adress,Seraline Wayar ta ajiye daure take da guntun towel daga wanka ta fito ma taji wayata da ihu ta fito tana kwalawa karuwan Kira harda Yan daudu su biyu,matan Suka zo su wurin goma tace an taba Mana Yar uwa,Yar uwar mu tana can Rai a hannun Allah matar Saurayinta ta kawo Yan Daba sun Mata mugun duka.

   Santana dan daudu yace ahayye an tabo jarabar duniya yau za aga bala’i ya rike haba yace oh Kinga star ku dakko makamai,Nima ga Nawa ya suro wani dogon ludayin juya miya,Daya dan daudun yace yau nake Jin jaraba shike nan sai a nemi illata Mana Yar uwa laifinta ko na mijinta ita Miracle sabo da Allah Ina ruwanta service fa aka dauketa ya tafa hannaye biyu yace kuzo mu kaddamar musu ke Yar uwa kiji samun waje dan Allah ya dakko almakashi yace aski zanwa shegiya a local government dinta sai na samu tsuliyar shegiya na aske ta kwal kwal Zan Mata muje,Star tace yau idan na dinga zubawa Yarinyar mari sai ta tafi gidansu a kafa, Wise ma daga wanka ta fito,itama Yarzabil haka,Manduwa da Star sune da wata matsiyaciyar shiga domin manduwa mini skert ne a jikinta sai half vest,ita kuma,da sauran karuwan duk ba me shigar mutunci su goma cif Suka hadu zasu je,wasu Suka taho Suma Suka ce ai dole Suma suje su kwatowa Yar uwarsu yanci,mutum biyar harda yare Suka karu,kananan mota uku taxi uku Suka cika su Sera dukkansu daure da towel su uku a haka Suka tafi sauran Kuma Babu me shigar mutunci ga Yan daudu mutum biyu.

    Suna zuwa kofar gidan masu taxi dinma nasu ne Yan duniya ne harda zana kwabo a kofar gidan Suka danne horn ba dagawa fiiiiiiiii suna zaga wajen da mota wasu da makamai wasu babu,Kuma sunci sa’a ba securities yau a gidan sai me gadi Kara da hayaniya tasa Sabreen data buya a daki gudun Kar Nawwar ya daketa ta fito Jin ihun da karadin tasan ba lafiya ba,har compound ta fito taga an banko kofar gate suna dukan gate karaf kararaf…wata Igbo a ciki tace who is she da karfi,Seraline daure da dan towel tace gata can Suka rugo gidan gaba daya suna durawa Sabreen ashar tsoro da firgici yasa Sabreen ta kasa motsi da kyar take daga kafarta tana ja da baya,Seraline ba jira tana zuwa ta cakumi wuyan Sabreen ta kwada Mata mari,ta sake kwada Mata mari tace dan uwarki Yar uwarmu Zaki sa a daka ta sake wanke ta da mari,Star tazo ta hankada Sabreen ta timata da kasa Suka Zo dukkansu Mata Suka dinga jibgarta,Yan daudu ihu Kawai da zage zage sukeyi suna shewa da tafi, Sabreen ihu babu damar Yi sai ta Fara basu hakuri tace wlh bazan sake ba babu ruwana da Yar uwarku daga yau,Wise ta make Mata Baki sai da jini ya fito ko a jikinsu Yarzabil harda fisgowa Sabreen nono ta kurma salati tace ko a bariki shegiya baza ki samu kudi ba,wannan a kwalta ba me zabarta bata da nono,Seraline ce tace ku kyaleta haka Naga jikin Yar uwarmu da sauki ganina na fito Ina dingishi,Sai lokacin Nawwar yaji hayaniya yaki karewa ya zaci ma securities dinsa ne suka dawo ya leko ta sama ya hango Sabreen kwance a kasa jina jina da ita ba Dan kwali rigar ma ta yayyage,jini ta baki na fita,jikinta duk rauni,Me gadi ma yana kwance a kasa Yan daudu sunci ubansa sun kwantar da shi a kasa Santana ya Dora kafarsa daya a ruwan cikin me gadi yace da dayan Miko min mudubi a jakarka na duba fuskata ko ta baci,Nawwar ne ya fito da sauri ya daka musu tsawa wannan wanne irin haukane zaku zo min gida ku daki matata,wanne irin hauka ne haka,Seraline tace Matukar za a taba Mana Yar uwa to wlh baza mu Bari ba, ba a taba irinmu a kwana lafiya,baiwa ce ka dauka wallahi duk ranar daka bari aka sake dukanta wallahi abinda zamuyi sai yafi wannan,tsawa Nawwar ya daka musu ya nuna musu hanya yace get out ko yanzu nasa a kamaku gaba daya,Wisa tana gyara daurin towel dinta tace dama ai ba Zama zamuyi ba dole zamu tafi mudai aka taba Mana Yar uwa baza mu kyale ba ko sojoji ka zuba gidan nan wallah sai mun tarewa ko waye Hanya mun Saba Masa kamanni,Ina ji nace ya Isa haka Wise kuje tunda Kun rama min ana Kara tabani zan kiraku kuje,Suka tafi abinsu Suka sake tashin motocinsu Kamar zasu kashewa mutum dodon kunne,Suna barin kofar gidan ya juyo ya kalleni yasan Yana masifa Zan gudu can bariki yace me yasa bakya ji? Me yasa kike da taurin kai? Lokacin Sabreen ta bude idonta tana kuka wiwi tana kallonmu, nace ya za ayi tasa karti maza su min duka daya ya rikeni ya daureni,Ido ya zaro yace ya rikeki nace ae sai da ya rungumo kirjina sau uku Yana taba min nono Kuma itace tace su taba na banza ne na karasa da kuka na fada jikinsa na rungume shi nace shi yasa nace gwara kai ka dinga tabawa tunda kana biyan kudi,Tsaki yaja ya janye jikinsa da sauri ganin Sabreen tana gani, tana daga kwance tace ta tabbata wallahi Karuwarka ce yau gidan ubana Zan kwana,duk dukan da taci haka ta mike Yana tsaye taje ta hado kayanta ta fito tana tafiya da kyar ta shiga motarta,ihu nayi Ina dariya nace bye bye,Me gadi da ya tashi tuni Yana uzurinsa ya bude Mata gate ta fice a tsiyace, Nawwar ya kalleni yace kinji dadi shike nan? dariya da farin ciki ya kamani nace ae mu indai za a taba mu to fa uwarsa baza tayi bacci ba ko waye in ka gaji ka maida ni bariki na ka huta ni banga abin takura ba a nan duk inda Naga Sabreen sai ta San fada damu ba dadi.

      Ido ya lumshe a hankali tare da juyawa ya koma Palo ya fada saman kujera Yana huci zuciyarsa tana Masa zafi ciki na koma nima na zauna Muka Yi shuru ni da shi,ba a fi 15mnt ba sai ga Kiran Baffansa,sai da yayi tunani dama ya daga Yana dagawa yaji ashar sabo da shi babban mutum ne amma Babu Kalar zagin da baya yiwa yaro sai da ya kutuntuma Masa ashar iri iri karshe yace to Dan uwarka Dan ubanka kazo gida Ina nemanka,to kawai yace ya tashi bazai iya driving ba yau driver dinsa na ya tukashi zuwa gida.

    Kowa ya zauna yayi Shuru Yana saurare Nawwar yana kusa da Maminsa, Iyamami itace ta Fara magana tace wallahi Nawwar ka bani mamaki ka bani mamaki tirrr da hali irin naka,Mami a ranta tace ba tirr ba ban haifi dan tirr ba wlh Allah yayiwa dana Albarka Inshaallah sai yaga dai dai,Iyamami tace dama wannan lusarar uwar taku ai ita ke zuga ku wato Kai ka girma mace daya ta maka kadan sai ka Kara da karuwa,to bari kaji ko zaka Kara aure sai dai a dangi a samo maka wacce aka sani aka San iyayenta da asalinsu,Muna wannan gari Wanda ya tara baki garin kazo nazo ace ka hadu da wata ka aura bazai yuwu ba ko bana raye Matukar da sauran yarana a duniya baka Isa ba,idan Karin aure kake so ka koma can danginmu Shuwa ka Nemo Yar dangi idan Kuma baza ka iya ba ka bamu zabi,Kuma ba yanzu ba sai Sabreen ta tara iyali,Mamin Nawwar ce tayi magana tace idan Allah ya rubuta ya zakuyi wannan fa hurumin Allah kuke shiga,laaaaaa……Iyamami ta dafe kirji kunji Salamatu abinda take fada min wato ke ba a Isa ayi magana akan yayanki ba sai kin shiga kin tare musu shi yasa Suka taso basu da tarbiyya basa ganin kowa da mutunci
Papa ne yace dan Allah ku kalli jikin Sabreen ‘yata Daya tilo tace gaba daya matan tsirara Suka Zo da Yan daudu sunfi su talatin Suka Mata dukan tsiya,Sabreen da bakinta yake a kumbure da idonta daya ya kumbure tace ai iya Yan daudu sunfi sunfi su goma,Nawwar ya kalleta tare da furta kiji tsoron Allah lokacin dai kin ji jiki bakya gani dai dai,Baffa ne yace rufe min baki yanzu kalli Yar uwarka kalleta matarka wata banza ta Mata haka idan baka Yi Wasa ba sai na tsine maka,Mama tana gefe tace ato a dauki mataki wallahi idan wani Abu ya samu yata tilo baza aga dai dai ba duk da nima Yar uwa ce amma ai Da baifi ‘Ya ba,Sultana ce tace wlh Namiji yafi ‘ya ko a gado ba daya bane,Baffa ne ya kifa Mata Mari ta dafe kunci yace uwata tana magana kina magana,Iyamami kuka ta fashe da shi tace dama yaran Salamatu basa ganina da mutunci sun tsaneni ta gama zuga su,Amaryar Baffa Yar gaban goshinsa sai yanzu tayi magana tace ato gwara ku gani da idonku nima da yarana biyu ne rak basa kaunata basa kaunar yarana Kuma jini daya muke dadin abin dai mijin ko kwana baiyi a dakinki sai dai ki dafa Mana a matsayin baiwa kike shi yasa ban damu ba,Iyamami tace ita take jawa kanta da kuturun iyayinta,Baffa ya kalli Nawwar yace ka tabbatar ka gyara kuskurenka idan ba haka ba ga shedu kar ku ce ban fada ba duk abinda na maka kaika ji,Kuma ka tababbatar ko wacece ta bar gidan nan Kuma Kar najita a Daya daga cikin gidajenka Zan dinga bincikawa Kuma Kar a kawota gidana ko bangaren uwarka ta koma barikinta kaji me nace? Nawwar yace naji,Sabreen tace Saura Maganar dazu Baffa,yace Ina sane ai tace dama baka kwana tare da ita Kuma kana da lafiya,idan da kana muamular aure da ita ai da mun ganta da ciki,Nawwar ransa ya Fadi da Sabreen har wannan zancen ta iya fada kwafa yaja a ransa,sai da Suka gama fadansu sannan Suka sallami kowa,Mamice ta Fara mikewa yaranta kaf Suka tashi Iyamami ta furta idan aka zagemu aka ci Naman mu Allah ya Isa munafukai duk kin lalata yara Anya Kuwa wannan jinin mu ce,tafiyarsu Suka Yi Suka barsu suna ta magana akan Mami da yaranta.

     Mami sama ta haura bedroom dinta,yaran gaba Daya Suka shiga Nasira da Hamra ta Fara Kora tace kuje kuyi Assignment dinku ayi Sallah Kuma,Sultana ta kalla tace kije kiyi Sallah ki shiga kitchen kiyi girki tace to ta wuce shi kuwa Autan nasu sarkin ball ya wuce dakinsa tuni,Nawwar kwanciya yayi a gadon Mami ita Kuma tana zaune a gefe a hankali tace wacece? Nawwar yace Mami ba fa wata bace,bana son karya me yasa baka ji Nawwar me yasa kake son sani a masifar mutananne? tunda kasan halinsu Kawai kabi umarni a zauna lafiya,Mikewa yayi ya zauna yace Mami kin san fa tsarin Allah dole haka rayuwarka zata bi,Kuma wlh ni nayi Niyyar taimakonta bazan fasa ba,Ido Mami ta zaro tace sonta kake Yi? da sauri yace haba Mami so Kuma Allah ya kiyaye bata layin Kalar matan Dana ke son aure ma,ni da nake son Ustaziya kullum a hijab Yar Shuru Shuru saliha bana son mace Yar duniya,nafi son me addini da hankali, Murmushi Mami tayi tare da cewa Allah ya baka to,yace Ameen,to fada min tunda kace ba sonta kake Yi ba me zakayi ka taimaketa Kuma wacece ita? yace ni so nake Kawai ta sanadina ta shiryu yanzu dalilin kawota gidana so nake na raineta na bata tarbiyya sannan na aurar da ita,au ashe yarinya ce ma shekarunta Nawa? Mami ta tambaya,yace 22yrs take,dariya Mami tayi tace Dan Allah Nawwar bana son Wasa 22yrs sabo da rainin hankalinka kace Wai zaka raineta ka bata tarbiyya ka aurar da ita,to ki bari Mana kiji labarinta Mami ba kya cin ribar zance

    Kunne Mami ta Miko Masa tace to Ina ji,Murmushi yayi yace to ki daina kallona ma kunyarki nake ji,yau kuma,dariya yayi yace I’m serious,Ina ji,yace Kinga Mami bana boye Miki Abu karki ce nayi rashin kunya, lokacin Sabreen tana min wulakanci Ina nemanta bata yarda ko naje na iske tayi bacci Kuma baza ta tashi ba,lallai maganin Iyamami yayi aiki,idonsa ya rufe Wai kunyar Maminsa yake ji,tace uhum Ina ji,shine naji haushi na gaji Kuma a lokaci Ina cikin yanayi na bukata,Mami tace Allah sarki My son Sannu,dariya ya sake saki yace Mami kunyarki  fa nake ji,to na daina Ina jinka,yaci gaba sai nace bari ma na fara Neman Mata na dinga bin titi shine na ganta,a lokacin ta Yi maka ka dakko ta ko? Mami ta tambaya yace ae,Amma ba abinda ya faru banyi komai ba,Mami Hannu ta daga sama tare da furta ya Rabbi na gode maka Ina Addua Inshaallah yarona bazai lalace ba na sani,daga nan ya bawa Mami labarina kaf da komai har labarina dana bashi cewar Ni Yar tsintuwa ce da labarin Dagaci inda na taso,Mami tana gama ji tace ya sunanta? Rabiah,tace duniya kenan idan kaji halin da wani ke ciki sai ka godewa Allah Kai.

  Abinda mutum zai Fara godewa Allah akai da aka Yi auren sunna aka haife shi ya taso cikin asali da dangi,idan aka jefar da Kai ko akasi yasa kazo a Dan tsuntuwa baka San kowa ba shike nan Kai baka da asali da nasaba,Babu dangi bare uwa da uba baka San kowa ba a duniya sai Kai kadai wannan kadai ya Isa a tausayawa yaran tsuntuwa da Wanda ke gidan marayu Allah sarki kaga rashin iyaye da dangi shi ya taba wannan yarinya da ace ta fada Hannu na gari da shikenan, idan aka samu akasi baka fada Hannun na gari ba to fa ka shiga Uku,a wannan Zamanin wa Yana zina da kanwa,Kani yayi da yayarsa,kanin uba ya Nemo Yar Kaninsa ko Yar yayansa ana samu uba me Neman yarsa to bare mariki Dagaci Wanda ya rike yarinya ganin bata da kowa irinsu Kuma Allah Yana musu baiwa da ba kowa ke samu ba sabo da Allah baya hadawa mutum biyu

      Wannan marikin nata yaci Amana matuka Kuma na tausaya mata,yanzu kaga Wanda ya riketa yaci amanarta ya koreta amma karuwai sun karbeta har fada suke akanta suna daukar Mata fansa,suna kiranta da Yar uwarsu su basu kyamaceta ba Zama ya hadasu na banza Amma sun dauki kansu Yan uwan juna ne,ga masu hankali Wanda basa shashanci sun tsani junansu Kuma suna Yan Uwa musulmai,wani ya taba musu ita sunzo sun daukar Mata fansa Allahu Akbar,kaima gashi Allah yasa maka ita a ranka,a’a Mami nifa ba so ne ba Kawai naga ta lalace ne da yawa shi yasa nake kokarin taimaka mata,Mami tace ka taimaketa da duk abinda zaka iya da karfinka da dukiyarka ka taimaka mata amma kayi da iyawa sabo da mahaifinka idan ya gane Kuna tare zai dauki matakin da baka zato kasan halinsa ita Kuma matarka bata da hankali ka sani Sarai zata sake fada musu,Amma yau Zan bika naje na ganta ashe itace Hamra take cewa kazo da wata ziza kyakyawa Sam bata Yi Kalar Kauye ba,yanzu kaje kayi Sallah in yaso sai muci abinci muje,no Mami bazanci abinci ba nasan ta dafa yanzu Yarinyar fa tana da Yar biyayya abinda nace tana Yi she is so caring, Sabreen bata bani abinci tunda na aureta naci banci ba babu ruwanta amma ita har rokona take yi sai naci dole,Mami kin gani har durkusawa fa,a haka tasan idan Ina Fushi kiji dan Allah dan lokaci kadan ta karance ni she is so brilliant,Mami tace kaji Yar baiwa Kudirar Allah,yace dama sunanta ne Kuwa Kamar kin sani Miracle ake ce Mata,ya sake furtawa,  Mami ki tashi kiyi Sallah tace to ko bakya Yi yau ne?  Slifas din dake kafarta ta dauka tare da jefa Masa ya fita da gudu,Tsaki Mami taja tace kaji min yaro dan Allah Kai yaran zamani Allah ya shirya ta kwanta Kuma bata Sallar Kamar ya sani.bai samu Sallah ba tasa yayi ya dawo gida a Hanya Suka hadu da Iyamami ta fito daga wajen danta tace au hararata kake Yi Nawwar gaba kake dani ko,bai kulata ba cikin takunsa ya shiga sashen Maminsa ya ganta a main Palo suna cin abinci fuskar Mami ya kalla ya ganta da kwalliyarta alamun ba a sa ruwan Alwala ba,sake lekawa yayi tace lafiya wai, Murmushi yayi yace ba komai,Sultana ce tayi magana tace Mami na koshi ni,Zama Nawwar yayi Yana latsa waya yace Wai Yarinyar nan Mami naga yanzu wani yanga take ji kalli tafiyarta,Sultana tasan tana magana zai ci ubanta Shuru tayi,Mami tace ai an Fara Zama Yan Mata baka gani tayi candy,baki ya tabe a ransa yace Mami baki San Yan Mata ba sai karuwai gasu nan kyawawan Yan Mata wata in kaga tana bariki sai kaji Takaici komai Allah ya bata amma ta watsar da kyan a bariki,a fili kuwa bai ce komai ba,Autansu ne ya shigo sanye da 3qtr da Riga armless,Hannu ya mikawa Nawwar harda cewa bros ya gida ya akaji da iyali,dariya Suka Yi gaba daya

    Ko a jikinsa ya zura hannaye biyu a aljihunsa yace me aka dafa? gashi ka gani jullof din taliya bazan ci ba indomie Zan ci ni, okay ka sa kwai kaji Autana,Nasira tace wlh kina biyewa Autanki Mami,sai da Mami ta gama ta dakko mayafinta na Arabian gown din Dake jikinta maroon da hand bag dinta tace tashi Kai mu tafi,Su Hamra Suka ce a dawo lafiya Yaya ka gaida gida,yace to,suna Fitowa akan idon Mama ai da gudu ta fada bangaren Iyamami tace taso ki gani da idonki uwar za a tafi wajen bokaye Yan tsubbu,an tafi wajen masu Juju tsafi Kinga sabo da yau an musu fada sunji basu samu nasara ba,Iyamami ta fito da sauri harda labewa tace anyi uwar banza me watsa yayanta dama nasan aikinta kenan,ai da gani ba sai an fada ba to li’ilafi wallahi,Mama ta rike baki tare da furta ta Kare a kansu sai gobe Sabreen zata koma,Iyamami tace Allah ya kaimu.

Ni Kuwa tun fitar Nawwar  nayiwa Seraline ta kawo min dogayen riguna haka dai na dan mutunci cikin kayana ta dan zabo kala hudu ta bawa Wise tunda ita tana da mota ma itace ta kawo min domin a motarta na koyi tukin mota itace ta koya min ta koyawa wasu ma da yawa,tana zuwa tace Ina shegiyar? nace ta tafi gidansu shima sun Kira shi,tace to idan ya koreki ki min waya nazo na daukeki ai da gatanki kina da mu babu Wanda zai taba Daya a cikin mu ko waye wala arne ko musulmi face mun dauki mataki,nace Wise kin San dai bani da mutunci ko? tace ah sai dai na bawa wani labari,na sake furta kin San dai bani barin ko ta kwana idan fada akace za ayi sai dai a mutu Kuma Ni fada dani baya karewa,Wise tayi ihu tace ai bama cin Kan jaki badai mu ba,na sake nuna kaina da yatsa nace Kuma kin san bani da kunya cikakkiyar fitsararriya ce ni wannan karuwancin ban shige shi da Wasa ba da karfina da komai nawa na tattaro na shiga Kuma na Fara kenan ba fita,wise tana ihunta tace yes ooooo mu mutu a ciki,center table na daka da hannuna Ina tsaye Ina zaga palon nace to an taro match wannan Yarinyar sai na hanata Shan ruwa ko wace ci uwarta dan burar….wise ta kundumo ashar nima na lailayota na dura nace ba dai sabo da Namiji take wannan haukar ba sabo da bana ko rike Masa hannu a gabanta shine take wani ae yane to wannan show din dole ya shigeta na girgiza gashina nace zata ga tsiya,Wise tace tasan Kuwa su waye masu siyar da gidan kashi,duwawu fa muke siyarwa ka shiga ka fita ka biya,a mazan ma me ta sani ba a cinyewa shegiya duwawu shi yasa  Zama nayi na tattale kafafuna sosai na baje tare da furta na tabbata bai taba nacking nata sosai ba,Muka kyakyace da wata mahaukaciyar dariya irin ta Yan duniya Muka tafa,Wise tace me Zan Miki yanzu Yar aikin Karuwai a da,nace a ai yanzu original karuwa ce cikakkiya ,tayani gyara gidan nan please mu canjawa furniture din nan wajen Zama yayi local yanda aka saka su baiyi making sense ba..kafin na rufe baki sai ga Yarzabil da Star Muka dinga iya shege gaba Daya Suka tayani Muka hadu Muka gyara gidan nan neat ko Ina Yana sheki da kamshi na musamman,dakinsa Dana Sabreen ne bamu gyara ba,Suka ce dakin ogan fa? Nace zanyi da kaina yanzu,sallama Suka min Suka tafi abinsu,Ni Kuma ban taba shiga dakinsa ba sai yau na shiga na gyara ko Ina Kal Kal har toilet dake gadon me turawa ne sai na canja mishi position shima komai na gyara yayi wani mugun kyau na turare da kamshi, na kunna ac na rufo dakin,a gurguje nayi wanka da sallar Isha sannan na shirya cikin wando tight fari tas da wata rigar material sharara daga kirji zuwa ciki an Mata landing bangare daya yayi tsayi sosai har kasa rigar take tabowa gefe Daya Kuma iyakarta gwiwa,grey color ce tayi kyau rigar sosai ba karamin kyau nayi ba dake dan jikina dumi dumi yake da Yar kibata kadan,baza ace dani ramammiya ba Kuma baza kace dani me kibaba, gashina da yaci gyara jelarsa na yawo a gado bayana na daura wani Dan mitsil din dankwali me santsi Wanda yanzu aka dawo da yayinsu grey Kalar rigar nayi kyau ainun Ina kamshi na Shiga kitchen na Fara shirya girkina na musamman kamshin turaren dakin da kamshin girkina ya gauraye palon a haka naji dirin motar Nawwar..

      Parking yayi a gidansa ya fito ya zaga tare da budewa Mami ta fito suka Shiga ciki,kofar yaji a kulle door bell ya Danna,hannuna na wanke nazo da sauri na Danna code din kofar palon na bude,Yar matashiyar dattijuwa na gani me Kama da Nawwar da gani ba tambaya mamansa ce,Murmushi nayi nace oh Sannu da zuwa kuyi hakuri wlh Ina kitchen aiki nake,Mami ta saki baki tana kallon wata princess a gabanta a ranta tace kyakyawar gaske ce gaskiya,Murmushi Mami tayi tace ba komai Suka shigo,Mami ta kalli cikin palon ko Ina ya canja ba yanda tasan shi ba ga tsafta ga kamshi ta ko ina ga Kuma girkin kamshin ya Isa,bayan sun zauna durkusawa nayi har kasa nace Ina yini,ta amsa da lafiya lau,na sake cewa ya gida ya yara? tace duk lafiya tana Murmushi,Nawwar na kalla Muka hada Ido nace Sannu da zuwa hope dai ba a maka komai ba ko ka tafi Ina ta tunani,yace ba komai,girkina na tuna akan wuta na mike da sauri nace girkina na shige kitchen da guduna Wanda ya bawa Mami dariya,ruwa da lemo me sanyi na kawo Mata a tire me kyau na tsuguna tare da tsiyaya Mata a glass cup nace kiyi hakuri ban San wanne Kika fi so ba Kawai na dai dakko na Mika mata,Mami ta karba tana cewa ba komai ta Sha, na koma kitchen na dakko Mata snacks din da nayi da rana na kawo Mata nace gashi kafin na Gama girkin kiyi hakuri,Murmushi Mami tayi,Nawwar yasa Hannu zai dauka caraf na rike hannunsa nace bafa naka bane,hannunsa ya janye da sauri Yana hararata nace ai Kuwa sai dai ka harareni ma na Mama ne,yace ke Wai sa’anki ne ni, baki na turo na murguda Masa baki, Mami tana kallo,Tsaki yaja,na koma kitchen na dawo na zauna a kasa ganin Mami na kujera ban zauna kujera ba,tace   nice Maman Nawwar,nayi Murmushi tare da cewa Sannu Mami,tace yawwa naji labarinki ya bani…kafin ta rufe baki nace wlh ya za ayi kin San kowa da sana’arsa to ni tawa kenan Muna dan siyar da idon garin ni tunanina ya fada Mata karuwa ce ni shi yasa,Kunya ta Kama Nawwar ya min wani mugun kallo yaci sa’a Kuwa mun hada Ido nace ai gaskiya ce a fada Mata gaskiya ta sani,Mami tace uhmmm ta jinjina Kai tace Allah ya kyauta, nidai dama cewa zanyi dan Allah karki shiga Harkar Sabreen kiyi hakuri ki kyaleta Kinga ko wace dole taji kishi da haushi a kawo Mata budurwa irinki gida,Nace Mami wannan bata son Nawwar ba wani kishi da take Kawai tana da dalilin tsanata,kin San ni nasan rayuwa ce mu duk irin wannan mun San shi muna karantar mutum,Kuma da alamu tana shaye shaye Kawai dai baku gane bane,to koma mene dai Ina rokonki dan Allah karki sake nace to Inshaallah Mami,mikewa tayi ta fita tare da Nawwar

    Suna fita tace Nawwar wannan Kuwa zata shiryu naji har alfahari take yi da karuwancin nata, Inshaallah Mami zata daina yanzu ai bata yi tunda Muka hadu bata sake kula kowa ba,to shike nan ka dai kiyaye Banda kebewa da mace wacce ba muharramarka ba kaji na fada ma,yace to ya tuka mota ya maidata gida suna ta shawarwarinsu Yana kaita ya dawo gida lokacin na gama girkin na gyara kitchen Ina jerawa a dining ya shigo da sallama na amsa, Dining ya karaso nace wanka fa? Kallona Kawai yayi yace Ina ruwanki abinci Zan ci,okay Zama yayi nayi serving nasa na zauna ni ban zuba ba,Yana cin abincin sai Naga Yana dan tunani nace akwai matsala ko? an maka fada sosai? Kai ya girgiza min a hankali Wai no,nace to meke faruwa ko nice,bai kulani ba,nace then sai na tafi gidanmu gobe…wani mahaukacin kallo ya min Wanda yasa nasa hannuna daya na rufe bakina da sauri.

     Yana gama cin abinci ya tashi na zauna kallon film Ina latsa sabuwar wayata dana siya da kudina iPhone me tsada,Wayar hannuna ya kalla ya iske Ina dannawa bai kula na siyi waya me tsada ba sai yanzu ta bayana ya tsaya na shiga WhatsApp group dinmu na Yan gidanmu karuwai Ana ta turo Xvideos yanda ake sex different style latest idan ya shigo gasu nan sunfi Hamsim tarrrrrrrrr yaga suna shigowa ban zaci Yana bayana ba ma,Wayar naji an fisge a hannuna na juya da sauri Naga shine, yace dama abinda yasa Kika siyi Wayar kenan,ya zaro sim Dina ya jefo min Yace idan baza ki rike karama ba keypad to ki bar rike waya ki zauna haka,nace Dan Allah ka bani na daina bazan sake ba please nace dubu dari uku na siya fa to ka biyani kudin Yana taka steps yace Zan Miki transfer

    Washe gari ranar Kwanan Mami ne abinci tayi ta Kai Ma Baffa part dinsa ta dawo sabo da baya bata kwananta ta rigada ta Saba zata Yi girki amma sai dai Amarya ta kwana da shi,dakinta ta koma sai ga Baffa ya shigo Yana fada gaba daya kin bata min Yara baki iya tarbiyya ba wayarta tana hannunsa Yana dannawa Mami tace me nayi Kuma,Kamar Sultana ce zata shigo wajena na bata kudin shopping amma yarinya tana hararata kece Kika koya musu amma ba komai Zan iya kwashe yarana na kaisu inda za a basu tarbiyya tunda ke baki iya tarbiyya ba ai Ina da wata matar sai na Kai su can,gaskiya ka isheni Kuma abinda ake a gidan nan ya ishe ni fa cewar Mami,au na isheki ma Kika ce? Mami tace ae ka isheni yanda nasan Nima na isheka da sauri ya furta kwarai kuwa kin isheni nima kin addabi rayuwa ta ya buga tsaki tare da kade babbar rigarsa ya bar part din Mami,Mami kwanciya tayi a saman bed tare da furta tabbas da kayi kuka a cikin jirgi gwara kayi farin ciki a Napep ga kudi ga gida har gida babu farin ciki amma ga wasu talakan suna Jin dadinsu.

    Zuwa Yamma Mama da kanta ta maida Sabreen suna shiga sanyi da kamshi ya dake su,palon Suka bi da kallo yanda komai yake shining,Mama ta kalli Sabreen da mamaki tace badai itace tayi aikin ba? itace ai Yar wahala ce sosai,baki ta tabe ta sake cewa naji kamshin girki na tashi ko itace a kitchen? Sabreen tace itace ai Yar wahala ce,sallama Mama ta sake kwalawa na fito rike da wuka da albasa a hannuna nace Sannu da zuwa Mama,Mama tace Kan uwarki ce Maman,kaga Yar iska ohhh wato yanka mu Zaki Yi ko ki sare mu da wuka shi yasa Kika fito Mana da wuka ,lallai duk abinda aka ce kinyi Zaki aikata ashe gawurtacciyar Yar daba ce bayan karuwancin,Ni na zaci me gidan Yana gida ma shi yasa nayi sallama ke kin Isa na Miki sallama karuwa,ohhh dama bai daukeki daga gidan nan ba,tambadaddiya me bin mazajen wasu,to wallahi tun wuri ki Fara hada kayanki ki bar gidan nan, baki na washe tare da furta Laaaaaaa ashe kin San ni karuwa ce,bari na sake tabbatar miki me dattin dankwali cikakkiyar karuwa ce ni na dade a cikinsa ki godewa Allah gidan Mijin yarki na zo ba gidanki ba gwara ki rufawa kanki asiri idan ba haka ba gobe da mijinki zan kwana,Ubana yafi karfinki wlh banza Fasika me bin maza cewar Sabreen,wani kallon banza na musu na furta a haka Kuma na kwace Miki miji tunda yana cinye min duwawu ya daki ta baya ya daki ta gaba ya daki center, Mama baki ta rike tare da sakin salati magana ta inganta,nace au da Wai tantama kike? to bari ki gani na wuce ta Gaban su na haura sama nayi knocking kofar sa lokacin Yana ciki Yana fesa turare ya shirya cikin wani yadi me tsada ruwan kwai Ina daga bakin kofa ko dakinsa ban shiga ba nace kazo kayi baki,kofar ya bude Muka jero Muka sakko kasa Mama tace kayi asara Nawwar,Nawwar Fuska ya bata yace nifa ba wani abu nayi ba na sabon Allah ba Kuma Naga dai gidana ne,Mama kuka ta saki tace shike nan Nawwar an Masa asiri yanzu ni surukarka kake zagi sai ta juya tana kuka ta fita driver ya ja ta sai gida.

     Sabreen ta kalle shi tace kaji dadi uwata ta tafi da kuka,yanzu uwata zaka ciwa mutunci akan Karuwa sai itama ta haura sama ta fada saman gadonta tare da fashewa da kuka,Nawwar dai ya rasa me ya musu, kitchen ya sameni yace Gama abincin muci sai na canja Miki gida,to nace Ina hawaye,fuskata ya leka Jin Ina shesheka,kuka kema kike yi to ke Kuma me nayi miki,a hankali cikin muryar kuka nace ba komai dan Allah ka kyaleni na koma inda nafi wayo inda babu Wanda zai takura min,Tsaki ya ja ya juya tare da barin gidan gaba daya,gidan Khaleel yaje a garden ya same shi babu kowa sai aiki da yake da system saman carpet din ya zauna tare da furta wajenka fa nazo,Khaleel System din ya ture gefe tare da furta Ina jinka,Nawwar labarin irin halin da yake ciki ya bashi,Khaleel Yana gama ji yayi dariya yace dama na fada maka wallahi Matukar aka sani baza ka kwashe lafiya ba,gashi Baffa yace ba gidansa bare a kaita wajen Mami Ni Kuma dangina basa kusa bare a kaita gidanmu,Kuma gaskiya ko wacece tsakani da Allah Dole baza ta yarda a kawo Mata sankaceciyar budurwa irin Rabiah ba,Kuma baza ka fita daga zargi ba a wajen mutane dole za a ce Karuwarka ce tunda har alfarhari take da karuwancinta dole a zargeka nace ka kyale Yarinyar kaki ji ance sonta kake Yi kace a’a ni gaskiya ban san me zance ba a Kai shawara guda ce ka aureta Kawai Kuma kafin hakan ka Kama Mata gida haya Wanda ba Wanda ya sani ga Baba kulu Yar Aikinmu mu baka aronta su zauna tare ka dinga kula da komai nata

     Nisawa yayi yace Ina tsoro gaskiya Kar ta dinga guduwa,Khaleel ya Bude bude Baki tare da furta to Kai Dan Iska sai kace wata Yar uwarka,Nawwar yace Zan gwada hakan ya zanyi amma wanne gidan za a sata yace wannan ai normal akwai gidan Dana gama a Nmandi Steven Estate karami 2 bedroom flat sai Palo da kitchen ai na gama biyan kudin gidan Rannan ma Maman Aabid tace na zuba furniture Kuma na zuba dama tunani nake na bawa kanin Babanmu ya zauna a ciki naga gidansa ya lalace amma yanzu ta zauna anan idan ta tashi sai nace su koma kawai,Nawwar yace ba damuwa a tura Baba kulu ta gyara gidan anjima sai na kaita,Khaleel yace idan ka dakko ta ka biyo ka dauki Baba kulu sai ku tafi gaba Daya sai su hadu su biyu su gyara gidan dama ai ba wani dirty,Nawwar yace thanks a Nan suka rabu Nawwar Yana tunanin Kawai ya auri Rabiah

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                  41-45

Official

By
AsmaBaffa

 

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

 

Page naki ne
BESTYNBEELAT

JINJINA GAREKI
NAJIDA ALIYU BICCA

 

          Lokacin Dana Gama abincina wanka nayi na canja zuwa Abaya arsh color me kyau,Sabreen na samu a Palo tana kallo da fara’a nace uwar gida ga abinci a dining na gama, ai Kamar sabon kamu haka ta mike tana nuna da yatsa ta furta babu ni ba ke Allah ya Isa idan Kika sake min magana na tsaneki,abincinki din banza to Dan uwarki bazan ci ba,tsayawa nayi Ina kallonta har wani fisge fisge takeyi da kanta tana girgiza kanta sabo da cocaine ta motsa, banyi magana ba Kawai na wuce dining na zuba abinci na na Fara ci hankali kwance sai ga Nawwar ya shigo, Sabreen mikewa tayi ana cewa oyoyo ta rungume shi sai yaga abin wani banbarakwai Kawai sai kallonta yake Yi da mamaki,ko kallonsu banyi ba harda zaunar da shi a kujera tana Masa Sannu da zuwa,baki ya tabe ya mike tsaye,hannunsa ta rike tare da furta Hubby ka tsaya ko indomie ce na dafa maka,kallonta yake kawai ko kunya bata ji yace yaushe Kika Fara bani abinci? da duk zaman me kike baki min girkin ba ya wuce abinsa dining tana kallo ya zauna a dining tare da ce min serve me,na zuba Masa lafiyayyen girki sannan na zuba Masa lemon da na hada Ina cewa Sannu da zuwa,yawwa ya amsa kin shirya yanzu zamu tafi Ina gamawa,to na furta,wani wawan Tsaki Muka ji Sabreen ta ja ta haura sama abinta,tana shiga daki biscuits da lemo taci ta koshi ta Fara shaye shayenta ta kwanta sai bacci,shi kuwa Yana gamawa na dakko kayana muna tafi.

    Mama tana komawa gida bangaren Iyamami ta shiga da kuka,Iyamami ta tambaya lafiya? Nawwar ne yau ya Kare min tanadi ya zageni yau ba zagin da ban Sha ba akan karuwarsa Kuma tana gidan har yanzu Babu alamun zata tafi,Iyamami Nan take ta Kira Baffa yana gida yazo wanjenta tace to danka dai ya nuna Mana bamu Isa ba ya zazzagi surukarsa sannan karuwa dai yace Zama daram tana nan,Baffa ransa ya baci wayarsa ya daga tare da Kiran Nawwar lokacin mun dakko Baba kulu Muna Kan hanyar zuwa Estate din ya dauki wayarsa Baffa fada ya balbale shi da shi yace kasan Allah idan baka maida karuwar nan inda ka dakko ta ba sai kaga abinda Zan maka,Nawwar yace kayi hakuri amma bata gidan ta tafi ma tsaki Baffan ya ja tare da kashe waya.
Mu Kuwa hadadden Estate din muka shiga har gidan, gidajene masu kyau flat duk irin daya sun Kai dubu a bakin gidan yayi parking Fitowa nayi da sauri na zaga tare da bude Masa kofa Ina murmushi,Fitowa yayi fuskar nan a daure,Baba kulu na budewa itama nace Babata fito,Baba Kulu tayi Murmushi tana kallona da kaunar yanda nake girmamata tun ganin farko yanda na gaisheta ya tafi da imanin Baba kulu sai kace Wanda ta Haifa a cikinta ta zaci wata ta kirki ce ni.

    Gidan ya bude muka shiga bai ma shigar da motarsa cikin gidan ba,gidane yayi kyau sosai nace wow furniture din yayi kyau,Baba Kulu sai ki dauki daki daya na dauki daya shike nan,yace sai gobe za a kawo muku kayan abinci,Baba kulu ta furta yau ma ni cikina a koshe yake yace mashaallah,yanzu sai ku gyara gidan Abinda kuke bukata sai ki turamin text,nace Banda waya ka manta ,Oops bari na kawo miki wayar nace kafin ka fita sa min number Seraline a wayarka na kirata yanzu zasu kawo Mana kayan,Ido ya zaro yace dare fa yayi,hmm ai mu ba ruwanmu da dare Kuma darenmu shine ranar mu,f yace sai kace Aljanu fada min number, na karanta Masa ya shiga tare da Danna kiran bugu daya ta daga tace hello waye,Wayar ya Mika min nayi magana nace Selarine miracle ce,an sake tabaki ne ko Yaya?na lissafa Mata abinda nake harda turarukan kamshi sabo da a layinmu duk akwai ana siyarwa,tace to bari na siyo amma kin San za a kashe dan kudi musamman turarukan kamshin dakin nace no wahala ki siyo sai ki fada nawa Kika kashe Zan Miki transfer,angama yanzu zamu zo dasu pretty, address din gidan na tura mata sannan na Mika Masa wayarsa,ya karba sannan ya fice,kafin ya dawo Seraline, Star da pretty sun siyo komai sun kawo ,Seraline tace gaskiya kina Jin Dadi shegiya,wani fari nayi da Ido sai ga Nawwar ya dawo kamshinsa ne yasa Muka juya Muna kallonsa mikewa nayi na karasa gabansa Kamar zan shige jikinsa nace ga saurayina na nuna shi nace wannan da kuke gani na Correct man,dan Albarka kenan,Allah zai masa Albarka,abinda yake min Allah ne Kawai zai biya shi,Seraline tace da shewa Yesssss…..Muka kyalkyale da dariya na sake juyawa Muna facing juna nace Seraline Saurayina me kudi ne akwai kudi,hannunsa na riko nace kalli agogon nan na diamond ne ki fada min wanne Namiji kuka gani Yana sa diamond sai saurayina ga kyau ga Naira ga addini ga kirki ga kyauta ai nasan ma Sai yaga daidai a rayuwarsa na karasa a sanyaye,shide kallona Kawai yakeyi yanda muke nishadi da kawayena sabo da yanda su Seraline suke amsa min da cewa ai Allah zai masa albarka, Star tace irinsu Allah ke so,nayi girgiza da kafadata nace wace duk garin nan da saurayi irin nawa,Murmushi Kawai yayi ya Mika min karamar Wayar a kwali da layina ya juya zai fita yace ki tabbatar Kun kulle gida kafin ku kwanta nace Ohhhh kaji caring ahhh kana fasa min kai you be better person, barin gidan yayi Muka ci gaba da gyaran gidan tare da su Star babu kida ma rawa muke yi Muna aiki dama gidan baiyi dirty ba sai da Muka Gama,Mun hana Baba Kulu aiki munce ta zauna ta huta abinta sai kallon abin mamaki take yi tace a ranta kamar karuwai ne fa,a ranta ta bawa kanta amsa da cewa tabbas sune Amma ba ruwana ni Kam bari na Kama bakina.

     Sai da Muka gama komai sannan Suka ce lokacin fita aiki yayi suna da fadin aiki yau nasan aikin gefen kwalta za a tsaya Neman customer nace nayi missing street dama Ina nan yanda ake tallan local government Yana birgeni,dariya muka yi Muka fito tare Zan rakasu suka hau napep nace aci dadi lafiya Allah ya kawo manyan customers,Seraline tace Banda irin naki mu bamu bukatar aure, ni nace muku aure zany?da alama yanda guy nan ya rike miki wuta ai aurenki zaiyi,baki na tabe na furta a baya farko farko na so aure amma yanzu Kam bana bukata bana son aure ni nafi son yanci inyi zaman kaina in dinga siyar da kaina shine dai dai,Seraline tace haka ake so kuji dadinki yarinya kiyi komai ba komai,nace na true talk, me Napep dai ya gaji ya fisge su Suka Yi gaba ni Kuma na koma gida, na iske Baba kulu a zaune nace Babata zo kiyi wanka ki kwanta ki huta,Baba kulu Murmushi tayi tace yar nan ni baku bari ma nayi aikin ba a matsayina na Yar aiki kuka hanani aikin kuka ce ni babarku ce na zauna na huta,ai na gode muku ‘yata,nace Hmm Baba kulu karma ki dauki kanki a Yar Aiki ki dauki kanki a Mamana kawai,Baba kulu tace na gode Yar nan Allah ya Miki albarka,Ameen na furta ta mike ta shiga dakinta sai da ta kalli dakin sosai sannan ta shiga toilet,Nima wanka nayi na kwanta dama bana Sallah yau na Fara period.

    Auren Gaji Yana ta matsowa har Saura sati Daya duk wani Abu anyi lefenta akwati hudu su a kauyen gani suke tafi kowa har yanga suke,Kaya masu kyan gaske,Amarya ta Sha gyara Aunty Amarya da Gwaggo kullum hudubarsu suke ma Amarya,yau ma da Yamma suna zaune Gwaggo tace kinji dai Gaji Muna fada Miki kina da ilimin zamani kin waye duk kauyen nan wa yayi makaranta ta gaba da sikandire sai ke da Mairo to kiyi amfani da bokonki ki nunawa kishiyar nan ke ba jahila bace,idan ta Miki karki ragawa shegiya ki taka ta,Kuma bance ki dagawa kowa kafa ba duk Wanda yace zai taka ki a Dangin miji,Aunty Amarya tace miji Kawai shi Zaki rike Kam da kissa da kisisina irin tamu ta Mata sannan ko shi yazo da rainin hankalinsu na maza karki yarda ki dora shi a tsarinki,Gaji tana ji tace ai Inshaallah ma Ina shiga za a saki uwar gidan ko tayi zaman bakin ciki,Gwaggo tace shaallahu Kuwa rubutun nan kinyi amfani da shi yanda aka saki ko? gaji tace da gudu ma ai duk abinda kuka bani ba Wasa,Aunty Amarya ta dakko sabon pillow din Amarya ta farke Kan dinki ta cusa laya a ciki ta mayar ta dinke da zare da allura tace Kinga babu me sanin akwai wani Abu ciki idan aka saka yadin gado ki cire pillow din da ya zuba Miki a gidan ki saka Masa wannan kullum ya dinga kwana akan laya, tace to,Gwaggo ta irga wake guda dari ba daya ta dakko kwai Wanda an gama rubuce jikin kwan da ayoyi ta hada tsubbunta aka dafa aka bawa Gaji ta cinye,Cikin lotion din da gaji take shafawa na gyara fata nan ma wani rubutu aka dan zuba aka cakude a cikin man,tozalin gaje na musamman ne da wani siddabaru a ciki Haka turare duk da sunan gyaran amarya ne, kafin biki sai da aka gama tsuma Gaji,Bangaren uwar gida Kuwa tunda ta tabbatar Alhaji Kabirunta Danbinni aure zai Kara itama iyayenta Suka tashi tsaye dama bata da uwa bata da uba a hannun kakarta ta girma kakarta itace ke karbo Mata magungunan  tsubbu wajen Malamai itama tana ta tsuma kanta gashi gida daya zasu zauna da Gaji,tace in Banda Kabiru ma dabba ne ni Zayyanatu  ai shike nan ayi mu gani wlh idan tazo ma Sai ta fita ta bar min gidana a shirye nake, Saura kwana uku daurin aure Zayyanatu tun kafin ayi jere ta shiga bangaren Gaji ko wanne kusurwa ta yarfa ruwan rubutu da tsintsinya ta fito ta rufe.
Bangaren su Gaji iyayenta sunyi sunyi suje suga gida tunda yace ya zubawa Gaji furniture ba sai sun siyi ko cokali ba komai akwai amma sai hanya hanya yake musu karshe ma yace shi yafi so idan an Kai Amarya a Yaba Masa da irin bajintar da yayi ya nuna musu hoton katafaren gidan a waya sai Murna suke yi yace sauran idan anje za a gani yasan sai sun gode Masa,daga Jin Haka sai hankalin su Gaji ya kwanta abinsu dama yace shi Dan Izala ne baza ayi Masa party ba albarkar aure yake nema,ranar daurin Aure 11am mutane Suka taru sosai da Dangin ango dana Amarya harda abokai aka sheda auren Fatima Usman da Alhaji Kabiru Danbinni Kan sadaki dubu talatin da biyar ko ganin Amarya baiyi ba Suka koma birni abinsu sai waya ya Mata.

    Amarya kuwa an hade cikin leshi fari da Golden ga jaka da mayafi cikin Yan school kawaye da Suka zo wata tana make up itace ta tsara Mata kwalliya da dauri ba karya Gaji tayi kyau dama kuma ta kara haske sabo da man da take shafawa me kyau,Gaji ango Yana sheda Mata an daura ta tambayi wasu Yara da Suka shigo gidan maza,ko kunya a gaban mutane dangi da kawaye tace Kai Sadakina Nawa? Yara Suka ce dubu talatin da biyar Gaji tace Kai dalla ku rufe mana baki jahilan banza bakwa zuwa makaranta ta ya zaku gane lissafi,wata tsohuwa ce ta shigo tana guda Amarya tayi goshi dubu talatin da biyar Sadaki ayiririir…wasu ma yan matan Suka shigo Sadaki talatin da biyar,kowa yazo sadaki dubu talatin da biyar, ai jikin Gaji yayi sanyi ta tsaya sororo tace naji masifa yanzu Danbinni ko waliyyai na ne Suka yanke Masa haka ai yasan na wuce ajin dubu talatin da biyar sai kace kudin kajin turawa guda biyar ko tinkiya karama ta kiwo,da ilimina da komai ubana ya kashe min kudi naje birni nayi karatu makaranta ta gaba da secondary sabo da Allah,ubana ya sakani a primary na Gama ya biya min secondary na gama bai gajiya ba ya sake Nemo min admission na shiga college na karanta Hausa English na gama aiki Kawai nake jira amma duk a dubu talatin da biyar Zan Kare,eyye Ni ba mummuna ba mashaallah dani, gani da hankali,Ina da burin bawa yarana tarbiyya wani wawan Tsaki taja ta fige daurin dankwalinta da aka mata ta zauna duk kowa sai jinta ake ana kallo,waya ta dakko a jaka ta Kira Danbinni bugu daya ya daga kafin yayi magana ta lullube shi da masifa

    Haba Danbinni a matsayinka da kudinka ka kalleni Kamar ni zaka biya Sadakina dubu talatin da biyar ko waliyyai na ne Suka yanke haka a matsayina ai ka kara yanzu dan wulakanci ma ka cike biyar din Mana su cike dubu arba’in amma Wai wani talatin da biyar mece dorin biyar din,da ilimina da komai ko yara Muka haifa kasan fa ABCD da sauransu duk Zan koya musu su Alif,ba’un,ta’un duk a dubu talatin da biyar nufinka Zan zauna na koya musu to wallahi ka shirya iya kudin daka bayar iya abinda zaka gani a gidanka,Danbinni yayi Murmushi yace ke me Kika dauki aure ne?Ashe ilimin da kike ikirari Baki da shi to an fada Miki siyen mutum ake a aure shi,Ibada ce fa Zaki yi, ke yanzu Indai har kina da tunanin akwai Dan Adam da zai iya biyan kudinki to lallai baki San me kike ba,ai ko silin gashinki Dan Adam Bai iya siyansa  a duniya bare sauran jikinki da komai ma,domin silin gashinki daya idan ya cire duk duniya babu me iya fito Miki da shi sai Allah to akwai Wanda zai iya biyan wannan kudin ke kina tunani? Tsaki ya ja tare da kashe wayarsa,Gaji tace ka gama dani Kawai tun daga nan Gaji ta daina shagali.

   Sai Yamma ana Shirin Kai Amarya Dagaci ya shigo gidan ransa a bace ya Kira Gaji ta fito daga cikin kawayenta ya irga dubu talatin da biyar cas yace Gaji gashi kudin sadakinki sai ayi hakuri,Gaji tace Wai Baba da gaske talatin da biyar idon Gaji ya ciko da kwalla,Dagaji yace Hmmm Gaji yaron nan yau ya gama kunyata mu a idon duniya ki godewa Allah ma da aka daura auren Saura kadan a fasa
Gwaggo ta dafe kirji sunja gefe suna ta kuskus Yan biki suna kallonsu kowa yasan ba abu me dadi suke tattaunawa ba

    Dagaci yace Danbinni da Suka zo da danginsa Muka yanke sadaki dubu dari mu a tunaninmu mun Masa sauki da karamci sai kuwa danginsa Suka Yi tsalle Suka dire Suka ce ai su dansu baida halin haka mamaki ya kamamu Suka ce a musu ragi,Gaji Zo ki ganmu inda kisan an jika biri a ruwa haka na koma na zaci karya ne, ke yo ba sai aka Fara ciniki ba wallahi Gwaggon Mairo inda kisan na kai Akuya kasuwa haka a bainar mutane Muka dinga cinikin yarki Gaji,Muka sakko dubu tamanin Suka ce Albarka,Muka dawo dubu sittin Suka ce Albarka,dubu hamsim, arba’in duk Albarka a talatin dinma sai da Liman yasa baki yace wallah idan basu Kara ba bazai daura aure ba Taya zasu Zo Masa da zancen radio da kullum ake fadar farashin Sadaki Suka ce Basu da ciko da kyar aka samu wani a wajen cikin abokai ya cika musu dubu biyar sannan aka daura aure,duk garin nan labarin mu ake Yi yanzu Maganar muce take trending inji yan media Suka ce trending, Dagaci ya kalli Gaji yace da alama akwai karya a lamarin Danbinni duk yanda akayi Danbinni ko airport bai sani ba shi da kanshi ya sawa Kansa Alhaji Danbinni makaryacin banza,Dagaci ya sake kurawa Gaji Ido dake Hawaye yace Gaji ta Yan kudu Suka ce you are in Soup,gaji ba Miya Kawai ba Hot Soup me zafin bala’i sai dai Allah ya tsare yanzu za a kaiki mu Kuma Muna nan Muna jiran tsammani muji me zai faru a can gidan Danbinni,Gwaggo tace na shiga Uku ni Gwaggo Anya ba mafarki nake ba,Dagaci yace bude idonki tar yamma ce karfe Uku da minti goma biki akeyi na Yar mu Gaji Muna cikin tararrabi,Gwaggo tace ba Danbinni ba ko Dan Madina ne Gaji in kinji wuya ki dawo gidan ubanki karki zauna bance kiyi hakuri ba karki sake kiyi hakuri a zaman aure a wajena ba hakuri kina Jin ba dadi ki gudo,Dagaci yace af da kaina zanje na dakko ‘yata.

    Gaji tunda ta koma wajen kawaye take faman rusa kuka an zaci kukan rabuwa da gidane basu San abinda Gaji taji ba shike damunta,Mairo ma taji labari Gwaggo ta fada mata itama sai da tayi hawaye,Aunty Amarya Kamar yaranta sabo da su zamansu da Gwaggo lafiya sukeyi basa kishi basa fada sai bacin rana matsalar kowa ta kowa ce Kamar Yan Uwa sabo da tsiyarsu tazo daya halinsu yazo daya rashin Imaninsu daya,Yamma nayi motoci biyu kanana kacal Danbinni ya turo Daya ta Amarya da kawayenta Daya ta dattijai Amarya tayi wanka ta canja wani material me kyau ta Sha kyau aka tafi kaita dakin miji Nasihar Gwaggo da Gaji Kawai idan taji wuya ta gudo gida,Shima Dagaci yace ni da kaina zanzo na taho da abata,Aunty Amarya kuwa tana kusa da Gaji itace zata kaita daki da wasu dattijai sai Mairo da wasu kawaye su hudu.

     Mu Kuwa washe gari da asuba bayan munyi Sallah bacci Muka koma sai 9 karar wayata ta tashe ni Ina dubawa Naga Saurayina wato Nawwar dagawa nayi cikin muryar bacci sallama nayi masa ya amsa cikin muryarsa me dadin saurare sannan yace hope dai kinyi Sallah,Murmushi nayi ba kunya ba komai nace a’a wallahi diga nake a bule nake yau Jini nake ka gane,na rasa dalili sometimes Kawai sai naji magana fit ta fito daga bani ko bana so na fada sai na fada Ina so na dinga Jin kunya amma na rasa dalili na kasa,Ina so ko Yaya na nuna cewar ni ta gari ce amma abin yaki, yace naji to ko kunya bakya ji,nace ai magana ce ta gaskiya kaga ma yanzu…katse ni yayi yace  anjima kadan Zan kawo muku breakfast,nace to kayi sauri yunwa nake ji, wayarsa ya datse,wanka na shiga nayi da brush na fito na shirya cikin wata Yar Riga Yar kanti har kasa wata me hannun vest daga sama Tasha roba ta same kasa ta dan bude kadan,nayi kyau shape dina ya fito sosai,Baba Kulu na samu ta fito ta dakko tsintsiya zata fara shara,da sauri na karbi tsintsiyar nace haba Baba ga yarki yaushe zaki shara Ina nan ki zauna ki huta zanyi komai,Baba kulu baki ta saki tace Yar nan Nifa Yar aiki ce,nace ba dai tare dani ba akwai abinda dai zan iya baki ki tayani amma banda me wahala,tace ayi haka Kuwa nace gashi ma anyi ki zauna zai kawo Mana abinci tace to Yar Nan Allah ya Miki Albarka , ina ta share Palo naji knoking tare da turo kofar gaba daya wani kamshi na musamman ya daki hancinmu,dagowa nayi na kalli bakin kofar sai da gaba na ya Fadi ganinsa da wani irin kyau na daban ka rantse balarabe ne Kuma a haka ba wani gayu yayi ba 3qtr ne a jikinsa da rigarsa me gajeren Hannu rigar tana da jerin botin a gaba da rigar da wandon irinsu daya irin kyan da Suka Masa ya baci sai kallonsa nayi baki ya turo gaba nayi sauri na dawo hayyacina sannan na karasa gabansa na rada Masa a kunne irin wannan kyau sai ka jawo na maka fyade, Ina kwana na furta ka tashi lafiya ya amsa da lafiya sannan Suka gaisa da Baba Kulu ledojin na karba a hannunsa kaina ba dankwali na gyara gashina me tsayi da kyau, nace ka zauna mana,kujera ya samu ya zauna Baba kulu na bawa nata ledar tana karba tayi godiya ta Shige dakinta ni Kuma na zauna a kujera Muna facing juna,na shiga kitchen na barshi Yana latsa waya plate na wanko har biyu da cokula  na fito,yace sai dai kuyi manage fa ba tea, wani chips ne da Naman kaza sai wata Kalar fried rice da pepper meat,sai fresh Madara da ruwa da lemo juice,glass cups na kwaso mana na juye abincin a plate biyu sabo da Leda biyu ne ya bani Banda na Baba kulu,Fresh milk din na zuba Masa a glass cup tare da Mika masa Ina cewa gashi,kallona yayi kadan yace kin iya abin masu aure why baza ki samu Miji kiyi aure ba,Fuska na bata nace ni dai bana so, shi dai shanyewa yayi na Mika Masa plate din chips and chicken ya karba Yana ci da fork da wuka ni kuwa Hannu na wanko na zauna Ina cin nawa,Ina ci Ina Santi nace Karuwanci wato duniya ne na kurbi ruwan juice nace badan Karuwanci ba Ina Zan tsinci kaina a nan yanzu kuwa dalili yasa sai Dadi nake ji wayyo Dadi zai sa nayi kuka ai duk Wanda yace nayi aure na bar karuwanci to ba karamin makiyi na bane,magana kike fada min ni makiyinki ne ko? Lemon dana kurba na hadiye da sauri nace haba ai duk duniya bani da kamarka kasan me na tsura Masa Ido nace I love you sha’awarka nake yi ka kara lalatani don Allah,baki ya saki yana kallo na a ransa yace wannan kuwa zata shiryu Anya, Fuska ya murtuke sosai tare da ajiye min abinci ya mike da sauri na rungume kafafunsa da hannuna biyu tare da furta kayi hakuri dan Allah bazan sake ba sai kana min Uzuri ni Jahila ce ka sani ba boko kasan rashin zaman aji, kafafunsa ya kwace zai fita nayi sauri na mike tsaye tare da Shan gabansa nace kayi hakuri please nima Watarana mamakin kaina nake yi ban San Sanda nake furta irin wannan maganganun ba Ina so na daina na kasa,wallahi da ba haka nake ba idan kaga Saliha Shuru Shuru to nice,Indai kina so in hakura sai kin yarda Za kiyi aure,Nan take idona ya ciko da kwalla nace wlh ni bana son aure idan ana min zancensa ma ji nake zuciyata Kamar zata fito,Salati yayi a ransa a fili yace sunnar kike adawa da ita lallai bariki ta Miki illa ya taka zai fita,da sauri na riko hannunsa Yana juyowa ya kasheni da mari yana huci idonsa ya canja Kamar wani zaki,tsoronsa ya kamani na dafe kumatuna na tsaya na zaci akan auren ya mareni sai na fada kirjinsa na fashe da kuka wani wawan hankadarwa ya min Kamar me Aljanu ya fisgo Wayar Tv ya Fara zuba min Yana masifa yace sa’anki ne ni Ina daga Miki kafa bakya ji ko muharraminki ne ni ko an fada Miki ni Dan kwalta ne irinki, ihu nake yi na zube a kasa Ina bashi hakuri,Baba kulu tana ji tace lallai ba shakka zaman bariki suke in ba Haka ba wacece Namiji na dukanta tana bashi hakuri haka,Fitowa tayi ta rike wire din dake hannunsa tana cewa haba Alhaji kayi hakuri Mana,shi kuwa sai kokarin fisge Wayar yake yi yace kyaleta bata Sanni bane dan Ina kyaleta,da yatsa ya nuna Ni yace duk ranar da Kika sake min Maganar banza wallahi sai kin gane kurenki Kuma Allah yasa na dawo gidan naji kin fita wani wajen nonsense ya furta tare da dungure min kai ya zuba min rankwashi kwasss….Ina kuka ban San Sanda nayi dariya ba yanda ya dungure min kai ne ya bani dariya,ganin Ina dariya ba karamin daure Masa Kai yayi ba yace Yar nan ba kalau take ba Rukiyya Zan kaita wata rana, Tsaki ya ja ya juya ya fice Ina cewa abincinka fa? Bai kulani ba na mike da sauri na Bude kofa har ya kai jikin mota nace Zan turo maka list din abinda muke bukata na kayan abinci,ko kallona baiyi ba  ya shiga motarsa benz baka ya bar Estate din.

     Sabreen Kuwa ganin bata ganni ba tasan na bar Mata gida sai Murna har da Kiran kawarta Jamcy ta fada Mata suna murna Jamcy tace Saura ke sai na hada Miki masifa a fili kuwa tace Ina tayaki murna kawata,Haka Sabreen ta sanarwa Mamanta na bar gidan Mama tace shege aka ce baya ji ai duk wani Namiji dole yaji tsoron matarsa yanzu dai ki rage shaye shayen nan dan Allah ki lallaba ki samu ciki kinji Sabreen Mama tayi Maganar da lallashi Sabreen tace an gama Mama.
Baffa ne ya samu Mamin Nawwar yake balbala Mata masifa ta ya Auta Nawaf zaizo na uku a ajinsu,tace yaro a ajinsu yazo na uku ai yayi kokari

  Tsawa ya Mata ke dalla rufe min baki ke dai baki iya tarbiyya ba bakya nuna musu Abu yanda ya kamata kin jawo Ina asarar kudin tara ni ga me kudin banza, duk yaranki basu da kokari dakikai ne,Amma ai yaran amaryarka masu kokari ne tunda naga Haidar yazo na 10 amma ita nata kokari Suka Yi Nawa yazo na uku kazo kana min fada ita ka kyaleta har murna kake yi ni sabo da baka so na ka tsaneni,in Banda ma ka rainani da nuna banbanci mene Nawa a position na yaro ita Ummyn Haidar bata laifi a wajenka kullum nice sabo da yanzu na girma na tsufa ga matashiya wallahi kaji tsoron Allah hakkina sai ya kamaka kwanana ma da kake tauye min ka bata sai dai na dafa na Kai maka itace da kwanan Miji Allah sai ya saka min inyi girki wata katuwa da kwana da miji bazan yafe ba,Mari ya zabgawa Mami dai dai Sanda Nawwar ya shigo Marin nan me karfi sai da fuskar Mami ta tasa yatsunsa reras a kumatunta abinka da fara,Ido Nawwar ya runtse hannunsa ya nutsa a cikin sumarsa me yawa da santsi ya hangitsa,nan take idonsa ya canja kamanninsa Suka sauya ransa ya Matukar baci amma ba abinda ya Isa yayi dagowa yayi yace Baffa….ba ruwanka muryar Mami ta ratsa kunnuwansa,bai hakura ba yace amma…shut up ta furta cikin karaji Shuru yayi,Baffa Yana muzurai Yana wani cin magani ya bige babbar rigarsa tare da furta da kayi magana Mana, uwarku ko ba mahaukaciyar bace dabba ce bata da hankali Kuma Watarana idan bata taka a Sannu ba sai na tsinke ragowar igiyar rubbish ya sake bige babbar riga fat ya fice a fusashe,domin shi ba sai Mami taje bangarensa ba da Kansa yake zuwa yaci mutuncinta ya Kara gaba,Yana fita Ummyn Haidar ta cakare matar so kenan ta sa Kaya na gagara ta kwama glass dinta tayi kyau itama kyakyawa ce amma bata Kama kafar Mami ba a kyau,Baffa Murmushi ya saki ya karasa inda take tare da furta sorry my love I keep you waiting,tace ba komai ka dinga dan sassautawa Mamin Sultana kasanta ballagaza ce duk da bata da nutsuwa ka dinga binta a hankali har Sanda zaku rabu lafiya,yace ai ba karamin hakuri nake da ita ba,Hmm na sanka sarkin hakuri ne ka Kara akan Wanda kake da,yace Inshaallah ya rike hannunta tare da furta muje ki rakani meeting din nan ni ake jira ya rike hannunta Suka shiga rantsatsiyar motarsa driver ya ja suna baya.

    Bangaren Mami Kuwa Samanta ta haura Kawai ta Shige bedroom dinta,Nawwar ya bi bayanta Idonsa yayi ja da gani kasan Yana cikin tashin hankali,Mami ya iske a tsaye ta juya baya hawaye Yana sintiri a kumatunta bakin cikinta yanda yake zaginta a gaban yayanta, Nawwar gabanta ya zagayo ya tsaya ya rungumeta kokari tayi irin na iyaye ta danne kukanta ta maida shi ta shanye abinta hawayen dake kumatunta yasa hannu ya goge Mata tas ta kalle shi Suka hada Ido tayi murmushin karfin hali,a hankali ya furta kiyi hakuri Mami ko ki muje ki koma gidana ki huta tare da su Sultana,ko kin tafi Kinga yace ko Ina Zaki ba ruwansa karki sake tambayarsa unguwa baki da amfani a wajensa yace idan ma sama Zaki tashi ki tashi,Ki taho mu koma ko Zaki samu sauki,Mami ta kalle shi tace da wata me hankali ka aura sai na koma amma Sabreen ce Nawwar sai ta karasani,yace to ga sauran gidajen nawa Mana ciki ki zabi Wanda yafi Miki,Mami tace na zabi gidan nan na can nesa inda ba mutane sosai is better amma kasan bazai bari na daukar Masa Yara ba ko Daya Kuma idan na barsu za a gallaza musu ne gwara na zauna kusa da Yara na sadaukar da farin cikina ga yarana duk tsiya gwara na bawa yarana tarbiyya da kaina idan na tafi ma hankalina Yana kansu,to idan sakin ki yayi fa sannan da yaran da su ya auro ki ba sai a bar Masa abinsa ba,no Nawwar uwa daban take ba irinku uba bane kayi hakuri Kawai Zan dai iya zuwa gidanka nayi sati biyu idan na huta sai na dawo,Yace Alright wancan gidan dai na wajen gari inda ba mutane? Mami ta daga Kai inda ba Wanda zai dameni,yace an gama gobe zan kaiki bari a zuba Masa Kaya wani part dinma ba a Gama ba ginawa akeyi na
sani Dan Albarka Allah ya muku Albarka,yace su Hamra suna school Kai Kawai Mami ta daga masa yace to yaje ya kawo Mata ruwa me sanyi yace Dan Sha ta karba ta sha sannan ya fita ya bar gidan yasan tana bukatar a barta ita daya, hankalinsa bai kwanta ba sai da ya Kira company na wata masu tsara gida a zuba furniture da komai na buka ko cokali baza ka nema ba,suka je Suka ga gida ya Fadi yanda yake son komai ya biya kudi washe gari da wuri aka hada komai da yace yanda ya dace na Yan gayu,abinci ma Mami baza tayi ba shi zaina kawo Mata Kawai hutawa zata yi ga gidan daf da bakin ruwa.

    Tunda ya dakeni ya tafi bai dawo gidan ba sai kayan abinci Naga an kawo a mota an shigar da komai store na shirya kitchen Muna zaman mu da Baba kulu tana bani hakuri akan dukan da na Sha duk da bata San me nayi Masa ba,ranar girkinmu mukayi ban ganshi ba sai washe gari da rana 2pm Ina dakina a kwance Ina sauraron audio na novel Wanda S Zaria Tv ta karanta a YouTube channel a wayata sabo da na gaji da kallo,Sallamarsa naji a hankali cikin muryarsa me dadi,Fitowa nayi sanye nake cikin doguwar Riga kasancewar kaf kayana na gidan da ya Fara kaini ya Aiko min da su,Fitowa nayi a nutse ya Saba ganin Ina gaishe shi yau yaga na zauna a kujera nayi mirsisi yace baki iya gaisuwa ba,Ina yini nace Kawai na shiga harkata shi sai yanzu ma ya tuna ya zaneni,ya sake furta haka akeyi,banyi musu ba na durkusa nace ka yini lafiya tsaki ya ja ya zauna duk na ganshi wani iri ba yanda na Saba ganinsa ba,nace lafiya? ya furta me Kika gani

    Nace na ganka kamar kana cikin damuwa ne,shi Kam yanda nake gane damuwarsa Yana birgeshi Kuma in tambaya,a fili yace ta ya Kika San a damuwa nake,ai ni Ina ganinka nasan idan ma kana good mood ko baka ciki,kitchen na shiga na tsiyayo Masa kunun ayar dana hada me shegen Dadi yayi sanyi na Mika Masa ya karba ba tare da ya kalleni ba,kayan jikinsa nake kallo kana shadda gani tsadar shaddar ta Isa wata fara, kafafu ya harde Yana karkada kafa Daya irin na masu izza da ji da kudi,tashi nayi na kawo Masa meat pie na nama da nayi yaci Kuwa sosai sabo da yunwa yake ji,nace ayi maka girki mun cinye Wanda na dafa,yace girki Zaki yiwa Mami…kafin ya rufe baki na mike tsaye Zan shiga kitchen yace to ki tsaya Mana kiji me za a dafa tukun da time din,nace me Zan dafa to Yi sauri ka fada min Mami guda ai dole kaga na mike, Murmushi yayi da bai shirya ba yace tuwon shinkafa danya miyar kubewa danya sai ki hada Mata wannan lemon da Kika bani na Sha yanzu nace to 5pm zanzo na dauka,sai tea da kayan kamshi nace ka dauka anyi angama ma, tashi yayi zai fita nace zanje siyo kubewa da kayan Miya bamu da ita yace okay ya fice,ba ko mayafi hulace Kawai a kaina sai Yar doguwar rigata me garen Hannu yellow a haka naje har kasuwa na dawo Ina Hanya Ina tafiya na kusa gida har Ina cewa Allah yasa bai ganni ba ya tafi,Kawai naji mota a bayana ana bina a hankali Ina juyawa naganshi da sauri yayi parking ya bude mota ya fito a fusace na kwashe da gudu dauke da ledata Ina gudu na fada gida na rufe gate din har da saka sakata,Tsaki ya ja ya shiga mota ya koma abinsa Yana huci har kasuwa konmayafi baby Haba.

     Amarya Gaji Kuwa ana mota an shigo city cikin Kano tana baza Ido taga ya gidan, ta ga an wuce cikin unguwanni masu kyau sai da a kazo unguwa wata marar kyau ko Ina kwata sai doyi da wari gidajen unguwar duk talakawa ne sai me dama dama gaba Daya rubabbun gidaje ne,Gaji tuni gumi ya lullubeta Gaban wata katuwar kwata aka yi parking bakin wani gida me dama dama ko sabon paint babu Wanda zai nuna alamar gidan Amarya ne,Gaji kasa hakuri tayi tace wai ko karamin Gate babu? Jama’a ku tayani gani ko idona ne,Aunty Amarya Fuska murtuke tace da driver yaro nan ne Kuwa? Da masifa yace idan ba nan bane Zan kawo ku ne dan Allah ku fita Ina da wajen zuwa Kuma kafin na dawo ku tabbatar Kun Gama idan ba haka ba wallahi duk wacce bata fito ba sai dai ta kwana a gidan Amarya,Gaji Fitowa akayi da ita haka kowa jiki yayi sanyi amma Banda motar dattijai Kawai guda sukeyi suna murna su Kam,motoci Suka juya Suka barsu a kofar gida,

  Aunty Amarya ce ta dakawa tsofaffi tsawa tace Kai dan Allah Kun damemu da guda,yo ayi Shuru Kamar gidan mutuwa ai Amarya sai da guda ayiririri Suka ci gaba da yi sai da Gaji ta dora hannaye a ka tare da kurma uban ihu a unguwar kowa yayi tsit Dangin Uwar gida Zayyanatu Suka fito da kawayenta makwafta ma Suka yo waje ana kallo,Yara Yan Mata har da maza sai da Suka zo sabo da ihun da Gaji take kurmawa hannaye ta daga sama sosai tace jama’a an munafunce mu anci amanar mu an yaudare mu an nuna Mana kudi wayyoooo….ta sake Dora hannaye a Kai Aunty Amarya ta rufewa Gaji baki ta jata sum sum tace ku muje ciki aka tafi,wata tsohuwa tace a tsaya Amarya tayi addua…kafin ta rufe baki Gaji tace baza ayi ba Ina wani Alkhairi anan,bana son zaman Lafiya Allah ya ruguza wannan aure Inshaallah bazan Yi sati biyu ba za a sake ni,Dangin Uwargida Suka saki shewa kwadayi mabudin wahala Yan Kauye anji kamshin birni,Aunty Amarya tace doyi dai wai ku nan har birni ne unguwa duk doyi talauci ya dinka Muku Riga da wando Ina kamshi a nan unguwa sai kace masai,Kawayen Zayyanatu Suka saki sowa, Zayyanatu ana daki Suka tafa da kawaye tace wlh sai ta bar gidan nan ko na haukatata,dama Zayyanatu irin masu bakin kishin nan ne Babu abinda baza su iya ba akan kishi.

     Wata dattijuwa tace Ina Uwargida ta fito ga Amana mun kawo Mata, Zayyanatu ba mutunci ko Kara babu ta leko sabo da haukar kishi ya zautata tace ni Allah ya gani ma ko wacce irin Amana aka bani sai na ci,karku ce ban fada muku ba wallahi sai naci amanarta,Amanarku sai na kafa Mata hakora na yageta yo ni ai duk unguwar nan ku tambaya kuji bani da Amana,Kinyi Asara Kuwa cewar Aunty Amarya,Zayyanatu tace uwarki ce tayi asara tazo har Gaban Aunty Amarya taci kwalarta ta haukace kishi ya rufe Mata Ido,Aunty Amarya ma Yar ta kife ce ta kwashe Zayyanatu da Mari har biyu nan take Dangin Amarya dana uwar gida Suka yamutse ko wacce ta cafki daya Suka Fara bata Kashi, Amarya Gaji ta jefar da mayafi tare da ture Aunty Amarya tace bani ita itace dai dai dani kishiyita ce Gaji ta fyallar da mayafin amarci kasa tayi tafiyar ruwa da Uwargida zayyantu abinka da girman Kauye ga Gaji da mugun karfi taci kwalar Zayyantu ta makureta da bango  sosai tasa kirijinta ta daki kirjin Zayyanatu tace kishi hauka ne Zan gwada miki na fiki hauka,gaba daya ganin Abin na Zayyanatu da Gaji yayi yawa kowa ya tsaya akayi cirko cirko ana kallonsu,Zayyanatu ta samu ta kifawa Gaji mari kafin ta dauke hannunta Gaji ta bata mari biyu ta shaketa a jikin bango tana wani shidewa sabo da bala’i idon Gaji har wani kakkafewa yakeyi Kamar me Aljanu ta juya ta hango kwalabar lemo 7up ta wawuro ta fasa a kasa tace me tsoron ta mutu shike rai Zan iya zuwa prison a kanki Dan kut…..Zayyantu taji wuta itama turmin daka ta dauka ta yo Kan gaji ta jefo Mata sai da ya samu Gaji a goshi kadan,goshin Gaji ya fashe, suna haka sai ga Dangin ango da ganinsu kaga talakawa futuk wata a ciki tace me Zan gani haka na shiga Uku kashe kanku zakuyi akan kishi,wannan tozarci da me yayi Kama wannan abin kunya da Danbinni ya jawo Mana da me yayi kama,Gaji huci Kawai take yi sai lokacin ta saki Zayyantu dake shake a hannunta,Zayya ta Fara shakar iska ta fashe da kukan munafunci,Wanda suke wajen abin ya faru sune Suka ce uwar gida itace da Laifi itace bata ja mutuncinta ba ai ko ba komai ko zaginta Suka Yi sai tayi hakuri ai ranar farko ce Amma har da marar musu dattijuwa Kuma basu kulata ba ta fito,

   Wata a Dangin ango tace kinyi asara Zayya tunda akace za a Miki kishiya Kika haukace a kanki aka Fara kishiya,duk unguwa gulmarki akeyi akan Namiji irin Danbinni talaka uban me kike tsinta a wajensa sai ma wahala mahaukaciyar shashasha,Gaji tace a fada mata wallahi da nasan haka yake ma bazan aure shi ba,ta sani da saninta Ni bala’i ce da kanta Nice jarabar duniya maganin duk wani Dan Iska ko wa ya ja da Gaji sai yayi kasa,Gaji Kamar Yar daba har da cije baki tana nuna kanta tare da sake furtawa a fada mata bada Wasa nazo ba na shigo da kafar haggu tunda tace bala’i za ayi wallah ta taro bantan bala’i ta ta taro alkaba’i icen kabari ce ni,yanzu ba zaman Danbinni zanyi ba Zaman zayya zanyi mu zuba ni da ke, wallahi tunda Kika mari uwata sai na mari taki uwar Allah ya kawota gidan nan dan me dirkawa uwarki ciki,Dan me dafa miki abinci kina yarinya,Dan wacce take Miki tsarki kina karama sai na ci uban da ya haifi babarki,shegiya me idon fatalwa sai kin San wace Gaji,Zayya taga ruwan bala’i tsoro ne ya kamata sai kuka,Gaji tace baki Fara kuka ba bari tukunna naci burar mijinki tukun sai naji madarar mijinki ta ratsani Zaki San wace ni,Oh yau na shiga Uku  ni Binta Danbinni ya hadawa Kansa bala’i,Aunty Amarya tace yawwa ki rama min Marina akan uwarta,Gaji tace for sure tana zaga gidan tana kallon kowa dai dai taga buta tayi ball da ita ta daki bango ruwa  tul tul buta ta fashe,Da kyar aka kwantar da hankalin Gaji sabo da Gaji su ko me zasu Yi da sa hannun iyayensu suke yi Kuma ba a musu fada ko me Suka Yi dai dai ne,Rabi Yar tsuntuwa ce kawai me hankali Shuru Shuru me ladabi da biyayya saliha yanzu Kam basu sani ba asirin Dagaci da ya Mata ba ya sa taci uwarsu a hauka da rashin kunya da fitsara Kuma ta kulle a ranta zata Zo har gidan Dagaci ta nuna masa.

    Amarya aka shigar dakinta guda daya tal ita kuma uwar gida nata biyu aka bar Mata sabo da masifarta gata da Yara biyu , gado me kyau da sip da mudubi Yan yayi ya sakawa gaji dakunansu da tiles har tsakar gida broken tiles ne,toilet ma da tiles, gefe daya kujera doguwa me kyau kayan kitchen ma a gefe sabo da munafuncin Dabinni ko Zayyanatu ta zaci Yan uwan Gaji ne Suka Zo Suka jera kayan bata San wasu matan daban ya samo Suka jera,kayan kitchen din da Gaji ta taho da su su aka ajiye gefe,zuciyar Gaji Kamar ta buga sabo da abinda tazo ta samu a gidan Danbinni karyar da ya Mata baza ta irgu ba,ji take Yi Kamar ta mutu sabo da takaici irin wannan Kuma akwai ciwo gwara mutum ya fadi gaskiya idan za a soshi a soshi dan Allah duk da cewa shima badan Allah ya auri Gaji ba temporary ya aureta ya dandanata ya saketa sabo da Yana mugun sha’awarta shi ba kudi ba amma sai Neman matan masifa,bai sani ba ya zaci Gaji kanwan lasa ce bai ma San irin Shirin da Suka yi ba ta tsumu matuka.

 

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               46-50

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Mmn Abida
Jummai Hudu
Mrs Aleeyu
Saudatu Rabiu
~Meenal
Ummulkhair
Maman Ra’is
Tigrotta
~Aunty
Mukhtar
0706571
~Fatimalawan600
Ummu Khalil
Humy

JINJINA
MRS MUKHTAR
MSZEETOWN

 

       Abincin da yace na dafawa Mami shi na zauna na tsara harda abinda bai sani ba sai da na Mata dambun naman kaza,nayi Mata snacks kala biyu komai a muzubi na musamman na zuba,na shirya komai da taimakon Baba kulu,sai da Muka ci namu Muka koshi sannan nayi wanka na shirya cikin doguwar Riga ya zanyi ya takura min da saka Kaya na mutunci,Ina Fitowa na dauki remote ya shigo da sallama na amsa sai ga Mami ashe tare suke,Murmushi nayi na Fara dariya kadan nace laaa Sannu da Zuwa Maminmu, tana shigo nace zauna dan Allah Zama tayi tana Dariya tare da furta Sannu Yan mata durkusawa nayi na gaisheta da ladabi ta amsa Nawwar ya saci kallo na,Baba kulu tana daki na kwala Mata Kira nace Baba fito ga Mami tazo Mamin Ogana Mamin saurayina tazo fito,Mami tayi dariya sosai tace ohh wannan yarinya,Baba kulu ta fito sun San juna Mami tana ganinta a gidan Khaleel Suka gaisa, nace bari a kawo ruwa,tace tafiya ma zanyi nace dama kwana Kika yi a nan Allah Mamin mu

    Tace a’a kamar kin san Hutu zanje wani gidansa a bakin ruwa,nayi kneel down da sauri Kamar ana bani punishment nace laaaa kamar na sani dan Allah ki huta a nan idan ba kya son hayaniya zanyi shuru na nuna sama da yatsa na nace Allah harda dangwalar yawu na daga yatsaya nace Allah,Mami tayi dariya,nace zan Miki girki da komai kullum zaki ji Dadi Mami kin ganni Ina da hankali,kin na nuna kaina nace ni macece me kirki Ina da kirki,Gani da Fara’a,Kuma na iya kula da mutum,yarinya me hankali Irina ga kirki Allah Mami,dariya ta Kama Nawwar yanda na gigice harda hada gumi nake faman yabon kaina nace,Mami dariya take nace Kuma gani da Kamala da nutsuwa Allah ni nutsatsiya ce Zan sake nutsuwa ko Saurayina ai shima ya sani shi yasa kika ga ya nace min Mami yaki barina na tafi ya manne min Kamar chewgum Ina korarsa yana likewa to yaga nutsuwa ga kirki,in yazo Mami abinci in ta ce Masa sai yaci nace ci ci Mana Ina lallabashi ruwa wannan sai na zuba masa sai ya min shagwaba yake sha,Mami sai dariya take Sha Ina tonawa danta asiri,Nawwar ya riko hannun Mami yace tashi mu tafi dare na yi,Hannunsa Mami ta bige karka dameni,amma Nawwar sai ya dinga hararata ya tsare gida dole nayi shuru,a haka Mami ta Mana Sallama da ni da Nawwar Muka kwashe abinci muka zuba a mota Suka tafi na dawo cikin gida
Haka Nawwar yake sintiri a hanya kullum Yana kashe Mana kudi shine gidan Sabreen shine gidana yazo ya dauki abinci ya kaiwa Mami komai nike dafawa Mami yazo ya Kai mata haka yana kaita yawon shakatawa dan taji sanyi a ranta,su Sultana ta barsu suna gida sun dameta da ta dawo gida amma tace musu zata dawo ne su Kara hakuri shi Baffa ma bai San bata nan ba sabo da bai damu da ita ba.

     Yau Ina wanka ya shigo sai da nayi wankan tsarki nayi Sallah sannan na zauna shiryawa ban San ma yazo ba suna Palo tare da Baba kulu suna hira sama sama har na fito sanye cikin wasu Pakistan riga da wandon wando ka rantse skert ne wandon wani fari kal rigar Kuma dark green taji ado ta hadu a cikin kayan da ya siya min ne mayafin a kaina na daura  na fito tare da neman kujera na zauna sannan nace Ina yini ka yini lafiya,ya Mami? yace tana lafiya nace mashaallah daga haka ban sake magana ba abinda bai saba gani a wajena ba Kuma ba haka ya saba ganina ba ya sanni da surutu,yace lafiya? Nace me ka gani? bana son zancen banza mene ne ke faruwa,dan lips dina na turo tare da furta gidanmu na tuna nayi missing dinsu kasan inda ka taso dole ya zauna a ranka, ni Kuwa a raina so nake yace naje can kauyenmu ta nan zan samu naci uban Dagaci zuga guda zamuyi, Tsaki ya ja tare da furta mutumin da yaso yayi raping naki sune abin tunani, kasan idan ka taso ko me ake maka dole kaji a jikinka,Mikewa yayi yace baki da aikin yi ne komai Kuna da shi ko?nace ae yace to dama tafiya zanyi gabana nane ya Fadi nace zuwa ina? zaka Dade? Baba kulu dama tuni ta koma kitchen wajen girkin da take mana,yace zanyi kamar 3weeks,Ina ne? Umrah zance,wow na furta ayi Mana Addua Murmushi yayi yace wa zai kulaki tunda baza ki shiryu ba Mamina kadai Zan yiwa,nace please ka taimakawa yar tsuntuwa Yar lelenka ce fa ni,harara ya watsa min,nace abincin Mamin fa? Ai ta koma gida Yara sun dameta ta koma sati Daya fa Kawai tayi ae Mana ai ta huta haka,mikewa nayi tsaye nace muje na rakaka kaje Dani airport yace no da matata zanje,dariya ta kamani nace sai kace matar kirki Yarinyar da kirji kamar Allo, Murmushi yayi yace Sabreen ce Yarinyar ki? Shekarun mu daya da ita to mate dina ce,dariya ta kamani nace kace tsohuwar guzuma aka aura maka yanzu nasan local government din ma yayi yaushi ya yamutse,bana son rashin mutunci ya furta yana bata rai ,okay naji idan zaka dawo zanje airport dakkoka na iya mota,  dan Allah yace okay,Na tsaya a gabansa Ina kallonsa na furta I will miss you na rungume shi,kin manta dukan da Kika Sha rannan ko,da sauri na ja baya Ina tambaya yau zaka tafi kenan yace ae Inshaallah zuwa dare, Kai na jinjina,Ni Kuwa nace za a sha zam zam a cika ciki shi yasa masu kudi kuke Mana wayo ku dankara laifi ku tafi Saudiya ku nemi yafiyar Allah, juyawa kawai yayi ya fice abinsa.

    Amarya Gaji ba a dade ba aka kwashe duk Wanda suka kawo Amarya aka tafi dasu gida,ya rage daga Uwargida da yaranta biyu sai Gaji a gidan,Ango bai shigo da wuri ba har aka maida Yan kawo Amarya gida suka yiwa Amarya waya sunje lafiya godiya ta musu,tana zaune babu ma ko mayafin a jikinta Zayya ta fado dakin ta Fara durawa Gaji ashar tace masu tare miki sun tafi dagani sai ke yau idan kin Isa kice Tak,Gaji mikewa tayi tsaye tace ba Tak ba nace Taka Takai, ta ci kwalar Gaji tana cewa dan uwarki sai kin bar min gida, Gaji tace Ubanki Sa’idu Dan Sa’ido,dama Gaji a munafuncin mutane sunji Sunan Baban Zayya Sa’idu Dan Sa’ido.. Ango ne ya shigo dauke da ledoji biyu,yace mene haka au har yanzu baki hakura ba Zayya duk irin tozartani da Kika yi bai isheki  ba dalla sakar min Amarya, Zayyanatu sakin Gaji tayi tare da fashewa da kuka tace Danbinni Kaine ka fada musu sunan ubana har na banza Allah ya Isa

    Danbinni bai ce komai ba ya mika mata ledar Naman Daya,ta fisge tana hararasa tace muga Dayar ko da banbanci nasan halin maza da munafunci ta bubbude ledar,Danbinni ransa ya baci yace Wai ke Zayya mene ne haka wacce irin rayuwa ce wannan kishi hauka ne Tsaki ya ja tare da fisge ledarsa yace bar dakin nan kafin Raina ya baci ai naji duk abinda Kika Yi ke da kawayenki da danginki daga kawo amarya ai kya bari ko me zakiyi tukun a kwana biyu ,zata fita yace tsaya zai Fara Nasiha akan su zauna lafiya kowa ta girmama kowa ai Zayya tsaki ta ja tace bazan ji ba karka ka bata bakinka wallahi Danbinni babu zaman lafiya ni da ita,Gaji tana Zaune gefen bed bata ce komai ba da katon tabo a goshi yayi wani dau har Zayya ta gama haukarta ta fice abinta,Gaji ta kalli Ango tace Alhaji Kabiru….shi kanshi wata muguwar kunya ce ta Kama shi yayi nadamar karyar da yayi musu yaji kunya matuka musamman da yaga Gaji ta Zauna a haka basu juya da abar su ba,duk munin halin mutum dole Yana da na kirki,nadama ta rufe shi,Gaji murmushin takaicin tayi hawaye ya zubo Mata tace suturar aro,motar aro,gidan da ka taba kaini dan ka lalatani shima na aro,gidan da ka nuna Mana a waya kace shine nawa shima na aro ,kudin da ka dinga kashe mana dan abinda ka tara ne ko shima na aro ne? Dan Allah Danbinni baka ji kunya ba,menene na karyar idan Allah yayi Zan aureka dole sai na aureka a duk yanda kake,Gaji ita bata San Danbinni auren sha’awa yayi da ita in ya gama biyan bukata ya saketa,yace nasan idan nazo Miki da gaskiya yanda kuke da son kudi to fa baza ki aure ni ba,ku mutanene kwadayayyu maganin irinku mu,amma ba laifi Ina dan samu a shagon wani da ya saka ni Dan abinda za a ci bazai gagara ba Inshaallah,shi Abu gaji ko mulki ne ana samunsa ko ta hanyar halak ko ta hanyar banza Matukar Allah ya rubuta zaka samu,shi yasa na sameki ta hanyar banza wato karya

     Gaji hawaye sharba sharba a saman kumatunta tace ka cuceni Danbinni ga matarka Yar bala’i Kai kanka tafi karfinka,da shegen katon cikinka sai kace mace me ciki wacce ake cewa Allah sauke mu lafiya, ciki Kamar irin tumbin kudi ne ashe ba komai sai Kashi a ciki, Danbinni yace to ya za ayi dani yarinya kinzo hannu kwadayi ya kawoki kin hadu da Zayya kawai idan ta Miki ki rama kiyi hakuri Amarya ki yafe min sonki ne yasa nayi Miki karya,Ina kaunarki ki yafe min Danbinni ya sake narke mata,wallahi duk komai na Ogana ne nake ara dake yaro ne matashi sai ya dinga goya min baya yace ai zaizo har gida ya ga Amarya,baki Gaji ta tabe tana hawaye tace uwar da ta haifi ogan naka Allah ya tsine Mata da Ogan naka harda kai da entire generation naku, sabo da Dabinni ya Gama sire mata,badan yunwa ba da Naman kajin da ya kawo baza ta ci ba amma haka Danbinni ya bude yace ci Mana kazar ya yago ya bata a baki Gaji tana shesheka tace Allah ya Isa ta lamushe kaza,ya sake yagowa Yana danne dariyarsa tana hawayen dai tace Zayya ma Sai na karya ta kuma wlh ka dameni sai na sace maka cikinka ta sake Mika baki ya saka Mata kazar ta hada da yatsunsa ta Masa cizo ba na Wasa ba sai da ya kurma ihu

   Amma ya daure ya dinga bata a baki ya lallaba ta gashi Danbinni Kalar matasan masu kudi ce da shi Kuma ba mummuna bane wankan tarwada ne da Yar kibarsa har ya Fara aje katon tunbi sabo da Yana cin Dadi gidansa ba laifi,sannan Kuma mutum ne me tsananin tsafta da iya shiga duk kayan da yasa kyau yake Masa ainun sabo da yayi Kalar kudi,Gaji tace wanka zanyi inane toilet din? a dakinta ya nuna Mata wata kofa dake rufe wacce ita Gaji ma bata kula da ita ba sabo da dakin katone sannan bakin ciki yana cinta yace ai toilet dinki a cikin dakinki yake yar gatana ya bude Mata ta ga karamar me dauke da siririyar kofa wacce baho bazai shiga ba sai dai a kaikaice toilet ta Sha tiles har jikin bango,sai ta danji Dadi,Danbinni harda cewa ai shi yasa Zayya tafi Jin takaicinki kiyi hakuri kinji Amaryata ki min Addua Allah ya hore min Zaki ji dadi Watarana sai na gina Miki naki ke daya ko ya Kika ce? Gaji tace kaji da shi ta Shige bayi tana murda pampo ruwa ya kawo har da shower ta sama,Gaji tace to ta nan dai na dan ci gaba tayi wanka da brush ta fito,shima ya shiga wanka tare da sake brush ya dauro Alwala ya fito ya iske gaji ta shirya cikin rigar wandonta Jean pencil ya kankameta ta saka bra,ta saka vest sannan ta kawo riga me rufewa har wuya irin ta sanyi duk uban zafin da akeyi ta saka T-shirt a sama ta zauna tana furta zaka ga tsiya.

      Zani ta daura ta saka hijab, Danbinni Yana kallo yace a ransa zaki San waye Danbinni Jallabiya ya saka ya jasu Sallah raka’a biyu yayi Musu Addua sannan yace tashi mu kwanta sai zumudi yake yi burinsa yau zai cika, Gaji ta gama damewa ta cire zanin ta kwanta a gefe, Suna kwance yace Amarya ta ya rungumeva hakan bai ce ya akayi tasa wannan kayan ba,yace gaskiya kayan nan sun Miki kyau kin birgeni,wani kulun Takaici ya Kama Gaji yana shinshinar kamshinta Yana shafa gashinta a hankali duk ya rude sai sakin wani irin numfashin jaraba yake yi,wuyan ta ya shiga kissing a saman uban rigar data jibga,a hankali Yana shafa kirjinta Gaji tana dariya a ranta tace taba bra malam

   Danbinni mikewa yayi ya fita sai gashi ya dawo ashe almakashi ya dakko ya boye ya dawo ya kwanta,sai da ta fara bacci yasa almakashin ya dinga tsarga ko wanne sutura da ta saka sai da yayi fata fata da kayan Gaji ta farka ta kalli kanta a duhu Kamar mahaukaciya,ta fara bala’i amma ta karfi ya riketa kamar me fyade haka yake sarrafa Gaji,
Harda cewa My love Zan samo Miki aikin gomnati ,ko me kike so Zan miki,gaji sakon na mijin nata Yana Kai Mata har kwanyarta tun tana zage zage, surutai yake zubawa,yace Dan Allah me kike so na siya Miki?a kanki Zan iya sata,sai Nishin dadi yake Yana sakin zance, Danbinni badai sanin ta Kan Mata ba tunda Yana Dan biye biye sai da Suka haukata kansu shi da Gaji,dama Sha gyara shi dai Danbinni bai taba Jin Dadin jikin kowa ba irin na Gaji ko matarsa zayya bai taba Jin abinda yake ji ba game da Gaji ta tafi da Imaninsa,a hankali ya Fara kokarin shigarta,Gaji ta saki Kara da karfi yanda Zayyanatu zata ji wai taji haushi, ai Kuwa sai da Zayya ta mike zaune sabo da bakin ciki ta kasa bacci gashi Kuma taji abinda ake yi Danbinni ya shigi Gaji tana ta zunduma kuka da ihu tana zafi zafi wayyo Antainar ka zafi,Zan mutu,Zayya tana ji sai ta fashe da kuka tace gobe akwai jarabar duniya a gidan nan wlh duk Wanda ya hana uwar wani bacci to shima bazai runtsa ba,Ihun Mijinta Danbinni taji abinka da karamin gida daki a jikin daki tana ji Danbinni yana zunduma ihun da ita bai taba yi mata ba, bata taba jinsa ya zauce haka a kanta ba,kishi ya sake lullube Zayya ta taso ta fito tsakar gida ba dankwali a kanta ta sake Jin sambatun Danbinni ko me kike so Zan Miki kece ruhina,I love you,bani da kamarki duk duniya,har abada bazan rabu dake ba,ihu yake sosai Yana cewa dadinki yayi yawa …..wallahi bazan rabu dake ba bazan taba rabuwa dake ba tare zamu mutu,duk duniya bani da sama dake,Gaji ta matsu ya kawo sabo da zafi sai kuka takeyi tana ture shi amma sai da ya dade sosai sabo da yasan mace,da zai kawo Kuwa kankameta yayi kamar zai tsaga Mata kashi tana faman Kiran Dagaci da Gwaggo ya juye Mata madararsa a ciki sannan ya zare jikinsa ya kwanta gefen Gajinsa,shi ji yayi ma Sai yanzu yasan me ake Kira da mace,yanzu yasan yayi aure,yanzu ma ya taba sex da duk ba Yi yake ba,wani kaunar Gaji ta Shige shi Kamar ya hadiyeta haka yake ji,a ransa yace lallai da na kusance ta a waje da nayi dana sani,yanzu gashi mallakina ce halaliya ta Inshaallah bazan sake zina da wata ya mace ba dama Zayya ce ta jefani ta hanani na Kara aure ita Kuma tayi min kadan mabukaci ne ni ta jefani cikin bala’in Neman Mata,Amma yanzu na samu Gaji ta ishe ni,Zayya kuka wiwi take Yi ta koma dakinta ta fada saman gadonta tana dirzar kuka Kamar ranta zai fita yaranta suna katifarsu su biyu suna ta bacci, ta tashe su ta fito da katifar waje tare da fatalo da yaran waje Kawai akan tana Jin haushin Miji sai ta hakke Kan yaranta,har ta kwanta yaran suna waje suna kuka abinka da uwa ta mike tana zage zage ta dawo da katifar dakinta ta kwaso yaran tana dura musu ashar Suka kwanta su Kam.

   Bangaren Gaji ango Yana ta lallabata Kamar wata kwai Gaji cewa take a banza makaryaci Dan karya wlh tunda ka biya Sadakina dubu talatin da biyar zaka ga tsiya a haka ya kaita toilet tare sukayi wanka Suka tsarkake ya gasata sosai da sosai sannan Suka kwanta bacci tana harararsa tana yatsina fuska tare da furta a banza.

    Sabreen Kuwa shaye shayen nata kullum Kara karfi yake duk kudinta sun Kare haka duk abinda ta samu a hannun Nawwar kayan maye take Sha,hakan bai isheta ba har wajen Baffan Nawwar take zuwa ta hada Masa karya tace Nawwar ya hanata kudin cefane babu kayan abinci a gidan haka zai bata kudi ta siyo kayan shaye shayenta,Yau ma ta Kai kwana biyu bata Sha komai ba,bata tambayi Nawwar ba take ficewa Yana Saudiyya Umrah ya kirata Kuma tana da number dinsa domin kullum sai ya kirata a waya sabo da ko a gida yanzu Yana bata hakkinta sai dai in bata so,idan bukatarta ta taso Yana biya Mata shima Kuma Yana nemanta duk da ba son hakan yake ba amma shi aure ba ayin abinda aka ga dama sabo da ibadane kowa sai ya kiyaye hakkinsa ko kana so ko baka so,Baffa ya fito zai fita sai ga Sabreen tayi parking din motarta ta tsuguna har kasa ta fashe da kuka tare da gaisar da Baffa da muryar kuka,Baffa yace lafiya dai Sabreen? Sabreen tace Baffa Nawwar ne zai tafi Umrah amma ko sisi bai bani ba na cefane duk da gidan akwai kayan abinci Amma Baffa da yatsuna yake so nayi girkin,Baffa yace ai Nawwar baida hankali bai gajeni ba Kamar ba ni na haife shi ba duk horon da zaka Yi to karka cuci mutum da hanashi abinci nan take ya ja tsaki tare da bude mota ya dakko dubu dari cash ya bata ta karba tana murna tayi godiya sannan tace Baffa a dawo lafiya bari naje na gaida su Papa yace to ba laifi ya shiga mota driver ya ja,ita kuma ta nufi bangaren Papa taje nan ma bayan sun gaisa hira tayi hira tace ai haka ya tafi ya barta ba kudin cefane ta langabe tana kuka sai da Papa ya bata 50k Suka Gama zage Nawwar tas Mama har da cewa yo uwarsa ta mallake danta komai sai ita zai bawa in banda Iskanci mace harda wani tafiya gidan danta Wai na bakin ruwa ta tafi hutu tsofai tsofai,Sabreen tace wa ya sani ko wani dadiro ne da ita a boye ba a sani ba,haka Suka dinga sharri kala kala sai dare Sabreen ta koma gida sabo da ta biya gidan su Jamcy.

     Ni Kuwa ya Kai sati a makka bai ko kirani ba tunda ya bani kudi sosai,baya gari na kirawo Seraline Suka zo su shida haka muke girkimu muyi hira kullum sai sunzo gidana munci kudi,yau ma cewa nayi su shirya zamu fita Shan ice cream ni Zan kaisu,key din motarsa Daya da ya bari gidana wata GLK na dauka na Shiga na Mata key na fita ba sosai na iya ba Wise ce take koya Mana tun Ina gidan karuwai, na kwashi kawayena Seraline,Star,Wise sai Dan daudu Santana Muka fita na fito da kudi na kashe mana,yanda nake murza motar nan a titi Kamar ta ubana,Seraline tace Dan ubanki gobe muje gidan su Nawwar wannan tsohuwar kakar tasu da Kika ce ta takurawa Maminsa muyi Mata warning,nace ku bari ba ruwanku sai sun shigo gonar mu rukun,Wise tace ai idan ta shiga gonarmu hhhhhhh tayi dariya tace sai taga shege,sai na Mata shege she go see Shege, Seraline tace gobe ko jibi zanje kauyen mu naga Innaya,muje a motar Nawwar Miracle muyi karya mu fita da Asuba muje muga su Dagaci mu cusa musu haushi dariya nayi nace kin kawo shawara

   Star tace idan kunje ku tabbatar sunji kunya, Sera ki kwana ki hakura da aikin nan na siyar da Gomnatinki gobe mu fita sai mu kwana a hotel jibi sai mu shiga kauyen Kinga kwana biyu mun dawo Nawwar bai San naje ba tace haka za ayi tace muje mu siyi sababbin Kaya na kece raini, direct wajen inda ake siyar da leshi Muka je ko wacce ta zabi Dan dubu Hamsim da gani ba karya,muka Siyi Shadda itama ta kece raini, Sai wata gown ready made kowa ta zabi wacce ta Mata, wajen masu dinkinmu Muka je su dama telolin na layin mu dinkin Yan karya suke irin mu Yan duniya ko yanzu kake so za a dinka maka in zaka cake kudi na zabi dinkuna irin na manyan Yara Muka ce a Daren zamu Zo mu karba suna da yawan gaske telolin katon hole ne teloli sunfi ashirin a ciki, ina da takalma da jakankuna masu tsada Suma da Nawwar ya siya min daga nan har yawo Muka fita Muka je Shan ice cream.

    Ai Kuwa dan Muna son karya da mota ne da a jirgi zamu tafi amma sai Muka tafi a mota,Muna zuwa mun San sai an zargi karuwanci muke Dole tunda zaman kanmu muke babu me aure ko a jikinmu sabo da alfahari muke da barikinmu,Mun ware wuta da asuba,Seraline ke tuka motar sabo da ta fini kwarewa Kuma ta Sha bin hanyar, ko hutawa bamu yi ba wuta muke Kawai ba tsoro ba tunanin rayuwa, sai dare Muka iso cikin Kano,tuni Sera tayiwa wani Alhajinta waya ta shigo kano,Har ya Kama mana hotel me tsada kowacce da dakinta Muna zuwa sauka Kawai Muka Yi,sai da Muka huta Muka Yi wanka tare da cin abinci, sannan Alhajin Sera yazo wani dan Majalisar tarayya ne me kudin gaske ne dan kasuwa ga siyasa ya rike mukamai da dama, ya shigo ya iskeni a dakinta ya dinga kallona Yana hadiyar yawu,Ido Muka hada ya kashe min ido,ya kalli Sera ya furta wannan kawarki ce? tace ae sunanta Miracle itama tamu ce,yace Ina so ko nawa Zan kashe tace bazan baka ita ba sai da sharadi yace na mene Fadi ko nawa ne, tace aikin Hajji zaka biya min,dariya ya kyalkyale da ita da wani Jan Idonsa gashi fari tas kyakyawa sai Jan Ido,yace an gama wallahi Zan na biya an gama bana da ke za a tafi,tace sai na tafi Ina can Zan hada ku yace kin San bana karya Alkawari karki damu,na kalli Sera Kawai nace to ka biya Mata ni kuwa zaka samu Local government, ya sheke da dariya yana nuna ni Kamar sabon Kamu irinku nake so kin min,nace Sera enjoy bari naje na kwanta na mata sai da safe.

     Sera Kuwa da Alhajinta zasu kwana,condom ta Mika Masa ya saka sannan Suka fara shoshalewa,washe gari Alhaji ya tafi, motar mu  na bada wanki aka Mata wanki na musamman ta fito kal, a nan Muka shirya Sera leshi blue ta Sanya ni kuwa shaddata na sa pink straight skert da wata riga hadaddiya nayi mugun kyau takalmi na da mayafi da jaka silver, sai kace yaran gomna haka Muka fito na maka glass na manyan yara irin kyan da nayi ba a fada naci dauri na musamman domin Sera ce ta Kira Mana wata me dauri tayi mana kawai abinka da yan duniya,Muna Fitowa a hotel din kowa sai kallonmu akeyi musamman ni da nake fara ana cewa da gani yaran masu hanu da shuni ne,Muna Jin wani Yana cewa ba zai wuce yaran gomna ba, dariya nayi a raina Seraline tace da zasu je suga gidan kasar mu da sai sun tsine mana nace ai jefe mu da duwatsu zasu Yi da zasu San asalinmu, yanzu tunda anzo inda Zan dan iya tuki nice driver

  Kamar motar ubana yanda nake wani gadara da Fadi na bude na Shiga Ina baza kamshi me tsayawa a rai,sai dariya muke da Sera mun cuci mutane masu kallo,nace Seraline kinga mu Fara yawo duk inda Muka hango Majalisar matasa muje muyi parking idan da dan shago ko ya yake muje mu dinga siyo Dan abu muyi show a garin nan ko banza babu kara’i nan gaba mun more,Sera tace irin wannan mota haka muje muyiwa maza kwalele yanda kike haka haukacewa za ayi Muka sheke da dariya naja mota Muka wuce, Muna tafiya a hankali tace yawwa shiga ta nan akwai taron maza matasa suna nan Yan zaman banza Kuma akwai kanti a wajen ko pad mu siyo,shiga layin nayi ai Kuwa dake Sunday ne yamma ta Fara duk sun fito wasu a tabarma wasu a bench gasu nan da Yan kwalisa,a opposite nayi parking tunda Muka shigo Suka tsare motar da kallo an hango farar Mata mazan Kano mayun fararen Mata,Seraline ce ta Fara fita ta zaga ta jikin kofata tana jirana na bude na Fara zuro kafata matasan nan Suka bi kafa da kallo sannan na fito da Yar jakata Muna tafiya ta gabansu Muka wuce Suka shaki kamshi Muna ji suna kus kus harda wow wani matashi yace da waccen zata so ni wallahi na yarda na Zama dan rikon Jakarta da na Shana gata da kudi ga mota na zabi wacce nake so na fita ta kashe min kudi ko kishiya bazan Mata ba babu ruwana biyayya Zan mata, Muka wuce muna shiga karamin shagon nace akwai chewgum orbit yace ai na Mika Masa kudi ya bamu guda Uku tun a nan Muka bare kwali daya Muka dauka sannan Muka fito tare da  mota yo mu ba Jin kunyar uban wani muke bare mu dinga hardewa sabo da kunya.

   Muna Jin wani Yana cewa sai kace daga kasar waje Suka sauka,haka muka dinga nuna wankan mu a gari muna yiwa maza Yan zaman baza masu matacciyar zuciya Wanda yanzu da yawa Samari mace me kudi suke nema wacce zasu ci banza, sun sha kwalele sannan Muka nufi kauyen mu, Seraline Kam Mamanta tana zargin ko karuwanci take ne amma Dan da yafi karfinka kana kallo sai addua ba yanda zaka iya da shi gashi idan an tambayi Yar uwarsu da aka turata can wajenta sai tace ai aikin restaurant sukeyi akwai wasu ayyukan na kamfani da suke Yi sabo da har ita din karuwa ce ba a sani ba,Kuma dalilin da yasa aka tura Seraline wajenta ba me Dadi bane idan ta zauna ma a kauyen surutu ne za ayi ta fama shi yasa basu damu su dai sai Addua.

   Muna shiga kauyen Allah yasa a Majalisar su Dagaci ta dattijai da suke Zama sai na hango wata me gyada gashi nike tuka motar, Seraline tace karki sake ko gidan Dagaci kije har mu koma naji ance anyi auren Gaji ai,matar na shararo da uban gudu Kamar Zan bi takan su Dagaci suka mike da gudu, parking nayi a gefen inda Dagaci suke sun zaci wasu manyan ma’aikata ne,Glass na sauke a hankali nace da me gyada siiiiiiii……motar na bude na fito gaba daya,da kyar Suka gane ni Suka tsura min ido suna kus kus wace wannan haka ko Yar Gomna ce ne? Jin magana ta nace ya ke me gyada nawa? Me gyada tace laaa Rabi Murmushi nayi tare da gyara glass dina da yatsa nace ashe kin gane nice,Dagaci yace Rabi ce wallahi yace Yar tsuntuwa ai Kuwa itace nan take yace ta tabbata Karuwanci yayi riba ashe a Karuwancin ma ci gaba akeyi haka,wasu da suke Zama wasu abin kyama,wani dattijo a ciki yace idan karuwancin na kucakai ne ba ai idan harka suke da manyan masu kudi ai ko Yar shugaban kasa Albarka,bakin ciki ya Kama Dagaci shi yafi so Rabi ta dawo abin tausayi ta bar gidansa wannan ai gaba ta ci,wani a ciki yace dama Dagaci ya fada Mana ance ta fada karuwanci ashe da gaske ne,Dagaci Yana da tabbacin asirinsa yaci Rabi yace ai Babu zargi tunda ka ganta tare da Saratu to sana’arsu kenan,Saratu Yar gidan Inna Wuro wacce ta Fara cikin Shege a kauyen nan aka dauke ta aka kaita Lagos wajen Yar uwarsu,ai ba wani aiki duk karya ce karuwanci take,dama ai Yar macece tunda Ubanta ya mutu kanin ubanta Bila ba ana zargin shi yayi cikin ba,to ga Rabi ashe can ta je dama abokin barawo ai barawo ne tun a kauyen nan halinsu daya,Dagaci a ransa yace da nasan haka zata ci gaba bazan ma yi Mata asiri ta fada bariki ba,idan ta sake zuwa naga taci gaba to asirin zanje na karya muga ta tsiya naga inda zata samu kudin,ai tunda ta hanani na sadu da ita baza ta zauna lafiya ba,a fili kuwa suna ta gulmarmu ni dai na koma mota Suka bude baki tunaninsu Zan gaishe su ko Dagaci,Amma motata nayiwa key na bula musu wata muguwar kasa nayi gaba,Dagaci yace ta rika lallai Kun gani ko kallo ban isheta ba bare ta gaisar dani ai tun tana yarinya haka take min a gidana,Suka ce gaskiya kayi hakuri cab.

    Gidan su Saratu Muka je,Inna Wuro sai ganin mu tayi katsam,tayi murnar ganin yarta,dakinta me kyau na bulon siminti harda tile sabo da Saratu ce ta rushe na kasar ta musu ginin bulon siminti ta saka tile ta zubawa Innarta kayan daki na zamani ta raba gidan ta barwa Kawu Bila kanin Babanta gidansa na kasa tunda baida mutunci,Inna sai murnar ganin mu takeyi tace ku zauna ta kawo Mana abinci dambu da ruwa tace gashi kuci,sai da Muka ci Muka Yi Sallah sannan Inna tace ashe Kuna tare ance Dagaci ne ya koreki ko,nace ae wlh na bawa Inna labari abinda ya faru Dagaci ya koreni dan gudun Kar ya hada min sharri a gari,Inna tace Allah ya saka Miki Yar nan, yanzu kema aikin gidan abincin kike Yi? Nace a’a ni Saratu ce ta hada ni da wani me kamfani ya bani aiki nice me kula da ma’aikatan ciki kaf Kinga dole na samu kudi,tace ai nafi yarda dake Rabi ke yarinya ce ta gari kowa ya sani a garin nan ke saliha ce tunda Naga Saratuna tare da ke nasan Alhmdllh yarinya ta bata lalace ba,ke ai duk garin nan an yarda dake,Kuma Indai bikinki yazo kizo na hadaki da dan uwana na Jangudo ya Zama waliyyinki dama Yana Jin tausayinki,dariya nayi nace Inshaallah Inna,Haka ta zauna tana ta Mana nasiha da fadan mu samu Miji muyi aure,Muka ce to Inna Inshaallah,yau zamu koma birni sabo da gobe da sassafe zamu koma can sabo da aiki,Inna tace oh bakwa gajiya to Allah ya tsare ai ni Alhmdllh Saratu ta gama min komai ‘ya daya tamkar da dubu,yarana biyar Maza gasu nan tunda Suka Nausa kudu ban San inda suke ba ko nemana basu yi basu San halin da nake ciki ba sai Allah ya azurtani da Saratu ba abinda ta raga min ci Sha da sutura komai Allah dai ya Miki Albarka Saratu Allah ya tsare min ke Allah ya shirya min ke,Allah ya muku Albarka gaba daya Muka ce Ameen Muka mike tare da yiwa Inna Sallama Muka bata kudi.

Muna Fitowa sai ga Gwaggo,Aunty Amarya,Mairo duk Dagaci ya basu labari baza su iya hakuri ba sai sunzo gulma,wani kallon banza na musu nayi ma Kamar naga kashi,baki Suka saki zance ya cika gari duk an cika wajen ana kallona,sai ga Bala me shago ya zo Wanda Zan tafi ya bani dubu daya Sanda aka koreni,nace Bala kayi gaggawa yanzu zanzo gidanka,ya washe baki yace Rabi nace Na’am na gaida shi na zaro kudi a jakata na irga dubu ashirin na bashi nace gashi ka Dan rage ayi hakuri sai na dawo,kowa sai kallo ya karba Yana ta godiya nace karka ce komai na fada maka a waya Ina aiki kasan kudu akwai kamfanunuwa nan gaba zan samo maka aiki kaima,Bala yace sai na jiki godiya nake,Yara Suka dinga Rabi Ina yini na dinga raba musu sababbin Yan dari dari dari biyu biyu,Wanda duk muke mutunci sai da na dan bashi wani abu Muka Gama karyar mu sannan zan shiga mota Gwaggo tace baza ki kulamu ba Rabi? wani kallon banza na mata na nuna kaina da yatsa nace ke baki da Chemistry a kanki ko? baki da Physics bare Biology ko? you dey mad na tofar Mata da yawu a gabanta na kalli Aunty Amarya nace Zan dawo ku jira sai na cire miki beli a gabanki na shige mita tare da daga glass din motar na bulbule su da Kura na ja Muka wuce,Muna tafiya Muka saki ihu a mota na daki sitiyari Ina dariya nace shegiya karya,kida Muka saki Muna tafiya muna dariya nace duniya da Dadi Allah ka bamu tsawon rai,Sera tace if you do anyhow you go see any how,shi yasa nayi shuru kiyi  musu da kanki zai fi musu zafi, sai da Muka  zo Kano nace Saura gidan Yan Uwana da Zan Kai ziyara gobe Zan kashe last Kobo na,Saratu gidan Marayu? Nace yes me Zan siya musu,Saratu tace har su biscuits da su Alawa ana siya kwali kwali a Kai idan kudinki ya karu sai kiyi dinkuna dana Yara da Yan mata etc duk a Kai,nace yanzu dai muje mall mu siya kayan Yara kanana Yan kanti mu gani,direct inda Kawai kayan Yara ake siyarwa Muka Fara zuwa,na siyi Kaya set sun fi set Hamsim dana Mata Dana maza dai dai karfina ba masu tsada can ba,sannan na siyi Inners panties da bra da vest ko wanne ya kai guda Hamsim Suma dai dai yanda Zan iya tunda Banda kudin da Zan iya siya su wuce masu araha,na siyi always pad yanda Zan iya na siyi Pampers na Yara itama da dan yawa, kudin da suka rage min gaba daya a jakata dubu goma ne,sabo da kudin Dana tara a iya accnt dina ya kusa million daya Kuma duk kudin Nawwar ne dake ba wani kashewa nake ba sai da dalili,Wanda nake kashewa a gari Wanda ya bani ne na cefane,Seraline tace to Nima bari dai na bada ko zan samu lada,nace naki kudin wallahi kudin Haram ne,Kuma wallahi Kika sake Alhajin nan ya biya miki Makkah da kudin karuwanci to ba lada ba na halak bane Kuma kin San bazan je ya kwashi dadina ba wallahi ki sani gwara ma ki sani ko kinje Allah bazai karba ba,Seraline tace nidai zanje ko Dan show ko banza nayi pics na dinga dorawa a status  Nima a San na Zama shegiya,nace to me Zaki Kara? tace Yan matan gidan zan siyawa kayan kwalliya su jambaki da powder masu araha dai da lipgloss Suma suyi kyau,Haka Saratu ta jibgi kayan kwalliya sosai harda su ribbom da yawan gaske ta siyawa Yan Yara kayan Wasa iri iri sannan Muka koma hotel kayanmu suna mota,yau ma tare da Alhajinta ta kwana suna watsewa.

    Washe gari 9pm haka muka je har daya daga cikin gidan marayu,Wanda ma’aikatan ciki ogogin basu sanni ba sabo da akwai wani Wanda shugaban gidan ne suke zuwa ganin Ina lafiya a gidan Dagaci,Muna zuwa aka raka mu inda mutanen suke yaran tsuntuwa duk dama kusan sune a gidan marayu abin tausayi Muna zuwa aka Fara bude Mana wani daki guda katon hole gaba Daya jarirai ne a ciki sabuwar haihuwa da masu kula da su,wani dakin kuma yarane Yan shekara daya zuwa biyu,wani Kuma daga Yan shekara uku zuwa biyar,wani Kuma daga biyar zuwa bakwai,daga takwas zuwa goma Sha,a Haka har Muka je dakin Yan Mata,ga bangaren samari da makarantunsu da Kuma filin wasanni da inda Kawai sana’oin Hannu ake koya musu,yaran Kuma da Basu Isa school ba sai kayan wasanni aka zube musu a dakin suna ta fama gasu nan cikin wahala duk suturar arziki Basu samu,a Raina nace bayin Allah mu dinga kaiwa na gidan marayu agaji suna bukatar taimako wasu sutura ta gagare su wasu kayansu duk sun yayyage an musu maho a agaza masu shi ba sai me kudi ba har kwance kaiwa akeyi,Kayan da Muka kawo Muka damka musu ,sannan naje na dauki wasu yaran Yan dagwai dagwai Ina musu Wasa hawaye Yana zubo min a kumatuna sabo da tausayi lallai Allah ya min niima da ba a gidan na taso ba haka Muka fito jikinmu a sanyaye amma Muna shiga mota muka saki kidanmu na Yan Nija Malam tuni mun manta Muka wuce can kudu.

   Sai tsakar dare na sauke Sera a gidanmu na karuwai sannan na koma gidana,Ina zuwa nayi parking na fito Ina dagowa nayi Ido hudu da Nawwar da Baba kulu a tsaye, tuni jikina ya dauki rawa dan bala’in Nawwar har tsakar dare yana jirana hankalinsa tashe ashe ya dawo ranar,Baba kulu tace Sannu da dawowa ke Kuwa Kika barni a gida baki fadamin tafiyar kwana zakiyiba yau kwananki biyu bakya gida Kawai kin bani kudin cefane ai kya fada min sabo da rayuwa,ga Alhaji tun yamma ya dawo na fada Masa ban San inda kike ba ya zauna ko nan da can bai fita ba sai dazu yaje gida ya dawo gashi har 3am bai tafi ba yace bazai tafi ba ashe kina tafe, nidai cewa nayi kawayenki ne Suka jajibeki kuka fita tunda da wannan me tsayin kuka fita,ran Nawwar ya baci sosai kamar an Aiko Masa da mutuwa jikinsa har rawa yake,kamanninsa Suka sauya Idonsa yayi wani ja,jikina rawa yake sosai a kasa na tsuguna nayi Kneel down na fara magana Ina yarfe Hannu nace bazan sake ba na tuba ka yafe min,gabana ya tako a fusace Yana huci yace gidan ubanwa Kika je Yana karaji,mikewa nayi nace wallahi Allah kauyen mu naje na rantse na fara ja da baya na take da gudu na bude gate zan fita ya riko rigata na kwala ihu tare da furta na shiga uku kayi min rai, ai Kuwa ya jawoni ta karfi na Fadi a kasa a haka ya jawoni kiiiiiiii har daki,Baba kulu tace baki kyauta ba ki jefa kanki a masifa kina biyewa karuwai,ai Kuwa har dakina ya jefani ya shigo waya ya jawo na tsure nayi tsalle na rungume shi,ya fisgewa amma naki yarda kuka na saki Ina cewa ka yarda dani wallahi da nayi wani abu Zan fada maka,ban taba munafuntarka ba karka manta a inda ka dakko ni na yarda na zauna da Kai bana fita ko Ina ka bari na maka bayani please,ka nutsu bazan Yi abinda baka so ba nasan abinda kake tunani ba haka bane,Ina kirjinsa na Fara Masa magana a kunne nace calm down,na sake rungume shi,abinka da shedan sai yaji wani sanyi a ransa tunda na rungume shi da kalamai na sai suka sanyaya masa jiki,gashi ji yake tsigar jikinsa tana tashi yarrrrr…..wani irin yanayi ya tsinci Kansa na musamman,yaji baya son barin jikina shi yasa ya kasa janyewa,Mu Kuwa Yan tasha dagowa nayi Ina kallonsa a hankali Idonsa ya dawo normal Ido Muka hada ya janye idonsa,nace kalleni Ina Murmushi, uhmm kaji fa Yan bariki mune mazajen,na sake cewa kalleni Sweety kallona yayi kadan a hankali na dinga matsawa da fuskata saitin tasa har na dora lips dina a saman tattausan jajayen lips dinsa nace I’m sorry,ai Maganar da nayi itace ta dawo da shi hayyacinsa samu yayi ya hankadaki saman bed na fada sai da na saki Kara,da yatsa ya nuna ni na fada Miki ba Dan Iska bane ki kiyayeni duk ranar da Kika sake taba min jiki sai Kinga me Zan miki idiot ya fice,Baba kulu tana jira taji duka sai taji luf bai fito ba tace iyyeee bariki shima na layinsu ne ai sai ta koma dakinta abinta tace su karata na daina shiga lamarinsu.

    Washe gari wata tafiyar ta taso Masa zuwa Scotland,har gida yazo Yana hararata ya min sallama har yanzu Fushi yake Dani Wai na tsotsar Masa baki abinda  Kawai lips Dina na Dora a nasa ba abinda na Masa Wai na shafa masa bakina da nake wa wasu mazan kiss da shi,amma Kuma ya kasa manta abin sai tunani yake da dadinsa yasan ma kiss dani zaiyi dadi,tunda ya tafi bai kirani ba amma Sabreen kullum sai ya nemeta babu fashi

    Sai da ya kusa dawowa sannan ya kirani a waya,Ina ganin number waje nasan shine ko dagawa banyi ba ni sai yanzu zai kirani sabo da raini wancan tafiyar ma haka yaki kirana amma ai in matarsa ce nasan zai kirata,Kira ya sake yi naki dagawa har ta tsinke,Tsaki ya ja tare da jefar da Wayar a saman bed dinsa,Bai sake Kira ba sai dare Ina jinta tana ringing naki dagawa,washe gari da safe ma haka a daki ma na bar Wayar Kan gado,Khaleel ya Kira lokacin Yana bacci matarsa Sufia ta Mika masa wayar tace Nawwar ne,dagawa yayi hello,Dan Allah Malam ka tashi kaje min gidan Yarinyar nan ka gani lafiya take,Sabreen ko wa? Sabreen din wa Malam Rabiah fa na kirata tun jiya taki dagawa Ina Jin ba lafiya ba kaje please ka min recording maganarta ka tura min ta WhatsApp,Khaleel yace kasan Allah Nawwar ka fada so,Dan ubanka sone ya kamaka tun wuri ka aureta Kar lokaci ya kure ma,Tsaki yaja yace shi yasa ni bana son harka da Kai ka fiye soki burutsu,to Makkah fa da ka tafi cewa kayi sabo da ita da Mami zaka je kayi musu addua, yace baza ka gane ba ni yanzu ai ‘Yata ce,hhhhh wannan wlh ko a auren Kauye baka Isa ka haifi kamarta ba cewar Khaleel,Nawwar yace naji Zan biya Mata aikin hajji ma taje tayiwa kanta Addua ko ta samu ta daina abinda take Yi, sai na dan taimaketa na aureta kaga ai tayi dacen miji,Hmmm kawai Khaleel yace sannan ya furta bari naje ya zanyi

  Da sassafen sai naji knocking na bude kofar Khaleel na gani ya kalleni sosai rigar bacci ce a jikina amma doguwa ce me gajeren hannu pink,Sannu da zuwa shigo na bashi hanya,ya shigo ya zauna na gaisar da shi ya amsa da fara’a yace dama Wai lafiya kike Nawwar Yana ta Kira Wai baki daga ba shine yace nazo na gani ya kike sai na fada Masa,dariya nayi nace kace lafiya lau nake kuma Ina ganin Kiran tunda ya tafi sabo da Allah bai kirani ba sai yanzu yasan da zamana,nace ya barni nayi tafiya ta ya kamani ya kankame ni ya makale yaki sakina sannan yayi tafiya ko ya kirani yace ya ji lafiya ko ba komai na samu number dinsa na dinga kiransa amma bawan Allah nan yayi mursisi yayi Shuru idan matarsa ce ai ya kirata ni kuwa ko oho dan dai Kawai Yana da kirki ne,Khaleel yace to kiyi hakuri dai ai kin San da dalili, ki Masa uzuri baki ga shi ya turo ni ba na gani lafiya,nace Allah sarki Kai ka mori aboki abinda yake yi Allah ne kadai zai biya shi,mutumin kirki Allah ya amsa Masa bukatunsa kace Ina gaishe shi kuma kace na Aiko Masa da kiss a kumatu da lips din kace ga kiss dina na cillo masaMmuahhh,Khaleel ya dinga dariya yace to zai ji bata San recording Nawwar yace yayi Masa,kafin ya bar gidan ya turawa Nawwar ta WhatsApp sannan ya Mata sallama ya bar gida Yana mamakin kyau irin na Rabiah,Nawwar Kuwa Yana online yaga Khaleel ya turo Masa recording,ya kunna Yana Jin abinda nake cewa Murmushi yayi kawai me hade da dariya yace Yarinyar Bata ji badan halinta ba na karbi kiss din dai, ya shiga harkarsa.

    Sai dare ya sake kirana na kwanta kenan ya Kira kasa kin dagawa nayi Kawai na daga, dagawa ta ke da wuya ya balbaleni da masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba,sai da ya gama akan naki daga waya Wai na Raina shi,nace to kayi hakuri baza a sake ba,da yamma kina Ina sai Kira nake,tsokanarsa nayi nace Allah sarki ka tambayi Baba Kulu Wani ne yazo wajena zance wai tsakani da Allah zai aureni a nan layin yake, Nawwar yace sai me ya ja tsaki karki sake fada min wannan zancen banzan haka ya ja tsaki ya kashe wayar, dariya na dinga yi,shi kuwa a can kasa bacci yayi yace to waye wannan wai babu wani mutumin kirki Wai da aure yake sonta Naga uban da zaizo zancen,nan take ya makawa secuties waya ya turo su gidan da yawansu sai gani nayi ana gadin ko Ina ba shiga ba fita bamu San dalili ba.

Masu Sharhi Ina godiya matuka.

Masu bukatar sauraren wasu Novels Dina Audio ku duba S ZARIA TV a YouTube channel dinta.

 

AsmaBaffa
08061929616🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

51-55

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naki ne
BINTA UMAR ABBALE

       Tunda ya tafi sai da ya kwashe sati uku sannan ban san zai dawo ba Ina kitchen Baba kulu ta tafi gidan Khaleel sai dare tace zata dawo,Ina cikin juya miyar kwan da nakeyi naji knocking gas din na kashe Fitowa nayi tare da bude kofa,kamshi ne na daban ya daki hancina Wanda ba shiri na dago nayi tozali da shi,yayi kyau ya Kara fari sosai dama gashi fari sosai duk haskena ya fini sosai,yayi kyau cikin kana nan kayansa riga farare ba karamin kyau ya zuba ba wandon Jean ne an yanka shi a gwiwa  gaskiya ya tafi da Imani na gashi dan matsashin saurayi,nace oyoyo yaushe ka dawo? Kin kafeni da Ido Kamar baki sanni ba bana son kallo,nace sorry kayi kyau ne sosai,Dadi yaji a ransa dan Kuwa Sabreen da ya dawo ko tace yayi kyau ai gashi ta bariki ta fada Masa,katuwar akwati ce nace yanzu ka dawo ne? yace Kamar wani marar Mata daga dawowata sai na sauka a nan,yana ajiye kayansa a gida ko Zama baiyi ba ya taho gidan Rabiah amma sai yace to tun 2pm Ina garin nan na sauka tuni sai Dana Yi bacci na huta na tashi nayi wanka da Sallah shine Kika ganni 4:50pm nazo,nace to Sannu da zuwa na shiga kitchen na fito da zobon da na hada dazu ya Sha kayan kamshi da abarba da ayaba a ciki in ka tace sai ka ganshi me kauri yayi Dadi matuka na kawo a juck da cup yayi sanyi sosai,na zuba Masa a cup na dauka na Mika Masa ya karba Yana Izza, kitchen na koma na karasa egg source din da nama sai Cous cous da na dafa tuni dama Baba kulu ce tace dan Allah nayi mana,Zubo Masa nayi zan Kai Dining yace ban iya tashi fa malama,gabansa na kawo na ajiye na dakko ruwa Eva,plate da spoon na dawo na zuba masa tare da Mika Masa ya karba yace wannan Yar iskar rigar da kika saka fa anyita doguwa kamar abin kirki tsaga ta gaba har cinya Kamar Yar arna go and change ya furta da tsawa, na kalle shi nace yo mu abin kunya ai gaba muka bashi ba baya ba,zan wuce daki yace dauki akwatinki tsarabarki ce harda na Makkah na hada lokacin Ina sauri ban baki ba,Kuma Allah yasa naga rigata daya a jikin Karuwar kawayenki,Ni dai murna nake Yi na ja akwati na Kai daki na bude Ina ta Shan kallo abina kamar me

    A ciki na dauki wata doguwar riga hadaddiya silver tayi kyau a gurguje nayi wanka nazo na shafa lotion na saka abata na shafa powder da lip gloss pink,gashina na gyara na Masa acuci sai mayafin rigar dama harda dan mayafinta na Dan yada shi a kaina nayi kyau tabi jikina shape Dina ya fito Kamar a sace ni na shafa turaruka na fito,har gama cinye abinsa tasa ya kwanta a kujerar Yana canja channel yaji kamshi na bai ko kalleni ba sai da nayi gyaran murya Ina murmushi dan ya juyo ya ganni ai Kuwa naci sa’a ya juyo ya kalleni kasa dauke Idonsa yayi a kaina,nace nayi kyau ko?kalli duwawuna a ciki gaskiya Wanda ya sameni yayi dace a’a kalli dan Allah ohhhh… baki ya tabe yace ni Zaki nunawa kyau kalleni na fiki kyau to me Zan gani, mikewa yayi zaune Ina so nayi control kaina na daina Kai kaina ga Namiji sai naji na kasa na rasa dalili sai dai naji Kawai naje Kamar ana fisgata.

    Mikewa yayi zaune Yana kamo tashoshi na karasa gabansa na sa yatsana a baki Ina ci Ina kallonsa yace ke kalau kike kuwa,da sauri na zauna Masa a cinya Ido ya runtse sabo da irin abinda yake ji a jikinsa gaba daya loosing control yakeyi sai ya kasa tureni sabo da irin turaren da Muka siyo a wajen Mazarkwaila na shafa dama ta fada Mana tace Namiji bazai so ya bar jikinka ba sabo da dadin kamshinsa,kyaleni yayi yaci gaba da canja channel ya diririce bai San ma Ina yake dannawa ba duk ya gigice hannuna na dora a kan nasa na cire remote din na ajiye gefe na juya na zauna daram muna facing juna nasan Ina magana watakil ya dawo hayyacinsa sai na rungumeshi tare da kwantar da kaina a kirjinsa,Ido ya lumshe nayi Murmushi dariya ta kamani yanda ya rasa inda zai saka Kansa,gemunsa na shafa da hannayena biyu na sauke bakina a nasa na Fara Masa kiss Wanda ke canja Masa tunani sai da ya bari yaji dadinsa sannan naji muryarsa da kyar tana rawa yace ta Allah ba taki ba nafi karfin kissarki shedaniya ya ture ni Saura kadan na Sha kasa na rike kujera da kyar na mike tsaye shima ya mike zai tafi nace I’m sorry sai lokacin naji haushin kaina sosai,yace cikin fushi bani bake tattaro kayanki ki koma inda na dakko ki I hate you,Ido na zaro yace kin ji me nace kije kiyi ta lalacewa tunda haka Kika zaba ni baza ki jefani a masifa ba wallahi ki koma can kici gaba daga inda Kika tsaya,na gaji sai Dora min bacin rai kike yi,baza ki jefani cikin fushin Allah ba ki tattara ki koma,mamaki ya kamani yace daga yau karki sake gobe na ganki a gidan nan, ya ja tsaki Kamar zai tashi sama ya bude kofa sai ga Baba kulu yace yawwa Baba zamanki ya kare tattara kayanki mu tafi,Baba ta kalleni taga na Dora hannaye a kai hawaye suna gangaro min a kumatuna bata ce komai ba tunda tare ta ganmu, Ina kallo ya saka Baba kulu a mota da kayanta Suka tafi ya maidata gidan Khaleel,Ni Kuwa kuka nake wiwi amma dan masifa sai da na ci abincina da ya rage na koshi na wanke komai da Muka bata Ina Yi Ina kuka Ina furta na cuci kaina sai da nabi ko Ina na gyara na rufe na kashe kayan wuta na tattara kayana har tsarabata a akwati biyu manya na jawo su na fito kuka nake sosai Kamar Raina zai fita,na rufe musu kofar gate na mike titi gaf da magriba Ina Jan akwatuna biyu hagu da dama,gashi unguwar ba abun Hawa na haya sai nayi tafiya me nisa Ina tafiya Ina kuka nace Rabi kin jawa kanki mutumin nan ba abinda ya raga miki gashi nan ai,sai da na fita Main road na shiga Napep ya kaini gidanmu na bariki sabo da kade kade da wasanni da nishadi yasa na Dan ji sanyi na goge hawayena na saita kaina kowa ya fito ga miracle sai yanzu ogan naki ya barki nace ae Ina dariyar yake,sai ga Yar zabil ta fito daga ita sai half vest da dogon tight wando tace Wai kice shegiyar sai yau Kika Gama Masa kwanakin ahh wannan ya daki harka,nace kin Sanni ai bama cin Kan jaki  tace for sure na true sis,nace Ina Sera? She dey inside na wuce sai rungumeni kowa yake har Yan daudu rungumewa mukeyi da su,Santana na rungume yace ahh ji kamshi kekam Karuwanci ya taimakeki,dukkan Yan gidan tunaninsu Ina yin sex Nima tunda bana cewa bana yi har Sera bata sani ba

    Ina shiga dakinmu Seraline ta ganni na shigo da akwatuna na fada saman katifa na fashe da kuka me tsuma zuciya,kallo na tayi tana mamaki sigarin da take Sha ta kashe tace lafiya fada min menene? nace cikin kuka Sera korata yayi Wai karuwa ce ni Kuma Ina sonsa da gaske wallahi na sake fashewa da kuka,Sera ta fashe da dariya tace heyyyyy Hajiyar love me na fada miki,me na fada Miki karuwa bata aure ko kinyi baki Zama lafiya Sabo da zarginki zai ta Yi,danginsa baza su taba sonki ba,kowa zai kyamaceki ko da kin shiryu baza a fahimci hakan ba,rayuwar mu ba Daya bace data kowa bamu da kunya bamu da tarbiya,Kuma daga Namiji ya Gama cinyeki karshe korarki zaiyi karya yake ba son Allah yake Miki ba,gashi kin kashe abinda Kika tara a gidan marayu sai kiyi hakuri a sake sabon lale karki Manta karuwa bata taimako abincina bazan baki ba so kin Saba dare yayi tunda ke kullum tasallah ce sarkin Sallah sai kiyi Sallah a fara Shirin fita Neman customers,nace bazan iya fita ba ni in Banda tunaninsa babu abinda Zan iya hasalawa,kin San Allah ba Wasa nake ba abincina baki ci jiya Kika ce min dubu biyu gareki,nace yanzu ma Saura dari biyar Sera tace to gwara ki tashi.

    Ba yanda na iya tashi nayi bayan munyi wanka nayi sallar Isha nayi adduoi nace Allah ka daidaita tsakanina da Nawwar ka sa Masa salama a zuciyarsa,shiri nayi sosai na saka guntun Bumshort da riga me dogon Hannu me santsi gabanta da botin Fara da zanen fulawa baki,wandon Kuma Baki,takalmi da jaka bakake na saka hular gashi na me tsada Dana barsu a dakinmu,Muka shirya tsaf 11:30pm Muka fita,na tsaya a cikinmu gamu nan reras damu Mata iri iri daasu kyau da munana ana ta dauka,Ni Kuwa na tsaya a wajen kamar gunki Ina tunanin Nawwar,Seraline ce ta daki kafada tace love no dey tire you? Haba ki saki ranki fa Hmmm, hayyacina na dawo na daga hannu Ina cewa customer,Nyash dey,big breast dey, duwawu for sale,local government for sale,come with your cash hot lady dey,Su Seraline duk sun samu customers Ni Kuwa na gaji na tsuguna a wajen na hada Kai da gwiwa na saki kuka,sauran matan ko wacce ta tabe baki basu kulani ba,mota ce ta tsaya a gabana fyalleliyar da ban taba gani ba na mike wani dattijo me Kamala ya sauke glass yace shigo,kallonsa nake Yi kamar na sanshi,yace Yan Mata kinyi min,nace Alhaji dama harda irinku Kuna lekowa nan? Yace jefi jefi mukan zo,a tsorace na bude gaban mota na shiga,yaja muka tafi,Yana kallon cinyoyina Yana lashe baki,Hannu ya Kai zai shafa na rike hannunsa da sauri,na bata rai,yace lafiya? nace farashi na da tsada,yace Nawa kike? Nace na Kai million daya, na baka kaina saida million idan baza ka iya ba saukeni,Alhaji ya kyakyace da dariya yace na Kara Miki 2million nace good Man,har ga Allah tsoro nake ji sabo da ban taba yi ba,ganin haka sabo da ya sauke ni  sai ka Kara min million daya,yace an gama ai kin min ni ko nawa ne Zan biyaki Yana dariya, wani rantsatsen hotel ya kaini cikin lafiyayyen daki, Ina zaune nayi tsuru tsuru Nawwar Kawai nake tunani jira nake yi na gudu

   Muryarsa na tsinta yace bari nayi wanka ko nace to,wayarsa ce tayi Kara ya daga da sauri naji yace sorry zanyi waya da Dana,karaf naji yace Nawwar wallahi kaji na rantse idan har ka sake dukan Sabreen sai na tsine maka,akan Kawai ta sake daukan kudinka tayi cefane,baka bata ne shi yasa,Nawwar yace yanzu Baffa ta daukar min 2million ban sani ba dollars Dina fa ta kwashe tasan na mene,to kaji me nace kayi hakuri akan million biyu sai na biyaka tsiyarka banza sakarai ya kashe wayar,gaba daya zufa ce ta lullubeni duk kuwa da ac din dake dakin,naji har muryar Nawwar a waya wallahi shine,Baffa ya shige wanka bai kula da halin da nake ciki ba,Yana shiga na tashi na dauki jakata na lallaba na bar dakin a hankali a nutse Kar ace wani abu nayi na rashin gaskiya na bar hotel din da sauri Ina barin hotel din na shiga taxi sai gida.

    Baffa Kuwa Fitowa yayi tsirara haihuwar uwarsa Yana cewa Baby na fito yaga wayam ya duba ba kowa bakin ciki ya Kama shi yace ya zata min haka gashi yau bazan iya jurewa ba ga Amaryata bata nan,akan ya kusanci Mami gwara ya nemi karuwa dama haka yake Yi mutum ne me tsananin sha’awa da bukata ko yaushe baya iya jurewa ko kadan,haka ya rasa ya zaiyi sai waya ya bugawa tsohuwar karuwarsa Star,tabbas Star ta gidanmu ya Kira tasan akwai kudi ai da gudu ta bar motar Wanda ya dauketa tace a gida ake nemanta ta tafi wajen Baffa a hotel din Dana bari tirr da masu Hali irin na Baffa na dawo gida na kwanta Ina ta mamaki amma ya damu sai na bar gidan dansa ashe shima dan hannu ne.

    Ina kwance a dakinmu nayi lamo abin duniya ya min zafi Banda tunanin Nawwar ba abinda nakeyi na kwanta Ina ta sharbar kuka,kofa naji anyi knocking sai ga Malika ta leko tace kunyi bako gashi zai shigo Kawai naga Nawwar ya shugo,kaina na maida saman katifa naci gaba da kukana,Murmushi yayi yace to kukan fa? Nayi masa banza,baza ki kulani ba,yace bari na bar Miki dakinki,da sauri na dago Ina hawaye nace ba…ba…bakina nane ya jawo min,da me? da nayi maka kiss,dama kace na daina na daina naki ji Ni ban San me yasa nake maka ba,na daina kaji kayi hakuri na fada cikin kuka,Bai ce komai ba na sake cewa ka yafe min na fashe da kuka tare da tashi na rungume shi ta baya,yace wayyo Allah ya rintse Ido da karfi ya furta zata kasheni a ransa a fili yace yanzu fa Kika ce kin daina a haka zan yafe miki,jikina na janye da sauri ya juyo muna facing juna yace fada min Rannan da bana nan Ina Kika je min da mota Kika Yi kwana biyu?

     Hannuna na yarfe Kamar wacce ta Kama wuta a hannun nace baza ka min fada ba? Yace yeah,nace karya Muka yi da motar Muka je kauyen Kano can inda na girma,Ido ya zaro yace Kano a mota? Nace ae Ina murmushi,kin iya mota dama nace kaji ka Ina Yar bariki ai mu komai mun iya ko Dan karya,ai mu Yan karya ne,In fada maka a motar Wise Muka koya itace ta koya min,da Seraline Muka je,Muka Yi dinkuna masu tsada kala uku,Muka tafi Kano Saurayin Sera ya Kama mana dakuna biyu ni Daya na kwana ita Kuma tare suka kwana,ya ganni yace Nima Yana ciki Wai ta bashi ni ya shiga local government dina zai biya Mata Makkah,Dan majalisa ne amma nace idan taje Makkah da kudin bariki to ba lada,tace ai Dan tayi show zata je tayi pic ta saka a media,in fada maka da Yamma na Kai mota wajen wanki taci wanka na Sha shaddar nan ka ganni kamar Yar gomna wanka ya Kai wanka, nace dole muyiwa maza kwalele masu zaman banza,a birnin nan Muka dinga burga da motar nan naci glass munyi pics a iPhone din Sera Zan tura maka kaga wankan ko Kai wallahi sai kace Excellent, Muka dinga bi majalisa Muna dan yin parking mu fito mu dan shiga shago muyi Yar siyayya mu fito,kaga idon maza duk an zanci yaran masu Hannu da shuni ne basu San da zasu ji tarihinmu to wallahi jefe mu ya kamata yayi,dariya ta Kama Nawwar Jin shirme Muka tafi Muka yi,Ina bashi labari nima Ina dariya cinyarsa na dakawa duka Kamar kawata mace Ina cewa sai da Muka girgiza maza masu zaman banza sannan Muka nufi kauyen,wayyo na saka hannuna na sakalo ta wuyansa nace zo kaga Rabi a Kauye ta waye dariya Nawwar ya saki ba shiri nima nayi dariya tare da dan dukan cinyarsa kadan da sauri nace sorry Ina dariya Ina sake dukan cinyarsa kadan Kamar dai yanda akeyi da kawa mace,yace to Ina ji nace haba na dinga fyalla Naira Ina yiwa Dagaci da su Gwaggo kwalele,Kuma nace Ina nan sai nayiwa Dagaci fidiyar dan akuya sai na koma Zan fita da fitata.

     Kudin da ka bani na cefane naje nayi karyata a Kauye Dagaci ya turo su Gwaggo suzo suga yanda na koma a gabansu ko kallonsu banyi ba ban ma nuna na sansu ba,nan dai na bawa Nawwar labarin komai har zuwan mu gidan marayu nace Naga Yan Uwana na fada Masa abinda Muka siya Muka kai,Yana Gama ji yace uhm ta wani bangaren kunyi dai dai ta wani bangaren Kuma Baku yi ba me yasa kuka je kauyen? nace karya ta kaimu,yace ai zarginku za ayi Kuna karuwanci za ace zaman kanku kuke yi tunda an San ba miji ne gareku ba,nace ai basuyi karya ba,mu abin kunya baya Muka bashi ba gaba ba,ransa ya bata sosai ba Wasa yace yanzu kaf kudinki sun Kare? Nace ae yace good  tunda a gidan marayu Kika karar ko ba komai kinyi abin kirki,kayi hakuri abinda nake maka ban San Sanda nake Yi ba sai naji kamar ana ja na,ya sake daure fuska yace kina so na hakura? da sauri nace ae,yace ki min alkwari duk abinda nace Zaki Yi babu musu Kuma dole kiyi,nace nayi Alkawari,yace in na furta ba musu ya Zama Dole,nace komai na yarda Indai zaka hakura,yace Marry me,Ina ji na furta kace me? Nace ki aureni,ji nayi kamar ya zuba min wuta a jikina ni bana son zancen aure a duniya sai naji tsananin damuwa daga lokacin na rasa farin ciki,nace ai ban San aure zaka ce ba ni bana son aure ko mene na yarda zan baka a duniya banda aure,taya Zan taima miki taya Zan zauna dake babu aure kina rungumeni kina min kiss ba aure tsakaninmu idan munyi aure Kuwa babu damuwa sannan ni karki tunanin sonki nake bazan taba iya rayuwar aure da karuwa ba,bazan iya saduwa da Karuwa ba inda maza da yawa Suka Shiga ba bazan iya Kai kaina nan ba,sannan magana ta Allah zai wahala na yarda da Yar bariki ko yaushe Ina zarginta,Kawai Ina so ne ki taimaka min kawai na karya dokar gidanmu daga kaina a daina auren dangi auren dole shike nan in kin min haka muka dan zauna komai yayi settling Zan iya sakinki in kina so,sabo da haka ko kin aureni ba sex ba feeling karki ji komai a kaina so ko wani sex bana so kisa a ranki babu wannan Kawai ga abinda nake so ki yarda ki bada Amanna na aureki shike nan

     Sai lokacin naji sanyi a raina nace tunda ba Zama zanyi ba ai da sauki,yace Kuma sai kinbi dokar aure abinda Allah yace kin nutsu,sannan auren nan yaki ne sosai kafin ma Baffa ya amince ayi shi,nace Baffa ne matsalar auren? Yace kwarai sai kinyi hakuri,Murmushi nayi nace wallahi yafi komai sauki Kuwa karka damu ka kwantar da hankalinka kaje gobe direct kace aure zaka kara idan ka fada masa Kawai ka kirani ka sanar dani, dariya yayi ya zaci shirme na ne a ransa yace wannan bata san waye Baffa ba,ai shi baya Wasa da kowa baida lokacin kowa ma daga aiki sai amaryarsa,a Raina ni kuma nace oh Namiji ba a mallakarsa dole ta wani bangaren Amaryarsa ta mallake Baffa akan Mami ta Zama ita ce on top amma bata mallake shi akan karuwai ba,ta zaci ita daya ce,ta hanashi kula matarsa ta sunna amma gashi Yana bin na banza,yace kin amince? Nace tabbas Ina da waliyyina a Kauye can kano, Kawai ka shirya ka fada Masa sannan ka sanar min,yace mun shirya to,Murmushi nayi yace wannan Yan iskan kayan da Kika saka fa? Nace shakatawa nake kafin na koma prison gidanka,yace bikin nan fa bazai wuce nan da sati biyu ko Uku ba Kawai ku shirya abinda zaku shirya ku fada min Baffa ko ya yarda ko bai yarda ba za a daura bai sani ba,nace karka damu da Kansa zai karbi aurenka,duk Wasa yake gani,skert na dora a saman wandon Nawa na rako shi har jikin wata motarsa red, kudi ya dakko 50k ya bani yace kudin abinci na sanki da shegen zuwa Saloon,nace to ya zaka Yi ka hadu da Yar duniya Yar bariki Local government guda muke siyarwa fa,yace jeki ni kudin na rike Ina fifita da su Ina ce masa Saurayina Dan dolo ya bada kudi ko nono bai tabawa ehhh ehhh ahhh nabi wani kida dake tashi a layin Kamar zai fasa dodon kunne da kyar ake Jin magana,na koma gaban motar Nawwar na dinga karkada masa mazaunai ina fifita da kudin,naki matsa Masa yayi reverse ya fita a haka ya bar layin,Malika ce tazo ta dana min duka ta Kara gaba dariya nayi nace yanci dadi, Santana yace kekam Karuwanci ya taimakeki kinfi kowa sa’a a gidan nan har yaushe Kika Zo garin nan da tsumman kayanki kina warin Kauye Wai gashi kinfi kowa samun me kudi kowa yazo neman ki sai me kudi Kuma sai kinwa kowa yanga,nace haka lamarin Allah yake wani baya sonka ya jefar da Kai wani sai yayi kuka akanka na wuce daki na kwanta sai bacci.

     Amarya Gaji Kuwa amarci Kawai suke Sha da Danbinni,angon bata wani so da kaunarta yake yi Yana Jin bazai iya rabuwa da Gaji ba,itama ta dan hakura ganin yanda yake bata kulawa,Zayya Kakarta da kanta tazo gidan ta kwantar Mata da hankali tace ba a kishi da fada baza kici nasara ba ai kwantar da Kai Zaki ki dinga hada Mata tsiya ta karkashin kasa cikin tuggu,sannan sai a hada da malamai ayi Mata Wanda zata bar gidan nan ai baza mu taba Zama ba baza mu barta ba Amma karki sake takalarta da fada ko ta kulaki da fadan ki maida abin Wasa zata ci ubanta,Zayya taji dadi tun daga ranar Gaji ta samu lafiya da Zayya ta zaci ta hakura,shima Danbinni haka har Yana murna, Kakar Zayya Kuma wani rubutu ta kawo wa Zayya a boye tace gashi kin ganshi sai kinyi wanka Zaki shafe jikinki da shi ki tabbatar ranar ya sadu dake in kinyi shike nan ita da miji shike nan,Gaji Kuwa washe gari Mairo tazo wani abin Hannu Kamar awarwaro na guru tace gashi inji Baba yace a hannunki Zaki daura babu ke babu masu tsafi ko me kishiya zata Miki a banza,yace karki Wasa da shi sai da ya siyar da gonarsa ya iya karbo shi tsada gare shi kusan dubu dari biyu ya kaiwa Malam sai da aka yanka rakumi,Gaji nan take ta daura abinta a hannu, duk akan miji suke sunnawa kansu tsafi,Zayya tana ta faman kashe kudi magani yaki cin Gaji sai amarci da love akeyi Kamar ma Kara kaunar juna suke yi,ganin haka Zayya ta gaza hakuri ta dawo da bala’inta,Gaji ma ba jira,Haka Kawai Zayya tayi girki Gaji ta fito ta bude miyar ta dandana tace gishiri yayi yawa ga shegen yaji ke a gidanku haka aka koya miki taki tarbiyyar kenan? Oh no wonder goyon kaka ce tasa kafa ta daki tukunyar Miya ta watse a kasa zayya ta taso Suka kaure da kokawa har waje kofar gida suna kokawa,mutane sun cika damkam ana kallo anyi anyi su bari sunki ji,Gaji harda ja da baya kamar wata rago ta taho da gudu Zayya ma ta taho Suka hade gwaraf Kara Suka saki zafi ya ishe su ko wacce tana sosa goshi da hanci,aka kwashe da dariya da ihu Suka sake rukumuwa Gaji tace sai na kashe ki nice ajalinki,Zayya tace nice ajalinki kafin ki Gama dani zan gama Dake bazan yarda ba Danbinni ya dinga Kwanciya dake Yana cika gida da ihu ba Ni Kuwa sai yayi Shuru a dakina,gaji tayi tafi tace heeee ba Maggi baki da Maggi Ni Kuwa ajino moto ce harda curry,Mutane da Yara sai ihu da shewa akeyi ana dariya zamani na waya ana ta musu video kafin kace me Abu ya cika tik tok sai gani akeyi har WhatsApp wasu sun saki ko waccensu ba mayafi suna ta fada kamar kaji anci dariya ganin Gaji tana dukan kirji tana cewa itace Maggi ajino moto harda curry ana ta yanko wajen ana sawa a media,Haka ana saka wajen zayya da tace ita Danbinni baya ihu da kuka idan Yana kwanciya da ita sai Gaji,Danbinni ransa ya baci ganin matansa sun baza media a ranar da kyar manyan Mata suka sasanta fadan.

     Nawwar ne ya samu Mami da zancen aurensa,tace mashaallah Allah yasa ka Zama sanadin shiriyarta amma ka dakko da zafi zaka jawo min bacin rai,Matukar Baffa yaji zaka auri bare to mun shiga Uku ba zai yarda ba watakil ma ya sakeni,Nawwar yace Wai Rabiah tace na fada da Kansa ma zai daura auren ban San dai mene ba amma na yarda da ita ko ma mene gwara Kawai ayita ta kare,Mami tace tab Nawwar bari na hada kayana nayi Shirin barin gidan Yana cewa tafi sai tafiya, Sultana suna Jin labarin Nawwar zaiyi sure Kuma bare wai ma karuwa Rabiah wacce akan zamanta a gidansa Kawai an kusa ayi yaki a gidan su kansu sun San zaman Maminsu ya Kare a gidan tunda komai danta yayi a kanta yake karewa tuni Suka Fara kuka suna addua.
Nawwar Kuwa sai da ya tara kowa na gidan har Sabreen sai da ya Kira ga Baffa,ga Papa,Mama,Iyamami,ana  jiran aji Nawwar me yazo da shi ya tara kowa haka, Mami tayi Miki Miki kusa da yaranta,Nawwar Kuwa Yana gaf da palon ya kirani a waya lokacin na tara su Sera na sanar musu komai har daukana da Baffansa yayi zaiyi sex dani,Star tayi shewa tace ai ni na dade da sanin Baban Nawwar Yana bin Mata tsohon kwartona ne shine ma ya siya min gida a Kaduna ya kaini makka,na more shi sosai Kawai fada Miki ne banyi ba,wannan ta kwana gidan sauki blackmailing nasa zamuyi mu biyu ni da ke muce lallai idan bai amince ba sai mun kawo video dinsa gida mun nunawa Amaryarsa Ummyn Haidar,sai Mun nunawa Dan Uwansa Baban Sabreen da Sabreen da Iyamami har Nawwar sai ya gani da kowa nasa sannan dole ki zauna gida daya da Sabreen da wannan gidan duniya ne Aljannar duniya ne,sannan idan yayi Masa baki ko ya saka Miki Ido a aurenki zamu saki video,tafawa mukayi su Santana Yan daudu Suka saki shewa,Sera tace Miracle da aure mu Kam aure sai dai a lahira waye ma zai aure mu sai dai muyi Ashawon mu,nace nima na dan wani lokaci ne zan dawo bafa son auren nan nake ba dole yayi min,Wayar Nawwar ce ta shigo,na daga da sauri yace yanzu Zan shiga ciki na Tara kowa Zan fada Kiyi addua,Murmushi nayi nace an gama, Yana datse Wayar Muka dauki shewa.

    Nawwar Yana shiga ya zauna,Papa yace Muna jinka Nawwar mene ka tara mu sai kace zaka raba Mana kadararka,Nawwar yace zuwa nayi na fada muku dan Allah kuyi hakuri ku yafe min Zan Kara aure,da sauri Sabreen ta shide tare da dagowa da sauri,Iyamami tace Yar gidan wace a dangi tunda ka damu uwarka ta zugoka ka nuna mana bamu Isa ba,dama ya tsaneni Iyamami cewar Sabreen ta fashe da kuka,Nawwar yace banyi Dan na batawa wani ba sai don na raya sunna,Kuma Allah yace ayi idan kana da Hali zaka iya adalci, Mama ce tace Kai dalla rufe mana baki zaka Kara aure dai sabo da baka son Sabreen jininka,Baku da aiki ku maza iliminku baya tashi da hadisin ku da Jan aya sai zaku Kara aure duk maza haka suke ba yau Muka taba ji ba,Papa yace zaka samu a gaba ka Raina mana hankali sai shegiyar Isa da mulki da mallaka da izza ana fada uwarku tace ai Kun gaji sarauta kakanta ne fa ya taba rike me unguwa tun irin sarauta ta kauye karka Zo Mana da gadara a nan wacce ka gada a wajen uwarka,Mami tace ai dai jininmu daya,yace ke ba Yar uwar mu bace can kisan danginki,Baffa ransa ya baci ya nuna Mami yace kece munafuka karki ce komai ke Kika zuga shi algunguma Ina jinka cikakke isasashe wacece a dangi kasan mu babu bare a cikin aure, fada mana wace,Nawwar ya gyara zama dan rainin hankalin Nawwar sai Kawai ya dakko musu labarin Rabiah yanda ta bashi tiryan tiryan sai da ya Kai aya yace wannan ba abar a taimaka bace wannan ba abar da za a tsaya a duba lamarinta bane,Ran Baffa idan yayi dubu to ya baci, yace na farko kasan a tsarinmu babu auren bare,amma dan ka maida mu wasu Yan Iska sai ka dakko bare a baren ma ba Yar asali ba sannan ma Yar tsuntuwa,karshen muni Kuma itace wace Muka sani ka Kai gidanka muke zarginta da karuwa,ai ba zargi bane karuwa ce cewar Sabreen tana kuka wiwi,ba a San Yar waye ba,Yar shege ce,mayya ce,jininsu babu na kirki,Basu da Nasaba bata da kowa, komai babu Kawai sai mu kawota cikin zuriarmu ta haifa mana mugun iri yaran zina cewar Baffa, to ka sani ni Sulaiman….kirrrrrrrr Wayar Baffa ta dauki ruri ya dakata da magana ya dauki Wayar sai ya ga Star ce take kiransa dama yau ma Yana so su hadu sabo da Amaryarsa bata nan ta tafi ganin gida,dagawa yayi ya mata Sallama tare da furta Ina meeting Zan nemeka anjima ya Kira star da Namiji Wai zan nemeka anjima dake Karuwan sun San irin wannan,sai tace bani minti daya hope ba a Jin maganata a fili yace ae da sauri

     Star ta furta ka tuna wacce jiya ka dauka a titi street din da muke tsaiwa? yace kwarai,tace to itace wacce danka ke son Aure Kuma kawata ce wallahi ka yarda tun wuri a daura aure Kuma idan an daura ba ruwanka da safgar Aurenta da mijinta Kuma tare zasu zauna da Sabreen din Kuma kaje kayiwa danka walicci idan ba Haka ba wallahi Muna da video dinka Wanda muke sex tare na dauki wasu Ina da su Matukar baka amince kawata aminiyata ta auri danka Nawwar ba wallahi kaji na rantse har gida sai nazo da kaina na nunawa Ummyn Haidar Amaryarka,Iyamami,Papa,da Nawwar Kai da dukkan family dinka kuma kasan Zan iya idan kana musu kazo mu hadu a hotel din jiya yau na nuna Maka videos din ka gani da idonka,yanzu ma ka bude WhatsApp dinka zaka ga wasu,Baffa gumi ya Fara hadawa da kyar ya iya magana yace Zan Kira anjima ya datse Wayar ya kalli Nawwar yace kowa ya tashi ya tafi na sallami kowa zanyi magana da Nawwar akan aikin gidan gonata da Zan bude Zan sake tara meeting,tunanin kowa har Nawwar a Kamfani aka Kira Baffa yayi asarar wata kadara yanda ya gigice yake hada zufa,har Iyamami fita Suka Yi da yakinin aure baza ayi shi ba,Baffa WhatsApp dinsa ya bude yaga videos dinsa guda uku tun daga Kansa har kafa tsirara Yana Sex da Star,bai sani  ba Su Star Indai zasu kwanta da mutum sai sun saka wata camera a boye Kuma baza ka gani ba,komai sai ta dauka incase ko zasu hadu da wani shege ya Raina musu hankali sai suyi blackmailing dinsa da shi,har su Sera duk haka suke yi,Baffa hankalinsa ya tashi da sauri ya goge na wayarsa gaba daya,ya kalli Nawwar yace na yarda ka aureta abinda Allah yace ba yanda za ayi idan na matsa karshe Allah zai iya dauke ni Kuma ayi abin bana raye,Kuma na duba naga abar taimako ce tabbas na yarda Zan Shige gaba Allah yasa Albarka amma da sharadi daga ni sai Kai Sai Mami zasu sani a gidan nan bayan haka ko kannenka Kar su sani gudun Kar Iyamami taji ta hana,idan an Riga an daura sai nace Nima ban sani ba munafuntata kayi na maka fadan karya nace lallai sai ka sake ta to karka saki abarka kuyi zamanku,jeka abinka yaushe ne bikin muje wajen waliyyin nata? Nawwar Kamar an dasa shi haka mamaki ya kamashi jiki a sanyaye yace Baffa ka Zama waliyyinta,Ni kuma Zan karbi aurena da kaina kaga shike nan tuwon mu man mu ya furta Yana dariya,Baffa a ransa Kamar ya fashe da ihu amma haka yayi yake yace acan kauyensu zamuje a Tara mutane a daura, yace an gama mun shirya Nan da 2weeks yayi? Baffa yace ai sati daya ma me kake jira tunda a shirye kake kana da gida da komai,Nawwar ya dinga mamaki maimakon murna sai da Suka gama tsarinsu sannan ya koma Yana bawa Mami labarin abin mamaki,ita kanta tace to lafiya kuwa anya lallai akwai wani abu a wayar da Baffa ya daga,tabbas Wayar nan ce da yayi akwai wani abu a kasa babba,ko ma mene Rabiah zata fada maka Watarana,yace tabbas daga nan fa Nawwar direct gidanmu yazo,Ya same mu Muna shirya gagarumar dinner da zamuyi har kala biyar Kuma shi zai biya ,sanye yake cikin shadda sky,na karaso jikin motarsa cikin abaya Ina karasowa Ina murmushi nace barka da zuwa Angona, Ido ya lumshe yayi Murmushi,nace ya kuka Yi? yanda Kika ce ya faru,nace Alhmdllh shike nan,Wai meke faruwa ne me kuka ce masa? nace karka damu Indai nice ana zuwa gabar da zaka ji Zan sanar da Kai kasan bana boye maka,nacewa yayi lallai sai na fada Masa nace tunda ka damu sai kaji to wata kwangila ce Suka fara da Saurayin star,Baffa ya Gama kashe kudinsa yayi domin wajen billions ya kashe shine Muka saka Saurayin muka ce yace idan bai yarda ba lallai zai janye kwangilar yasan shine da asara Kuma mutumin Sakataren gomnati ne na federal,shine ya yarda kaga munyi sa’a, Nawwar dai Yana mamaki yace Naga Baffa ne ya Saba da asara Kuma shi bai fiye son kudi haka ba akan kudi ba a tursasa Baffa yayi abinda baiyi niyya ba,nace to a nan sai yaso kudin Kam domin munyi nasara dan sai da mutumin yace ma Sai yasa EFCC ta bincike shi tunda Yana hada harka da gomnati kaga Kuwa kudin gomnati ba Wasa,Nawwar yace idan wannan ne Zan yarda dan Yana harkalla da gomnati sosai,Murmushi nayi dan Kuwa na tsara yanda star tace Yana harkalla da gomnati suna bashi kwangila, sabo da bai kamata dansa ya San ubansa yana Neman Mata ba,sannan bai Dace mu iya fadawa Nawwar ba in munyi haka ba Amana,da ace Baffa gonarmu ya shiga to zamu iya keta shi ta ko Ina ba ruwanmu da duk Wanda zai sani mu dama bamu hada Hanya da arziki ba bamu sanshi ba bare mu kyale.

    Nawwar na mikawa paper nace gashi mun tsara yanda bikin zaiyi,karantawa yayi yaga uban miliyoyin da Muka tara Masa,yace ku duk harkarku ba sauki a ciki yasa biro yayi cancel dinner yace guda daya za ayi tal bana son wannan shirmen party din Ni ba Dan bariki bane,nace to ai dai za ayi dayar ko? yace Inshaallah,nace sai lefe gidan su Sera za a Kai a Kauye,yace ba damuwa,karanta paper din ya sake yi yaga na rubuta kudin gyaran nono ba wani sakayawa sai lokacin ya kula ma,dariya yayi a ransa, yasa biro ya rubuta Boobs ki bar wannan a hannuna Ni Zan gyara shi da kaina,ya duba kasa yaga na rubuta Local government Kar a manta da kayan shaving dinsa,sai Kuma kudin siyen kayan gyara wajen sabo da wajen ya Kara lipton duk da wajen cewar yaji Lipton dama,Ya rubuta ke ga Lipton a wajen ango ai Yana nan zai tsoma shi a ciki,a ransa yace Yarinyar nan tayi balain rainani gani takeyi Kamar ban San komai ba ma irin ga wani ajawo,kwafa ya ja Ina jinsa nace Wai rubutun me kakeyi Kai? In kin karba Zaki gani, ya gama soke Wanda zai soke ya bani takardar yace zanyi transfer hole Kuma za a kama,karba nayi nace thanks ya shiga mota ya tafi,ni Kuma na koma na zauna a saman bench din da muke zaune Muna shirin biki.

    Takardar Muka karanta Muka ga abubuwan da ya rubuta shewa mukayi da ihu nace yeeeeeee shima Dan duniya ne yeeeeyyyyyyyyyy Muka tafa da su gaba Daya Muka hada hannaye waje Daya harda Santana Dan daudu yace Warrrrrrrrrr inji gwanja za a daki ganga wallahi aci uwar gayu ranar sai na saka bra katuwa ko na samu mashinshini,dariya ya bamu Muka kalle shi,ai ba jira washe gari tuni mun buga gate pass,gyaran jiki kuwa munyi shawara kayan kamshi da sauransu za a min a dafa Ni da kamshi yanda duk inda na zauna ma to fa kamshi zaiyi kwanaki bai bar wajen ba,sai gyaran skin sai maganin infection kawai,shi na Fara gaba daya Sera ce ta biya kudin Wai gudun muwarta gashi komai namu me tsada muke Yi dan mu ba garorin Yan bariki bane kucakai layinsu daban,kafin kace me kowa yasan zanyi aure a barikin duk shiri akeyi Mata da maza Wanda muke harka,duk Wanda ka gani dan wanka ne da karya da kashe kudi sune a bikin,anko ma wani materials me tsada aka fitar kala hudu kowanne agroup da Kalar nasu a wajen,maza Kuma shadda Muka fitar kala hudu irin na kalolin material din,sea blue,milk,purple sai silver,su Star nasu Sea blue Suka zaba, duk wata karuwa sai da ta gayyato Saurayinta data fi good time da shi Kuma yayi ankon Kalar na group din da take,Karuwan sun min Kara akwai hadin Kai ko wacce da kudin data bani sun tara min kudi sosai har maza.

   Tuni mun fadawa Inna a waya ta sanarwa Dan uwanta Jangudo me tausayina sai Murna yake shi ya bawa dattijai da su liman Alawar daurin aure ya fada musu ranar,shi Kansa Dagaci sai ji yayi an Kai Masa gida ana gayyatarsa a masallacin Juma’a na garin, yace ashe za ayita asirina bai ci Yarinyar Nan ba aure ma zata yi,to wallahi ko anzo sai na sa Iyayen yaron da kansu sunce sun fasa yanzu haka basu San Yar tsuntuwa bace,Gwaggo tace ai nima nan sai inda karfina ya kare,Aunty Amarya mamaki da bakin ciki ya hanata magana Sam,mu Kuwa ana jibi daurin aure ranar Friday zamu Yi dinner Saturday ana gobe aure zamu tafi Kauye idan an daura daga can za a dakko Amarya,Saura kwana hudu biki Nawwar ya hada lefensa Mami ce ta hada komai akwatuna set biyu guda goma Sha hudu ko wacce da kyar take rufuwa, Abin a sirri ake yinsa dole Mami da Seraline suka tafi can Kauye a jirgi,suka sauka a airport dake kano taxi Suka shiga me kyau har Kauyen Suka Kai Lefe,ai Kuwa Sera har gidan su Gwaggo taje tace an kawo lefen Rabi kuzo ku kalli abin farin ciki ko yarinya me iyaye  bata isa ta Kama kafar Rabi ba, kawai ta juya tayi tariyarta,su Kuma da son gulma da wuri Suka fice har Mairo ita da Aunty Marya ga Gwaggo Suka je tun daga ganin Mami Suka tsorata sun San ba talaka ne ba yaron,suka ga Kaya iya Kaya Saratu tana daga musu tana cewa Kudirar Allah ta sauka a kauyen nan idan da hankali ya Isa izina,Rabi yanzu tafi karfin mota sai dai yawo a jirgi, Gwaggo hassada ta motsa kasa karasa gani Suka yi harda cewa komai sai anyi karya ai Zamanin nan ba lefen ba ciyarwar shine aikin,Mairo tace uhmm ayi mu gani Suka juya Suka fice,Mami Murmushi tayi tace sune Suka rike Rabiah lallai dole taci wahala, da Yamma Suka koma a jirgi aka bar lefen a dakin Inna.
Dagaci sabo da bakin cikin Jin labarin ya nemi Yara Yan daba ya biyasu kudi yace suje cikin dare su zarewa Inna wuka su sato Masa kayan lefen tas,Kamar Inna ta sani a daren tasa Jangudo yazo da yaransa maza samari Suka kwashe lefen tas aka maida gidansa,tana bacci cikin dare sai gasu sun banko kofarta dama bata rufe ba,makamai Suka zare Mata,Inna ta saki Salati tana hawaye suka ce Ina lefen da aka kawo wani ya shaki wuyanta,Inna ta rafka salati tace ai sun koma da abinsu inda Amarya take me za a bar lefe a nan ayi da shi,ku duba dakin,dakin gaba Daya Suka caje ba komai sakinta suka yi Suka koma a daren suka sanarwa Dagaci Suka Kara gaba abinsu.

  Kayana da ango duk mun dinka na fitar biki kaf, ba Wanda yasan ana biki a gidan Baffa sai Mami sai Baffa,yau ta Kama ranar dinner tunda aka sa bikin banga Nawwar ba komai Khaleel yake aikowa,ya Sha tsiya wajen Khaleel Kawai share shi yake yi, itama Sufia tace ai Dole nabi Mijina Khaleel musha kallon bikin Yan bariki dole akwai show,yace ai komai shigar dai hausawa za ayi inda kisan kina Kano, ranar 8pm za a fara sabo da haka wajen make up kowa cikinmu da inda ya tafi, nikam tawa inda sai wane da wane ke zuwa nan naje Wanda Ango ne ya biya,su Sera suna can tasu,abinka da masu samari kala kala dukkan matan kusan kowacce ta karbo shegiyar mota a wajen samarinsu,mota ce da mota ke tashi sai wadda ka gani,har wasu masu abota da yaran masu kudi duk an gayyato su sunyi anko Kuma Yan Mata na kece raini ba a magana Sabo da masu kawaye ma sun gayyace su, Kai kace bikin wata Yar wani ce da, waje ya hadu dama na manya ne, 8:30pm an gama min make up, munsha kayan namu Kalar decoration din wajen da aka yi Fari da dark pink sai Silver gaba Daya wajen walwali yake, ni rigar Amaryar tawa gown ce daga kasar waje yayi order online dark pink tana Jan kasa daga baya,sama ta kamani me dogon Hannu Net,sai gogoron da aka daura min Silver da takalmi da jaka silver Kalar shaddar jikinsa,hularsa da takalminsa duk Kalar shaddarsa Yar gaske an Masa babbar riga ta matasa dai dai shi, Khaleel ke driving dinsa a bayan sabuwar motarsa ta bugawa a news fara duk ta Sha adon flower da zare pink kana gani kasan ta Amarya da ango ce, daga wajen makeup din na fito wacce ta min ta rike min kasan rigar har motar na shiga ta rufe tana mana murna Khaleel yaja Muka wuce,hannuna wata a layinmu bahaushiya ta iya lalle tana yiwa hausawa karuwai, ita ta zana min ta gani ta fada ja da baki hannu da kafa nayi kyau abin ba a cewa komai, Khaleel yace Amarya kinyi kyau sosai wlh dama me kyau ce,nace na gode Friend

   Nawwar yace mu ganki na juyo sosai harda fari na lumshe Ido dan Wai yaga gashin idon da aka saka min sosai, hannayena da ya Sha lalle da abin hannu na amare na daga Masa ya gani na juya Masa tafin hannun ya gani,Khaleel yace kaiiiiii gaskiya lallen yayi,Nawwar yace Wai mene haka bana son munafunci,dariya yayi yace to sai ka bari a daura sai mu daina fada amma yanzu bata zama taka ba,Murmushi nayi na zare takalmin kafata tare da dago kafar daya nace ka gani, Khaleel ya leko da Kansa ya maida Kansa wajen tuki,Nawwar yace Allah ya kyauta maka Khaleel,kafar ya gani tayi kyau yace good, maidata dan Allah kin dameni,sai da na maidata yace muga hannun naki na Miko na dama,yace na hagu,na Miko masa hannunsa yasa a aljihu ya saka ya zaro gidan zobe ya bude naga zoben gold me tsada Dan karami hannuna ya rike ya saka min zoben a yatsana na kusa da karamin yatsan da kyar ya shiga yayi min cif cif,na washe baki nace yayi kyau thanks gidan zoben ya saka min a jaka tare da kudin liki masu yawa Yan dubu dubu sababbi,Khaleel yace gulmamme abinda kakeyi kenan,Bai kulashi ba, tun kafin mu karasa wajen event din muke jin kida na tashi Kamar hauka Yan gayu ana ta Shiga Su Sera Amarya suke jira suna waje wajen su goma sauran Kuwa an gama cika ana cashewa rawa suke ta rashin kunya ta fitsara Amma da aji ake yinta ba hauka ba yau ranar nutsuwace da yanga da aji, Yar zabil tana ciki itace MC ma,akwai wasu masu rawa a gidan karuwai ba rawar da basa Yi Mata da maza Yan rawar Solo ne ai kuwa sune suke takawa gwanin nishadi ana ta kallo suna mimimg wakokin hausa, a ciki Mc tayi magana da turanci Amarya da ango sun iso tayi da hausa kuma,kowa Zama yayi aka nutsu, mu Kuma muna mota me camera ya Mana pics iya Amarya da ango,Muka fito aka Yi mana harda frnds a wajen sannan a waje abokan ango sunfi su goma ga Mata kawayena Sufia ma tana cikin ayari mun gaisa da ita,Fara tafiya mukayi zamu shiga ango ya rike min hannu, Sera da wise suke rike min riga ta baya,Muna zuwa bakin kofa aka canja kidan Amarya da Ango muna tafiya ana fesa Mana snow da golden burzer kanana har sit dinmu na musamman.

    Dinner ta Matukar kayatar duk da an zubar da daraja a wajen amma yanda muka tsara anyi abin da iyawa a tsari da birgewa kowa zaice wayewa ce tayi yawa a wajen, anci an Sha an zubar da liki,Ango har daloli ya lika ana ta sawa a tiktok da sauran media, Allah yasa Sabreen tana ta bacci Jamcy ta watso Mata pics da videos Amma tana ta baccin asara ta kashe wayar gaba daya an Sha kwaya, sai da aka gama Dinner angwaye a guess house dinsa aka sauke su komai a gidan Su Khaleel akayi Mami ma tana can duk da ba Wanda ya sani.

    Washe gari Sunday Muka Yi Shirin tafiya Kano kauyen mu ai a ranar da yawanmu Mata munfi ashirin Muka dira a kauyen ango ya biya jirgi Muka zo Kano Muka shigo a taxi, angwaye sai da safe zasu zo a jirgi su ma da Iyayen Ango,Sabreen an manta da waya ana ta bacci in ta tashi ma wanka take taci abinci tayi Sallar da Zata iya ta koma bacci,gamu iya karuwan da yawan mu Muka dira Wise tace dole Dagaci yasan mun shigo gari.

 

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               56-60

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Khadija Dandume
Mrs Mukhtar
Maman Afrah Ik
Fairdausi m Sani oum Meenal
Mrs Aminullah
A’eesha
Aisha S Maibankeey
Mom Islam
Khadeeja Sageer(Umee)

Gaisuwa gareki
Aida Maman Tasnim

     Anga rida ridan yan Mata ai ni yarinya nake tashi cikinsu,damasu Dj dinmu Muka dira speakers manya manya sun Kai goma Sha biyu kida suke badawa kamar zasu fasa gari,Inna har Yan matan kauyen ta rabawa alawa, dama mu mun Saba ba abinda ya dame mu da Kauye katon dakin  da Inna ta gyara ta bamu Muka baje dayan dakin Kuma kayanmu Muka ajiye,sai da Muka tsara komai akan ba shaye shaye duk me Shan wani abu tayi hakuri zuwa kwana daya, Yan matan Kauye kasa zuwa cikinmu suka Yi dama Yara ne gidan Dagaci ne Kawai da Mairo ita Kuma Bata zo ba, komai mun siya na abinci, tun kafin muzo na turawa Bala kudin ya siyo ya Kai gidan Inna,Wani abin Kuma da abinmu Muka zo,amma Muna zuwa Inna da matar Jangudo an dafa Mana shinkafa da miyar,salat Kawai Muka yanka Muka ci Muka barta ga lemukan biki Muna ta sha,akwai abincin Kuma da Muka bayar a cikin birnin Kano za ayi Mana fried rice sai waina da miya,alala,da tuwon shinkafa miyar Agushi har na angwaye su fried rice ce da pepper  chicken sai waina da miya, har fura mun bada ayi ta Yan gayu munyi order duk kudin Nawwar ne Wanda ko waya bamu yi sai da dalili,Yara sun zo gidan Inna sun tsaya Mana a Kai suna kallo sabo da Muna zuwa duk kana nan Kaya Muka saka a jikinmu ko wacce sura a bankade wani yaro ne zai Kai 13yrs ya tsurawa Wise Ido sanye da half vest da dan guntun wando gashin nan yaji gyara gata itama fara Kuma ta Kara da Mai tayi Kal Kal,wise ta kalli yaron ta Mika Hannu wuf ta kamo shi tace Dan ubanka zo na baka nono ka sha,ihu ya saka zaiyi kuka yana wutsil wutsil tace ai sai ka Sha nono shegen yaro ka tsura min ido,zuwa nayi Ina dariya na kwace shi ya fice da gudu, Star tace gobe fa sai an kawo Mana motoci biyu sabo da zirga zirga,nace karku damu za a kawo ai na fadawa Ango yace Already an kawo motocin ma har Wanda zasu kwaso angwaye daga airport Kun San Yana da mutane a nan, Inna kuwa da makwafta suna ta Shirin abincin da zasu bawa Yan Kauye mutan kauyen, Bluetooth speaker muka kunna a gidan muna ta rawa,sai dare bayan munyi sallar Isha nace wai Mandula baza ta zo bane,kin manta a cikin Kano fa gidan kawarta ta zauna itace zata taho da abincin idan an hada,sai Kuma me Make up da zata taho da ita,nace ai sai ku fada min yanzu ita za a kaiwa mota? Sera tace ae mana nace ai to an huta ma mota daya tayi ko wacce zamuyi amfani da ita? Wise tace yeah ku tashi mu dan zaga garin Mana mu gani tunda gobe ba time,wasu Hijab Muka saka wasu abaya Muka fito kamar mutanen kirki dake da wutar nepa ko Ina haske ana ta hada hada a kauyen mun fito duk inda Muka yi sai kallo harrrrrr samari ana ta cacar baki,wani me tsaurin Ido Sani ya turo yaro wai Ya nuna Yar Zabil tazo,nace inji wa? yace Sani na gidan Sale me Alewa dariya nayi nace sisi baza ki samu ba ubansa ma Alawar Dinya Madi yake siyarwa,Yar Zabil tace kut ni a kauyen nan ai duk sai dai na aike su ta ja tsaki Kai muje,Sera tace Sani guy na taba tsinka Masa Mari tana Dariya.

    Gidan Dagaci Muka shiga nace a nan na girma,Dagaci suna tsakar gida suna gulmata na kawo karuwai, sai gamu da yawan mu mun shigo dama tsokana nazo ba gaishe su nazo Yi ba,Dagaci Yana ganinmu ya mike da masifa ku fitar min a gida Kar ku lalata min tarbiyyar iyali ku tafi can gayyar tsiya,Star ce ta kalle shi da hularsa tasa Hannu tayi fatali da hular Dagaci tayi fatali da ita na sa kafa na take hular, tace Kai dalla rufe mana baki,nace tunda ka Mana you must collect nayiwa kirjin Dagaci kwass na rankwashi kirjinsa ,yace kuyi abinda zakuyi shegu tambadaddu sai nasa hukuma ta Kamaku ,Malika ta furta da kuwa ka taro bala’i wallahi da sai na sa an kwace sarautarka karka cika Mana baki muke da masu fada a kasar nan,nace ni da kaina sai nayi maganinsa mark my words,Mairo ce ta mike tace iyyeee anje birni anyi clean an tsinci turanci a kwalta to wallahi ke baki Isa ba ke din banza banzaye karuwai an zo ana mana burg….Mari taji tas tas tas har uku tuni Wise ta Gama da ita,hawaye ta saki da kuka, Star tace kina sake magana wallahi sai mun tara Miki gajiya baki san waye mu ba,ta nuna Dagaci tace Kai Kuma Muna nan zuwa kanka yanzu gidanka Muka zo amma nan gaba zaka ji mu karka manta bama gaggawar daukan fansa, Azzalumi an baka amanar marainiya kaci tunda kaci amanar Rabiah you must see shege, Gwaggo ce ta taso da bala’i Yar Zabil taci kwalarta ta hankadeta ta fada Kan Aunty Amarya tace yanzu biki Muka zo zamu dawo Kun tabo bala’i sai mun hanaka Shan ruwa a garin nan wlh wannan Dagacin sai an kwace zaka ga masifa,na kalli Gwaggo na furta idan Gaji ta dawo kuce ta shirya nace muje dan Allah dama kawoku nayi mu isar da sako,Wise ta dinga foli foli da tukane da kwanika a gidan da kafa,na nuna Dagaci nace dan gyatimarka akan na hanaka local government dina cikin dare kake zuwa gabanka a dage ya kalli samaniya kana rokata na baka hadin Kai shine kuka min sharri kuka bata min suna wallahi Allah sai ya bimin hakkina Kuma sai na ci takashin uwarku Dan me dirkawa uwarka ciki Ina bala’i harda hawaye naci gaba me chemist din da kuka sa ya rubuta Ina da ciki sai Kun karyata kanku na karasa Gaban Gwaggo da Amarya nace sai kun bada sheda a gaban kowa kafin ku bayar a lahira,Aunty Amarya na tugewa dankwali na wullar da shi nace ubanki ne yayi min cikin Yar gidan Ubale me tsire,ubanki Ubale shine ya min cikin? Aunty Amarya ta mike ita ga marar kunya nace wallahi kina magana sai nayi tsirara naci ubanki a nan sai na miki tsirara,komawa tayi baya tayi mukus,Gwaggo ta mike ta cakumoni nace ku barni da ita na dauki Gwaggo dama ba kiba nayi sama da ita na watsota waje Dagaci ya kasa motsi bai taba ganin jaraba irin wannan ba,Mero ta fito tana zagina Sera ta kamata ta dinga jibgarta Kamar ta samu jaka,Gwaggo ta mike ta rukuma kokawa dani ita ga Yar bala’i tana cewa Yar tsuntuwa Yar cikin Shege

   Dama munzo da Santana mutane da makwafta an cika ana kallo,Santana ya falfalo Yana ihu ya dora Hannu a ka Yana cewa na shiga Uku za a kashe Mana Yar uwa Yana gyara daurin zaninsa a saman Jallabiya ya kalli Su Wise yace kun tsaya za a kashe Mana Yar uwa ya dakko dutse wani Dan karami Yana yarfe Hannu Yana furta wash nauyi ya jefawa Gwaggo a hankali ya rike hannunsa da sauri Yana fari Yana karairaya ya furta na Shiga Uku zata min illa hannuna wooo, su Wise ne Suka hadarwa Gwaggo Muka lakada Mata duka,wasu Kuma Suka tafi wajen Aunty Amarya ta fada dakinta tana ihu Suka bita ciki Santana yace ko karkashin gado ta shiga ku kamota,Dagaci abin yafi karfinsa yasan shi kanshi Yana magana Karuwan zasu ci ubansa,Santana Yana ta ihu Yana Karuwai in action wlh an taro Barcelona da Madrid Dole a caskale wuuuuuu yau ana batakashi da kyar makwafta Suka kwaci Gwaggo Amma duk da haka zage zage take tana haki,Aunty Amarya suna fitowa ta sawa dakinta key,Dagaci Kansa buya yayi a dakinsa yaga shima zamu iya dukansa, mu kuwa ficewa Muka yi mun Gama kullawa dagaci yanzu kam,Dagaci yace ayi auren mu gani idan Zaki ji dadinsa gobe Kuma iya yina saina rusa auren nan kwafa ya ja ya tafi Yana lallashin matansa,Mero ta fara kuri tace ai sun tafi da su tsaya Mana su gani Ina ma Gaji tana nan yau da sai dai a mutu.

     Sai da Muka gama yawonmu sannan Muka koma gida 11pm Muka kwanta bacci, a ranar Mairo ta Kira Gaji ta fada Mata abinda muka Yi musu,ita ga yar masifa tace gobe da wuri zanzo zasu ga inda ake masifa. washe gari tea Muka Sha harda harda kwai aka soya Mana duk kudi Muka bada aka siya, su Inna sun gama tuwon daurin aure da akeyi a kauyen tuwon danyar shinkafa miyar taushe duk an kwashe a Leda an adana a manyan cooler, 11:30am ne daurin auren,sabo da haka 11am angwaye Suka zo,duk munyi wanka ko wacce ta saka sabon kayan data dinka na kece raini Malika ta iya make up itace ke musu tana musu dauri,ni kuwa Amarya tsadajjen leshi na saka white and golden takalmina golden da jakata da mayafina,wata gown aka dinka min fitted amma a tsakiya an yanke rabi anbi wajen da adon abu,ta gaba sai kace riga da skert ne amma ta baya kuma fitted gown ce nayi mugun kyau, dake mulmul nake dai dai dani ga mazaunai manya sai na fito wata Queen,Mandula ce tayi parking da mota a gaban angwaye dake sanye cikin manyan shaddoji abokan ango da Yan uwan Baffa na can maiduguri da shi Kansa Baffan suna cikin hadaddiyar mota Baffa Kamar ya fasa ihu Yana ta kunci dansa zai auri bare marar asali Kuma ga Kauye ma abin ta ko Ina ba kyau, Nawwar da rukunin abokansa sun Kai su ashirin da wani abu harda Auta Nawaf kanin Nawwar, ango ya sha wata farar shadda da babbar riga ta zamani ya coka Yar hula kalar takalminsa farare komai fari,motar ma da aka dakko shi daga airport Fara,irin kyan da ya zuba ba a cewa komai kowa shi yake kallo a wajen,Ni Kam me Make up tana ta tsarani tsaf,Mandula ce ta murzo motar da Nawwar yasa aka Kai Mata a cikin birnin Kano taci wankanta itama cikin wani danyen material peach ta Sha make up light,takalminta me tsini ta fito gasu dama da kibarsu ba rammiya sakamakon supplement na yanzu da Mata ke dannawa cikinsu,Fitowa tayi tare da bude bayan motar komai an shirya shi na musamman take away dinmu ma da aka zuba abincin na daban ne,har lemuka duk an zuba a jakar take away din,su Sera ne Suka fito Suka tayata shigar da kayan ciki,ta Kira Khaleel ya bude bayan motarsa ta zuba musu nasu abincin na angwaye,aka bude mota Daya cikin na Iyayen Ango aka basu nasu da yawa, Suma aka ware nasu aka saka musu a mota sai da Mandula ta sallami kowa Saura na Yan daurin aure mutan kauye za a karasa basu,sun ware nasu Dana bakin su,tana gamawa ta kulle motar ta tako zata wuce Nawwar tace ango tana Murmushi yace sannunki kirjin biki,Auta ne yazo da sauri yace Ina Amaryar Yaya,Nawwar yace ga kawarta nan bita ta kaika wajenta,Mandula ta rike hannun Auta,tace ya sunanka yace shi Auta Kawai ake fada masa tace to,ya zama dan saurayi suka shiga gidan da shi, Kawai yaga Yan Mata iya Yan manta ya rasa wace Amaryar ma, an Gama kwalliya dauri ake min Yana ganina yace wannan ce ma amaryar naga tafi kowa,gabana ya tsaya Ina ganinsa na gane kanin ango ne domin sunyi kama,yace Amarya nace Auta ne naji ai Mami tana zancen Autanta yace ai duk tafi so na,nayi dariya yace yunwa nake ji Aunty,nace a bashi abinci ya zabi waina da miya yaci yasha lemo da ruwa yaci ya koshi yace anjima zanci fried rice nace to Allah ya kaimu,masallaci ana shirye shiryen daurin aure Dagaci yazo aka nuna Masa uban Ango da Ango Kansa

    Bakin ciki ya kusa kashe shi yace da gaske masu kudi ne ai larabawa ne cab ai sai yaje wajen Baffa ya Mika Masa hannu Suka gaisa yace bawan Allah mutum me Kamala irinka ka yarda danka ya auri Yar tsuntuwa tsintarta fa akayi,Baffa a ransa yace wallahi nima dole ce ta sa,amma a fili sai yace ae ai mun sani ita Yar tsuntuwa ba mutum bace? Iyaye ne suka haife ta sabo da Haka yaro Yana so Allah ya nufa wa ya Isa ya ja da ikon Allah,jikin Dagaci yayi sanyi matuka yace Babu riba Kawai na koma wajen malamina yafi min a daura kawai sabo da bacin rai zamewa yayi bazai ji an daura a gabansa ba ya koma gida,Liman sai Neman Dagaci yake a matsayinsa na Babba a gari Kuma Wanda ya rike yarinya amma an neme shi an rasa ashe dan kar ma aje nemansa gona ya tafi ya samu bishiya yayi shimfida ya kwanta Yana bacci abinsa.

    Mutanen garin sunyi Kara sun cika kamar kasa cikar da ba’a taba Yi ba a garin a daurin auren wata sai akan Yar tsuntuwa kaf garin nafi kowa tara dan Adam,wasu ma kallo ya kawo su,dubban jama’a ne Suka sheda daurin Auren Rabiah ta daina amfani da sunan Dagaci a matsayin Uba tuni ta koma Rabiah Muhammad Nawwar tunda bata da kowa a duniya ta zabi Muhammad Nawwar,Jin sunan da Liman ya kira ya sa Nawwar Jin dadi harda sunansa a sunanta Rabiah Muhammad Nawwar,shi Kuma Nawwar Ibrahim, Baffa shine waliyyin Amarya,Nawwar ya karbi Aurensa yanda yace babu Kara,ga masu uban Dj sun shirya tsaf,Sadakina dubu dari biyu,Jangudo da yaransa su Suka dinga raba goro a wajen da alawa sannan suka fitar musu da abinci tuwon da su Inna sukayi,Fitowa mukayi gaba daya kallo ya dawo kanmu,Nawwar ya tsaya a gabana nace to an daura? ya furta uhm,Nan aka Fara zuba ruwan pics ta ko Ina wayoyi ne ke tashi,ana haka me Dj suka saki ganga kida Kamar zai fasa kunnen mutane, Wise ce ta fara bude rawa a gaban dattijai Yan daurin aure Basu watse ba ta fara takawa kowa ita yake kallo,Abokan ango an baza Ido ana kallo wani Sabeer a cikinsu yace wannan tsagera ce ta kirki,Murmushi muka Yi mun San bai ga komai ba,Kafin mu rufe baki Malika taje tana mata liki farrrrrrrr da Yan dari dari tana gamawa tabi sahu tana cashewa,dariya ta Kama angwaye dan Kuwa Malika gwana ce a rawa yanda ta duka ta tana wargaza mazaunai tab,Wasu su Sera Suma suka shige suna zuba liki suna rawa,Angwaye ai sai Suka gyara tsaiwa Suka ce sun fasa tafiya yanzu Suka fito da take away dinsu,fararen kujerun da Muka aro haya aka jera musu da yawa Suka zauna a gaba sauran Yan kallo Mata da maza suna baya mu Kuwa iya kawaye Muna ciki,Mc yace Amarya kadai ake son gani a fili ai Nawwar yasan ya Zama dole nayi rawar nan ya sani ma shi yasa Bai ce ma komai ba.

      Duk fili suka bani na shiga aka canja min kida tun Ina Yi kadan kida Yana ratsani na karbi speaker nace Ango ka yafe min Zan tsokani shari’a da Speaker a hannu nake rawar Ina Jin kunya Wai a haka amma yanda nake Cashewa,Auta kanin Nawwar ya shigo Yana min liki hannayensa na rike da hannayena biyu Muna facing juna a haka muna rawa kasa ai Kuwa kawaye Suka rufe ni da ruwan Naira Dj yana caskar kudi,suna fita Angwaye Suka shigo Kai an zubar da Naira Kan uba,gajiya nayi na fita sabo da make up dina,Nawwar ko daya bai ma tashi ba tukun yace zaiyi nasa, Kawayene Suka shiga su Uku Malika da Wise tare da Manduwa yau ana Shan kallo Yan kauyen sai ihu suke ana kallon iya shege karara a haka ma munyi da sauki,suna fita aka Kira Ango da Amarya Muka mike muka shiga sabo da iyayin Nawwar Wai a filin rawar za a sa Masa kujera kamar wani sarki ya zauna a tsakiyar wajen Yana Shan ruwan roba,ni kuwa rawata na dinga yin cin koshi ka rantse ba Amaryar bace,mikewa yayi ya dinga zuba min ruwan Yan dubu dubu, ana ta dauka a wayayi,Sera ce tazo ta min rada kuyi kiss zamu dauka a waya nace bazai yarda ba,sai kace ba mace ba ai karuwancin Zaki tuna,dariya nayi Ina dan takawa yana min liki,na dora hannuna daya a kafadarsa na maida dayan ma a kafadar na dora yace ta ya Zan Miki likin Wai bakya Jin kunyar mutane ne fa abokaina zasu ce baki da tarbiyya nace sai yanzu suka sani kiss zamuyi dauka za ayi zai zame nace Allah kana guduwa sai na kunyataka a wajen nan ka sanni, ai Kai kace kaji ka gani ka aureni, mu bama Jin magana ka bani hadin kai,yace to kiyi sauri na gaji,Yatsa na dagawa su saira su dauka haushina yaji Yana ta fada bai Dace ba wannan a musulunci Wanda yanzu ya Zama ruwan dare mutane da yaran masu kudi gani suke birgewa ce wayewa ce,a hankali nace kaine fa zaka min Ido ya zaro tare da furta na shiga Uku nidai,please  karka kunyata ni Zan kunyataka wallahi, Ido ya rufe aka canja slow music a hankali na dora bakina a saman nasa ya min kiss a nutse ana dauka na rungume shi sai aka dauki tafi da ihu yeeeeeeee Yan kauyen Suka Fara cewa yeee ya tsotsi bakinta alquran,billahillazi bakinta ya lasa kunga sun rungume da gani sun Saba tun a waje,Yan matan kauyen shewa Suka dauka yau Muna ganin bariki yehoho ahayye chasss…,Khaleel bai taba zaton abokinsa ya fetse haka ba sai yau dariya ya dinga yi, sai da Muka gama likawa juna kudi Yana min Ina Masa sannan Muka fita,Khaleel yace Lover boy,Nawwar ya hade rai tare da Zama,abokai su abin ya birge su sosai dama duk gasu Yan gayu yaran masu kudi,Wise bata gajiya sake shiga tayi tana yiwa kanta da kanta liki tana cashewa,Autan su Nawwar yaga duwawuka sai tsalle suke yace wow ya radawa Nawwar irin wannan Zan Aura nima Yaya idan na girma da wuri za a min aure,Nawwar yayi dariya a ransa a fili yace sai kaci ubanka wlh ni ban San ma ya akayi ka biyo mu ba,Mami ce tace nazo yaci gaba da cewa Auren Kauye za a min da wuri ni wallahi ba sai na girma ba,na daina kula Yan class dinmu wajen Aunty Rabiah zanzo ta hadani da kawarta,Nawwar yace sai na zaneka bari mu koma gida tunda baka kunya,Shuru yayi bai sai sake magana amma ya zurawa Mata ido.

    A wajen muma muke cin take away dinmu har Yan Kauye Suma sun samu da yawa sun samu, tare zamu tarkata da angwaye mu koma can Anambra, duk munfi yin rawar wakokin Yan kudu su Muka iya Kamar kannen Naira merly, 2pm aka tafi Sallah wanka Muka sake tare da canja Kaya wannan karon ba make up Kawai dauri mukayi kowa tayi wacce zata iya, muka fito na sha shadda dark purple nayi kyau, su Kuma ankon Atamfa Suka saka me kyau sunyi kyau daga nan aka dora da kida da rawa tare da sabon liki, babu Wanda zai so ya bar wajen nan,sai lokacin muka raba waina da miya aka sake ci da ruwa da lemo, bamu Ankara ba har 5:30pm sai Inna ce tazo tace Yan Kai Amarya sun shirya,sannan Muka tashi daga kida,masu kida Suka hada kayansu da motarsu suka tafi abinsu suna murna sun Sha kudi.
A gurguje nayi wanka sabo da zafi na canja cikin Net less fari yasha hadadden dinki na Sha takalmi da jaka fari aka min dauri na yafa mayafi me kyau fari da adon silver,turaruka na shafa Wanda kayana komai an tattara su tuni sunyi gaba  Angwayen da Suka Fara tafiya su aka bawa Suka tafi da komai dama kayan lefe ne, Wanda na cire Kuma Sera ta ninke ta tattara komai a jakata da na zubo kayan sawa na biki suna wajenta tsinke namu bamu bari ba, Jangudo ne yace tunda Kai Amaryar ba addini bane iya kawayen ma sun Isa ga angwaye ai sun Isa Kai Amaryar

    Ba sai an sake wahalar da Ango ba Watarana idan ta haihu sai aje Mata,Inna tace hakan ma shawara ce shike nan aka fasa a Raina nace da ace Ina da iyaye Dole sai an rakani dakin miji amma ya zanyi haka Allah ya tsara min wannan yasa zuciyata ta karye na fashe da kuka,duk sun zaci kukan Kai Amarya nakeyi Suka dinga dariya Yar bariki da kuka za a kaita dakin miji  suna ta tsokanata, Nawwar ganin Ina kuka dariya ta Kama shi yace Amma Yarinyar nan ba karamar Yar rainin hankali bace lallai Ina ganin Yar duniya,ki gama  tikar rawa gata dama zaman kanta takeyi ta Gama sanin da Namiji me yayi Saura.

   Muna jikin Motar da Ango yake tsaye mu da kawayena kaf Inna tana cewa Allah ya tsare kinji Allah ya kade fitina,a zauna lafiya kinji dai nasiha ta to Allah ya bada sa’a ya bada zuria dayyiba na manta ma kuka nakeyi nace Ameen Ameen Allah ya bani me hankali,Inna sai da tayi dariya da su Star ana ta dariya har angwaye, Inna tace aure sai hakuri kiyi hakuri da mijinki komai yace to banda musu da gardama da taurin Kai,ba a jayayya da miji,Miji yafi Gaban Wasa,Nawwar Yana gefe yace dama ta rainani Kuwa Inna,Inna tace wallahi idan kina so ki gama da duniya lafiya kibi Allah kibi mijinki yanzu ba da bane baki da kamarsa,yanzu mulkinki ya Kare shi zai haye karaga shi zai Fara nasa mulkin sai yanda yayi dake,Nawwar yace ai tuni ma na fara Inna,Inna tace lokacinka ne banga laifinka ba dan nan kayi abinka,Amma mace dai ki sani Rabi bata da wani yanci Matukar a gidan miji take,ta kalli Nawwar tace wallahi kai Kuma idan ka zalunci marainiya ubanka zaka ci a wajen Allah yo Allah ba ruwansa,ka kula da ita ka Zama gatanta ka Zama mijin marainiya,kaga Allah Kai ya damkawa amanarta Amana fa aka baka banda banbanci tsakanin matanka ka kamanta adalci, Kar kaji Daya tafi daya iya kwanciyar aure ka wulakanta daya,su Star suka kaure da shewa, Nawwar ya kalli Inna da sauri,Inna tace ae zaka zuba min Ido ku maza imaninku a nan yake da kunji ba bayani to mutunci ya Kare abinda kuka iya kenan soyayyarku kwanciya da mace ba uwar da kuka iya a nan kuka iya soyayya musamman hausawa sai a lokacin za a fara Ina sonki bani da kamarki,kece gwanata,jarumata,dausayin raina, kece tekun zuciyata,ya turmin dakan dake lugude a zuciyata  Nawwar ya sheke da dariyar da bai shirya ba,kowa dake wajen motar dariya yake su Seraline harda ihu,Inna tace yo ai mun sani muma zamaninmu munyi soyayyar nan tsiyar maza wacce ce bamu gani ba,sai kana haihuwa shike nan an juya ma baya sabuwa ake nema Allah yasa kai a kudu kake Allah yasa dai ka koyi halin arziki,dariya na dinga Yi a boye cikin mayafi,Nawwar ma Dariya ta kume shi Khaleel dake Gaban mota da Driver sai dariya suke Kamar ba gobe,Nawwar yace mun gode Inna za a kiyaye,Inna ta furta ato kun girma dai idan Kun gyara ruwanku idan baku gyara ba ruwanku Inna tana gida tana baccinta.

    Zamu Shiga mota tace ban Gama ba ke Rabi na sanki da zafi yanzu ba a wa miji Fushi,ba Kuma a juyawa miji baya ke gaki Allah ya albarkace ki da Ido kamar Madara ki dinga sanyaya Masa zuciya da kallo,ke bakisan da kallo ma idan mace ta Isa sai tayi juya Miji ba,Nawwar Yana ta dariya yace banda ni Inna,Inna tace wane mutum karya kake yaro baka hadu da tsohon Hannu bane mu irinmu muka sa Namiji a gaba ai ya shiga Uku,Muka sake kwashewa da dariya kaji tsohuwa wa zai kalleta ma harda yabon kai, Rabi nace Na’am tace kuka bazai fishshe ki ba sai kin tashi sosai gidan kishiya zaki, ba a kishin fada,duka ko zagi gasa ake a wajen me gida,idan ta bashi Onga Kinga kayan Miya ne dai ko to karki sake kuyi abu iri daya a’a ke karki bashi Onga ki bashi Madara,Idan ta bashi Milo ke ki bashi farfesu,haka akeyin tsere  Nawwar kunya ta kamasu Ni Kuwa ko a jikina nace to Inna tace yawwa dare nayi kuje sai munyi waya,muka shiga mota kowa ya shiga Driver yaja mota dariya Kawai muke Yi Kamar me,Allah sarki Inna na bata Atamfa da leshi da sabulai cikin kayan lefena,sannan na bata kudi su Wise ma sun bata kudi akwai dadin Zama.

     Sauran duk sun rigamu zuwa airport muna zuwa dama jirgi na kasa Muka shiga da kayan mu Nan ma an Mana pics duk an watsa a media,har Muka sauka lafiya na Kira Inna nace mun sauka ta Mana fatan Alheri na rufa mayafina a Kai Amarya sosai,Mami da kawayenta su Uku da Maman Khaleel da Sufia a Airport suka tarbemu cikin shigar su ta Alfarma, sauran abokan Ango da Ango bayan an sake pics suka tafi kowa sai Khaleel da Nawwar Suka shiga mota driver ya ja su zuwa gidan Khaleel can suka Yi wanka a part dinsa Suka canja Kaya sannan suka Yi Sallar magriba da Isha suka zauna suna kallon pics suna Hira da labarin irin dadin da bikin yayi.

    Mu kuwa Mami tana gefe na a mota da sauran kawayena a wasu morocin Muka nufi gidan Sabreen,Mami a mota tana ta min Nasiha sosai akan zaman aure karshe tace dan Allah ki kiyaye ki farantawa Nawwar shima ya samu farin cikin da duk wani da Namiji ke samu karki biyewa rudun duniya da kawaye ki kula da aurenki ba abin Wasa bane shine darajar duk wata mace, rayuwar waje da Kika Yi wannan ya wuce da ba yanzu bane a manta da waccen rayuwar a Kama wannan kinji Rabiah dan Allah kiyi hakuri da halin kowa ku zauna lafiya,Kar naji ba daidai ba,nace Inshaallah,Mami tace ke ba yarinya bace Rabia kin San komai a kiyaye,Nawwar ya nuna Miki gatan da ba kowane zai iya ba,nace na sani Mami karki damu Inshaallah tace yawwa Yar Albarka Allah ya muku Albarka a haka Muka karasa gidan an canja tsarinsa gaba daya komai anyi sabo abin ya bada citta, Sabreen ta tashi a bacci tayi wanka ta fito Palo tana kallon furniture din da aka canja komai na gidan an canja an gyara ko Ina Yana kamshi mamaki ya kamata tace nasan dai anyiwa gidan nan gyara to waye yayi shara da mopping ko Ina na kamshi,wayarta ta tuna da ta kashe yau kwana kusan biyu bata tuna kowa lokacin ta sha kwaya da yawa,wayarta ta kunna ta kunna Data ta shiga WhatsApp Kawai taga wasu duk sun cire status din wasu sun saka bikin sabo da an kashe kudi musamman Dinner din,taga pics farrrr jamcy ta turo da videos ta bude nan ma Nawwar ta gani da Rabiah da kawayenta kamar ango da amarya,Pics din maza ta gani a masallaci alamar wajen daurin aure,sai ga pics din Amarya da ango a wajen daurin aure ga kawaye sai rawar Dj,tana bude wani taga Nawwar yayiwa Rabi Kiss a filin rawa suna ruwan kudi an ci uwar Naira,ihu ta saki tare da mikewa tsaye Zumbur tace na shiga Uku na,guda taji a gidan motoci suna ta shigowa,da gudu ta fada dakinta ta cire atamfar da ta saka ta canja Riga da wando tace yau za a kwashi bala’i kafin na sanar da Baffa da Iyamami,dama ba samu damar daukan Baffa a pics ba shi Yana daura aure ya fice ya bar kauyen daga nan ma kasar ya bari ya wuce US Dan karma a dame shi,yace wa Iyamami da Yan Uwa da matansa ya tafi Us su basu San ma daga wajen daurin aure ya wuce ba yayi haka ne Dan ace ai baya gari ma aka daura.

     Sabreen wuka ta dakko a kitchen ta rike tana huci Yan kawo Amarya Suka shigo Mami ce a gaba sai kawayenta da Kuma su Sera,ai Sabreen tana ganin gayyar su Sera sunfi ashirin suna guda suna cewa wata tara a zubo Mana twins,Wise tana shewa tace a bawa ango local government sosai,yau Ango zaiji banbanci ya samu GRA masu kirji fanko a ja baya,Allah ya taimaki ango an kawo masa me kirji a cike,Mami kunya ta kamasu gashi sunki yin Shuru sai fitsara suke suna cewa ayi magana mu naushi bakin mutum, da sauri Sabreen ta wayance wukar data dakko ta ajiye a Center table tace daga kitchen na fito Ina girki ashe kune ta juya salin alin ta maida wukar inda ta dakko,sai ta zagaye ta bayan kitchen ta fice waje tare da tare taxi ta fada motar ta bar gidan a million, tana fita a gidan ta fashe da kuka sai gidansu tana yiwa me taxi bala’i yayi sauri.

    Mami tace Sabreen fito Ina da magana da ku,Shuru shuru,Sera tace ta gudu fa ta bar gidan Naga fitarta,Mami tace Allah ya kyauta to,Sama aka haura da ni cikin hadadden dakina nima,sabo da a saman ma part uku ne,part din Nawwar,Nawa sai na Sabreen,kowa sai kallon gida yake ana yabawa,dukkan kayan lefena da tarkacen kayana har na gidan Karuwai da kayan gyaran jikina duk an kawo suna part dina su Misha su Muka bari tunda baza suje kauyen ba su suka shirya min komai na part dina har kayan Suka goge Suka gyara gidan ko Ina Kal Kal dama dakin ogan yasa key,Basu shiga part din Sabreen ba,sun Sha mamaki irin yanda suke karaf karaf a gidan amma bata tashi a bacci ba,ko Ina kamshi yake na musamman sunyi aiki babba na gyara gidan.

     A gefen bed dina na zauna komai nawa na dakin milk and brown ne,Ina zaune mayafi a kaina,sauran Suka ce to Amarya sai munzo nan da sati asha amarci lafiya,na dinga musu godiya Suka tafi,su Mami ma da Sufia tafiya sukayi ya rage daga ni sai Sera,Star da Wise,na cire mayafin Muna ta hirar bikin Muna kallon pics,nace in ya bari na siyi waya Zan tura please ,Sera tace wallahi Indai sun tabaki ki Kira mu,nace ya zama dole,ki kula sosai Kinga ta Fara daukan wuka Kar ta shammaceki cewar Wise Nace Allah dai ya tsare, Sallah nayi abina, Suka Shiga kitchen Suka Sha Madara da lemuka Suka dawo Muna zaune har 10pm sannan Suka min Sallama zasu tafi nace zanyi kuka karku tafi,Muka kwashe da dariya har ni, nace sai na biku ni Muna ta dariya,nace wayyo first night ya zanyi tsoro nake ji,Muka fito tare Muna ta dariya sai ga Sabreen ta dawo a compound ta ganmu har Amarya tace Yan bariki tayi ciki da gudu,shareta Muka yi Amarya ce da rakiya har waje kofar gida,Nawwar ne ya karaso da motarsa da mamaki glass ya sauke ya musu godiya sosai yace a fadawa sauran Yana godiya Suka ce zasu ji Suka Shige Napep din da Suka Kira sai gidan bariki, kirji na dafe nace Allah sarki Kwalta,Stree ohh duniya Ashawo work me Dadi da yanci ai Zan dawo ne soon ana sakina Zan dawo Yan Uwa Ina nan zuwa ba da dadewa ba nace bye bye Street Ina daga hannu,Nawwar Yana kallona Yana ji tunda a saitina yake glass dinsa a sauke yake,Kai ya girgiza yace in kin gama sai ki koma ko,ciki na shiga na koma dakina da sauri na rigashi shiga na zauna saman bed na jawo mayafina na rufe kaina zuwa fuskata na nutsu,ya shigo lokacin tsaki ya ja ya ajiye min ledata cike da nama da abin dadi,Daya ledar hannunsa dakin Sabreen ya nufa.

     Ya isketa ta dora Kai a jikin mudubi tana rusa uban kuka,shi dariya ma ta bashi yaushe ta Fara kishinsa,Kafadarta ya dafa tare da furta Babyna lafiya bai taba kiranta da Baby ba sai yau,mikewa tayi tsaye Zumbur tare  da daga masa Hannu tace dakata Malam me zaka ce dani zakayi aure ka fada min baza ka fada min ba sabo da cin amanarka sabo da zaka auri Karuwarka ai ka Dade kana cin Amanata tun kafin ayi aure ka Gama da ita dole ka boye min Kuma kaje gobe Iyamami tana nemanka,Murmushi yayi yace karki sake Kiran matata da karuwa ya Zama last idan ba haka ba Zaki ga abinda Zan Miki Kuma Iyamami ta Isa dani ne bazan je ba ki fada Mata kice nace baza a zo ba duk abinda zakiyi kiyi, aure kuma na kara ke kin Isa wace ke da sai na fada Miki tunda bacci Kika zaba kije ya isheki yaja tsaki tare da jefar mata ledar namanta ya fice abinsa.

    Part dinsa ya shiga ya kalli ko Ina kaca kaca duk dirty babu me gyara Masa shi kyankyaminsa ma yaji a haka yayi wanka ya fito ya shirya cikin kayan baccinsa ya kwanta sai bacci,ni kuwa ganin yaki shigowa na bude naci abinda zan iya na ajiye sauran nayi wanka da brush nayi Shirin bacci cikin gown Yar guntuwa ko cinya bata rufe ba peach nayi adduoi sannan na kwanta baccin gajiya ko farkawa banyi ba sai asuba,na tashi Ina saman Sallaya ya dawo daga masallaci ya bude kofata a hankali tare da lekowa ya ganni saman Sallaya juyawa yayi ya wuce abinsa ban ma San ya leko ba,part din Sabreen yaje ya duba tana ta bacci tashin duniya yayi taki tashi hakura yayi ya koma dakinsa ya koma baccinsa.

     8am na tashi na gyara ba garena Kal Kal Yana kamshi,fitowa nayi na gyara ko Ina har Palo dama ba dirty sabo da jiya an gyara,masu kula da compound sunyi nasu,part dinsa na shiga Yana bacci, toilet na fara wankewa sosai sai da ta dawo tana shining ko Ina,sannan na kunna turaren wutan na turiri Wanda ba hayaki yake ba da ruwa ake hadawa a kunna sai turiri Kawai, na fito a toilet na hau gyara Palon tunda na dawo palon ya farka a bacci amma bai nuna min ya tashi ba,gadon nasa na turawa na tura Yana Kai na kaishi gefe sai da na gyara side din sannan na dawo da shi inda yake dake ko waye akai kana danna Abu a jiki zai matsa da kansa,sai da nagama gyarawa shima dakin na hada turaren na turiri,na fesa room freshner me kamshin turaren wuta na, nazo na tattara kayansa kaf na koma toilet na zuba su a washing machine na wanke su tas naje na shanya a waje ta wajen garden,na dawo na iske ya shige toilet nace hmm ya tashi,haka na gyara bed din na canja bedsheet din sabo me kyau wancan na kwashe na kaiwa yaron gidan nace ya wanke a injin wanki idan sun bushe ya hada da kayan Nawwar dake shanye ya goge yace an gama.

     Kitchen na shiga bayan na Gama duk wani gyarana ko Ina sai kamshi, na gaji Kawai tea na dafa na soya dankalin turawa da kwai na kawo dining na shirya komai,na leka Zan kirashi na same shi Yana shafa lotion a bakin kofar nace na gama breakfast na koma dakina wanka nayi na shirya cikin atamfata super me tsada Riga da skert nayi kyau sosai Kamar zanje biki.

   Fitowa nayi na iske sai lokacin ma ya fito ya zauna a dining,Ina karasowa  na Masa gaisuwar Yan Jagaliya nace yane ya akayi ne? Kallona Kawai yayi na furta ina kwana ka tashi lafiya,ya amsa min da lafiya,sanye yake cikin kana nan Kaya wasu grey Riga da wando marasa nauyi,tea din na hada Masa na zuba Masa komai sannan na tura Masa gabansa,na hada nawa Ina Sha
Yana mamakina duk surutu na yau banyi magana ba bance komai ba,ya bude baki zaiyi magana wayata ta dauki ruri,Murmushi nayi na daga tare da cewa Seraline,tace Amarya ya aka kwana nace lafiya lau ku fa tace lafiya sumul,ya gajiyarku?sai godiya ya amarcin fa an Sha kauna buri ya cika ko ta furta murmush na saki   hade da dariya nace ae Kinga dake virgin ce da yanzu sai mun Zo gashi wannan dariyar baki Isa kinyi shi ba nace to ya za ayi,Ina ogan naku,Ogana dai ko, dariya Sera tayi tare da furta to ki gaida shi nace zai ji,Yana  zaune yana Shan tea nace Seraline tace a gaisheka Ina amsawa yace,ya na ganki yau haka haka? Mika nayi da hamma nace gajiya ce kawai,rawar da kuka Yi ma ta Isa ta sa muku ciwon jiki,nace mun Sha aiki fa mijin Sabreen,Murmushi yayi yace mijin Sabreen ko ,nace ae ai nata ne ni da nazo temporary,hakane ya furta,nace na bar Mata kwanana gaba daya har na bar gidan nan na bar mata, jiya na kwana daya Ina ta irgawa kwanakin barina gidan nan kaga dai jiya aka daura kwana daya kenan, yace ke kin Isa kice Wai kin bawa wata kwananki ni fa Kinga ba abinda zanyi dake Hajiya,nace ai na sani nima ba so nake kayi wani abu dani ba yawwa ehe,Sabreen ce ta fito ta Sha wanka cikin kana nan Kaya tayi kyau tana zuwa sabon salo kujera ta ja ta zauna itama tare da furta Ina kwana Sweetheart, shi Kansa mamaki yayi bata taba gaisar da shi ba,sabo da Kar ya disgata yace lfy,ta ja cup ta hada tea dankalin gabana tasa Hannu ta janye da kwai sabo da tsokana,ban kulata ba na daure na share, Tsaki ta ja Wanda ya jawo Nawwar ya kalleta ya kamata tana kallona tana hararata, tace Yar tsuntuwa ma an iya girki ko a barikin Kika koya? Ko da yake ance karuwai sun iya girki fa,gashi kinci Sa’a kin auri daduronki,Nawwar ya Mata wata uwar tsawa, Murmushi nayi nace kyaleta ai gaskiya ta fada,Yar tsuntuwa ce Karuwa a da amma yanzu Kuma matar Nawwar dadiro na, na auri mijinki yanda ya narka kudi ya aure ni ke ba haka aka Yi ba,kyauta aka bashi ke lika masa akayi baya so aka Masa auren zumunci,kasa rike shi Kika Yi ya fita daukan karuwa Kuma ya sameni ya makale min da Kansa ya gani yace yaji a haka Yana so na sabo da idan bani to rayuwarsa tana cikin garari,ke ai kishin banza kike tunda baki San ma mene aure ba, da wata ce ke jiya a gidan nan baza ta iya bacci ba yanda muke zunduma ihun dadi daren amarci na tabbata da bakiyi bacci ba jiya to yau gidanku zaki tafi amma kina ta shaye shaye taya zaki sani Yar kwaya,Yar giya Yar Coccaine irinki dama wanne zaman aure zaki iya ai sai bacci…ya Isa haka bana son shirme Nawwar ya fada cikin fushi,na daki table da hanuna nace badai haka take so ayi ba to mu zuba mu indai fada ne harda na siyarwa dan kutmar…Dan me……shut up ya rike Hannu yace muje bana son rashin hankali,Yana Jana Ina tirjewa Ina wutsil wutsil Ina furta Dan babanki Yusuf da Uwarki Zuwaira munafuka Wanda basu iya tarbiya ba sai naci….Jana yayi muka haura sama da ya gaji ma Ina faman tirjewa sai ya daukeni cak,Sabreen ta saki kuka tana furta yanzu ta zageni haka a banza uwata fa Zuwaira tace yanzu Ina magana ta nada min uban duk ko ta gayyato karuwai suyi min jina jina to zata ci ubanta wlh nasan yanda zanyi tunda a fili tafi karfina.

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

AsmaBaffa.
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                   61-65

Official

By
AsmaBaffa

 

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Haleemart Ameenu
Maman Zulaihat
Khadeedodo
Nererh
Nanah
Zainabgohe
Mmn Humaira
Saudat Safiyan Maman Inam
Amatullah Kamshi
Firdausi A Nagwaggo
Ummiauwalu72
Alhamdulillah

Injija ta gare ki
Ummulkhair
Mrs Chief

 

       Sullubewa nayi tare da tsayawa a gabansa Ina kallon Sabreen a kafar bene, Sabreen ta sandare a tsaye na bishi zamu hau sama na juyo nace kuma idan na ganki a part dina wallahi sai kin karba a jikinki,yanzu zamu shiga ciki Kuma kin San idan akace mace da Namiji sun kebe a daki kin san me zai faru,sannan a wannan harkar ta dadi na Saba ihu sosai,I like to shout well well,I like to cry well so Kar na ganki kusa da part dina lokacin Ina enjoying life dina, juyawa nayi Ina wasa da botin din rigar Nawwar nace Honey hoho My Baby, ka tuna na jiya irinsa nake so ai ban San da salon ba sai jiya ya bani sweet,hannunsa na rike nace muje local government kaikayi take naja hannunsa Muka Yi ciki mamaki yasa ya bini da kallo abin Nawa daure Masa Kai yake,Muna shiga part dinsa Sabreen ta rushe da kuka ta kifa kanta a table tana ta faman kuka,tashi tayi fuuuu tayi dakinta ta Sha kwayoyi ta fada bed sai bacci.

   Ni Kuwa Muna shiga bedroom dinsa na fashe da dariya na zauna a gefensa inda yake zaune nace nasan yanzu tana can tana kuka,ai mu ka fada Mana Daya sai mun fada maka goma bata San mu bane wajen fada ba a jayayya da Yan duniya, yace kinji dadi to? Nace sosai na fada saman bed dinsa Ina dariya Ina tsalle,karki lalata min gado,wuyansa na shako ya fado saman gadon ya kwace jikinsa nace yau baza kaje Office bane ka tashi ka tafi,yace ba inda zanje shike nan bazan huta ba,tunda ba amarci kake ba mene amfaninka ka tafi kawai,a gidana Wai ki dinga korata kin takura min fa,Hannu na na tura a rigata Ina Sosa gefen Boobs dina nace kurji ne ya fito taba kaji na rike hannunsa ya fisge abinsa Yana dariya yayi kwanciyarsa,nace kaje ka gaida Mami Wai mutum bazai fita ba,banza ya min nace ayi mace shike nan sai kace an auro kwarkwara sai dai a dinga kulani da rana dare ba nawa bane,dariya yayi ba shiri yace kin dameni wlh ki tafi ki bani waje,tashi nayi na fita ya bini da kallo tare da lumshe Ido bai sani ba bacci yayi gaba da shi,Nima kwanciya nayi a dakina sai bacci sai 12pm na tashi a gurguje na fada kitchen na shirya girkina lafiyayye sai 2:30 na gama komai na jera a dining naje nayi wanka dama nayi Sallah,leshi na zaba cikin kayan lefena maroon doguwar Riga ne dinkin manyan Mata na saka na fito Ina walkiya,Ina zama a dining naji ya shugo naga har yayi wanka ya canja cikin Jallabiya ashe masallaci yaje ya dawo, a palon ya zauna ya dauki remote,tashi nayi na tuna Izzarsa shi yasa na karasa kusa da shi na zauna a gefensa sannan a hankali nace abincin fa ko nan zan kawo

   Yace sai anjima,sabo da me? ya furta Kawai,nace a’a gaskiya ban yarda ba sai Mami taga ka rame tace laifina ne,a hankali ya juyo ya kalleni tare da cewa Wai ni yaro ne shike nan ban Isa nace a’a ba sai kin min musu,ka bari idan ka koma bangaren Uwar yaranka sai ka Mata wannan na furta tare da mikewa na jawo hannunsa,mikewa yayi  ya Isa dining nayi serving nasa Muka Fara cin abincinmu,Yana ta yanga nace idan baza ka iya ci ba nazo na baka a baki ni a wajena ba komai bane,Tsaki ya ja yana wani ci a hankali na taso na dawo gabansa na jawo kujera na zauna,Sai ga Sabreen ta fito itama ta Sha wankan shadda,ai ganinta da sauri na tsiri shafa Masa gashi,shi bai ma San ta shugo ba,nace  Babyna abincin yayi dadi ko,Sabreen ya gani sai lokaci ya gane abinda nake Yi sabo da itane ashe, Sabreen Tsaki ta ja tace mu bama Kai kanmu sai di azo a same mu a haka ma Muna yanga Mata masu aji kenan,nace ke kenan baki ji sunanki ba Sabreen ni Rabiah babu hadi,ga baya ga gaba dan Allah kalle shi baki ga ya Kara fresh ba? Girarsa na koma shafawa da yatsa nace ya samu me Nono kirjin ba faranti bane cika Masa hannaye sukeyi, Sabreen ta hayayyako da bala’i ya daka Mana tsawa Enough……nace zaren ba Kalar yadin bane shegiya Yar gidan Zuwaira me wagegen baki Kamar kofar gari ko ubanki Yusufa ya Isa ya kawo min walgi wlh kina bude baki sai na tashi na tafasa Miki jiki….tsawa ya min bana son shirme Shuru Muka yi yaja tsaki yaci gaba da cin abincinsa.

     Sumarsa naci gaba da shafa masa Ina Wasa da ita wani dadi yake ji Yana so a dinga taba masa ya Kan sashi bacci ma,Sabreen baki ta tabe ta ebi abincin tace baiwa wahalalliya dole ki dafa naci ta wuce room dinta a ranta tace zaku gane kurenku ai Iyamami dan bata samu Baffa ba ne,wannan auren sai an raba shi,ni kuwa lemon na tsiyaya masa nace Wai har yanzu bamu kwana biyu ba ne na matsu aurena ya kare, bai ce min komai ba har ya gama ya sha ruwa tare da goge bakinsa da tissue ya mike yace jeki ki dakko min mukullin mota a Kan gadona Zaki ganshi,a gabansa na tsaya Ina murmushi nace kaga dalilin da yasa bana son auren nan sai kana zamanka me dadi a dinga aikenka Kawai wani yazo ya dinga saka mutum aiki dakko min kaza bani kaza,haba Wai shike nan kana aure baza ka huta ba,Ido ya zaro tare da furta oh magana Zaki fada min kawai kice baza kije ba alright ya juya da sauri zai dakko da Kansa da sauri na rungumo kugunsa nace wayyo zanje Wasa fa nake yi na kankame shi sosai,sake ni dariya nayi tare da jawo shi baya da dukkanin karfina ban San Kawai sakar min jiki yayi ba gani nake yi karfina nane Ina haki na haura sama da dan gudu na naje na dakko na dawo da gudu nace gashi yace ba na wannan motar ba na manta Yana kasan pillow na juya da gudu Ina juyawa ya dinga dariya Yana sani ya min haka dana yi gudu sai na birgeshi yanda komai na jikina ke rawa,dawowa nayi Kamar zanyi kuka nace babu fa key na gani da yawa a wajen, yace Zaki ga yafi kowanne girma sauri karki bata min rai na juya da gudu gudu gudu sauri sauri naje na dakko na tako steps da gudu sosai sallamai Mami Muka ji ta shigo ni ta hango Ina gudu,tace sai kin fadi ko Rabiah,Ina haki nace Sannu da zuwa Mami Ina murmushi

     Itama murmushin tayi tace Kuna lafiya,nace Bari nazo mu gaisa na shiga kitchen na kawo Mata abinci da ruwa da lemo sai fruits dana yanka,Nawwar Kuwa Zama yayi kusa da Maminsa Suka gaisa,zuwa nayi na durkusa har kasa na gaishe da Mami ta amsa da kulawa tare da furta Ina Sabreen din fa?nace tana dakinta,Kira min ita nace to na nufi sama har part dinta,bedroom dinta na tura Kawai na shiga na iske gabanta kayan maye ne iri iri,ta zuba garin Coccaine a yar takarda tana ta faman sheka tana bubbuga kanta idonta yayi jajir ta fita a hayyacinta,banyi mamaki ba tunda wannan shine Karo na biyu dana taba gani,Sanda nazo a matsayin Yar aiki na gani yanzu na sake gani,tana ganina tsoro ya kamata jikinta ya dauki rawa gashi tana wani fisge fisge ita kadai Murmushi nayi nace Karo na biyu kenan kinga da ace wata ce da tuni na tona Miki asiri,idonta Yana rufewa nace Mami ce ke kiranki,cinkin muryar Yan maye tace baaaa zaaaan iiiiiyaaaaa taaaaa shiiiii baaaa baaaaaaccci…..naaaaa…..keeeeee….ji…tana Gama fadin haka daga zaunen ta kwashe tarkacen ta tura kasan gadonta komai da komai ta fada saman bed sai bacci.

     Fitowa nayi jikina yayi sanyi ace mace ta maida kanta marar amfani a duniya daga bacci shike nan bata da lokacin komai, Palo na koma nace bacci take Yi,Mami tace ki taso min ita Magana zanyi daku dukkanku,nace dazu fa tace kanta na ciwo ta Sha magani shine ta dan samu bacci,idan ta tashi zuwa dare sai ya kawo mu har gida ni da ita inaga zai fi,Murmushi Mami tayi tace to tunda bakya so a tashe ta ,Nawwar yace ita wace baza ta tashi ba,kyaleta Zan dawo zuwa daren dama gidan kawata zanje idan na gama abinda nake sai na sake biyowa,nace to nan taci abincinta sosai Muna hira ta mike Muka rakata har mota ta tuka ta tafi,hadari ne ya hado sosai nace ya zaka koma ciki Kai da zaka fita,na fasa dama wajen Mami zanje Kuma ta zo anjima zata dawo,a Palo Muka zauna na kamo mana Nigerian film Muna kallo,aka yi abin dariya ni ban San me akace ba sai gani nayi Yana dariya,nace Allah sarki Jahila Rabi dan Allah ka dinga fassara min ba iyawa nayi ba kasan kadan nake tsinta nafi Iya pidgin English,ance a saki a school kin ki fafur, nace Allah ya kiyaye katuwa dani bazan gane komai ba ni yanzu me Zan iya a karatun boko ai Ni yanzu duniya ce a gabana,dariya yayi yace kin san baki da hankali Rabi wai anya dai dai kike kuwa,kina da auren kike fada min duniya ce a gabanki, baki na turo nace lokaci ma baya sauri ni na matsu a sake ni na Kama gabana,wato fadan da Inna ta Miki Baki ji ba kenan? banji ba ai ni bana ji ba a fada min naji,Allah ya sawwake miki Kuwa me yasa yanzu tunda aka kusa biki kika daina cewa kina son Sex? ko a taba miki boobs, dariya nayi nace laaaa Allah ya yaye min ji nayi na daina fada Kawai yanzu ma tunda aka Yi bikin naji bana son sex din na tsani Harkar ma burina yanzu a sakeni na tafi,mamaki ya kashe Nawwar yace wato ke duk abinda Allah baya so shi kike so,anyi aure ai dole a cinye ki,Fuska na bata nace ni wallahi yanzu bana so Kawai saki nake so,ji nake Yi Kamar Ina prison bana son gidan nan ban san Sanda na Fara hawaye ba gaba daya ji nake Yi na tsani gidan bana son Zama wani zugi nake ji a raina na rasa Jin dadin zuciyata

   Kallona yayi da mamaki ya zauna sosai tare da tambaya Wai da gaske kike yi? fashewa nayi da kuka sosai babu batun Wasa a ciki, Ido ya zuba min na kifa kaina a kujera Ina ta fama cikin muryar kuka nace dan Allah ka sake ni wallahi bana son auren nan, to naji kiyi Shuru,da kyar na kokarta tare da tsaida hawayena,yace idan na sallameki Ina Zaki? nace inda ka ka dakko ni,kinfi son can da nan? Na daga Masa Kai da sauri,yace to nawa Zan biya ki zauna na wata daya, nace ni bana son kudinka ko sisi Kawai ni ka yarda na tafi,yace missing dinsu kike yi? Nace ae ni kawayena nake son gani da gidanmu,idan na kaiki kin gansu zaki hakura mu dawo? Kai na daga Masa da ae amma nafi son sakin yafi min dadi

Ransa in yayi dubu to ya baci amma haka ya daure ransa a bace cikin fada yace bazan sake ki ba kiyi duk abinda zaki yi, Shuru nayi Ina Jin tsoron fushinsa a hankali cikin shagwaba nace to kayi hakuri zan dan sake jira,Tsaki ya ja nace I’m sorry na dawo gabansa na durkusa tare da daura kaina saman cinyarsa na kifa kaina sannan nasa hannayena na rungumo kugunsa Ina shakar kamshinsa me sanyi da dadi,kwafa naji ya ja a hankali na dago kaina Ina kallon yanda ransa yake a bace,nace fa kayi hakuri Zan zauna na daina ban San Ina yin wani abin ba sai dai naga nayi Allah Kuma Ina Jin zuciyata tana baci haka Kawai, banza ya min nace kayi magana nace kayi hakuri Please, saman cinyarsa na koma na zauna daram muna facing juna,ajiyar zuciya ya saki tare da furta washshsh…domin ji yayi gaba daya Yana Jin wata sha’awata Wanda dama kadan yake jira daurewa yayi da kyar yace ki dagani mana bana son Iskanci ya furta da masifa,nace to Kaine kaki yin hakuri,bazan Yi ba ko dole ne yace, hannayensa ya hade waje daya tare da lankwasa su Suka bada rukuss, kaina na kwantar a kirjinsa na narke a jikinsa,gashin kaina ya kalla wanda dama na cire dankwalin bayan tafiyar Mami,dariya nayi nace Mijin Sabreen kaga ko Watarana Seraline customer dinta yazo dakinmu Ina bacci,sai farkawa nayi na ganta a zaune a cinyarsa haka babu Kaya a jikinsu,tana haka na fara yin gaba inyi baya a cinyarsa nayi dariya na tsaya nace haka Suka yi,kallo na yayi sai da naji tsoro yanda Idonsa yayi ja har wani ruwa ya tara a ciki, tunawa nayi yanda nake ganin maza idan suna sha’awa ko suna romance.
Wise na tuna da tace idan namiji ya Kai wani stage na sha’awa Matukar bai kawo ba to babu macen da wani bazai nema ba,tambaya na jefo Masa nace sha’awa? Ido ya lumshe,dariya nayi nace kace Kai Ustaz dan Allah abun ashe dai Yana da lafiya,ai na zaci Ustazu ne baka ji,dan Murmushi yayi amma Sam baya hayyacinsa bai ma san ya tallafe min kugu ba da hannayensa ba

    Hannayena na saka cikin lallausar sumarsa ta bayan Kansa na matso da kansa saitin nawa na dora hancina dogo saman nasa ji nayi ya sake rikeni sosai a hankali na hade bakina da nasa na fara tsotsa Kamar Zan cinye Masa baki,karbewa yayi ya fini ma tsotse nawa bakin yana tande min shi,zip din rigata naji yana ja kasa nace wayyo yanzu bana so na daina so wlh dan Allah bana so ni karka taba min nono Ni bana so,kyalewa yayi tare da janyeni ta karfi daga jikinsa ya jefani saman kujera ta gefe ya tashi yaja tsaki yace ni mantawa ma nayi sabo da jiki da jini shi yasa karki kawo Zan iya kusantarki kaddara tasa na aureki amma ba abinda zan tsinta a jikinki tunda an riga maza da yawa sunyi me Zan ji,na kalle shi tunda nake sai yau naji zafin Maganar da ya fada min,nace to ka sakeni mana ko na maka dole ka aureni ka sakeni mana,shi yasa tun farko nace bazan Yi aure ba ni ban dace da aure ba,ba irin matar da za a aura bace,karshe ayi min gori a dinga zargina ko a goranta min ni Yar tsuntuwa ce Yar shege ce ni shi yasa nace bazan Yi aure ba ka nace sai ka aureni,jikinsa ne yayi sanyi sai yaga bai kyauta ba shima amma haushin na sa Masa sha’awa ko kulani baiyi ba ya juya tare da taka steps da gudu na Isa wajensa nabi bayansa Nima Muna taka steps na furta nace ka sakeni ka sakeni ka sakeni Yana juyowa ya kashe ni da maruka har uku tare da nuna ni da yatsa idan Kika sake min Maganar saki sai na Miki illa Yana rufe baki Sabreen na Fitowa ta tashi a bacci yau da wuri kasancewar bata Sha da yawa ba Kafin tazo kusa ina hangota da sauri na sauke Hannu na daga kumatuna na goge idona Ina murmushi me kyau a hankali nace wayyo kishiya ta gata nan ta taho kayi shuru zata raina ni,in taji sai tayi mana dariya juyawa yayi Yana tafiya na dafa kadarsa Ina cewa ban koshi da Kai ba My Salmankhan,my Sharukhan,gaskiya yanda dazu fuck din nan yayi dan Allah ka dinga hakuri Kar ka rame yawan sex Yana ramar da mutum,dariya ce ta mugun kamashi da sauri ya bude dakinsa ya fada ciki na bishi na banko kofar bam,Sabreen ta bimu da kallo tace da gaske saurin yake zasu Kara yi ai wallahi baza ta Sabu ba dole na tafi gida yanzu kuwa,Sabreen bata tambayi Nawwar ba sai karar mota muka ji,ta window na leka Yana kwance bance Masa ita bace,yace waye? nace Uwargida ce,hmm Kawai ya furta,Zan fita yace Ina zagi je? nace dakina,zo ki min kitso,Murmushi nayi nace to na haura saman bed din na zauna yana kwance Ina kokarin kitsa sumar amma yawan nata bai kai a kitsa ba haka na dinga cukurkuda Masa gashin amma sha’awa ta hanashi sukuni,Ina kallonsa na lakanci Sam baya hayyacinsa,ruwan sama ne ya tsuge me yawa na tashi na kulle windows na saki labile dakin sai yayi duhu dundum Kamar dare sabo da gari yayi bakikirin na hadari da ruwa na gaske, T-shirt dinsa na dakko na cire kayana na saka tasa,bai San me nake Yi ba ya juya baya ga duhu,so yake yayi bacci ma,Ina linke kayana daga kwancen ya tube rigarsa bai fiye bacci da riga ba sai boxers kawai ya kule a blanket,Rigarsa na dauka na linke na Adana har nawa kayan sannan na haura saman gadon,bai San na cire kayana ba,sai t-shirt da pant

   Nima bargon na Shige gefe,gaba daya na lakanci baya hayyacinsa tausayi ya bani,na matsa jikinsa ta baya na rungume shi,ajiyar zuciya ya saki me karfi,yaji sam kamar ma ba kaya a jikina hankalinsa ya Kara tashi har yana nema yayi loosing control,a hankali nace da ace Sabreen bata fita ba ai da ka je wajenta sai ta baka abinda kake nema tunda ni kaga maza sun gama dani, harda marina kana yawan dukana wlh duk Sanda haukata ta juyo kanka baza kaji Dadi ba,ka daina taba min lafiyar jiki,Indai nice barwa Sabrewn kwana na,a hankali ya juyo muna facing juna yace really? Nace ae na bar mata yace to ta gode bari ta dawo sai ki fada Mata da kanki a gabana,dariya nayi na sake shigewa jikinsa nace wlh bata Isa ba ko yau na haihu sai na karbi miji.

     Fuskarsa yasa tana saitin tawa a hankali ya shigar da bakinsa cikin nawa,yana min wani irin tsotsa ta musamman jikina ya hau rawa Ina Jin wani dadin da ban taba ji ba a jikina,amanna na bada sosai yana tsotsar bakina Ina tuna abinda Naga su wise suna yiwa maza na jiyar dasu dadi,kirjinsa na fara shafawa Ina taba nipples dinsa yaja wani ajiyar zuciya ya shide,to mu dai bamu da kunya a hankali na tambaye shi da dadi? yace yeah naci gaba da murza masa,bakina na sa a Kai Ina tsotsa zaucewa yayi tare da furta washshsh…ahhhhh…, Boobs dina ya kama a riga yana murza mun su cikin salo da kwarewa,nace wayyooo Zan haukace Baby dadi nake ji, surutai nake yi Ina nishi,rigata ya zare min tare da jawoni jikinsa,naji hajiya Babba ta mike ashe ya cire wandon nasa ma,tsoro naji ban taba sanin haka take ba sai yau gabana ya fadi,nace amma baza muyi sex ba ko? yace min ae yana dora bakinsa a manyan dukiyar Fulani na Sabo da ba karya a kwaisu sutu sutu a tsaye gwanin birgewa shi yasa Nawwar bai same su wajen Sabreen ba yanzu Kam abin nema ya samu shi yasa ya nace musu ya dame su da murza da tsotsa sai kace jariri baya min da zafi a nutse yake min komai, pant dina ya kama zai janye naki yarda yace ba sex zanyi ba fa ba abinda Zan Miki,nace Ni dai ban yarda ba,saki yayi tare da furta ni dai Ina Shan wahala kina gana min azaba wlh Ina cin ubana a wajenki ,dariya na dinga yi,nace to kawo kai na maka abinda kake so

    Hannuna ya kama ya Dora akan Antainarsa najita me tsayi ga kauri ta mike sankamkam tana huci da numfashi,nace Subhannallahi ke ki dinga salalawa kanki kaji tana motsi ita kadai kamar Abu me rai, dariya na bashi sosai amma kadan yayi baya cikin hankalinsa a hankali ya furta kisa naji dadi please Amaryar Nawwar, nace dama Inna ta fada a nan fagen kuka iya love ai shike nan,na fara matsa masa ita Ina sarrafata yanda naji su Sera suna fada,duk inda naji sunce in an taba a jikinta ana Jin dadi sai da nayi Masa Yana ta Nishin dadi Kamar ba Nawwar ba kunya babu shike bani salo Ina masa yanda yake so sai dan ihu yake Yana nishi, nace kayi kneel down ai Kuwa yayi nace shegiya harka anji harka sai abinda nace, a bako nasa Antainarsa ban taba Yi ba amma yawan ganin Bf a dakin su Wise yasa duk na sani na gwada Kuwa duk da naji ta cika min baki Kuma ta min yawa Kamar zanyi amai haka na daure tissue ya jawo a gefen bed ya bani ba ji ba gani Kawai na shiga sarrafa masa ita a bakina idan yawu ya taru na zuba a tissue,Yana Danna min can ciki na Fara kakarin amai abinka da ba a Saba ba,gurnani yake Yana Nishin dadi ya Kama gashina ya hade gaba daya tare da damkewa a hannunsa Yana yi Kamar yana sex, ni kuwa ba kunya nake ji ba idan na cire zan zuba yawu a tissue sai nace da Dadi? baya iya magana Sabo da a zauce yake Muka ci gaba da gashi Ina jinsa yana Kiran sunana yafi a irga Yana cewa da dadi,lokacin da zai kawo gashina ya damke sosai kamar zai cire min Kai,zarewa yayi zai zuba madarar tasa a tissue nace a’a ni ka bani na shanye Ina so minerals ne fa,a tissue ya zuba abinsa bai kulani ba,nace yanzu anyi asararsa abu me tsada,haushi naji ni naji ganin a Bf ana sha naji Kuma bana kyankyamin Nawwar ko kadan babu abinda nake kyankyami nasa,haushi naji na maida rigata na kwashe tissue dake kasa na zuba a bakar leda na fita na saka a dust bin na dawo ya zaci ma bazan dawo ba nayi fushi,na dawo na kwanta,juyowa yayi yace Fushi Kika yi?nace a’a akan Sperm dinka zanyi Fushi Allah yasa bature ya mana yogourt abinmu in Ina so gata can a fridge kaje da abinka,Ni tunanina ganin turawa suna lashewa suna wani Jin dadi na zaci zaki ne da shi Kamar Madara shi yasa na damu,dariya yayi yace to ki daina hada dadin yogourt da sperm ba hadi yogourt ai tafi dadi,nace ba wani ni zaka yiwa wayo Kawai Naga bakin ciki kake min baka so naji dadi kaje ka bawa Sabreen dan Allah idan ta Sha a fasa Mata kofa sabo da kiba,Zan Sha yogourt dina haka,Ni zaka yiwa wayo gashi nan ana Sha ana cewa baby you are Sweet ayi ta cewa sweet,honey,sugar mace an dildila Mata a baki kaga ta zauce ta fita hayyacinta tana lashe lashe ai dama nasan yafi yogourt dadi kuma ai shike nan Dan an hanani sabo da ni bani da gata bani da iyaye ba kowa bace ni ba komai rayuwa ce,Nawwar dariya ta kamashi yace Wai ke kamar ba Yar duniyar ba in Kika Yi wani abin Kamar baki San da Namiji ba,Shuru nayi Kawai inaso duk Sanda ya kusanceni ya Sha mamaki,bacci ya kwasheni,shima Yana yin Shuru sai baccin ya samu nutsuwa sosai.

     Sabreen gidansu taje ta fashewa da Mamanta da kuka tana fadawa Mama yanda Rabiah ta mallake Nawwar,Mama tace kinga naga Alama Iyamami baza ta iya komai ba,Papanki da ita Naga Kamar bakinsu daya da Baffa zasu dinga Mana karya wai tunda ya tafi sau daya ya kirasu Kuma wayarsa bata shiga kiji a son zumuncinsu nasan Baffa bazai taba Mana haka ba Yana kaunar danginsa Kawai na lakanci Iyamami da daurin gindinta aka Yi auren,ke babanki ma ban yarda da shi ba,kin san shi da son kudi dama sabo da kudi ya nace sai kin Auri Nawwar sabo da ya mallaki kadarori to gashi ke kina wahala ko cikin baki samu ba shi Kuma Bai samu kadarar ba,Kawai yanzu da kaina Zan dauki mataki ki tashi ki koma gidanki kiyi Shuru zanzo jibi zan kawo miki abinda ya dace,Sabreen tana shesheka tace ya kamata kiyi sauri Mami abin yayi yawa,karki damu tashi ki tafi Kar ma wani ya ganki, Sabreen ta mike ta fito ta shiga motarta sai gidan Jamcy, tana zuwa nan ma Jamcy ta bawa labarin komai,Jamcy a ranta tace nima yanzu haushin Karuwar nan nake ji ta hanani shiga gidan Sabreen dole mu hadu mu koreta,Nan take Jamcy tace ki bani sati daya zamuje wani kauye ki dai San karyar da zakiyi ya barki,Sabreen tace yo ni ai bana tambayarsa duk inda naga dama zuwa nake,Jamcy tace to ki tanadi kudin jirginmu da dubu dari biyu,Sabreen tace bani da sisi yanzu haka ma Coccaine Dina kadan nake Sha sabo da Kar ta kare kafin na samu kudi amma karki damu dole ko satowa sai nayi a dakin Nawwar,tafawa sukayi sannan tace tafiya zanyi ta mike ta shiga mota ta dakko hanya.

     Sai wurin magriba na farka na ganni a jikinsa ya kankameni, jikina na janye sai kuwa ya farka nace tashi magriba ta kusa Kar ka rasa Jama’i,wanka ya shiga yayi wanka ya tsarkake jikinsa sannan ya fito,Ni Kuwa na kwashi kayana Ina part dina wanka nayi nayi Sallah sannan na fito sanye cikin rigarsa me dogon hannu ta kawo min rabin cinya a haka na fito sabo da tsona,kida na kunna a speaker Bluetooth na ajiye a kitchen Ina girki Ina cashewa na hada da karamar wayata,na cika gidan da kida, ana yin Sallar Isha na kashe naje nayi Sallah na dawo na sake kunna kidana da guntuwar rigarsa gata me santsi ruwan zuma, banyi abinci me wahala ba,a dining na shirya komai,na koma na gyara kitchen din Ina wanke wanke Ina cashewa,Nawwar sai da yayi Isha sannan ya dawo gida, Yana shigowa Mami ma ta dawo gidan,Sabreen ma ta dawo,Mami tace badai gida Kika koma ba Sabreen,baki ta zumbura tana murguda baki lokacin shima Nawwar ya same su a compound. Suka shugo gaba daya suna ta sallama amma kida yasa bana ji,Mami ce ta leko kitchen din juyawa tayi Kawai ganin shigar dake jikina rigar Nawwar dinta na saka Kuma Ina ta rawa Ina wanke wanke,Murmushi tayi tace yara kenan basu da damuwa,Nawwar ne ya shigo da kansa ganin rawar da nake sai na birge shi gaba daya ya shagala da kallona rigar tasa ta min kyau,juyowa nayi na ganshi to ba kunya garemu ba gabansa na tako Ina rawata,Hannu yasa tare da kashe kidan Yana Murmushi yace Mami tana jiranki,Ido na zaro nace dakko min hijab dan Allah,yace ai ta riga ta ganki,ni dai ka dako min hijab,Fitowa yayi yace gata nan yaje dakina ya dakko Hijab din da ya gani a gefen gadona ya dawo ya Kai min na saka har kasa sannan na fito na samu Mami a zaune da Sabreen,nace Sannu da zuwa tace yawwa,durkusawa nayi na gaishe ta Wanda Sabreen Kawai cewa tayi Ina yini daga haka bata sake magana ba,Nawwar zaiyi magana Mami ta Hana sabo da Sabreen gida zata je tayi sharri Iyamami da Baffa su ci Mata mutunci sabo da Haka Nawwar Yana gani Sabreen tana abinda taga dama amma baya magana Sabo da Yana cewa wani abu to akan uwarsa zata yi wabi akan ran Maminsa ya baci gwara ya rabu da ita iya kaci ya Mata nasiha idan bata ji ba shike nan.

    Mami hada mu tayi ta Mana nasiha sosai akan mu zauna lafiya,Sabreen tana ji tana yatsina fuska sabo da raini,Mami tashi tayi nace abincin fa,tace Alhmdllh nace Wai Ina Auta ne da su Sultana sunki zuwa,Zasu zo ne Inshaallah cewar Mami nace Allah ya kaimu,Nawwar ne ya raka Mami motarta shima ta Masa nasiha sosai sannan ta tafi.

      Yau ma a dakina na kwana bai neme Ni ba Nima ban je ba,washe gari ma Sam bamu hadu sosai ba sai wajen cin abinci sabo da bai yini a gida ba wani abu ya taso a Office,yau kwana na Uku yauma da sassafe ya fice,yau Kuma Mama ta zo da rana ta sameni Ina Kujeru,ko kulani bata Yi ba Ina ta wuce sama Kawai bangaren yarta,Sabreen ta gama gyara dakinta kenan tayi wanka Mama ta shigo,tana murna suka gaisa Mama ta zauna tare da furta sauri nake Yi ta zuge Jakarta ta dakko wani garin magani da wani ruwa ta mikawa Sabreen tace gashi sai kin bari ba kowa Zaki tube kayanki ki kwaba maganin da wannan ruwan sai ki shafe jikinki da maganin idan ya shigo ki tabbatar a gidan da ke ya Fara tozali Kuma ki tabbatar shi kadai ya ganki shima ke kadai ya gani,Yana shigowa Kawai zaninki zaki cire ya kalleki tsirara da ya ganki a zigidir da maganin a jikinki to an gama shike nan kin mallake shi,amma idan Kika bari wani ya ganki ko kishiyarki to magani bazai aiki ba Kuma baya bada shi sau biyu sau daya yake bawa mutum ki kiyaye abinda ake ciki ki fada min a waya,Sabreen tana murna tace ai Kuwa ya fita gaf yake da shugowa yanzu yayi Amarya ba ya dadewa.

    Ni kuwa Ina gama aikina da girki na koma dakina nayi wanka na kwanta sai bacci,Sabreen har dakina ta leko ta tabbatar bacci nake yi,Nawwar ta Kira a waya ya daga tace ka kusa dawowa ne? Yace Ina Hanya mene? ba komai ta kashe wayar,da sauri ta tube zindir ta kwaba magani tare da shafe jikinta yanda akace ,tana Jin dirin motarsa ta daura zani Kawai ta fito main palon kasa ta dan labe,ai yana bude kofa ta bude zanin data daura gaba daya ta rike gefe da gefe,haihuwar uwarta tace My love I need you Sai da ta tabbatar ya kalleta sosai sannan ta maida zanin ta daura,tana kallonsa ta sandare a wajen ganin Nawwar da wani Wanda suke business ya sauka daga Canada yazo gidansa, kunya da bakin ciki Suka lullube Nawwar,abokin aikinsa Rayyan yace wannan fa kalau? Nawwar yace Aljanu ta hadu dasu tun da dadewa yace eyya sorry na ganta ban San zata Yi haka ba,Nawwar yace ba komai,Zama suka yi a palo, Rayyan ya fahimci Nawwar baya hayyacinsa sai ya daga Wayar karya yace nemansa akeyi akwai matsala,Nawwar yace ai baku gaisa da wifey na ba,kafin ya rufe baki na fito cikin adon leshi riger da sker dark brown.

    Gata nan ma,Rayyan yace wannan ce matar taka waccen fa? yace itama ita uwar gida ce,Rayyan yayi dariya tare da furta wannan Kam tayi Allah Sanya Alkhairi yace Ameen,karasowa nayi tare da Zama na gaida Rayyan da fara’a,Nawwar ya furta Wai so yake ya tafi,nace tun yanzu wannan ai ba zuwa kayi ba bamu karbi wannan zuwan ba gaskiya ko abinci ai kaci,dining Muka koma nayi serving nasu suna ci Rayyan sai Santi yake Ina dariya,bayan Nawwar na koma na tsaya hannayena suna saman kafadunsa dai dai wuyansa ina masa tausa a wajen wuyan Yana cin abincinsa, Rayyan yace nima dai Zan bada himma nayi auren nan,dariya nayi nace ai gwara dai duk suna maka wayo kana zaune a gwauro,Gane min hanya Mamana ta gaji da ni,sai da Suka gama cin abubuwan dana hada sannan Rayyan ya mike tare da furta Amarya kin iya girki gaskiya mashaallah yau sai na bada da labari,godiya nayi ya zaro kudi dubu Hamsim ya ajiye min a table,nayi godiya yace ba komai,Nawwar rakashi yayi har katuwar motarsa ya tafi shi Kuma ya dawo gidan.

     Yana dawowa gida direct dakinsa ya wuce ya fyalli takarda ya rubutawa Sabreen saki daya ya fito ya shiga part dinta,sake isketa yayi tana kwaba wani maganin tana shafawa a jikinta,takardar ya jefa Mata yace kije na sakeki saki daya sai kiji dadin yin tsafin a gidanku,Sabreen maganin ta jefar a kasa tare da kurma uban ihun da yasa nayi part din nata,a ciki na ganshi nace lafiya Sabreen ashar da zagi ta hau dura min ta uwa ta uba har da cewa tunda Kika sa ya sake ni wallahi kema sai an sakeki sai nayi sanadin fitarki a gidan nan, Nawwar na kalla nace au sakinta kayi ai sai ace Dan kayi Amarya ne ai duk irin dadin da kake ji a wajena bai kamata ka saketa,Haba Honey nasan kana Jin dadi a jikina yes kana samu nutsuwa yanda kake fada min baza ka iya Zama da kowa ba sai ni amma bai dace ka saketa ba, tsaki yaja ya juya, Sabreen tace wallahi ba inda zanje Zama daram ka saki banza wofi, ficewa nayi abina shima yayi gaba.

     Gaji amarci Kawai suke kwasa da tayi Niyyar barin gidan yanzu mugun kaunar juna suke Yi ita da mijinta Danbinni,Zayya Kuwa haukar kishinta takeyi Kawai kullum sai sunyi fada da Gaji dake gaba dayansu basu da hakuri,Danbinni kudin cefane ya bawa Zayya yace gashi idan Gaji ta tashi a bacci ki bata shinkafa da Miya za ayi dama shi baya son Mai da yaji,Gaji tana tashi a bacci Zayya ta watso mata dari uku ta cinye dari bakwai, Gaji ta zaci baida kudi Kawai ta dafa wake da shinkafa,sai da ya dawo ya dinga fada Yana yiwa Gaji Sababi,Gaji tace to ai kudin baza su Isa ba dari Uku fa ka bayar,wacce dari ukun? Haka Zayya ta bani,yace ke Zayya ke…Zayya ta fito yace Ina dubu dayan da na baki na cefane, Zayya tace ita fa ta bawa Gaji kudi,Gaji ta hau rantsuwa ita sisi ba a bata ba sai dari uku,Danbinni gaba dayansu ya hada ya musu fata fata Gaji ta yini tana kuka an Mata sharri.

    Maryam Mairo yayar Gaji wani Dan daba ne a school dinsu ya nace Yana sonta ita kuma bata sonsa ko kadan har Suka gama school Suka dawo gida bai San garinsu ba sai yanzu Najib ya samu address dinsu, mugun kaunar Maryam Mairo yake amma taki sonsa ko waya in ya mata bata dagawa,gaba daya ran Najib ya baci cikin yaransa yan daba Suka je har gidan Dagaci cikin dare Suka sace Mairo,Gwaggo sai ihu sukeyi bayan tafiyar Yan daba a motarsu cikin daren mutane Suka cika makil ana jajanta musu,Gwaggo tana ta faman kuka tana na Shiga Uku Mairo ta Yan kidnapping basu San zafin haihuwa ba wlh da sun sani da basu saci dan wani ba,Dagaci sabo da duk yaransa yafi kaunar Mairo shima sai da yayi kuka,Mairo Kuwa sun shaka mata Abu bata San Ina take ba har cikin garin Kaduna inda Najib yake gidansa yasa a kaita wani flat me dan kyau cikin bedroom ya Kai Mairo tare da kwantar da ita a saman gadonsa, ya sa Mairo a gaba Yana bulbula taba sigari.

Masu bukatar sauraron audio na wasu novels Dina ku duba YouTube channel  S ZARIA TV

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                   61-65

Official

By
AsmaBaffa

 

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Haleemart Ameenu
Maman Zulaihat
Khadeedodo
Nererh
Nanah
Zainabgohe
Mmn Humaira
Saudat Safiyan Maman Inam
Amatullah Kamshi
Firdausi A Nagwaggo
Ummiauwalu72
Alhamdulillah

Injija ta gare ki
Ummulkhair
Mrs Chief

 

       Sullubewa nayi tare da tsayawa a gabansa Ina kallon Sabreen a kafar bene, Sabreen ta sandare a tsaye na bishi zamu hau sama na juyo nace kuma idan na ganki a part dina wallahi sai kin karba a jikinki,yanzu zamu shiga ciki Kuma kin San idan akace mace da Namiji sun kebe a daki kin san me zai faru,sannan a wannan harkar ta dadi na Saba ihu sosai,I like to shout well well,I like to cry well so Kar na ganki kusa da part dina lokacin Ina enjoying life dina, juyawa nayi Ina wasa da botin din rigar Nawwar nace Honey hoho My Baby, ka tuna na jiya irinsa nake so ai ban San da salon ba sai jiya ya bani sweet,hannunsa na rike nace muje local government kaikayi take naja hannunsa Muka Yi ciki mamaki yasa ya bini da kallo abin Nawa daure Masa Kai yake,Muna shiga part dinsa Sabreen ta rushe da kuka ta kifa kanta a table tana ta faman kuka,tashi tayi fuuuu tayi dakinta ta Sha kwayoyi ta fada bed sai bacci.

   Ni Kuwa Muna shiga bedroom dinsa na fashe da dariya na zauna a gefensa inda yake zaune nace nasan yanzu tana can tana kuka,ai mu ka fada Mana Daya sai mun fada maka goma bata San mu bane wajen fada ba a jayayya da Yan duniya, yace kinji dadi to? Nace sosai na fada saman bed dinsa Ina dariya Ina tsalle,karki lalata min gado,wuyansa na shako ya fado saman gadon ya kwace jikinsa nace yau baza kaje Office bane ka tashi ka tafi,yace ba inda zanje shike nan bazan huta ba,tunda ba amarci kake ba mene amfaninka ka tafi kawai,a gidana Wai ki dinga korata kin takura min fa,Hannu na na tura a rigata Ina Sosa gefen Boobs dina nace kurji ne ya fito taba kaji na rike hannunsa ya fisge abinsa Yana dariya yayi kwanciyarsa,nace kaje ka gaida Mami Wai mutum bazai fita ba,banza ya min nace ayi mace shike nan sai kace an auro kwarkwara sai dai a dinga kulani da rana dare ba nawa bane,dariya yayi ba shiri yace kin dameni wlh ki tafi ki bani waje,tashi nayi na fita ya bini da kallo tare da lumshe Ido bai sani ba bacci yayi gaba da shi,Nima kwanciya nayi a dakina sai bacci sai 12pm na tashi a gurguje na fada kitchen na shirya girkina lafiyayye sai 2:30 na gama komai na jera a dining naje nayi wanka dama nayi Sallah,leshi na zaba cikin kayan lefena maroon doguwar Riga ne dinkin manyan Mata na saka na fito Ina walkiya,Ina zama a dining naji ya shugo naga har yayi wanka ya canja cikin Jallabiya ashe masallaci yaje ya dawo, a palon ya zauna ya dauki remote,tashi nayi na tuna Izzarsa shi yasa na karasa kusa da shi na zauna a gefensa sannan a hankali nace abincin fa ko nan zan kawo

   Yace sai anjima,sabo da me? ya furta Kawai,nace a’a gaskiya ban yarda ba sai Mami taga ka rame tace laifina ne,a hankali ya juyo ya kalleni tare da cewa Wai ni yaro ne shike nan ban Isa nace a’a ba sai kin min musu,ka bari idan ka koma bangaren Uwar yaranka sai ka Mata wannan na furta tare da mikewa na jawo hannunsa,mikewa yayi  ya Isa dining nayi serving nasa Muka Fara cin abincinmu,Yana ta yanga nace idan baza ka iya ci ba nazo na baka a baki ni a wajena ba komai bane,Tsaki ya ja yana wani ci a hankali na taso na dawo gabansa na jawo kujera na zauna,Sai ga Sabreen ta fito itama ta Sha wankan shadda,ai ganinta da sauri na tsiri shafa Masa gashi,shi bai ma San ta shugo ba,nace  Babyna abincin yayi dadi ko,Sabreen ya gani sai lokaci ya gane abinda nake Yi sabo da itane ashe, Sabreen Tsaki ta ja tace mu bama Kai kanmu sai di azo a same mu a haka ma Muna yanga Mata masu aji kenan,nace ke kenan baki ji sunanki ba Sabreen ni Rabiah babu hadi,ga baya ga gaba dan Allah kalle shi baki ga ya Kara fresh ba? Girarsa na koma shafawa da yatsa nace ya samu me Nono kirjin ba faranti bane cika Masa hannaye sukeyi, Sabreen ta hayayyako da bala’i ya daka Mana tsawa Enough……nace zaren ba Kalar yadin bane shegiya Yar gidan Zuwaira me wagegen baki Kamar kofar gari ko ubanki Yusufa ya Isa ya kawo min walgi wlh kina bude baki sai na tashi na tafasa Miki jiki….tsawa ya min bana son shirme Shuru Muka yi yaja tsaki yaci gaba da cin abincinsa.

     Sumarsa naci gaba da shafa masa Ina Wasa da ita wani dadi yake ji Yana so a dinga taba masa ya Kan sashi bacci ma,Sabreen baki ta tabe ta ebi abincin tace baiwa wahalalliya dole ki dafa naci ta wuce room dinta a ranta tace zaku gane kurenku ai Iyamami dan bata samu Baffa ba ne,wannan auren sai an raba shi,ni kuwa lemon na tsiyaya masa nace Wai har yanzu bamu kwana biyu ba ne na matsu aurena ya kare, bai ce min komai ba har ya gama ya sha ruwa tare da goge bakinsa da tissue ya mike yace jeki ki dakko min mukullin mota a Kan gadona Zaki ganshi,a gabansa na tsaya Ina murmushi nace kaga dalilin da yasa bana son auren nan sai kana zamanka me dadi a dinga aikenka Kawai wani yazo ya dinga saka mutum aiki dakko min kaza bani kaza,haba Wai shike nan kana aure baza ka huta ba,Ido ya zaro tare da furta oh magana Zaki fada min kawai kice baza kije ba alright ya juya da sauri zai dakko da Kansa da sauri na rungumo kugunsa nace wayyo zanje Wasa fa nake yi na kankame shi sosai,sake ni dariya nayi tare da jawo shi baya da dukkanin karfina ban San Kawai sakar min jiki yayi ba gani nake yi karfina nane Ina haki na haura sama da dan gudu na naje na dakko na dawo da gudu nace gashi yace ba na wannan motar ba na manta Yana kasan pillow na juya da gudu Ina juyawa ya dinga dariya Yana sani ya min haka dana yi gudu sai na birgeshi yanda komai na jikina ke rawa,dawowa nayi Kamar zanyi kuka nace babu fa key na gani da yawa a wajen, yace Zaki ga yafi kowanne girma sauri karki bata min rai na juya da gudu gudu gudu sauri sauri naje na dakko na tako steps da gudu sosai sallamai Mami Muka ji ta shigo ni ta hango Ina gudu,tace sai kin fadi ko Rabiah,Ina haki nace Sannu da zuwa Mami Ina murmushi

     Itama murmushin tayi tace Kuna lafiya,nace Bari nazo mu gaisa na shiga kitchen na kawo Mata abinci da ruwa da lemo sai fruits dana yanka,Nawwar Kuwa Zama yayi kusa da Maminsa Suka gaisa,zuwa nayi na durkusa har kasa na gaishe da Mami ta amsa da kulawa tare da furta Ina Sabreen din fa?nace tana dakinta,Kira min ita nace to na nufi sama har part dinta,bedroom dinta na tura Kawai na shiga na iske gabanta kayan maye ne iri iri,ta zuba garin Coccaine a yar takarda tana ta faman sheka tana bubbuga kanta idonta yayi jajir ta fita a hayyacinta,banyi mamaki ba tunda wannan shine Karo na biyu dana taba gani,Sanda nazo a matsayin Yar aiki na gani yanzu na sake gani,tana ganina tsoro ya kamata jikinta ya dauki rawa gashi tana wani fisge fisge ita kadai Murmushi nayi nace Karo na biyu kenan kinga da ace wata ce da tuni na tona Miki asiri,idonta Yana rufewa nace Mami ce ke kiranki,cinkin muryar Yan maye tace baaaa zaaaan iiiiiyaaaaa taaaaa shiiiii baaaa baaaaaaccci…..naaaaa…..keeeeee….ji…tana Gama fadin haka daga zaunen ta kwashe tarkacen ta tura kasan gadonta komai da komai ta fada saman bed sai bacci.

     Fitowa nayi jikina yayi sanyi ace mace ta maida kanta marar amfani a duniya daga bacci shike nan bata da lokacin komai, Palo na koma nace bacci take Yi,Mami tace ki taso min ita Magana zanyi daku dukkanku,nace dazu fa tace kanta na ciwo ta Sha magani shine ta dan samu bacci,idan ta tashi zuwa dare sai ya kawo mu har gida ni da ita inaga zai fi,Murmushi Mami tayi tace to tunda bakya so a tashe ta ,Nawwar yace ita wace baza ta tashi ba,kyaleta Zan dawo zuwa daren dama gidan kawata zanje idan na gama abinda nake sai na sake biyowa,nace to nan taci abincinta sosai Muna hira ta mike Muka rakata har mota ta tuka ta tafi,hadari ne ya hado sosai nace ya zaka koma ciki Kai da zaka fita,na fasa dama wajen Mami zanje Kuma ta zo anjima zata dawo,a Palo Muka zauna na kamo mana Nigerian film Muna kallo,aka yi abin dariya ni ban San me akace ba sai gani nayi Yana dariya,nace Allah sarki Jahila Rabi dan Allah ka dinga fassara min ba iyawa nayi ba kasan kadan nake tsinta nafi Iya pidgin English,ance a saki a school kin ki fafur, nace Allah ya kiyaye katuwa dani bazan gane komai ba ni yanzu me Zan iya a karatun boko ai Ni yanzu duniya ce a gabana,dariya yayi yace kin san baki da hankali Rabi wai anya dai dai kike kuwa,kina da auren kike fada min duniya ce a gabanki, baki na turo nace lokaci ma baya sauri ni na matsu a sake ni na Kama gabana,wato fadan da Inna ta Miki Baki ji ba kenan? banji ba ai ni bana ji ba a fada min naji,Allah ya sawwake miki Kuwa me yasa yanzu tunda aka kusa biki kika daina cewa kina son Sex? ko a taba miki boobs, dariya nayi nace laaaa Allah ya yaye min ji nayi na daina fada Kawai yanzu ma tunda aka Yi bikin naji bana son sex din na tsani Harkar ma burina yanzu a sakeni na tafi,mamaki ya kashe Nawwar yace wato ke duk abinda Allah baya so shi kike so,anyi aure ai dole a cinye ki,Fuska na bata nace ni wallahi yanzu bana so Kawai saki nake so,ji nake Yi Kamar Ina prison bana son gidan nan ban san Sanda na Fara hawaye ba gaba daya ji nake Yi na tsani gidan bana son Zama wani zugi nake ji a raina na rasa Jin dadin zuciyata

   Kallona yayi da mamaki ya zauna sosai tare da tambaya Wai da gaske kike yi? fashewa nayi da kuka sosai babu batun Wasa a ciki, Ido ya zuba min na kifa kaina a kujera Ina ta fama cikin muryar kuka nace dan Allah ka sake ni wallahi bana son auren nan, to naji kiyi Shuru,da kyar na kokarta tare da tsaida hawayena,yace idan na sallameki Ina Zaki? nace inda ka ka dakko ni,kinfi son can da nan? Na daga Masa Kai da sauri,yace to nawa Zan biya ki zauna na wata daya, nace ni bana son kudinka ko sisi Kawai ni ka yarda na tafi,yace missing dinsu kike yi? Nace ae ni kawayena nake son gani da gidanmu,idan na kaiki kin gansu zaki hakura mu dawo? Kai na daga Masa da ae amma nafi son sakin yafi min dadi

Ransa in yayi dubu to ya baci amma haka ya daure ransa a bace cikin fada yace bazan sake ki ba kiyi duk abinda zaki yi, Shuru nayi Ina Jin tsoron fushinsa a hankali cikin shagwaba nace to kayi hakuri zan dan sake jira,Tsaki ya ja nace I’m sorry na dawo gabansa na durkusa tare da daura kaina saman cinyarsa na kifa kaina sannan nasa hannayena na rungumo kugunsa Ina shakar kamshinsa me sanyi da dadi,kwafa naji ya ja a hankali na dago kaina Ina kallon yanda ransa yake a bace,nace fa kayi hakuri Zan zauna na daina ban San Ina yin wani abin ba sai dai naga nayi Allah Kuma Ina Jin zuciyata tana baci haka Kawai, banza ya min nace kayi magana nace kayi hakuri Please, saman cinyarsa na koma na zauna daram muna facing juna,ajiyar zuciya ya saki tare da furta washshsh…domin ji yayi gaba daya Yana Jin wata sha’awata Wanda dama kadan yake jira daurewa yayi da kyar yace ki dagani mana bana son Iskanci ya furta da masifa,nace to Kaine kaki yin hakuri,bazan Yi ba ko dole ne yace, hannayensa ya hade waje daya tare da lankwasa su Suka bada rukuss, kaina na kwantar a kirjinsa na narke a jikinsa,gashin kaina ya kalla wanda dama na cire dankwalin bayan tafiyar Mami,dariya nayi nace Mijin Sabreen kaga ko Watarana Seraline customer dinta yazo dakinmu Ina bacci,sai farkawa nayi na ganta a zaune a cinyarsa haka babu Kaya a jikinsu,tana haka na fara yin gaba inyi baya a cinyarsa nayi dariya na tsaya nace haka Suka yi,kallo na yayi sai da naji tsoro yanda Idonsa yayi ja har wani ruwa ya tara a ciki, tunawa nayi yanda nake ganin maza idan suna sha’awa ko suna romance.
Wise na tuna da tace idan namiji ya Kai wani stage na sha’awa Matukar bai kawo ba to babu macen da wani bazai nema ba,tambaya na jefo Masa nace sha’awa? Ido ya lumshe,dariya nayi nace kace Kai Ustaz dan Allah abun ashe dai Yana da lafiya,ai na zaci Ustazu ne baka ji,dan Murmushi yayi amma Sam baya hayyacinsa bai ma san ya tallafe min kugu ba da hannayensa ba

    Hannayena na saka cikin lallausar sumarsa ta bayan Kansa na matso da kansa saitin nawa na dora hancina dogo saman nasa ji nayi ya sake rikeni sosai a hankali na hade bakina da nasa na fara tsotsa Kamar Zan cinye Masa baki,karbewa yayi ya fini ma tsotse nawa bakin yana tande min shi,zip din rigata naji yana ja kasa nace wayyo yanzu bana so na daina so wlh dan Allah bana so ni karka taba min nono Ni bana so,kyalewa yayi tare da janyeni ta karfi daga jikinsa ya jefani saman kujera ta gefe ya tashi yaja tsaki yace ni mantawa ma nayi sabo da jiki da jini shi yasa karki kawo Zan iya kusantarki kaddara tasa na aureki amma ba abinda zan tsinta a jikinki tunda an riga maza da yawa sunyi me Zan ji,na kalle shi tunda nake sai yau naji zafin Maganar da ya fada min,nace to ka sakeni mana ko na maka dole ka aureni ka sakeni mana,shi yasa tun farko nace bazan Yi aure ba ni ban dace da aure ba,ba irin matar da za a aura bace,karshe ayi min gori a dinga zargina ko a goranta min ni Yar tsuntuwa ce Yar shege ce ni shi yasa nace bazan Yi aure ba ka nace sai ka aureni,jikinsa ne yayi sanyi sai yaga bai kyauta ba shima amma haushin na sa Masa sha’awa ko kulani baiyi ba ya juya tare da taka steps da gudu na Isa wajensa nabi bayansa Nima Muna taka steps na furta nace ka sakeni ka sakeni ka sakeni Yana juyowa ya kashe ni da maruka har uku tare da nuna ni da yatsa idan Kika sake min Maganar saki sai na Miki illa Yana rufe baki Sabreen na Fitowa ta tashi a bacci yau da wuri kasancewar bata Sha da yawa ba Kafin tazo kusa ina hangota da sauri na sauke Hannu na daga kumatuna na goge idona Ina murmushi me kyau a hankali nace wayyo kishiya ta gata nan ta taho kayi shuru zata raina ni,in taji sai tayi mana dariya juyawa yayi Yana tafiya na dafa kadarsa Ina cewa ban koshi da Kai ba My Salmankhan,my Sharukhan,gaskiya yanda dazu fuck din nan yayi dan Allah ka dinga hakuri Kar ka rame yawan sex Yana ramar da mutum,dariya ce ta mugun kamashi da sauri ya bude dakinsa ya fada ciki na bishi na banko kofar bam,Sabreen ta bimu da kallo tace da gaske saurin yake zasu Kara yi ai wallahi baza ta Sabu ba dole na tafi gida yanzu kuwa,Sabreen bata tambayi Nawwar ba sai karar mota muka ji,ta window na leka Yana kwance bance Masa ita bace,yace waye? nace Uwargida ce,hmm Kawai ya furta,Zan fita yace Ina zagi je? nace dakina,zo ki min kitso,Murmushi nayi nace to na haura saman bed din na zauna yana kwance Ina kokarin kitsa sumar amma yawan nata bai kai a kitsa ba haka na dinga cukurkuda Masa gashin amma sha’awa ta hanashi sukuni,Ina kallonsa na lakanci Sam baya hayyacinsa,ruwan sama ne ya tsuge me yawa na tashi na kulle windows na saki labile dakin sai yayi duhu dundum Kamar dare sabo da gari yayi bakikirin na hadari da ruwa na gaske, T-shirt dinsa na dakko na cire kayana na saka tasa,bai San me nake Yi ba ya juya baya ga duhu,so yake yayi bacci ma,Ina linke kayana daga kwancen ya tube rigarsa bai fiye bacci da riga ba sai boxers kawai ya kule a blanket,Rigarsa na dauka na linke na Adana har nawa kayan sannan na haura saman gadon,bai San na cire kayana ba,sai t-shirt da pant

   Nima bargon na Shige gefe,gaba daya na lakanci baya hayyacinsa tausayi ya bani,na matsa jikinsa ta baya na rungume shi,ajiyar zuciya ya saki me karfi,yaji sam kamar ma ba kaya a jikina hankalinsa ya Kara tashi har yana nema yayi loosing control,a hankali nace da ace Sabreen bata fita ba ai da ka je wajenta sai ta baka abinda kake nema tunda ni kaga maza sun gama dani, harda marina kana yawan dukana wlh duk Sanda haukata ta juyo kanka baza kaji Dadi ba,ka daina taba min lafiyar jiki,Indai nice barwa Sabrewn kwana na,a hankali ya juyo muna facing juna yace really? Nace ae na bar mata yace to ta gode bari ta dawo sai ki fada Mata da kanki a gabana,dariya nayi na sake shigewa jikinsa nace wlh bata Isa ba ko yau na haihu sai na karbi miji.

     Fuskarsa yasa tana saitin tawa a hankali ya shigar da bakinsa cikin nawa,yana min wani irin tsotsa ta musamman jikina ya hau rawa Ina Jin wani dadin da ban taba ji ba a jikina,amanna na bada sosai yana tsotsar bakina Ina tuna abinda Naga su wise suna yiwa maza na jiyar dasu dadi,kirjinsa na fara shafawa Ina taba nipples dinsa yaja wani ajiyar zuciya ya shide,to mu dai bamu da kunya a hankali na tambaye shi da dadi? yace yeah naci gaba da murza masa,bakina na sa a Kai Ina tsotsa zaucewa yayi tare da furta washshsh…ahhhhh…, Boobs dina ya kama a riga yana murza mun su cikin salo da kwarewa,nace wayyooo Zan haukace Baby dadi nake ji, surutai nake yi Ina nishi,rigata ya zare min tare da jawoni jikinsa,naji hajiya Babba ta mike ashe ya cire wandon nasa ma,tsoro naji ban taba sanin haka take ba sai yau gabana ya fadi,nace amma baza muyi sex ba ko? yace min ae yana dora bakinsa a manyan dukiyar Fulani na Sabo da ba karya a kwaisu sutu sutu a tsaye gwanin birgewa shi yasa Nawwar bai same su wajen Sabreen ba yanzu Kam abin nema ya samu shi yasa ya nace musu ya dame su da murza da tsotsa sai kace jariri baya min da zafi a nutse yake min komai, pant dina ya kama zai janye naki yarda yace ba sex zanyi ba fa ba abinda Zan Miki,nace Ni dai ban yarda ba,saki yayi tare da furta ni dai Ina Shan wahala kina gana min azaba wlh Ina cin ubana a wajenki ,dariya na dinga yi,nace to kawo kai na maka abinda kake so

    Hannuna ya kama ya Dora akan Antainarsa najita me tsayi ga kauri ta mike sankamkam tana huci da numfashi,nace Subhannallahi ke ki dinga salalawa kanki kaji tana motsi ita kadai kamar Abu me rai, dariya na bashi sosai amma kadan yayi baya cikin hankalinsa a hankali ya furta kisa naji dadi please Amaryar Nawwar, nace dama Inna ta fada a nan fagen kuka iya love ai shike nan,na fara matsa masa ita Ina sarrafata yanda naji su Sera suna fada,duk inda naji sunce in an taba a jikinta ana Jin dadi sai da nayi Masa Yana ta Nishin dadi Kamar ba Nawwar ba kunya babu shike bani salo Ina masa yanda yake so sai dan ihu yake Yana nishi, nace kayi kneel down ai Kuwa yayi nace shegiya harka anji harka sai abinda nace, a bako nasa Antainarsa ban taba Yi ba amma yawan ganin Bf a dakin su Wise yasa duk na sani na gwada Kuwa duk da naji ta cika min baki Kuma ta min yawa Kamar zanyi amai haka na daure tissue ya jawo a gefen bed ya bani ba ji ba gani Kawai na shiga sarrafa masa ita a bakina idan yawu ya taru na zuba a tissue,Yana Danna min can ciki na Fara kakarin amai abinka da ba a Saba ba,gurnani yake Yana Nishin dadi ya Kama gashina ya hade gaba daya tare da damkewa a hannunsa Yana yi Kamar yana sex, ni kuwa ba kunya nake ji ba idan na cire zan zuba yawu a tissue sai nace da Dadi? baya iya magana Sabo da a zauce yake Muka ci gaba da gashi Ina jinsa yana Kiran sunana yafi a irga Yana cewa da dadi,lokacin da zai kawo gashina ya damke sosai kamar zai cire min Kai,zarewa yayi zai zuba madarar tasa a tissue nace a’a ni ka bani na shanye Ina so minerals ne fa,a tissue ya zuba abinsa bai kulani ba,nace yanzu anyi asararsa abu me tsada,haushi naji ni naji ganin a Bf ana sha naji Kuma bana kyankyamin Nawwar ko kadan babu abinda nake kyankyami nasa,haushi naji na maida rigata na kwashe tissue dake kasa na zuba a bakar leda na fita na saka a dust bin na dawo ya zaci ma bazan dawo ba nayi fushi,na dawo na kwanta,juyowa yayi yace Fushi Kika yi?nace a’a akan Sperm dinka zanyi Fushi Allah yasa bature ya mana yogourt abinmu in Ina so gata can a fridge kaje da abinka,Ni tunanina ganin turawa suna lashewa suna wani Jin dadi na zaci zaki ne da shi Kamar Madara shi yasa na damu,dariya yayi yace to ki daina hada dadin yogourt da sperm ba hadi yogourt ai tafi dadi,nace ba wani ni zaka yiwa wayo Kawai Naga bakin ciki kake min baka so naji dadi kaje ka bawa Sabreen dan Allah idan ta Sha a fasa Mata kofa sabo da kiba,Zan Sha yogourt dina haka,Ni zaka yiwa wayo gashi nan ana Sha ana cewa baby you are Sweet ayi ta cewa sweet,honey,sugar mace an dildila Mata a baki kaga ta zauce ta fita hayyacinta tana lashe lashe ai dama nasan yafi yogourt dadi kuma ai shike nan Dan an hanani sabo da ni bani da gata bani da iyaye ba kowa bace ni ba komai rayuwa ce,Nawwar dariya ta kamashi yace Wai ke kamar ba Yar duniyar ba in Kika Yi wani abin Kamar baki San da Namiji ba,Shuru nayi Kawai inaso duk Sanda ya kusanceni ya Sha mamaki,bacci ya kwasheni,shima Yana yin Shuru sai baccin ya samu nutsuwa sosai.

     Sabreen gidansu taje ta fashewa da Mamanta da kuka tana fadawa Mama yanda Rabiah ta mallake Nawwar,Mama tace kinga naga Alama Iyamami baza ta iya komai ba,Papanki da ita Naga Kamar bakinsu daya da Baffa zasu dinga Mana karya wai tunda ya tafi sau daya ya kirasu Kuma wayarsa bata shiga kiji a son zumuncinsu nasan Baffa bazai taba Mana haka ba Yana kaunar danginsa Kawai na lakanci Iyamami da daurin gindinta aka Yi auren,ke babanki ma ban yarda da shi ba,kin san shi da son kudi dama sabo da kudi ya nace sai kin Auri Nawwar sabo da ya mallaki kadarori to gashi ke kina wahala ko cikin baki samu ba shi Kuma Bai samu kadarar ba,Kawai yanzu da kaina Zan dauki mataki ki tashi ki koma gidanki kiyi Shuru zanzo jibi zan kawo miki abinda ya dace,Sabreen tana shesheka tace ya kamata kiyi sauri Mami abin yayi yawa,karki damu tashi ki tafi Kar ma wani ya ganki, Sabreen ta mike ta fito ta shiga motarta sai gidan Jamcy, tana zuwa nan ma Jamcy ta bawa labarin komai,Jamcy a ranta tace nima yanzu haushin Karuwar nan nake ji ta hanani shiga gidan Sabreen dole mu hadu mu koreta,Nan take Jamcy tace ki bani sati daya zamuje wani kauye ki dai San karyar da zakiyi ya barki,Sabreen tace yo ni ai bana tambayarsa duk inda naga dama zuwa nake,Jamcy tace to ki tanadi kudin jirginmu da dubu dari biyu,Sabreen tace bani da sisi yanzu haka ma Coccaine Dina kadan nake Sha sabo da Kar ta kare kafin na samu kudi amma karki damu dole ko satowa sai nayi a dakin Nawwar,tafawa sukayi sannan tace tafiya zanyi ta mike ta shiga mota ta dakko hanya.

     Sai wurin magriba na farka na ganni a jikinsa ya kankameni, jikina na janye sai kuwa ya farka nace tashi magriba ta kusa Kar ka rasa Jama’i,wanka ya shiga yayi wanka ya tsarkake jikinsa sannan ya fito,Ni Kuwa na kwashi kayana Ina part dina wanka nayi nayi Sallah sannan na fito sanye cikin rigarsa me dogon hannu ta kawo min rabin cinya a haka na fito sabo da tsona,kida na kunna a speaker Bluetooth na ajiye a kitchen Ina girki Ina cashewa na hada da karamar wayata,na cika gidan da kida, ana yin Sallar Isha na kashe naje nayi Sallah na dawo na sake kunna kidana da guntuwar rigarsa gata me santsi ruwan zuma, banyi abinci me wahala ba,a dining na shirya komai,na koma na gyara kitchen din Ina wanke wanke Ina cashewa,Nawwar sai da yayi Isha sannan ya dawo gida, Yana shigowa Mami ma ta dawo gidan,Sabreen ma ta dawo,Mami tace badai gida Kika koma ba Sabreen,baki ta zumbura tana murguda baki lokacin shima Nawwar ya same su a compound. Suka shugo gaba daya suna ta sallama amma kida yasa bana ji,Mami ce ta leko kitchen din juyawa tayi Kawai ganin shigar dake jikina rigar Nawwar dinta na saka Kuma Ina ta rawa Ina wanke wanke,Murmushi tayi tace yara kenan basu da damuwa,Nawwar ne ya shigo da kansa ganin rawar da nake sai na birge shi gaba daya ya shagala da kallona rigar tasa ta min kyau,juyowa nayi na ganshi to ba kunya garemu ba gabansa na tako Ina rawata,Hannu yasa tare da kashe kidan Yana Murmushi yace Mami tana jiranki,Ido na zaro nace dakko min hijab dan Allah,yace ai ta riga ta ganki,ni dai ka dako min hijab,Fitowa yayi yace gata nan yaje dakina ya dakko Hijab din da ya gani a gefen gadona ya dawo ya Kai min na saka har kasa sannan na fito na samu Mami a zaune da Sabreen,nace Sannu da zuwa tace yawwa,durkusawa nayi na gaishe ta Wanda Sabreen Kawai cewa tayi Ina yini daga haka bata sake magana ba,Nawwar zaiyi magana Mami ta Hana sabo da Sabreen gida zata je tayi sharri Iyamami da Baffa su ci Mata mutunci sabo da Haka Nawwar Yana gani Sabreen tana abinda taga dama amma baya magana Sabo da Yana cewa wani abu to akan uwarsa zata yi wabi akan ran Maminsa ya baci gwara ya rabu da ita iya kaci ya Mata nasiha idan bata ji ba shike nan.

    Mami hada mu tayi ta Mana nasiha sosai akan mu zauna lafiya,Sabreen tana ji tana yatsina fuska sabo da raini,Mami tashi tayi nace abincin fa,tace Alhmdllh nace Wai Ina Auta ne da su Sultana sunki zuwa,Zasu zo ne Inshaallah cewar Mami nace Allah ya kaimu,Nawwar ne ya raka Mami motarta shima ta Masa nasiha sosai sannan ta tafi.

      Yau ma a dakina na kwana bai neme Ni ba Nima ban je ba,washe gari ma Sam bamu hadu sosai ba sai wajen cin abinci sabo da bai yini a gida ba wani abu ya taso a Office,yau kwana na Uku yauma da sassafe ya fice,yau Kuma Mama ta zo da rana ta sameni Ina Kujeru,ko kulani bata Yi ba Ina ta wuce sama Kawai bangaren yarta,Sabreen ta gama gyara dakinta kenan tayi wanka Mama ta shigo,tana murna suka gaisa Mama ta zauna tare da furta sauri nake Yi ta zuge Jakarta ta dakko wani garin magani da wani ruwa ta mikawa Sabreen tace gashi sai kin bari ba kowa Zaki tube kayanki ki kwaba maganin da wannan ruwan sai ki shafe jikinki da maganin idan ya shigo ki tabbatar a gidan da ke ya Fara tozali Kuma ki tabbatar shi kadai ya ganki shima ke kadai ya gani,Yana shigowa Kawai zaninki zaki cire ya kalleki tsirara da ya ganki a zigidir da maganin a jikinki to an gama shike nan kin mallake shi,amma idan Kika bari wani ya ganki ko kishiyarki to magani bazai aiki ba Kuma baya bada shi sau biyu sau daya yake bawa mutum ki kiyaye abinda ake ciki ki fada min a waya,Sabreen tana murna tace ai Kuwa ya fita gaf yake da shugowa yanzu yayi Amarya ba ya dadewa.

    Ni kuwa Ina gama aikina da girki na koma dakina nayi wanka na kwanta sai bacci,Sabreen har dakina ta leko ta tabbatar bacci nake yi,Nawwar ta Kira a waya ya daga tace ka kusa dawowa ne? Yace Ina Hanya mene? ba komai ta kashe wayar,da sauri ta tube zindir ta kwaba magani tare da shafe jikinta yanda akace ,tana Jin dirin motarsa ta daura zani Kawai ta fito main palon kasa ta dan labe,ai yana bude kofa ta bude zanin data daura gaba daya ta rike gefe da gefe,haihuwar uwarta tace My love I need you Sai da ta tabbatar ya kalleta sosai sannan ta maida zanin ta daura,tana kallonsa ta sandare a wajen ganin Nawwar da wani Wanda suke business ya sauka daga Canada yazo gidansa, kunya da bakin ciki Suka lullube Nawwar,abokin aikinsa Rayyan yace wannan fa kalau? Nawwar yace Aljanu ta hadu dasu tun da dadewa yace eyya sorry na ganta ban San zata Yi haka ba,Nawwar yace ba komai,Zama suka yi a palo, Rayyan ya fahimci Nawwar baya hayyacinsa sai ya daga Wayar karya yace nemansa akeyi akwai matsala,Nawwar yace ai baku gaisa da wifey na ba,kafin ya rufe baki na fito cikin adon leshi riger da sker dark brown.

    Gata nan ma,Rayyan yace wannan ce matar taka waccen fa? yace itama ita uwar gida ce,Rayyan yayi dariya tare da furta wannan Kam tayi Allah Sanya Alkhairi yace Ameen,karasowa nayi tare da Zama na gaida Rayyan da fara’a,Nawwar ya furta Wai so yake ya tafi,nace tun yanzu wannan ai ba zuwa kayi ba bamu karbi wannan zuwan ba gaskiya ko abinci ai kaci,dining Muka koma nayi serving nasu suna ci Rayyan sai Santi yake Ina dariya,bayan Nawwar na koma na tsaya hannayena suna saman kafadunsa dai dai wuyansa ina masa tausa a wajen wuyan Yana cin abincinsa, Rayyan yace nima dai Zan bada himma nayi auren nan,dariya nayi nace ai gwara dai duk suna maka wayo kana zaune a gwauro,Gane min hanya Mamana ta gaji da ni,sai da Suka gama cin abubuwan dana hada sannan Rayyan ya mike tare da furta Amarya kin iya girki gaskiya mashaallah yau sai na bada da labari,godiya nayi ya zaro kudi dubu Hamsim ya ajiye min a table,nayi godiya yace ba komai,Nawwar rakashi yayi har katuwar motarsa ya tafi shi Kuma ya dawo gidan.

     Yana dawowa gida direct dakinsa ya wuce ya fyalli takarda ya rubutawa Sabreen saki daya ya fito ya shiga part dinta,sake isketa yayi tana kwaba wani maganin tana shafawa a jikinta,takardar ya jefa Mata yace kije na sakeki saki daya sai kiji dadin yin tsafin a gidanku,Sabreen maganin ta jefar a kasa tare da kurma uban ihun da yasa nayi part din nata,a ciki na ganshi nace lafiya Sabreen ashar da zagi ta hau dura min ta uwa ta uba har da cewa tunda Kika sa ya sake ni wallahi kema sai an sakeki sai nayi sanadin fitarki a gidan nan, Nawwar na kalla nace au sakinta kayi ai sai ace Dan kayi Amarya ne ai duk irin dadin da kake ji a wajena bai kamata ka saketa,Haba Honey nasan kana Jin dadi a jikina yes kana samu nutsuwa yanda kake fada min baza ka iya Zama da kowa ba sai ni amma bai dace ka saketa ba, tsaki yaja ya juya, Sabreen tace wallahi ba inda zanje Zama daram ka saki banza wofi, ficewa nayi abina shima yayi gaba.

     Gaji amarci Kawai suke kwasa da tayi Niyyar barin gidan yanzu mugun kaunar juna suke Yi ita da mijinta Danbinni,Zayya Kuwa haukar kishinta takeyi Kawai kullum sai sunyi fada da Gaji dake gaba dayansu basu da hakuri,Danbinni kudin cefane ya bawa Zayya yace gashi idan Gaji ta tashi a bacci ki bata shinkafa da Miya za ayi dama shi baya son Mai da yaji,Gaji tana tashi a bacci Zayya ta watso mata dari uku ta cinye dari bakwai, Gaji ta zaci baida kudi Kawai ta dafa wake da shinkafa,sai da ya dawo ya dinga fada Yana yiwa Gaji Sababi,Gaji tace to ai kudin baza su Isa ba dari Uku fa ka bayar,wacce dari ukun? Haka Zayya ta bani,yace ke Zayya ke…Zayya ta fito yace Ina dubu dayan da na baki na cefane, Zayya tace ita fa ta bawa Gaji kudi,Gaji ta hau rantsuwa ita sisi ba a bata ba sai dari uku,Danbinni gaba dayansu ya hada ya musu fata fata Gaji ta yini tana kuka an Mata sharri.

    Maryam Mairo yayar Gaji wani Dan daba ne a school dinsu ya nace Yana sonta ita kuma bata sonsa ko kadan har Suka gama school Suka dawo gida bai San garinsu ba sai yanzu Najib ya samu address dinsu, mugun kaunar Maryam Mairo yake amma taki sonsa ko waya in ya mata bata dagawa,gaba daya ran Najib ya baci cikin yaransa yan daba Suka je har gidan Dagaci cikin dare Suka sace Mairo,Gwaggo sai ihu sukeyi bayan tafiyar Yan daba a motarsu cikin daren mutane Suka cika makil ana jajanta musu,Gwaggo tana ta faman kuka tana na Shiga Uku Mairo ta Yan kidnapping basu San zafin haihuwa ba wlh da sun sani da basu saci dan wani ba,Dagaci sabo da duk yaransa yafi kaunar Mairo shima sai da yayi kuka,Mairo Kuwa sun shaka mata Abu bata San Ina take ba har cikin garin Kaduna inda Najib yake gidansa yasa a kaita wani flat me dan kyau cikin bedroom ya Kai Mairo tare da kwantar da ita a saman gadonsa, ya sa Mairo a gaba Yana bulbula taba sigari.

Masu bukatar sauraron audio na wasu novels Dina ku duba YouTube channel  S ZARIA TV

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               66-70

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Maman Ibtisam
Maman Murtala
Mum Basma
Rahama Mamuda(Maman Hajiya)
Gwaggonsu
Mamu Galadima
Ummul Ayyan
Fa*eeza
Jannat collection

      Mairo tana bacci sai washe gari da safe wurin 11am ta farka da kuka,Ido hudu tayi da Najib a zaune a gabanta sanye cikin gajeren wando baki da singlet,Najib baki ne kyakyawa Masha Allah,Mairo tsoro ya kamata tace Najib kayiwa Allah ka maida ni gidan Iyayena ta rushe da kuka,sigarin dake hannunsa ya kashe cikin muryarsa katuwa ta Yan daba ya furta kin San Ina sonki Mairo ki yarda ki aureni ko me kike so zanyi Zan daina abinda bakya so,Mairo tace Allah ya kiyaye wallahi bana sonka bana kaunarka Kuma har abada bazan so ka ba,murmushin yake yayi ya mike yace kiyi wanka ga toilet nan nima nayi wanka ya fice abinsa,Mairo ganin ba sarki sai Allah ta mike ta Shiga toilet din fes da ita Kuwa taga sabon brush ta dauka tayi sannan tayi wanka tare da daura Alwala tana Fitowa ya shigo dauke da abinci da Kaya kala uku a Leda ya ajiye Mata tare da ficewa ya barta,a gurguje ta duba kayan taga dogayen riguna ta dauki Daya ta saka sannan ta zauna taci lafiyayyen abincin da ya kawo Mata sai da ta gama ta koma saman gadon ta kwanta tana hawaye,Shugowa yayi daga shi sai boxers Yana Murmushi ganin har abincin ta ci yace ko ke fa,wata Allura ya dakko a saman mudubi ya zuka,Mairo ta zaro Ido tana Wai me zaka min,bazan cuceki ba kin sani dadi zamu ji, Mairo ta mike zata gudu ya damko ta tana hannunsa ya riketa ta karfi tana ihu sosai yayi sauri ya Kama hannunta ya riketa ta ko Ina sannan ya Mata Allurar a damtse,Nan take jikinta yayi wani sanyi ya saki motsi ma kasawa tayi.

    Tana ji tana gani ya dauketa ya dorata saman gado ya zare Mata kayan jikinta gaba daya,komai nata ya bayyana a waje,Kirjinta a cike tantsam gigicewa yayi ya Fara kissing dinta a baki mairo sai dai hawaye Kawai amma baza ta iya komai ba,kirjinta yake murzawa Yana tsotsar bakinta sosai cike da kauna ya rude Yana aika Mata da sakwanni tana Jin komai tun bata Jin Dadi har ta Fara ji jiki da jini kasa tabuka komai tayi sai dadin da kawai take ji,hawaye na zubo Mata kamar famfo haka ya samu ya buda kafafunta ya shigeta a hankali ya dinga ragargazar dadinsa Yana ihu Yana furta dukkan kalaman da suka zo bakinsa,ita kuwa Mairo zafi da azaba yasa ta barke da mahaukacin kuka amma ba kuzarin kwala ihu,ya dade yana Abu daya har ya samu gamsuwa,dama shi Kam barshi wajen daba da shaye shaye a
Mata sai sama sama idan baya sonki bazai kwanta dake ba amma Matukar sonki ya darsu a ransa to gwara ma ki so shi a daura muku aure idan ba haka ba zai nema ta hanyar banza,Baban Najib likita ne Babba Kuma babarsa lecturer ce shi kadai Suka haifa sai abinda yake so iyayensa Kawai sai dai su bashi kudi,karatu ma shi Degree yayi a makarantar su Kuma su Mairo NCE,yaki yin aiki yaki sana’ar komai sai dai a bashi kudi da motarsa me tsada,asalinsu Yan Jigawa ne amma a Kaduna suke zaune,Yan Mata uku ya taba so Kuma dukkansu sai da ya dinga sex da su daya dama Yar duniya ce shi yasa take yin family planning bata samu ciki ba har tayi aure,ita kuma dayar shi ya lalata har ciki ya Mata ya kaita aka zubar ta samu Miji tayi aure,Mairo Kuwa son da yake Mata na aure ne amma taki yarda sam.

    Bangaren Dagaci da Yana Shirin zuwa ayiwa Rabiah asiri ta koma Neman maza da Aurenta yanda za a saketa har abada sai Katsam aka sace Masa Mairo har gida shike nan ya daina zancen Rabiah gaba daya Suka bazama wajen Malamai suna ta faman bada kudi Allah ya fito da Mairo,Gaji tunda taji labari tazo gida tana cewa tun bikin Rabi da naji nace zanzo naci ubansu sai Danbinni yace idan na fita a bakin aurena shi yasa ban Zo ba,yanzu Mairo shike Nan yanzu haka tana can ana jibgarta suna ta jimami kwananta biyu sannan ta koma gidan mijinta
Dagaci yana tsaye ya kalli arewa ya tsurawa sama Ido Kawai abin duniya ya masa zafi Yana son Mairo fiye da komai a duniya,hawaye ne ya digo Masa ya goge da sauri Jin yaransa maza sun shigo gida da gudu suna fada Masa Baba miciji ya sari Audu babban dansa a maza,Dagaci ya bazama ya fice da sauri tare da Imrana da karamin,Suna zuwa Suka iske Audu a kwance Yana lumshe ido,Dagaci yace yaushe abin ya faru tunda kuka ga ya sare shi ai sai ku taho gida,ya dauki Audu ya wuce da shi wani Kauye gabansu kadan inda ake bada maganin miciji,Gwaggo tana ganin Su Imrana tace ya Audun? an tafi da shi wajen magani,Aunty Amarya tace ai miciji ne ana warkewa ana bashi magani Zaki ga ya warke,Gwaggo tace ae ai ya taba cizon Ladi me awara itama a gona kamar Audu na,Kuma gashi ta warke,Dagaci Yana zuwa aka dinga bawa Audu maganin miciji Yana amai dama amai ake so yayi ya dinga zazzaga Amai Kamar ba gobe har Audu ya fice a hayyacinsa ya Fara Suma,Me magani abin ya daure Masa Kai yace ai Yana Amai da yawa ai shike nan amma Suma yake,aka dakko ruwa ana shafe Audu ko minti biyar ba ayi ba Audu yace ga garinku nan, Dagaci yace ya mutu ya tashi a fusace ya shaki wuyan me magani ya dinga dukansa a baki da hanci sai da yayiwa me magani jina jina,mutane Suka shugo da gudu ana kawo dauki matar me magani ta fito itama tana kuka,Dagaci yace wallahi Kaine ka kashe min yaro,masu rabon fada Suka ce kwanansa ne ya Kare ba magani bane micijin ya dade da cizonsa ba a dauki mataki ba,Dagaci yace wallahi karya ne ba ruwan Allah shine ya kashe min yaro ya dinga zazzaga bala’i da zagi iri iri yayi fatali da magungunan bawan Allah yayi fata fata da kayan dake dakin me magani kowa Yana kallonsa har ya gama sannan ya juyo ya nuna me magani da yatsa yace Zan dawo kanka wallahi tunda ka kashe min yaro sai na dauki fansa sai na kashe ka nine ajalinka ya dauki gawar Audu ya goya a bayansa mutane suna Allah ya shirya ya fice ya hau machine dinsa sai gida,Gwaggo da Aunty Amarya suna ganin gawa da sauran yaran Suka Fara zunduma ihu a unguwa dama a kauyen haka akeyi, kowa yasan anyi mutuwa a gari,tuni labari ya cika gari,Gwaggo tana kuka harda dirza goshinta a saman siminti

    Tana wayyo Allah na shiga uku Auduna,Audu ba karamar wahala na Sha ba da cikinsa haka haihuwarsa Naci azabar da ban taba ji ba,Wayyo Audu na shiga Uku na lalace,ita Kuma Aunty Amarya sai ta leka gawar Audu ta dawo dakinta da sauri tace oh Audu nawa yaro sarkin zuciyar nema Indai da Audu to bani da matsala na shaku da kai Audu sai ta fashe da kuka,Dagaci ne ya bugawa Gaji waya ya fada mata Gaji tana Zaune tare da Danbinni ta mike zumbur tace Audun mu kanina ya mutu me magani ya kashe mana Audu nan gaba Audu shine zai Zama uban mu idan ba ran Baba,wayyo ta fice tsakar gida da gudu tayi wuri wuri ta dawo ciki da gudu tace Danbinni Audu babu fam fam,Zayya tana ji tace harda cewa Kamar a kansu aka fara mutuwa halin tsiyar ku ma ya jawo muku,Gaji ce ta fito da katon Hijab zata tafi gida ta kalli Zayya tace murnar mutuwa murnar banza gobe zata iya fadawa danginka dan kinyi murna Ina nan zanji ta fada kanki banza akuya,Zayya ta mike tana bala’i ni na kashe Miki Audun me ya dameni,Gaji tana cikin zafin mutuwa bata San Sanda ta dauki Zayya tayi sama da ita ta dokata da kasa ta tsallake ko juyowa bata Yi ba ta fice,Danbinni ya kalli Zayya dake murkususu a kasa yace ke Kika jawa kanki ya taimaka ta mike sannan yabi bayan Gaji ya sata a mota ya bata kudin mota yace sai gobe zaizo ta tafi.

      Gaji tana zuwa gida ta iske har an Kai Audu sai Yan zaman makoki, ciki ta Shige tana kuka ba Wanda ya kula ta wuce ta kwantar da kanta a kafar Gwaggo itama Gwaggo zuciyarta ta sake karyewa Suka fashe da kuka a tare sabo da Gwaggo ita Kuma tafi son Audu duk cikin yaranta, Mata a cika dakin Yan uwan Gwaggo Dana Dagaci da Yan gari Suka ce sai hakuri kowa na haka ne,Gwaggo tace yaron nan badai yaci zalin wani ba sai dai aci nasa,Haka abinci idan akaci yace Gwaggo bari na miki shara yaron nan haka zai share min dakina tas,har wanke wanke wallahi sai dai idan baya gida,Watarana yace Gwaggo idan nayi kudi Zan kaiki Makkah nace to Audu na ashe Audu bazai rayu ba,na Gama sa rai Audu idan yayi kudi zai kaini Makkah Gwaggo ta fashe da kuka, Aunty Amarya tace Audu kullum yaron nan ki duba kullum Yana dakina komai yace Aunty Zan Miki,hattana wankin nan bana Yi a gidan nan Audu ke tattarawa yayi min,Gaji tace haka wacen satin da yaje gidana yace Gaji ni dai dari biyar Zaki bani na dakko na bashi yace yawwa watakil ma baza ki sake bani ba har abada  to ba sai ma na sake dawowa gidan naki ba,Yan dakin Suka dauki kalmar Allahu Akbar yaji ajikinsa su Gaji suna ta kuka Kamar ba gobe.

    Sabreen a waya ta Kira ta sanarwa da Mama da Papa tare da Iyamami,Iyamami har part din Mami taje taci mutuncin Mami tace Kuma wallahi Matukar bai dawo da Sabreen ba baza kiji da dadi ba,Mami ta kalleta Kawai tace shashasha Jahila Wacce bata San me take ba,Mama ta ja kwafa tayi waje, Lokaci Amaryar Baffa Ummin Haidar ta shigo sashen Mami taji abinda ke faruwa bata ce komai ba sabo da ita duk abinda ake Yi a gidan bata Shiga daga ita sai yaranta sai danginta miji ne Kuma a hannunta yake sai abinda tace to mene abin da zata zafafa shi yasa har wajen Mami take shigowa idan taga dama,tana Jin ma abinda ake magana akai Kawai ta fice ta koma part dinta ta dauki waya ta Kira Sahibinta Baffa suka shiga hira suna soyewa ita Kuwa Mami bata San ma number dinsa ba in Banda ta Nigeria,Iyamami tana Gama masifarta Mami ta Kira Nawwar, Yana Shirin fita ta Kira wayarsa,dagawa yayi suna gaisawa tace da gaske ka saki Sabreen? Nawwar a Palo ya zauna ya bawa Mami labarin abinda tayi,yace dama na gaji wallahi da abinda Yarinyar nan ke min,Mami tace kayi hakuri Nawwar ka maidata dakinta,zaiyi magana tace bana son ji umarni na baka kawai, to kawai yace ya kashe wayarsa ya fita abinsa bai dawo gidan da wuri ba ma har 11pm Shuru Shuru,gajiya nayi da jiransa ga abinci Ina ta gadi sabo da Matukar kana da kishiya to sai ka kula da abincinka sosai Kar a hada maka mugunta Ina Palo Ina gadin abinci,har naje nayi Shirin bacci cikin Yar guntuwar rigar baccina Purple Ina zaune a palon har na Fara gyangyadi,wayarsa na Kira bata Shiga ba naci gaba da jira,sai gashi ya dawo ko karar mota banji ba sai sallamarsa naji Kawai Ina dan gyangyadi na,idona na bude a hankali na kalle shi Ina murmushi na amsa sallamarsa tare da mikewa nace Sannu da zuwa yace yawwa shima da Murmushi Yana kallona rigar baccin ta Masa kyau nayi kyau a ciki,yace baki bacci ba?

    Ina ta jiranka ko lafiya ko ba lafiya ban sani ba gashi Ina ta kiranka taki Shiga,ya kalleni tare da cewa ashe kin damu dani haka? Ido na lumshe na bude su tare da cewa mace da mijinta ta ya baza ta damu da abinta ba, haka Kawai ya tsinci Kansa da Jin wani dadi a ransa har ya kasa boyewa sai da ya murmusa,nace abincin fa,wanka zanyi,nace no ai gwara kaci Kawai idan ka tafi sama ba sakkowa sai bacci ai yafi dadi,hannunsa na riko Muka zauna a dining nayi serving nasa ya dauki Spoon yana cewa Wai ke duk a wannan kazamin gidan naku Kika iya girki haka kullum da Kalar da kike yi,dariya nayi nace da fa Sanda nazo daga Kauye cewa nayi bazan Yi Iskanci ba,ba Wanda Zan bawa jikina,Kuma a gidan babu me baka abincinsa kyauta komai ba mutunci sai da kudi,kaga duk yanda muke da su Sera da ace yanzu Zan koma da Zama can to sai nayi bariki babu me iya bani ko ruwa kyauta,to da nazo gari Seraline ta dauki nauyina na 2wks kullum tana ce min na Fara fita street naki yarda,shine tace to baza ta sake ciyar dani ba tayi kokarinta sannan dakinta bazan kwana free ba sai na Fara biyan kudin haya,sai nace ni dai bazan siyar da jikina ba sai nace da Zan samu aikin wanke wanke da shara da nayi,sai tace ga masu dan kudi ne a gidan tsab zasu biyani,lokacin ta hadani da Wise,Star da Yar Zabil na Fara musu girki da ayyuka, aike etc kullum a gidan ana rainani ana min kallon banza,dare Daya naji babu abinda nake so face na fara karuwanci burina ya dawo Kawai so nake na shahara a karuwanci sunan har wani dadi yake min,Kamar fa me Aljanu lokaci daya naji idan ban fara Karuwanci ba sai naji kamar ma ni ba mutum bace Kawai burina ni dai maza su daukeni su bata ni, gaba daya kunyata ta gudu dama Zama a gidan tunda a gabanmu har sex ana yi,zancen banza tun kana da kunya har sai ta gudu,ai tunda na sa a raina Zan Fara duniyanci gaba daya sai da nafi Yan gidan fitsara amma lokacin ko an fita dani kwalta sai dai na gama tallan jikina a titi Ina azo aci dadi motoci maza iri iri suna zuwa sai nace sai idan za a biya daga million daya zuwa sama sabo da Headquarter  dina a cikin GRA take komai akwai ciki, kowa sai yayi tafiyarsa hmm ai an Sha fama Kawai na yanke Masa labarin iya nan ganin Sabreen ta fito ta wuce kitchen,nace kaci abincin ka tsaya kana kallona ko spoon daya baka ci ba,labarin naku ne ba dadin ji,spoon din na karbe nace kawo na baka a baki,sake karbewa yayi abinsa ya fara cin abincinsa da Kansa

   Sabreen ce ta fito ta ja tsaki tace aikin banza wa Zaki nunawa kula da miji,Nace ke Zan nunawa ke me Kika iya idan ba bacci ba,zuwana gidan nan bawan Allah bakya bashi hakkinsa gashi nan daga zuwana sabo da yawan amarci gaba daya na kwashe Vitamin c da b da e da a da d da f duk na kwashe su a jikinsa Babu Saura ko daya na barki nan, ke gashi nab kullum sai karmashewa kike Kamar ana yankar Naman jikinki ana Miya da shi to Babu Minalerals duk na hada na kwashe daga jikinsa ba abinda Kika iya sai fada, da bala’i Sabreen tace ke har wani dadi zakiyi,nace fes ma kuwa domin ance yanda bakin mace yake Kato can ma haka yake Kato,karamin Baki karamin can wajen.

   Nawwar Yana jinmu ya gaji da fadanmu ya mike yace yanzu ku duk akan wannan kike fada ya nuna Antainarsa Yana cewa to ku yanke ku rabata kowacce ta dauki tata, nace kawo wuka kaga aiki dariya yayi yace muje ya janye ni, Sabreen tana tsaye sororo,Ina tafiya Ina girgiza Mata jiki nace muje Oven ya dauki dumi sai gashi kawai ya kamata a sa min memory Ni kaina dariya nayi nace yau da Sabreen taji kida Kuwa iri iri,yau Nawwar ba bacci sai kida Kawai na juyo na zuba Mata gwalo nace Wakar Sangaya zamu kamo, dariya ta Kama Nawwar yace wai dick din nawa ne Memory dinki? Nace ae Mana a saka shi cikin cellular sai kida da Sabreen ta Sha kida irin irin sai dai ta toshe kunnenta yo Ango yaji gashi a Oven,Nawwar ya dinga dariya iskancin nan na Rabia ya ishe shi.

   Satinta biyu su Sera Suka zo min yini naji dadi mun tsula tsiya a gidan,da guzirin magangunansu na Mata washe gari kuma Baffa ya dawo gida,ko hutawa baiyi ba Papa yaje Masa da zancen auren Nawwar, barazana ya dinga Yi yana fada yace zan sa Nawwar ya saketa dole.

   Haka muke zaune rayuwa tana tafiya sai dai nayi girki na gyara gida Sabreen da Nawwar suci su koshi,tun sau daya da ya taba romancing Dina washe garin kaini bai sake ba Nima ban sake ba,Muna zaman mu a haka na matsu ya sakeni na tafi tunda har na kwashe satikai a gidan Nawwar na gama gajiya da gidan,baya Zama sosai ya koma aiki sosai,Ina Shirin damunsa akan ya sakeni, yau ya dawo bayan yaci abinci dakinsa na bishi har yayi Shirin bacci zai kwanta na shiga fuskata ba walwala,Yana kwance a saman gadonsa Kawai na tsaya a kansa na turo baki Kuma na kasa magana,kallona yayi yaga naki kallonsa Kawai na tsurawa bango Ido,dariya na bashi ya murmusa ya dago ya sake kallona na sake cuna baki gaba,hannunsa ya mika saman drawer ta jikin gadonsa ya dakko wasu takardu tare da Miko min su,nayi banza da shi ban ko karba ba.

    Yace rike cikewa zakiyi form ne na biya Miki aikin Hajji,zabura nayi na juyo da sauri na washe baki nace Allah? yace Zan Miki karya ne,ihun murna na saki tare da dira tsalle na dire a Kan kafafuna nace na fasa tambayar sakin karka sakeni kaji na fasa barin gidan Ina nan tare dakai ko Watarana nace ka sakeni ka kwada min Mari biyar ka cimin mutunci ko ka fada min bakar magana kace Yar tsuntuwa Yar kwararo,dariya yayi yace ba ruwana bare kice nace, takardun na karba na kalla nace Allah sarki ashe kana sane dani, takardun na ajiye da sauri nace me kake so Fadi ko Mene zanyi,yace bana son komai,na nuna gabana da hannuna nace dan baka sani bane kake gudun Oven dina a tsaftace yake kana cutar kanka baka sani ba,yace Indai wankewa ne da ruwa dama a tsaftace yake Mana,zancen na share na haura saman bed din,da sauri ya dauki pillow Yana dariya ya rufe fuskarsa pillow din na fisge yasa hannaye tare da Kare fuskarsa Ni Kuwa ko Ina kiss nake masa har na rike hannayensa biyu ai Kuwa ya maida labbansa ciki ya danne sai habar kawai

   Nace au hakane shikenan hannayensa da na rike da hannayena na dora saman manyan boobs dina nace ai akwai  wani idan kaki kiss,Ido ya  bude ya kalleni Muka hada ido nace kasan mu fa Indai rashin kunya ce to a cikinta muka ginu,gwara ma ka taba,yace sakar min hannu,a zuciyarsa Yana cewa Allah yasa Kar ta saki hannun wlh dadi ne da ita ko hannuna ta rike Kamar zan zauce haka nake ji, ai Kuwa sakin hannun nayi na tashi na kwashi takardun nace na iya rubuta hausa da karantawa,turanci ma Ina dan iya rubuta wani abin kadan na karanta kadan bazan iya cikewa ba sai dai na fada maka ka cike,yace shi yasa nace na saka ki a school kinki,nace nifa Allah bazan iya karatun boko ba yanzu babu karatun da zanyi Zan dai iya yarda idan ka kawo min malamin turanci ya koya min karatun turanci da rubutu shike nan Kawai dama kaga Ina tsintar wani Kuma na iya pidgin ba laifi,yace to shike nan.

    Tashi yayi yana tambayata abubuwa Yana cikewa har ya gama sannan yace Saura passport gobe ki shirya da wuri 8am zamu fita a miki,nace to Allah ya kaimu na gode Allah ya saka da Alkhairi Allah ya Kara budi,yace Addua zakiwa kanki sosai shi yasa tare zamu tafi nasan akan abinda nake so kiyi adduar idan ke kadai ce ba yi zakiyi ba,nace fada min wlh zanyi nasan akan me ma kake so nayi adduar,Kawai Allah ya shirya ni na daina zancen Karuwanci nayi zaman aurena,na dawo mace nutsatsiya,yace ae abinda ke damunki Allah ya yaye Miki ko? nace Ameen ai har abinda nake ji a zuciyata dan baza ku sani ba ni Ina ji,yace kafata dai kafarki,to na furta Ina murna.

    Washe gari Kuwa na shirya cikin Abaya me kyau blue naci takalmi da jakata masu tsada,shima ya zuba kyau cikin kana nan kayansa,Muka fita tare uwar baccin tana ta fama ya kaini aka min international passport daga nan nace ka kaini wajen su Sera idan ka tashi daga Office Sai ka biyo ka daukeni,yace na kaiki dai Ina tsaye ku gaisa mu wuce idan Kun matsu da hirar suzo gida wajenki,nace to shike nan kaini hakan,har can ya kaini Yana parking na fito a mota da Santana dandaudu naci karo ya rike baki tare da furta wow Miracle kinganki Kuwa yanda Kika koma sai kace daga inji aka fito dake gaskiya auren nan ya karbeki nima da Zan samu Wanda zai aureni haka a Yar iskata ai da naji dadi,dariya nayi nace Santana kenan,Wise ce ta fito sanye da guntun wando da riga hannunta sigari ce take sha tana ganina ta saki ihun murna sai ga Mata suna fitowa,Star ce ta karaso daga ita vest Bumshort ta fada jikina tana cewa shegiya kin ganki Kuwa wlh kinyi kiba kinyi kyau Kinga duwawunki Kuwa yanda suka sake komawa,Seraline tana Fitowa itama ta shafa fuskata tace kaji laushi oh Karuwanci ya taimaki Yar uwa,dariya nayi sai ga Mandula tana gani ta Fara rawa suna ta zuwa Muna gaisawa nace sauri nakeyi amma Zan samu time na dawo Suka ce ai ko baki zo ba Zaki ganmu ma nace good Muka danyi hira sama sama sai taba jikina sukeyi Wai na Kara kyau,damuna yayi da horn dole na musu sallama Muka tafi,Muna Hanya yace sai wani tabaki sukeyi sai kace yar lesbian yana jan Tsaki nace sai gidan Mami,dake Maminsa ce ba musu sai gamu a wani katafaren gida gari guda gidane na ubansu muka shiga.

    Parking yayi sannan Muka fito Muka jera zuwa part din Mami direct gaskiya ba karya,palon Muka shiga da sallama,Mami tana palon da yaranta kaf suna hira suna kallo,ganinmu da Nawwar Mami ta washe baki tana Jin dadi tace sannunku da zuwa,Durkusawa nayi tare da gaisheta kannen Nawwar sai kallona sukeyi har Suka gaishe ni Suka gaida Nawwar sannan muka zauna,Mami ta sa aka kawo Mana kayan ci iri iri mun dade kafin muyi musu sallama muka tafi ko wajen su Iyamami bamu leka ba yace baza mu je ba sabo da maganganu marasa dadi  gida Muka nufa kawai,ai Muna Fitowa sai ga Iyamami ta shigo daga waje alamar unguwa taje,kallona tayi tace ke Hala kece amaryar tana yatsina fuska nace ae,ke farin naki ma Kamar ba na Allah ba sai kace jikin kazar da aka fige Kalar kyankyami amma a haka a kanki ake gallazawa Yar dangi Yar asali ba Yar tsuntuwa ba,Murmushi nayi nace tunda nayiwa Ogan ai dama bana bukatar yabawar wani Yar katuwa,Kuma kowa ya ganni wlh yasan gaskiya ba farin kanti bane Kuma har abada Sabreen baza ta Kama kafata ba,Kuma sai dai hassadar mutum ta cishi ko wanene billahillazi, Iyamami baki ta rike tace ke Allah daga kawo ki wato dangi ma baza ki mutuntasu ba da sauri na bata amsa da ae duk wanda ya dagulamin rai sai na dagula masa nasa bare ke da baku ja girmanku da mutuncinku ba Kun isheni wlh ki kiyayeni Iya Watarana sai na sa an Miki fyade wlh ki kiyayeni kinci darajar Nawwar amma ba a Shiga gonarmu,Dan ubanki kisa ayi min fyaden ban taba Jin Yar iska irinki ba tsofai tsofai Dani zaki ce zaki sa a mini fyade sai ta fashe da kuka tana salati tayi ciki.
Nawwar farin ciki yayi shi Kansa Iyamami ta isheshi a rayuwa.

  Bayan mun dawo gida Sabreen ya nema anci sa’a bata Yi baccin ba bata da kudi kayan maye sun Kare,Nawwar ya sameta tana gyara part dinta yace Zan biya Miki Makkah Aikin hajji ko Umrah? tace a’a ni kudin nake so Zan siyi abu me muhimmanci na gaji da zuwa makka,Bai kawo komai ba yace Zan tura Miki kudin aikin Hajji ya juya ya fita,Yana fita ta hau tsalle da murna,nan take ta Kira Jamcy tace kudi sun samu ki sa Mana ranar zuwa Kauye karbo maganin,tace to an gama ki shirya next week mu tafi,tace to an gama ya batun Fara kasuwancina naki? Sabreen tace Zan Fara mana ki hadani da Wanda Zan Sara a wajensu Ina son kayan maye kin San yanzu cinikinsu akeyi matan aure ma Sha suke a boye,Jamcy tana Dariya tace baki da matsala,a ranta tace Indai wajen boka ne na gama hada baki da shi za a iya kamaki a abinda zai baki idan na koreta sai na kori Karuwar Karuwar tafi min wahalar kora,kawaye a daina yarda da kawaye wajen abubuwa musamman Harkar malamai za a iya hada Baki a dinga damfararki kudi ko wani Abu.
Ni Kuwa Nawwar ke koya min aikin hajjin da zamuje yanda ake komai duk da cewa tare zamu amma duk wani hukunce hukunce sai da ya sanar dani na rike komai,a international zamu je ba a hukumar alhazai ba shi yasa komai aka gama Mana sharp sharp cikin sati daya.

Ana gobe zamu tafi duk wani shiri munyi,ga Seraline,star da Wise mazaje sun biya musu suma dama yanzu Mata sai ayi badala Kawai dan an biya musu Makkah aje ayi pics ayi karya aikin kenan duk wasu sabo da ayi karya ake zuwa ko ta hanyar haramci ne Kamar yanda su Seraline Suka bada kansu aka biya musu aikin hajji,Sera  Alhajin da yace ta bashi ni shi ya biya Mata taki ce Masa nayi aure tace sai ta dawo zata hada shi da ni bayan tasan Karya ne,su sun riga mu tafiya ma,kafin mu tafi Nawwar ya siya min Sabuwar iPhone me shegen tsada itama Sabreen ya tura Mata kudin,ranar Kuma tace zataje wajen kanwar Mamanta bai hanata ba tace yini zata Yi yace a dawo lafiya dama idan Zaki fita ai ba a fada min kike ba,ita dai tafiyarta tayi Suka hadu da Jamcy ashe kauyen ma a nan Anambra yake wajen wani matsafi in Suka maka aiki Kamar yankan wuka sabo da tsafi ne.

     Suna zuwa wajen wani Jan bedsheet ne an zagaye wajen da shi ko Ina wasu kaho ne mutumin jikinsa daure da Jan yadi a jikinsa Yana zaune suka shiga,bayan sun zauna da turanci yace meke tafe da ku,Sabreen da turanci tace kishiyata ce ta dame ni a gidan mijina ta sa mijina ya tsaneni gaba daya ta ita yake ko banda ni ,a baya bana sonsa aka Mana aure amma yanzu Ina sonsa.
Matsafin ya daga Kai sama sai da ya dauki wasu mintuna sannan ya kalle su yace me kike so ayi Mata?Kawai a sa ya saketa saki uku ya Mata dukan tsiya shine Kawai bukatata,Arnen nan yayi dariya ya dakko wani kullin magani dan kadan yace gashi ta karba yace kiyi Masa abinci ki juye masa shi du a abinci idan ya ci an zakiga aiki,farin ciki ya Kama Sabreen tace kudinka nawa ne? Yace dubu dari biyu nan take ta zaro a jaka ta bashi tana godiya Suka tafi,Jamcy tace matsala ta Kare shike nan suna ta murna, Suna tafiya bokan ya turawa Jamcy dubu hamsim ta accnt dama tace ga abinda zai karba idan sunzo sannan zai bata kasonta shine ya bata nata Jason cikin kudin Sabreen.
Sai dare 9pm suka dawo lokacin ma ni nayi bacci a dakina,Nawwar kuwa Yana Shirin kwanciya shima sabo da jirginmu da asuba zai tashi, Da tun 4:30am na tashi tuni nayi wanka da brush na shirya cikin sabuwar Abayata baka me adon silver nayi Rolling kamar wata balarabiya na fito bayan nayi sallar Asuba na fito dauke da yar jakata rataye a kafadata,takalmi da jakar Silver,kayan mu Kuwa da Muka eba kala biyu ne rak yace ma siya can cikin jakarsa na zuba m,Ina Fitowa Palo ya fito shima.

    Fresh milk da Lipton na dan tafasa shi Kuma ya shiga sanar da Sabreen,Sabreen sabo da tana Shirin sa Masa magani a abinci ko baccin kirki kasa yi tayi,Yana shigowa tashi daya yace Sabreen ta mike zaune Zumbur shi Kansa yayi mamaki,yace zamu tafi aikin Hajji anjima kadan jirginmu zai tashi,Gaban Sabreen ya Fadi tace amma ya baka fada min ba tuntuni sai da zaku tafi ni dai Kawai ka daukeni banza wofi a wajenka Allah ya Isa cutata da kake Yi a gidan nan ta fashe da kuka sabo da kayi Amarya shine kake wulakantani,Tsaki ya ja ya juya zai fice ta rike rigarsa tamau wallahi baka Isa ba na gaji da wulakancin da kake min a gidan nan,rigarsa ya fisge ta sake fisga ta rike Yana juyowa ya dauketa da Mari Wanda ba shiri ta sake shi ya juya ya fita abinsa Yana masifa,a zaune ya ganni Ina Shan tea dina na fresh milk da bread da ragowar naman jiya, Ina jinsu suna fada da Sabreen ban nuna naji bama nace zaka Sha? Wanda nake Sha ya dauke tare da shanyewa yace ashe da dadi,ragowar na tsiyayo na ciko Masa cup na hada Masa da sugar nima na sake hada ragowar da ya rage Muka zauna Muka ci Muka koshi tare da kuskure bakinmu,na dakko chewgum Orbit na bashi biyu Nima na tauna biyu na maida sauran jaka yace muje Saura 15mt a fara screening, driver ne ya kaimu airport har an kusa gama screening muka bi layi aka mana sai jirgi, sit dinmu daya Ina gefensa sai Selfie nake Mana da videos,Kaina na shiga dauka Ina video nace Alhmdllh.. Alhmdllh… Alhmdllh Allah ya sauke mu lafiya Allah yasa muyi hajji mabruk,dariya yayi yace ba saban ba duk kin dame mu, pics da videos na zaba masu kyau na maka a WhatsApp nayi status harda sauran social media dina na saka,Wise suna can su tuni kullum Ina ganin nasu a Madina Kamar mutanen kirki,ai suna ganin Status dina Suka ce mayyar aure gata ga mijinta tare Suka taho babu shanawa kullum ya manne Mata Kai masifa,Sera tace ai Rabi tana ganin ta kanta da aure,tana Shan wahalar auren nan.

      Muna sauka a Jeddah madina Muka nufa Muka,kwanan mu biyu na nemi su Sera nace mu hadu a masallacin Muka hadu bayan mun fito daga Raudah, Muka rungume juna Nawwar Manniru yana gefe na,Star tace kunzo lafiya ya akaji da sanyin tiles dariya ta kwacewa Nawwar Kamar bamu San tiles ba,nace wlh ana Haka ruwan Saudiya yake dama malam kana wanka Yana darewa a jikinka,Laaaa ai haka Nima na gani ruwa baya Zama a jikin mutum in kina wanka kina zubawa Yana darewa malam, Wise tace, fatan kina cika cikinki ki da zam zam,wa zaiyi Wasa da zam zam ma samu ya wanke Mana zunubi, Kalli yanda fuskar mu tayi hasken musulunci to Sallah kullum ba fashi munzo garin Manzo,Star harda rera Mana wakar kasida ta yabon manzo baiti Daya tace a Kano na iya ta,Muna ta nishadi,Nawwar Yana ta dariya yace na gaji fa a gurguje Muka dinga zuba hotuna da videos muna posting Nawwar yana kallonmu ya tafi hotel dinmu yace sai na taho gida,daga nan siyayya muka wuce muka dinga jibgar Kaya na ubansu banda,sai dare kowa ya wuce masaukinsa,Ina komawa yaga uban siyayya yace kina cinye guzurunki bazan Kara Miki kudi ba,wanka na Shiga na fito nayi Shirin bacci Yana kallona,dama bed dinmu daya gashi karami baya kulani nima bana rike ko hannunsa sai da mu farka mu ganmu manne da juna,saman bed na haura  nima gefe,yace wannan kawaye sai kace Yan uwanki ko Yan uwanki baza ki so su haka ba,nace kafata ciwo takeyi wash Allah Ina shagwaba,ba dole tayi ciwo ba Kuna ta uban  yawo

     Mikewa yayi zaune a saman bed din yace muga kafafun ya jawo kafafun tare da dorasu a jikinsa Yana daga zaune,sun birge shi farare masu kyau luwai luwai dan matsa min su yake a hankali Ina Jin wani dadi har wani lumshe Ido nake yi,yana min massage sai da na Fara bacci sannan ya kyale kafar ya kwanta bacci,juyawa nayi tare da rungume shi sosai,da kyar ya samu bacci ya kwashe shi sabo da abinda yake ji a kaina shi Kuma sabo da yanda yake jina a ransa baya so ya kusance ni yajini ba virgin ba zai ji haushina ya rasa sukuni shi yasa yake tsoro.

   Haka sosai yake karanta min adduar da zanyiwa kaina da ma wasu har da shi Kansa kuma Ina Yi din akan halin da nake ciki,haka har Muka sauke Aikin hajji Muna makkah Muka gama iya kwanakin da Muka samu sannan Muka yo gida abinmu.
Sabreen kuwa tana gida in Banda shaye shaye ba abinda take yi sabo da ta samu kudinta na aikin Hajji,ta hakura da kashe kudinta wajen boka daga gwadawa sau Daya yanzu tace da tuggu zata fidda ni,tare da neman shawarar Jamcy,Ni Kuwa satina Daya da dawowa naje na yini a wajen Mami.

    Sai Yamma likis na fito da ma da motar Nawwar na zo Ina Fitowa na hadu da Baffa tare da Amaryarsa,dake makira ce ita sai tace Wai ba Amaryar Nawwar bace? na juyo nace ae, shine baza ki je ki gaishe ni ba ku fa yaran zamani haka kuke baku da tunani,a gaban Baffa nayi mata wani kallon banza sannan na furta ai baki Kai aje a gaida ki bane ke din banza ke Ina tunanin naki yake har kina da tunani duk abinda kayiwa wani sai an Miki Kuma wlh dan kin San ya juyawa Mami baya a banza mu mun San kafin ai daram akai kwandi a Sannu Allah zai tona miki asiri,Baffa yayi mukus Yana so ya taka min birki Yana tsoro na da kunya sabo da yasan me ya aikata, Ummin Haidar tace Baby kana jinta fa wannan bai kamata a bar Nawwar ya zauna da ita ba,Tsaki na ja sabo da nasan tun zuwana Naga Baffa Kuma na gaida shi gaisuwa ta mutuntawa Kamar komai bai faru ba shi yasa na shige mota abina, Su Iyamami basu San ma Ina zuwa gidan ba tunda na Mata tatas ko ta ganni bata fitowa

    Baffa bayan na tafi muzurai ya Fara tare da furta Zan dauki mataki a kanta Kamar yanda Kika Sanni to tunda ta taboki ta jawa kanta,Ummin Haidar tayi Murmushi tare da rike hannun Baffa suke shiga mota driver ya ja Suka fice.
Sai da na koma gida washe gari na gama gyara gidan nayi girki,wanka na sheka naci gayu cikin kana nan kaya,Ina Palo Ina kallo naji motar Nawwar driver ya dawo da shi,mikewa nayi Yana shigowa na furta oyoyo tare da fadawa jikinsa tare da furta Sannu da zuwa,Sabreen ce ta fito sabo da ranar girkinta ne,ranta ne ya baci tace ke malama mayyar maza yau ba kwananki bane,juyowa nayi nace ohh kiyi hakuri na manta na saba ne,Tsaki taja tare da zuwa ta bangaje ni na kusa kaiwa kasa na rike kujera,fuskewa nayi kallona yayi Muka hada Ido ya kashe min ido Daya tare da furta min sorry,Sabreen kuka ta saki tace baka da hurumin Mata kallon so ranar girkina wlh bazan yafe ba ai kallo na ne ya zu ni zaka yiwa kallon tunda nice da girki,yanzu ni zaka yiwa wannan kallon ba ita ba,Nawwar yayi dariya yace kallon ma ni da idona kina da ilimi Kuwa haka akace kallo ma baza ka yiwa wata ba,ai Ina gani kallon kallon soyayya kake mata wato kayi missing dinta muje ta rike hannunsa Suka juya zasu tafi,juyowa yayi Yana daga min hannu,Ido na kashe Masa Ina Masa fari,Muna Murmushi Muna ta magana da Ido,abincin da na dafa na tarra na kwashe komai na kaiwa masu aiki maza  na ebi nawa naci na koma dakina,Sabreen kuwa bata Yi girkin komai ba ganin nayi abinci shine tace suje suci abinci sabo da kullum Nike abinci ko ranar girkinta ne sabo da Nawwar nakeyi idan banyi ba to bazai ci abinci ba Kuwa shi yasa yace nayi hakuri na dinga Yi Kawai yau Kuwa bazan iya hakurin bashi ba,shi yasa na bayar da abincin na wanke kwanikan na ajiye,gajiya nayi da Zama a daki na fito Ina kallon film,sai kuwa ga Sabreen ta fito,daga baya Nawwar ya fito ta duba dining Babu abinci ta duba kitchen taga komai a wanke das alamar ba komai.

     Dawowa tayi tace Dani Ina abincin? Mikewa tsaye nayi nace kanwar uwarki ce ni ko ta ubanki,ke na gaji da abinda kike min,In zauna kullum na dafa muku abinci Kuma ranar girkinki baiwar uwarki ce ni, ko siyena kika yi banza Jahila kidahuma wacce bata San me take ba duk haushi nake ji Nawwar Yana tare da ita kishi ya rufe min ido,harzukowa tayi da masifa Nawwar ya daka Mata tsawa yace ke bana son hauka idan kina son Miji me ya hanaki kiyi girki ko yaushe ita ke abinci bata taba gajiyawa ba sai yanzu ke har kina da bakin magana,wayata ce tayi Kara Wanda tana kusa da Nawwar kallon screen din yayi yaga an rubuta My love,Ido ya zaro na Mika Hannu Zan dauki Wayar ya rigani dauka tare da dagawa ya Kara a kunne,Muryar Namiji yaji yace Hello Babyna ya Kika je gida jiya? Kinje lafiya,ya gajiyar jiya,kiyi hakuri jiya na gajiyar dake da yawa kece kina da dadi,Allah Miki baiwa Sweety gaki da ruwa…..datse Wayar yayi nan take Muka ga idonsa ya canja,jikinsa na rawa ransa ya baci,kallonsa nayi nace lafiya wace ta kirani ko su Sera ne na Kai hannu Zan karbi Wayar a hannunsa ya mike a wani hasale ya zai haura sama,na mike tsaye, Sabreen nan take ta washe baki ta gyara Zama,idona ne ya cika da hawaye nace wai mene akace ne na sai Mika Hannu Zan fisgi wayar Mari ya sake kwasheni da shi,Raina yayi mugun baci yanzu abu kadan ya dinga dukana wlh bazai yuwu ba Dole na dauki mataki na kwaci yanci na,yana huci yace baki da hankali  mahaukaciyar Ina ce ke ashe baki San me kike ba,waye wannan dama jiya ba gidan Mami Kika je ba iskancinki Kika tafi da aurena ki dinga Neman maza,Kuka na fashe da shi tare da durkusawa har kasa nace wallahi ban San komai ba gidan Mami Kawai naje na rantse da Allah,lier ya furta ya mike zai bar wajen na rike Masa kafafu Ina kuka Ina furta wallahi banje ko Ina ba babu abinda na aikita,juyowa yayi yace waye zai je ya Miki saving number din kato da My love waye zaiyi haka,kin bani mamaki ya juya ya haura samansa, Sabreen shewa ta saki tace neman maza har a gidan miji ana da aure tsiyar karuwa kenan shi yasa ake son ka auro Yar asali Yar dangi ba Yar kwashe kwashe ba,yo Yar tsuntuwa ai kowa yasan Yar shege ce oh anyi gado,anyi gadon iyaye ta juya tare da haurawa sama.

     Nawwar ya zauna a gefen bed ya rasa inda zai sa Kansa bacin rai ya Masa yawa sai tunanin maganganun da gayen ya fada yake yi,Ni Kuwa a nan na zauna Ina mahaukacin kuka Kamar raina zai fita har na gaji na tashi na haura sama dakina na fada saman gadona in kuka ranar ban iya bacci ba shima Nawwar haka,da safe ban fasa aikina ba nayi duk abinda nake Yi har abinci,dakinsa Kuwa ban leka ba gudun wulakanci,steps na hau shi Kuma ya taho zai sakko ya Sha wanka ta jikinsa na raba Zan wuce ya bangaje ni nayi baya na rike karfen steps din da kyar tsaki ya ja ya wuce ya fice abinsa ko abincina bai kalla ba.

   Sabreen ce kawai ta fito ta danni abincin da na dafa tace an gaisheki me gidan bai so yanzu,bata ita nake yi ba,dakinsa naje Zan gyara naji ya kulle gam,dakina na koma na zauna Ina ta tunani har ga Allah tunda Muka je Makkah naji Kamar an yaye min komai naji Ina son aurena bana son barin gidan sannan naji rayuwar bariki bata birgeni ko kadan bazan iya bada kaina ba,ko asirin ne na Dagaci ya karye oho.
Ina zaune a gidan kullum Nawwar baya ko kallona har ya gaji ya bani wayata amma baya ko kallona,damuwa ta min yawa kullum a Addua nake da sallar dare kuka Kuwa baya yankewa a idanuna.
Ina gida yau Sabreen ta fita unguwa shi Kuma ya fita aiki da yamma likis Wanda nasan gaf yake da dawowa, Ina zaune kawai naji an turo kofar Kamar Wanda ya shigo yasan code din kofar,wani saurayi ne matashi baki da shi ya shigo na mike tsaye Zumbur a tsorace Ina cewa waye kai Malam,My love ya furta,ihu na saki Ina cewa dan girman Allah na rokeka ka fita karka kashe min aure wlh Ina son mijina Ina son aurena yanzu, ban sanka ba Kawai kace min your love Dan Allah,Karar motar Nawwar naji hankali na ya tashi na taka zan gudu,mutumin nan ya damko ni ban San waye ba ya rikeni Kam tare da jawoni jikinsa yana kissing din dokin wuyana dake baya na juya Ina kokarin guduwa Ina dura Masa ashar,Hannu yasa ya toshi min baki yane cewa Ina sonki Baby kina da  Dadi bana iya rabuwa dake,Nawwar Yana shigowa mutumin Yana furta shekaran jiya fa kin jiyar dani dadi me yasa yanzu Kika ki,kafin mijjnki ya dawo munyi mun gama ko kin manta yanda muke yi, Yana Jin motsin Nawwar ya sakeni da sauri tare da ja baya,ni nasan Nawwar ya shigo tunda naji kamshinsa,shima ya sani da gani kasan turo shi akayi amma Nawwar bazai gane ba,a wajen Nawwar ya sandare,Ni Kuwa zubewa nayi a kasa na rushe da wani irin kuka, Saurayin tsayawa yayi Yana kallona tausayina ya kamashi shi kanshi sai yaji bai kyauta ba, Amma tuna kudin da aka Masa Alkawari sai ya bar gidan da gudu Nawwar Yana tsaye Kawai ya haura sama,nima ban ce Masa komai ba Kawai kuka nake yi sabo da bani da abin fada, Gajiya nayi na tashi a wajen Kawai na nufi dakina Ina share hawayena sabo da zargina da akeyi dole kowa ya yarda shi yasa Kawai na zabi wasu kayan na cika akwatina na fito na ja Allah yasa ba kowa a palon na fice na,Masu aiki suna kallona na fice na bar gidan ina kuka.

 

AsmaBaffa
08061929616🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               71-75

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

 

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

Page naku ne

Maman Hibbat
Ummu Zee
Murjamashi
Ummy
Maman Zahra
Maman Walida
Mom Khalisat
Ummee
Beauty Zahra
Aminaidriskafe
Ummu Afnan
Mufeedart
Jagabanyakubu
Samira Haru Batir
Manaajahooh

Gaisuwata ga
Maman Samha

        Direct gidanmu na nufa Ina zuwa dakin Sera na nufa sai gani na tayi na fado dakin Ina kuka,saman katifar mu na fada Ina cin uban kuka,Sera tace Wai lafiya nifa bana son irin wannan Iskancin,me aka Miki? hawayena na goge nace ki Kira wise da star munfi kusa na muku bayani,Wise ce ta shigo da sigari a hannunta tana Sha,Star kuwa codeine take kurba Kamar me Shan lemo ta zauna itama tace ke lafiya Miracle kike kuka haka,a nutse na basu labarin komai karshe nace ni bana so mijina ya sakeni shi yasa na gudo,Wise tace tab wannan bazai wuce aikin kishiya ba idan itace ma zata Yi bayani da kanta ta tabo bala’i ta jawa kanta,Star ta furta yanzu bai baki takarda ba baza ki zauna a nan ba duk tsiya aure Yana da daraja ga mu da muke kaunarki da gaskiya tashi mu tafi na kaiki gidan wata kawata ce, babbar mace ce Bata da aure mijinta ya mutu ya bar Mata dukiya na taba taimaka Mata lokacin da motarta ta samu matsala a daji Hanya zata je arewa shine dalilin haduwar mu tayi tayi na daina karuwanci na koma gidanta zata rike ni naki yarda muje can ki zauna ko Nawwar yazo mu Kuma zamu ce baki zo nan ba gudun Kar ma ya ganki ya sakeki,dariya Sera tayi tace wato Miracle kice gudun saki ne ya fito dake tun kafin ya dankara miki saki? Nace ae Suka kwashe da dariya,nace ba Maganar Wasa bace wannan tam Ina zumbura baki,Sera tace ga abinci nan yanzu na dafa sai ki ci ki tashi ku tafi, dama yunwa nake ji naci na koshi Muka fito ni,Sera,wise da Star muka tafi can wajen Matar me suna Hajiya Abida, Muna zuwa ta karbe mu da murna gida ne hadadde me kyau da motocinta biyu tana da Yara uku duk suna Arewa Bauchi a nan suke makaranta sabo da su samu tarbiyya ta addinin musulunci,gata da Yar aikinta mace daya,sai Namiji a bakin gate shi ke Mata wanki da guga da kula da gidan,gida ya Sha flowers da furniture masu kyau.

Muna zuwa ta karrama mu sosai aka kawo Mana kayan motsa baki,sai da Muka danyi hira da ita sannan Star tace Hajiya Yar uwata na kawo miki ajiya tana da aure sai ta fadawa Hajiya abinda ya faru dani a gidan Nawwar,Hajiya Abida ta tausaya tace bazai wuce sharrin kishiya ba so take a koreta Kuma ta Allah ba tata ba,da sauri na furta Inshaallah Ina nan da mijina mutu ka raba,na kalli Hajiya nace Ina son mijina sosai da ban damu da auren ba amma zuwana Makkah Allah ya amsa Addua ta yanzu bana sha’awar bariki ko kadan mijina da aurena sune a gabana,tallan duwawu na gama Inshaallah,Hajiya Abida tayi dariya ita kunya ma muke bata sabo da magana direct muke fada ba wani sakayawa,a nan gidan su Star suka barni, Suka koma gida Suka tattara mutanen gidan Wanda ake mutunci su Yar Zabil duk dai wanda suka je bikina suka zauna  sama katuwar tabarma guda biyu da alawoyi da yawa a leda suna zaune sunfi mutum ashirin,Santana yace dan Allah wai Kun taramu kunce akwai magana Yar uwarmu Miracle tana da matsala a gidan miji,Madula tace to me za muyi Mata itace ta Kai kanta in Banda Addua me zamuyi Mata,Seraline tace yawwa duk da mun San mu masu laifine a wajen Allah amma Addua itace zamu hadu muyi shi yasa na tara mu,wata me suna Destiny tare da Peace Wanda su arna ne dama Suka ce muma zamu Yi Mata irin tamu oya a fara.

     Seraline tace ni shugaba da na tara wannan taro zan Fara,Salati goma ga annabi,Mandula tace ya ma akeyi ku dan tuna min,Allahuma salli ala muhammadun wasallim na Fadi dai dai ko? Yar Zabil tace to Allah ya amsa hakane tana wani fari da Ido tana karairaya,Santana yace karami ne a salatin akwai na Ibrahimiyya shine darrr amma wannan yafi sauki Suka karanta,Seraline ta sake cewa suratul bakara kafa uku uku,Allah ya daidaita Miracle da mijinta Nawwar su dawo su jone su manne Kamar da,Allah ka duba kawar mu Miracle Kar ka bari Aurenta ya mutu Allah karka bari Nawwar ya saketa,ko wace ta hada Mata wannan tuggu Allanmu kayi fata fata da koma waye kayi raga raga da ko waye,kasa gobara ta kone dakin ko waye,Idan Sabreen ce Allah kasa duwawunta yayi tsutsa,su Kuma sauran suna cewa Ameen Seraline ta furta fatiha ta shafa tace wata tayi Mana itama,kowa a ciki yayi Miki Miki suna kallon kallo duk sun manta ma adinnin nasu sai sunyi tunanin yanda ake yi.

    Wise ta daga hannu sama tace Suratul Tauba kafa daya,ba Wanda ya iya har ita me fadar,Suratul bakara ma ko aya daya ba wacce ta iya fada bare Tauba,ai Kuwa bata jira ba itama taci gaba ta daga Kai sama da hannaye tace Ya Allah mun San mu masu laifi ne kullum sai munyi maka laifi ita kanta Miracle babu irin laifin da bata maka ba ta bada gabanta da baya duk har center an daki harka da ita yanzu ta tuba tayi aure tana son mijinta tana son aurenta,Ya Allah Muma gamu dai Muna ta siyar da local government dinmu masu laifi ne mu ya Allah ta Kara kwalawa da karfi ya Allah duk Dan iskan cikinmu Wanda baya ji Allah kayi daga daga damu…kowa baki ya bude yana kallon Wise tana jawo musu masifa duk cikin addua,Santana yace ke rufani ki sayani ke Wise min Shiga Uku,wise da taci gaba tace tunda munki ji gamu ya Allah kayi maganinmu Allah karka kalli laifinmu ka yafewa miracle ka yafe Mana karka bari Nawwar ya sake ka barta da mijinta ya Allah karshe tace Fatiha Alhmdllh an karba Addua ta karbu,Star ce itama ta daga hannu sama ana cewa Ameen tace Ya Allah Suka hada baki tare da furta Ameen,ta sake Furta Allanmu Suka ce Ameen wannan haka yake Allah ga bayinka,Star tace Allah Nawwar,Nawwar,Nawwar mijin Miracle zai saketa ya Allah karka bashi dama,Ya Allah ka sa Masa tausayin miracle da kaunarta Allah karka bashi damar sakin Yar uwar mu,Miracle tana son bawanka Allah karka bari a saketa kasa ya nemi matarsa miracle ta koma gidanta Allah kasa tana komawa ya Mata ciki ta haifo Yan biyu,Ameen Suka hada baki.

    Madula ce ta karbe Adduar da furta istingifari kafa dari,kowa ya Fara Astagafurillah har kafa dari dari Suka Yi abinsu sannan bata rokawa Rabin komai ba ta shafa tace Ameen,Santana ya karbe Yana cewa Allah ka daga gidan Nawwar kayi sama da shi ka kife shi a kasa ka hada da Sabreen din a juya kanta kasa a cake ta karairaye Allah karka kashe ta a barta ko Ina a karairaye shike nan ya Allah Suka furta Ameen,Manduwa tace Allah kasa mota ta kade Sabreen tayi Mata markaden kayan Miya a kwalta,Yar Zabil ta saki wakar kasida ta yabon manzo suna amsawa tayi baiti Daya suka Shafa da Ameen..Daya bayan daya kowa da Kalar adduar sa,Peace christain itace ta karba ta Fara wakar church sannan tace Papa God tana wani fari tace Jesus abeg ka taimaki Miracle mijinta ya maidata gidanta,we are all sinners kullum sai munyi zunubi Papa God ka taimaki Yar uwar mu Suka hada baki da Ameen,Peace ma wakar church tayi ta yabi Jesus sosai sannan tace Ameen a haka sai da kowa yayi adduarsa ya Gama sannan Sera ta bude Alawa chocolate me shegen dadi Suka rabawa junansu ko wacce guda biyar biyar Suka bare suna ta sha Wai Sadaka ce maganin masifa ,Suna haka Saurayin Seraline ya buga Mata waya yace ya dawo gari daga Dubai tazo zata Taya shi kwana daga nan ta kwashi kayanta sai hotel dinsa,Suma sauran haka duk sunyi Shirin tafiya aikinsu kamar ba sune Suka Gama Addua yanzu ba.

    Nawwar bai San na bar gidan bama,Bai neme ni ba gudun Kar ya yanke hukunci cikin fushi,kwana daya Shuru bai ga ko gilmawata Sabreen ma tayi mamaki bata ganni ba tace ko ya sakeni ne sai da ta duba ko Ina na gidan bana nan wani farin ciki ya kamata burinta ya cika tunda bata ganni ba tasan ma ya sakeni,Nan take ta Kira Jamcy tana bata labari tace ke aiki ya Kare ma mu kwanta mu huta ya saki shegiya,Jamcy a ranta tace Saura ke dan ubanki duk ku fita ku bani waje a gidan sannan na samu damar shigowa gidan.
Wasa Wasa har kwana uku Nawwar bai ji ko motsi na ba,kasa daurewa yayi ya nufi dakina ya duba wayam,ko Ina sai da ya duba babu ni, wajen masu gadi yazo ya tambaya Suka ce oga ai tayi kwana uku da Muka ganta da akwati tana kuka ta bar gidan nan,hankalinsa tashi yayi yace to ni me nace Mata nayi magana ne da zata bar gida ya ja tsaki yace idan ta gaji ta dawo ya koma ciki amma me tunaninta sai ya hanashi sakat in banda Rabia babu abinda yake tunawa yace idan ta koma gidan jiya fa tsaki ya ja tare da furta to ni mene abin damuwa da ita tunda nasan ba sonta nake ba,ni kuwa har na Saba da Hajiya Abida Muna zaman mu girki ma tare da ni da Yar aiki muke yi na bata labarin ni Yar tsuntuwa ce taji tausayina, kullum Nawwar Yana raina in Banda tunaninsa bani da aikin yi,Ina tuna rayuwar mu tare da duk wani moment da muka Yi spending tare,yanda yake nuna min kulawa,yau ma bayan na gama komai dama wayata na kasheta gaba daya tunda na bar gidansa ban sake kunnawa ba,a saman bed dina nake kwance Ina tunaninsa ban San Sanda na Fara hawaye ba,a haka Hajiya Abida ta sameni,ta zauna ta taba kafata dan ban San ta shigo ba,a firgice na motsa na ganta,hawayena na goge a hankali,tace Rabiah yaushe Zaki daina kuka hakuri shi zakiyi Inshaallah zai neme ki,murmushin yake nayi har hakorin makana na Gold ya bayyana a hankali nace kina gani kwana na Uku su Sera sunce bai je Nema na ba Kinga Kawai ya kyaleni nayi rayuwata ya manta dani,Yana da Mata ba abinda ya dame shi dani, dama ba so na yake ba nice nake sonsa na rushe da kuka sosai,Hajiya Abida babu irin lallashin da bata min ba amma naki Shuru sai kyaleni tayi ta tafi.

      Nawwar kwanansa bakwai bacci sai barawo ya kwashe shi ala dole,a daddafe ya kwashe sati sati duk ya rame sabo da tunanina, Kuma ko Mami bata sani ba a wajen su Iyamami taji ya saki amarya su ma Sabreen ce ta basu labari sai Murna suke suna jifan Mami da babake maganganu har ta gaji yau Nawwar yazo da Yamma ta kalleshi Yana cin abinci tace Nawwar lafiya kuwa? Me Kika gani Mami? hmm tace a baya naga tunda kake tare da Rabiah baka cin abincina amma yanzu kullum anan kake cin abinci safe rana da dare,sannan baka da nutsuwa duk ka rame na rasa gane Kan abin sannan naji wajen su Iyamami suna min dariya Wai ka saki Rabia ta kawo kwarto gida,murmushin yake yayi yace ba haka bane Mami Kawai dan fada Muka Yi bata Jin maganata shine fa na Mata fada sai tayi yaji ta tafi ni Kuma banje na dawo da ita ba,Mami tace Kana da hankali Kuwa Nawwar ya zaka bar matarka ta tafi Kuma baka je ba,kuma kasan bata da kowa sai Yan duniya bariki dai zata koma tunda can ne gidan nasu,ashe karya kakeyi ba taimakon nata zaka Yi ba,Mami ita fa tayi tafiyarta,Nawwar baka da hankali gashi nan ka damu kana son Yarinyar nan kaki ganewa ne Kawai,Allah ya kiyaye ya furta, ni bana sonta Kuma bazan so ta ba ni na gaji ma bazan iya taimakon ba na fasa Kawai a bar zancen,Murmushi Mami tayi tace wai me tayi maka ne? yace ba sai kinji ba,tace to ai duk so ne gashi nan baka so aji laifinta Kar wani yayi tunanin wani abu a kanta anyway yanda ka gani koma mene Watarana zaka fada min ni dai na baka shawara ba dai dai bane baka saki matarka ba ka barta ta koma bariki ba Allah zai tambayeka.

     Shuru yayi ma Mami Yana cin abinci Yana tsaki har ya gama ya tashi ya fice ya bar gidan,layinmu na bariki ya nufa Yana zuwa ya samu Sera a waje,taje Suka gaisa tace Ina kawata? Kansa ya daure yace wacce kawar taki bayan satinta guda da yin yaji Kuma nasan nan zata zo,Sera tace bata zo ba gaskiya to Ina Kuwa Rabia zata tafi bata sanar min ba,Nawwar ya zaro Ido yace Wai da gaske kike ba nan tazo ba idan Wasa kike ma kin San dai bana Wasa dake, Sera tace tab ai kuwa ita tasan inda ta tafi bata nan gidan wlh,Nawwar yaga fa da gaske ne hankalinsa ya tashi matuka,yace kira Inna kiji ko can ta tafi,Inna aka kira tace bata je ba ko kauyen ma ba Wanda yaga Rabi a can,Nawwar ya rasa inda zai saka Kansa gashi an wuce sati Ina zai neme ta,haka ya koma gida jiki a sabule,Sabreen tana Shan kallonsa sai Dadi take ji burinta ya cika ga mijinta baya cikin farin ciki, Addua da sallar dare ya Fara ba ji ba gani,har aka sake kwashe sati shi kadai ya fara hawaye shi matarsa yake so,a Daren ya tafi wajen Mami sai ganinshi tayi duk ya fada Yana zuwa har da kwalla Ya shiga bawa Mami labarin komai da ya faru tsakaninsu karshe yace Ina ji a jikina akwai wani Abu a kasa gaskiya Rabia baza tayi haka ba shi yasa ban dauki mataki ba ita Kuma Kawai sai tayi tafiyarta ya karasa da marairaicewa yanzu Mami ya zanyi wallahi karya nakeyi Ina sonta ban taba son wata ba Kamar ta kawai na kasa yarda da ita ne ganin a inda na dakko ta farko,Mami dariya tayi sosai tace tun ba ayi nisa ba ka fadi gaskiya,Nawwar yace Mami kina dariya Allah ni Ina sonta bazan iya rayuwa ba sai da ita,Mami ta zuba Masa Ido tare da furta Nawwar In love Rabia ta ciri tuta,yanzu mafita daya kaje ka lallaba kawayenta zai wahala Basu san inda take ba,Mami kije wajensu zasu fi Jin maganarki please,ka bani number Sera din Kawai yace bani da ita,tace to bari na shirya muje da Kai yaji wani sanyi a ransa.

       Ni Kuwa zuwansa na farko Sera ta Kirani a Wayar Hajiya Abida ta fada min na dinga murna Ina murna farin ciki nake ji marar misaltuwa amma Jin Shuru bai koma ba naji na koma gidan jiya,Bayan Mami ta shirya har layin Suka je yaci sa’a ya hadu da Star, Bayan sun gaisa ta gaida Mami wacce ta fito ta jingina a jikin motar tana kallon barikin da yanayin mutanen Dake wajen,tace lallai wannan bariki ce ta kirki,Star ai Sera ta samu tace dan Allah kizo mijin Miracle sun zo da Maminsa,wlh tausayinsa nake ji naga Kamar shima ya rame irin Miracle mu hadasu Kawai ko dan halin da Miracle ke ciki,Seraline Fitowa tayi Suka zo wajen Mami bayan sun gaisa Mami tace dan Allah Saratu idan Kun San inda Rabia take ku fada mana kunga harka ce ta aure ba abin Wasa bane please,Star ce tace mun sani amma mufa gaskiya baza a dinga dukar Mana Yar uwa ba,miji ya dinga dukanta yana Mata wulakanci sabo da bata da gata ya sameta a bariki a bagas shike nan da me zata ji da kishiya ko da su Dagaci ko kuwa da halin Dangin miji zata ji ga kuma uwa uba miji haka Kawai wlh baza mu yarda ba idan ba a sonta a kyaleta mu Muna son a barmu, Nawwar ya harari Sera sai da tayi dariya ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa Kika ce baki sani ba,Sera tace tuba nake amma Kar a sake taba mana Yar uwa Suka shiga bayan mota har gidan Hajiya Abida mace me Kamala da mutunci,yayi farin ciki ganin ba a bariki ta zauna ba yaji wani Karin kaunarta a ransa,Suna shiga Haj Abida ta fito Suka gaisa shima Yana palon,tace shine mijin Rabia akace ae,tace Kai mashaallah tayi dace bari na kirawota tana dakinta,tana Shiga ta samu Ina bacci,Fitowa tayi tace ai bacci takeyi,Nawwar yace bari na ganta ya mike tare da shiga dakin Kawai kayana ya harhada a kwati ya fito da su ya saka a mota ya dawo har inda nake kwance ya daukeni Kamar jaririya ya kaini gaban mota ya ajiyeni,Sera tace su a nan zasu yini gidan Hajiya Abida,Mami tace wato mace tafi uwa ni sai dai na zauna a gidan baya tana dariya ta shiga ta zauna Ina ta baccina sanye nake cikin doguwar Riga marar nauyi ta yadi me santsi kaina da hula a Kai me kyau,Mami ya sauke a bakin gate tare da cewa thanks sai nazo,ciki ta shiga tana Masa tsiya,Yana Hawa titi Kamar Zan farka Kuma ban farka ba sabo da na tara bacci Kuma ni Ina da nauyin bacci sosai, a hankali yake tafiya gudun Kar na tashi

     A hankali na bude idona bacci bai sakeni ba gefena na kalla na hango Nawwar Kamar a mafarki na zaci mafarki nakeyi idona na murza sosai naga dai ba bacci nake Yi ba a hankali na furta Ina yini,Tsaki ya ja ya kalleni Kawai tare da maida Kansa ga tukinsa,nace baka sakeni ba dama? Kafadarsa na dafa nace Wai Kaine Nawwar ba mafarki nake Yi ba? Shuru bai kulani ba,na sake cewa Wai kaina so nane da yawa haka baka Fushi da ni,Nawwar ne kuwa? Fuskarsa na leka tare da furta Nawwaru…Muka dinga Addua a kanka rabona da nayi Addua tun a Makkah sai da na bar gidanka,su Seraline Suka dinga taruwa irin yanda ake adduar rokon ruwa suna ta Mana Addua zo kaga yanda fuskar mu ke kyallin musulunci sabo da tsabar Addua wani haske goshin mu yayi na musulunci su Seraline Suka Yi wani hasken musulunci adduar da Suka min kaiiiiii gaskiya munyi addini Addua Kamar ba gobe kalli yanda nayi wata Kamala sai fa da na Zama wata Yar kwarya kwaryar waliyya gaskiya na Sha Addua ji nake wani fresh sabo da tsoron Allah

   Dariya yayi a ransa Wai a haka shine abin proud adduar tasu ta Dan lokaci a fili ya furta karki dameni ni,nace a hankali yanda bazai ji ba na furta almasifatu kanwar azaba,Ashe yaji ya tambaya me Kika ce? Cewa nayi ka jawo na rame kalleni rama har nono sun dawo wasu gasu nan Allah ya taimakeka baka tabawa da kaga ta kanka ji zaka Yi Kamar ka tsinko dan lemon zaki karami,dariya ta Kama Nawwar ya kasa dannewa sai da ya murmusa,nace tsaya a siyi pad matar taka an jima kadan Zan Fara yoyo na kusa,slow yayi yace ta Kare ne duk yawan wacce na siya Miki? nace ai kyauta na yiwa su Sera Kawai ka siya min wata sannan accnt dina ba kudi ka tura min sannan dinkuna na an dinka ban karbo ba,yasan halinmu da kashewa Kai kudi Kawai parking yayi a wani Shopping mall,nace ka taho da ice cream,kamar bai ji ba sai gashi ya siyo min har ice cream din, ya kawo min,tun a motar na Fara Shan abina,Muna tafiya Wai a Dole haushina yake ji,dariya ya bani nace dinkunan kala uku ne Dan fake fake ne 20k,yace sai kace ke aka zana a jikin kayan,dariya nayi nace ka dinga kyautatawa iyalinka Allah zai Kara buda maka duk nasan komai kanayi karka ji komai kayi komai ba komai duniya ce dole mu baza mu bita a Sannu ba da gudu zamu bi a barmu, nace Addua ta karbu, kunnawa min kida yanzu na warwasa,hmm yace Kawai Yana kallon na kunna kidana.

      Sabreen tana Palo ita daya gidan duk dirty kaca kaca amma ko a jikinta sai sallamata taji mun shigo tare da Nawwar, Nace  Honey Kauye tayi na gode da barina da kayi naje unguwar nan kaga ko ba komai na gaisa da iyayena da Suka rikeni,naji dadin tafiyar nan kaga ai nayi zumunci,Sabreen a ranta tace wato dama ba sakinta yayi ba unguwa taje Kauye ashe Kuwa akwai bala’i wlh Zan iya kisan kai bari nayi sabon shiri,kwafa ta ja Ina kallonta bata ko kalle mu ba sai da kyar ta kalli Nawwar ta dauke kanta,ice cream Dina naci gaba da tsotsa na Mika Mata roba daya tare da furta uwar gidana ga roba daya nasa hannuna a saman kanta nace wannan gashin ai sai a zaci dambu ne mu rufa Masa wawa,kutmar….keda ice cream din ta kutuntuma min ashariya ko a jikina,shi kuwa tuni ya wuce samansa nima bangarena na wuce.

       Ina hutawa Fitowa nayi na zage na Fara gyara gidan,Da dakinsa na Fara lokacin hankalinsa ya kwanta Yana zaune gefen bed dinsa Yana latsa system dinsa na wanke toilet kal kal na fito nasa Hannu tare da dauke system din daga gefen bed din na matsar da ita gefe sannan nazo na riko hannayensa biyu nace Yi hakuri ka tashi,mikewa yayi Yana Jin sanyi a ransa,bed din nake gyarawa Yana Kare min kallo kamar zai cinyeni sabo da sanye nake da guntun wando da kyar ya rufe min duwawu da rigata t-shirt peach wandon Maroon,Shi kuwa sanye yake cikin dogon wando da riga iri daya farare tas rigar me dogon Hannu harda hularta yayi kyau sai kamshi yake,Yana kallona Yana ganin girmana sabo da Ina da tsayi da Yar kibata normal komai yaji,sai da na gama da gadon nasa sannan nace zauna tare da rungume shi na zaunar dashi a haka na dawo Masa da system dinsa inda take sannan na share nayi mopping ko Ina ya dauki kamshi sannan na fito ko Ina sai da na gyara banda bangaren Sabreen,kitchen na Shiga na fara girkina gida ya dauki kamshi,Nawwar ya dade rabon da yaji kamshin nan sai ya dawo Palo ko Ina Yana shining ya zauna a nutse,su Sultana ne Suka shigo da sallamar su,na fito Muka gaisa na zauna Muna surutu Nawwar yace yunwa nake ji fa,tashi nayi na koma dakina na dauro zanin Atamfa akan dan gutun wandona,hakan ya Masa Dadi yace a ransa lallai kin Fara hankali.

     Waina da miyar da na Fara Yi na zubo musu da kemo da ruwa sannan na kawo musu chin chin,kitchen naje Ina aikina har na gama suna hira abinsu sai da na gama na zubo Masa nasa wainar inda yake na kawo gabansa a manyan flasks na koma kitchen Ina cewa da Kannensa kuci fa kun San dai nan ba bakon gida bane,idan bata Isa ba sai na Kara musu dan Allah kar ku ji kunya,Su Sultana sai Murna sukeyi sun samu aunty me kirki,sai da na kawo Masa komai gabansa sannan na zauna,sai da suka ci Suka koshi nace Mami tana son Masa?Suka ce ae nace to na zuba muku sai ku Kai Mata,shi kanshi yaci wainar nan sosai fiye da zato na,da zasu tafi haka na cika musu flask sannan miyar daban suka tafi da ita,suna tafiya na cire zanin na fito kusan tumbur dani, kallona Nawwar yayi kawai Ina mamaki a raina wai ya akayi bana birge shi ne,Sam baya sha’awata,cinyoyina na tale yanda Muka saba zaman mu na Yan kwalta,Muka sake hada Ido ya maida Kansa ga tv,gabansa na dawo na tsaya tare da furta ban gane ba fa,yace what? Nace Kai billahillazi sai kayi sha’awata na gaji koma yane Kawai kayi sha’awata yawwa ehe Indai ana so a zauna lafiya Kawai ayi sha’awata haka Kawai sai gana min azaba akeyi,Dariya na bashi ya dinga Kuwa kyalkyalawa Kamar ba Nawwar ba,tsayawa nayi Ina kallonsa,sai da ya gama yace dama wai dan ni kike yi? baki na turo nace ban sani ba,Hannu ya miko min na kalli hannunsa na Mika masa nawa hannun nayi a hankali ya jawoni na zauna a hannun kujerarsa ya Kare min kallo ya sake tuntsirewa da dariya,Fuska na kwabe cike da shagwaba na mike a fusace Zan bar wajen ya sake riko hannuna naji wani yarrrrr a jikina, jikinsa ya jawo ni na fado saman cinyarsa bayana yake karewa kallo ko Ina fari luwai luwai,a saman dokin wuyana ya dora bakinsa a hankali cikin wata irin murya me rikita mata ya furta me kike so? nace ba komai Kawai,oya Ina jinki me ya faru naga gardi rungume da matata? Sannan Wanda ya Kira fa Yana Miki ya gajiya? Nan take idona ya ciko da hawaye na zame a hankali na koma kasa na zauna sosai sannan na dago idona Ina hawaye,yace ba kuka nace ki min ba,nace idan na rantse zaka yarda? Kasan bana karya wallahi duk abinda nasan nayi shi Zan fada maka,ban San komai ba akan Wanda ya kirani a waya Kai sheda ne da ace Ina da maza masu kirana da ka sani amma Inshaallah very soon zaka fahimta,sannan Wanda yazo gidan kawai ganinsa nayi a Palo ya fado Ina kokarin guduwa ya damko ni Kawai na barwa Allah duk Wanda ya min haka Inshaallah asirinsa sai ya tonu,Kawai kasan mu a baya an San mu a duniyanci ko yaushe a zargi muke shi yasa da anga irin wannan za a yarda kasan a inda ka dakko ni Kuma na yarda na zauna da kai Kuma bana boye maka komai tsakani da Allah nake zaune da Kai,mu yanzu ba Wanda bazai Mana sharri ba sai ka Kai zuciyarka nesa fa sannan akwai abinda nake kokari ka samu shine shedata lokacin zaka yarda dani .

    Har na gama bashi cikakkiyar amsa Yana kallona yace na gamsu da ke,nace na gode da fahimta da wani ne da tuni ya dade da sakina,me zance da Kai sai godiya,Ni Kuwa me zance da kai ai a duniya bani da kamarka Kuma na gode Allah ya saka a Aljanna firdausi,Ameen ya furta Yana Jin sanyi da wata nutsuwa a ransa,ya akayi kika daina min kiss? nace Naga Kamar baka so,ki daina daka tani ni kunya ce dani ba iya komai nayi ba yayi min wayo ban gane ba,dariya nayi na koma saman cinyarsa na zauna nace ka daina Jin kunyata nifa ba kunya ce dani ba zan iya tubewa a gabanka,yace Allah? nace ae to mu a fada Mana fitsara shi yasa nake so kaji dadi kaki Kai Kuma,Ni mene ma zaka ji kunyata ni ba malama ba bare ace Ina kwarjini,yace to ku ai Kun waye da irin wannan harka ni ai sai dai ki koya min,duk ban gane wayo bane,nace Kai da kake da mata bata baka ne? Yace to ita kunya ni kunya bama iyawa sosai, dariya nayi tare da furta ba wani ka iya kowa fa a fagen nan dan iskane Allah nayi kasa da muryata cikin rada na furta harda ubana tunda yayiwa uwata cikina,baki ya rufe da hannu yace Kika zagi Daddy,nace waye Daddy din ni bani da kowa gashi nan ana cewa Yar shege ce ni,mikewa nayi nace good night na wuce part dina,wanka nayi tare da tsaftace lungu da sakona yanda na Saba sannan na fito nan haka bayan nayi shirin bacci cikin wata guntuwar rigata pink,Ina Shirin kwanciya naji wayata tayi kara na duba Nawwar ne,Ina dagawa yace zo ki kawo min green tea, Fitowa nayi naje na hada Masa na nufi dakinsa Sabreen an Sha kwaya ana ta uban bacci.

      Shiga nayi daga shi sai boxers jikinsa ne me kyau ya dauki hankali na ina satar kallonsa na ajiye masa Zan juya yace Kun rainani a gidan nan ko wacce ranar girkinta sai tayi tafiyarta part din ta to daga yau nan kwana,Dadi naji amma na danne,kallona yake yi na zauna a gefe nima Ina kallonsa,muryarsa na tsinta yace kina son hakkinki ne a baki? Kai na girgiza alamar a’a,yayi mamaki yanda da nake roko amma yanzu nace a’a, Ido ya tsura min yace da gaske? nace da gaske na furta babu alamar wasa,to ni idan Ina so fa? dariya ya bani na danne sannan nace ni bana so yanzu,Zan iya tayaka kwana kamar da yanda baka taba ni,Amma yanzu ni harkar ciye ciyen nan ba so nake ba,ba kalau kike ba to infection ya kamaki,dariya na dinga yi nace akan me Infection zai kamani a toilet dinku ta gidan yawa da kike zuwa kina shiga ya Miki illa baki sani,3days Indai Kika ci gaba a haka asibiti zan kaiki dole kina da infection matar da kullum kike roko sai an lalata ki,pillow na dauka tare da rufe fuskata,baki ya bude yace ahhhhh gaskiya ba kalau ba ruqiyya kike bukata yau kece da kunya? harda rufe Fuska? Saman gadon na kwanta tare da kife kaina a Kan katifar Ina dariya kasa kasa yace Wai da gaske kike kunyata kike ji yau? mikewa nayi zaune duk na rasa inda Zan saka kaina wata kunyarsa nake ji,kaina na dauke na kalli gefe Ina murmushi na zaro harshe kadan duk cikin kunya,dariya yayi tare da furta ikon Allah Miracle guda yau da kunya addua tayi Allah ya amsa,dama kiss dinki da Kika Saba danne Ni ki min da shi Kika min yafi kunyar nan taki ni ban Saba gani ba,Jin yace Kiss na tashi na fece da gudu na bar dakin,ya tsaya baki bude yace kalau take Kuwa.

     Ya zaci kunyar ta wasa ce,sai da ya fito breakfast dake yau bazai fita ba,sai yaga har na gaishe shi bana kallonsa Kuma gaisuwar ba irin wacce mafi akasari nake Masa ba to yane? ya akayi? Ya garin ne? Ina serving nasa ban kula shi ba Kuma ban kalle shi ba ,dariya ta kamashi Kamar wata sabuwa haka na koma masa, yace to za kawo English teacher din? nace Inshaallah,Baki ya saki yace wai kece da Inshaallah har kin San Allah yanzu? na sake cewa Alhmdllh ba laifi,tagumi ya zuba Yana kallo na,yace ko dama Ustaziya ce ne ta lalace,dariya nayi bai gama Shan mamaki ba sai da yaga na canja channel na kamo sunna tv, dama karatun Qur’ani inayi idan na ga dama sabo da yanda na Saba tun Ina kauye,Sabreen ce ta fito taga mun Gama break Muna kallon wa’azi dariya ta tuntsire da shi tace ba wani alaye da zaki mana Kai Allah ya tsinewa karuwa kaji,karuwa ta Kai duk inda ta Kai a duniyanci wato sabo da an kamaki da kwarto shine Zaki canja salo,kallonta nayi nace Subhannallahi wannan kazafi ne Allah ya hana, kiyi harkarki nayi tawa idan ba haka ba Zan ladabtar dake da ayoyin Allah,Nawwar dariya ta kamashi ya Saba shi ashariya da zagin fitsara iri iri a gidansa, Sabreen ma dariyar ce ta kamata ta wuce dining,Nawwar na kalla nace ka kaini gidanmu,me zaki yi Kuma da’awa zanje,Sabreen ta kwashe da dariya sai ga su Sera su wurin bakwai sun shigo,tashi nayi Muka Yi ihun mu da Muka saba tare da rungume juna,Nawwar ne yace sannunku da zuwa shi Kam suna birge shi da kaunar junansu da hadin kai,Zama sukayi Suka gaisa nace me zaku ci,Suka ce sai da rana yanzu sun koshi,Kallo na sukayi Wise tace Miracle ya hasken musulunci? Nace Alhmdllh ai na baku labari tun a waya sai naji Kawai tuba da nadama tazo min lokaci daya Kamar ana ruwan sama haka nake ji addini na zubo min da tsoron Allah kafin safiya na cika makil da tsoron Allah,Tagumi Suka zuba Suka kafe ni da Ido,nace Ina fada muku Kamar a mafarki na tashi naji tuba da tsoron Allah sun fado min Kamar yanda naji farar daya karuwanci nake so, Seraline tace no wonder gashi nan goshinki sai shekin addini yake,nace ah ai walwali nake yi,Yaranki sun samu uwa ta gari nace wallahi ku tayani murna Ina haihuwa yarana zasu Sha tarbiyya tun Ina da ciki yaron zai iya Karatun fatiha dariya mukayi gaba daya,na nuna Nawwar nace idan muna saduwar sunna ma idan ya gasu cikin Oven Babu kiri’ar da baya ja,

     Star tana dariya tace au memory din nasa ashe yanzu ba waka bace karatune a ciki? nace ae Mana,Nawwar Jin fitsarar tamu ta daban ya mike tsaye Star  tace mu Kuwa Muna nan sai siyar da takashi mukeyi,nayi dariya nace Allah ya shiryeku kawayena Zan ta muku addua,yawwa ki Mana Addua mu yanzu mun manta rabanmu da karanta ko Bismillah, Nawwar yaji tausayinsu Mandula tace Ina so na shiryu wlh Amma bazan iya ba karuwanci ya shiga jini na sosai bana so ma na daina dan a Ina Zan iya Shan sigari? Kun San bana free da hayaki duk yanda akayi Bob marly ya biyo ta tsatson mu shi yasa na gado shi,dariya Muka Yi nace wlh kuwa baki Isa ba gidan aurena ne nan ba bariki ba sai dai ki fita daga gidan ki Sha abarki,tace an gama ta mike ta fice daga gidan gaba daya a can Kan layi ta dinga bulbula hayaki,Baki da wani aiki mu tayaki? Nawwar a ransa yace Allah sarki ji kauna dan Allah kamar yan uwa,cikina Sera ta shafa tace Wai har yanzu baza muyi Yara bane kinki samun ciki haba Miracle ni wlh kin bani haushi ko bakya zagewa ne a daki harka,ki dage rana daya zaki samu,nace ke muke jira kizo ki koya Mana yanda akeyi dan uwarki kaji min yarinya,haka muke ta hira har Nawwar yayi bako Khaleel ne yazo gidan Suka ma can bangaren baki,Sabreen kuwa tana part dinta tana Jin haushi Nawwar Yana barina ina abinda Naga dama Kuma tana ganin wani kallo da yake min kullum kamar zai cinye ni.

     Washe gari Jamcy ce tazo ta bawa Sabreen wani magani tace guba ce ke tunda ita take yin abincinta ki sa Mata a abinci taci dan ubanta ba a lokacin zata mutu ba bare a gane a hankali zata fara aiki a jikinta tana lalata Mata kayan ciki a hankali har ta Fara cuta slowly sai mutuwa Kinga babu me ganewa,tafawa sukayi Sabreen tace an gama Indai ba mutuwa Yarinyar tayi ba to bazan ji dadi ba.

 

Masu Neman Jin wasu Audio na novels Dina kuje YouTube channel na S ZARIA TV

MASU SHARHI INA GODIYA MUSAMMAN YAN GROUP DIN YAR AIKIN KARUWAI.

 

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                76-80

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naki ne
Mom Sani

Gaisuwa ga
Ummu Lateefah

       Washe gari da rana abinci na gama Nawwar baya nan sai na zuba nawa a plate Zan ci Ina sauri naji wayata tana Kara ashe Sabreen tana leke na tana ganin na haura sama ta fito lokacin yazo dai dai da shugowar Star gidan ita kadai unguwa taje ta biyo gidana zata ci abinci,taga Sabreen Sanda ta fito ta nufi kitchen yanda take kalle kalle ya nuna bata da gaskiya,Kawai sai Star taji bata yarda da Sabreen ba wayarta tana hannunta ta bi bayanta da Sanda itama ta leka kitchen din,ganinta tayi ta fito da wani garin magani fari tas,da Sauri Star ta fara daukanta da waya sai da ta Gama dauka sannan ta shigo kitchen din,Sabreen a gigice ta juyo tunaninta Rabiah ce, gumi ne ya Fara keto mata jikinta ya Fara mazari,Star gwanar daukan abu ne a waya,wayarta ta dannowa Sabreen video dinta tana zuba magani,tsoro ya kama Sabreen a kasa ta zube tana rokon Star dan Allah ki rufa min asiri

   Star Murmushi tayi tace kina so na rufa Miki asiri? tace dan Allah,to fada min maganin mene kike zubawa,Sabreen ta tsaya inda inda tace to bari naje na nunawa….kafin ta rufe baki Sabreen tace ta kisa ce idan an ci a hankali take kashewa mutum kayan cikinsa sai ya Fara cuta slowly slowly har ya mutu,Star tace oh my God yanzu rashin imanin naki ya Kai na kisa? Akan kishi Wai me yasa mata muke haka ne akan kishi sai mace ta kashe kishiya,miji,ko yaran kishiya banda Wanda ake haukatawa,tace to wannan bayanin da Kika Yi na maganin shima nayi recording sabo da hujja,Kuma wallahi duk abinda ya samu Rabia kinji na rantse kema se ya same ki mark my word in dai Yar uwar mu ta mutu wallahi Wallahi sai kin mutu yanda kika dauki hukunci haka zamu dauka a kanki,Kuma Ina nan zuwa kanki wannan abin da Kika yi ba banza ba,Sabreen ta mike ta fice sum sum,Fitowa nayi na iske Star a kitchen ta juye abincin da na zuba a plate cikin Leda baka tana wanke plate din,nace wai dama har kin karaso? Ae tace min kawo ,nace ya naganki ranki a bace? Naga wucewar Sabreen itama Kamar ranta a bace zaginki tayi naci uwarta,ke dalla rufe min baki banza wa ya ce Miki idan kin San kishiyarki bata da Imani ana ajiye abinda za a ci a ko Ina Wai part dinki ba akwai kitchen ba na rasa dalilin da sai kinzo kasa kinyi girki sai kace shashasha,nace idan nayi girki a sama dining Yana kasa bana son wahalar sakko da abinci shi yasa,a sa dining table din Mana a sama ba naga akwai wajensa ba,karki sake girki a nan kinji dai abinda na fada Miki Kuma kin San bazan ce Miki haka a banza ba Dole akwai dalili ki koma da girki a part dinki, nace Wai wani abu ne ya faru? idan baki ji ba ci gaba da girkin a nan ta ja tsaki ta fice da abincin a Leda a hannun ta,tsoro ne ya kamani,na dauki sauran anbincin dake flask na juye a katuwar Leda na fita na bawa me gadi nace ya kai cikin shara na dawo ciki na wanke komai na koma sama nayi sabon girki.

   Sabreen kuwa ranta ya baci da aka kamata ita da Rabiah ma taci abincin da sauki,wannan takaicin yasa ta zuba Coccaine dinta a jikin drawer ta bed ga kwalaben giyarta kanana masu mugun karfi,ta kwasho kwayoyinta sunfi talatin ta zube a gefe,tana sha Nawwar ya dawo bata sani ba lokacin Papa ya bashi sako ya bata na kudi,dakinta ya nufa direct Yana shiga isketa ta kafa Kai tana faman shekar Coccaine tana bubbuga kanta tana girgizawa alama tana caji sosai, baiyi magana ba bata hayyacinta ta daga Yar kwalabarta ta tiltile guda a cikinta tana shekar Kuma coccaine,Kwayoyin ta iba cikin hannunta,tana dagowa taga Nawwar dishi dishi take ganinsa duk da haka sai da tayi surrender amma ta riga ta bugu,dariya ta Fara kyakyatawa tana kallonsa tace tace Nawwwwwwwwarrrrrrr wanne ne na gaskiyar which one is you? Da yawa nake ganinka,wayyoooo dadi ta sake kafa Kai tana shekar Coccaine dinta,tana wani fisge fisge Kamar ana tsira Mata Allura,kwayoyin ta afa duka a bakinta ta hadiye da kyar tana rike waya ta shaketa tace ahhhhhh shiiiiiiii….ta sake girgiza kai tana furta no tension ta saki ihu da Kara ta sake Danna hancinta Kan garin mayenta tana sheka garin duk ya makale a hancinta da gefen bakinta,kwalaba daya ta giya ta sake  dagawa ta bulbulawa cikinta ta tura kasan gado,komai ta shanye sai yaga ta tura kasan gado wato a nan take boyewa,kallonsa tayi idonta yayi jajir lokacin bata gane waye ma,tace Niiiiiiii…..zaaaaaaaa……a …yiwaaaaa….iskanci….heeeeeyyyyy…..dariya ta kwashe da ita harda buga kafa….tace poison na zubawa shegiyaaaa….wacce akace Wai kishiyata ce….karuwa…dariya ta saki…..kawarta har ni zata Kama…..taaaaa….daukeni a waya…..ta juye abincin….wallahi bata ci ba….bare ta mutu….so nake ta muuuuuttuuuu…. Nawwar ta nuna da yatsa tace kaje kace ta mutu….bana sonta…sai na kashe ta……na…zuba ….Mata guba…..bata ci ba…. wayyoooo…bata ci ba….gashinta ta hargitsa gata da gashi itama me tsayi….kuka ta fashe da shi….ta mike tsaye da ihu ta dauki kwalabar giya ta bugata da bango ta tarwatse tace….bata ci gubar ba…..ohhhh fuccckkkkkk…ai ba komai na barbada mata na boka a Kan gado tana kwanciya zata Fara cuta ba ita ba tashi…fadawa tayi saman bed tana lumshe Ido sai bacci…

    Nawwar ya gama daskarewa a wajen da kyar ya iya daga kafarsa ya fito,tunawa yayi da abinda tace ta saka wani a bed ya tako part dina da sauri ya sameni Kawai Zan zauna a saman bed dina ihu ya saki na tsaya da sauri ban zauna ba,Yana karasowa ya fisgo ni jikinsa bai San Sabreen kwayarta ce kawai ta motsa amma ba wani magani data barbada min,saman bedsheet din ya cire ya kaishi cikin washing machine ya dawo yace ki dinga kulle part dinki idan baki ciki,to kawai nace Ina kallonsa,yau gaba daya Kansa ya dauki zafi sabo da haka ma Yana yin wanka zazzabi ya lullube shi sosai,sai da na Shiga Kai Masa abinci na hango shi a cikin bargo yana rawar sanyi, da sauri na karasa inda yake nace zazzabi ai Kuwa ya kamaka da yawa gaskiya,ka Sha magani? ae ya furta da kyar,nace ka Sha Kuma bai sauka ba sanyi kake ji haka,hankalina ya tashi nace to ni me Zan Kara maka duk kaurin wannan bargo ace baka ji dumi ba ai ba kanta,Idonsa yayi ja sosai jikinsa yayi zafi har nishin wahala yakeyi,kayana na cire gaba daya daga ni sai bra da pant ta bayansa na tsaya na cire dan bai San me nake yi ba har na shiga cikin bargon na jishi daga shi sai dogon wando marar kauri,bra dita na balle sabo da so nake na dumama shi da yawa ko zai rage mu ba wata kunya ce me yawa ba yanzu ne ma da na samu sauki.

     Matsawa nayi jikinsa sosai Muna kallon juna amma shi ta Kansa yake yi, sosai na manne a jikinsa tare rungumoshi jikina sosai da sosai na hade kirjina da nasa albarkatun kirjina suna kirjinsa duk da halin da yake sai da ya shiga wani hali jikinsa gaba daya wani abu ke masa yawo,bai sanda ya sake kankameni ba,ya rungumeni zam zam a jikinsa yana murza dokin wuyana,fuskarsa ya shigar cikin wuyana yana shakar kamshina me dadi,Yana Murzata a jikina a hankali ya dago da Kansa tare da hade bakina da nasa yana kissing dina gaba daya rawar sanyi ya daina tunda na shigo hankalinsa ya tashi ya daina Jin zazzabin,a hankali yake cinye min bakina cikin nutsuwa,hannayensa ya maida saman gashina yana shafawa cikin nutsuwa,a hankali sai gashi mun mike zaune a tsakiyar bed ba tare da mun shirya ba,ya kalli manyan boobs dina masu kyau wanda sun dade suna tsole masa ido,a hankali ko kunya yo mu babu na furta sun maka? Dariya na bashi yace ke dai kina so ace sunyi ko? Nace Kai duk jikina nafi kaunar su kasan Kuwa yanda nake ji da su Ina adana su ashe naka ne ma,dariya ta sake kamashi a ransa yace wacce ta gama rabawa maza itace me adana min,da sauri ya kautar da zancen bai son tunawa ma,zuciyarsa ya danne ya dora hannayensa biyu saman su ya saki ajiyar zuciya nima haka,Ido na lumshe ya fara lagude su yana Wasa dasu cikin kwarewa da wayewa, tuni na fara fita daga hayyacina abinka da angama lalacewa a baki dama kadan nake jira,so nake yayi amfani dani Kawai na fita daga zarginsa amma shi Kuma yaki Kawai gani yakeyi na gama rabawa maza,sosai na zage Ina faranta masa duk inda nasan zaiji dadi sai dana taba duk ya haukace min ban taba sanin haka yake ba sai yau,sai Nishin Dadi yakeyi Yana bani umarni Yi min kaza da kaza duk ina yanda yake so,hannu na daura a Antainarsa wacce ta mike kawai tayi fushi ta kumbura agaji take bukata,shi naga ko pant bai cire min ba ma’ana bazai kusance ni ba kazama ce ni na rabawa maza kaina,Raina ya baci da haka na fahimci nufinsa tsab tun daga yanda nake taba shi Yana gocewa sharewa Kawai nakeyi baya so ya Kai kololuwar da zai kusance ni ma tunda mutumin da Sabreen ma Allah ya Isa ta Sha yafi a irga daren farko sabo da ya kusance ta a ba virgin ba bare ni da nawa ya fito fili Wanda nasan ko na rantse Masa ban taba yi ba bazai yarda ba shi yasa na rabu da shi Kawai a haka idan yaji da Kansa ya fahimta amma yaki gwada kusantata ma bare ya sani.

     Ganin bazai ma taba gabana ba shi yasa Kawai na Kama Antainarsa na shiga Sha Masa Ina tsotse masa ita yanda yake min ihu da gurnani Yana Kiran sunana baza kace Nawwar bane na dauki lokaci Ina Sha Ina Masa wasanni Ina jiyar dashi dadi har zai kawo Yana so ya cire abar a bakina na rike ya kawo a bakina na zaci sperm din Dadi ne da shi ko wani Zaki Jin su Sera sunce Wanda yake birge su idan sun yarda da lafiyarsa suna Shan nasa shi yasa nake taso nima na Sha ko naji madarar da suke fada sai da na hadiye naji ba wani dadi,kaina yana kasa lokacin ya samu farin ciki sai wani murna yake yana nishadi,dago kanki na gani na dago a hankali Ina murmushin yake yace bude bakinki,budewa nayi yace Wai kin shanye nace ae Saura kadan nayi kuka badan na danne zuciyata ba,shi kuwa ba abinda ya dame shi sai wani dadi da yake ji Yana Jin dadi Wai na iya Shan madararsa,duk macen da ta maka ba karamin sonka take yi ba,sha’awa Kawai ya taso min shi yaji dadinsa baruwansa sabo da son kai.
Dannewa nayi Kamar ban damu ba nace bari na kawo maka abinci yace zanci ai na warke da taimakonki thanks,kayana na maida na tashi sai da nayi wanka na sannan na fito cikin wata gown me Fadi ce amma iyakarta cinya,Abincin na kawo a tire na ajiye na kawo Masa komai na ajiye,Yana jikin mudubi Yana shirinsa bed din na gyara neat na sake fesa room freshner, a saman Sallaya ya zauna na zuba masa na zauna a gefen bed din,yace ke baza kici ba? na koshi nace,Jin munyi Shuru Kuma ana son mace ta dinga samo Hira tana tayashi da hira ba Kawai miji yayi dunkum ba kema mace kiyi dunkum, kaje wajen Mami Kuwa na tambaya,yace yau ban je ba 2days ma kenan ban je ba,nace ya kamata kaje kuwa Mamin mu guda,Murmushi yayi yaji dadi,nace su Sultana wai sunyi candy? a nan ya dinga bani labarin makarantun da suke,nace amma sai naga kamar Nasira tana da saurin fushi,dariya yayi yace shegen zuciya gareta,Auta nake so yazo min hutu,yace ai Kuwa yace zaizo Wai ke ai akwai amana tsakaninku,da ba Sabreen Zaki dinga ganinsa sai ma ya dameki baya ji,haka Muka dinga hira har na ware na daina Jin ba dadi.

    Mairo Zaune take a dakin da Najib ya boyeta Wanda tunda ya kawota ya Kai sati uku kenan kullum sai yayi amfani da ita yanda yake so,tun bata Saba ba har ta hakura,tayi kuka ta godewa Allah har ma ta hakura,ya siya Mata kayan sawa ready-made, ganin ta rame ta lalace kullum tunanin iyayenta take yi sai Najib yaji tausayinta,shigowa yayi yau da safe ya Sha wankan shadda milk yana wani sheki Kamar sabon ango,tana zaune saman gadon ta rakube a gefe abin tausayi,saman bed din ya haura yace idan kin koma gida Matukar baki bani hadin Kai ba idan na kiraki a waya dole ki dauka sannan idan nazo gidanku wajibi ki fito,da sauri ta daga Masa Kai,yace wallahi idan Kika samu ciki Kika zubar min kinji na rantse sai na karar da danginku kaf,nan ma Kai ta daga tare da furta to,bakinsa ya jefa cikin nata ya Fara kissing nata kamar ba gobe tare da Kama boobs dinta Yana latsawa yanda yake so,da kyar ya daure yace tashi mu tafi,Kamar an tsundumata a aljanna farin cikinta ya kasa boyuwa harda cewa sai yaushe zaka zo? Yace Kawai idan naga dama Zaki ganni sai lokacin suka fito daga gidan tare da shiga wata mota benz me kyau ya tuka Suka tafi harda kayan da ya siya mata har kauyensu ya kaita amma bai karasa ciki ba ya ajiyeta a nan ya juya yayi tafiyarsa

   Dole ta taka a kafa har gidansu mutanen gari sai tambaya suke mairo daga Ina kike babu Wanda ta kula sai dai idan ka ganta kasan ta rame suka dinga labari Wanda Suka saci Mairo sun dawo ita
tana shiga gida Gwaggo ta saki Salati tana kwalawa Dagaci Kira Aunty Amarya ta fito ita da taba kafadun Mairo tare da girgizawa tace wallahi itace Mairon mu ce,Dagaci Yana zuwa ya jefar da butar dake hannunsa yace Mairo ta Alhmdllh,Mairo ma murna take Yi taga iyayenta su Imrana Suka shigo Jin labarin a gari da gudu Suka fada jikin Mairo, Mairo tace Ina Audu? Gwaggo ta kalli Dagaci a hankali Dagaci yace Audu bayan tafiyarki miciji ya sare shi Allah yayi Masa rasuwa a wajen magani,Mairo ta fashe da kukan mutuwar Audu kaninsu.
Yan Uwa da abokan arziki sai Murna ake zuwa Mairo ta fito,washe gari aka bugawa Gaji waya tace zata zo.

     Zayya da Gaji kishinsu baya karewa,Zayya ta samu sabon malami kakarta ta kaita,malamin yace Zan Miki aiki Wanda Zan haddasa musu fada kowanne ya kasa hakuri daga haka an gama,duk abinda malamin yace ta aikata ta binne layar daya bata a kofar gida,sannan ya bata wata takarda yace ta koneta ta kwashe tokar ta shanye haka tayi Kuwa,Gaji tayi shirinta zata tafi gida wajen Mairo sai ga Danbinni ya shigo a fusace Yana masifa baki da aiki sai jarabar yawo da tafiya gida,Gaji da rashin kunya bata da hakuri tace naga dai da bakinka kace ka barni naje yanzu zaka zo ka dameni ta ja wawan tsaki,Danbinni yace to na fasa barinki koma ciki,ai wallahi tunda nayi niyya to nayi niyya Kuwa ba fashi ko uwarka ce bata Isa ba,Danbinni ya furta haka Kika ce? Gaji tace kwarai kuwa yace to idan kin tafi karki dawo,gidanka din banza mene a ciki in banda wahala Dan karya azzalumi, Dabinni daki ya shiga ya rubuta Mata saki ya fito ta kalli Gaji yace Gaji na sake ki saki Daya,tace tayi kadan ai a Kara,yace na sake ki saki biyu,zuciya ta kwashi Gaji tace idan Kai Dan halak ne cikin uwarka Talatu da take kabari idan ubanka ne yayi cikinka aka haifeka da jini ka cike min sakina uku dan me dafa maka abinci kana yaro ka sakeni,dabba jaki Wanda bai San me yake ba,Danbinni ya damki Gaji ya Mata dukan tsiya ya farfasa Mata jiki sannan yace na Sake ki saki uku igiya ta Kare tashi ki tattara kayan sawarki kuma wallahi lefen dana Miki da duk wani Abu nawa baza ki taba min ba ki kwashi iya na garinku da na auro ki da su.

    Gaji kayanta ta tattara a buhu duk iya abinda tazo da shi shine a dan buhu ta fito ta bar gidan da takardar sakinta da Danbinni ya bata,Zayya tana daki tayi Kamar bacci take yi murna ta Gama cika Mata zuciya tace Danbinni idan zaka Yi aure dari sai na kore su,Gaji Kuwa da kuka ta Shiga gidansu,tace Danbinni ya nuna min iyakata sai da ya min dukan tsiya sannan ya min saki uku,ban san hawa ba ban San sauka ba akan Kawai zanzo gida ganin Mairo,Dagaci ya karbi takarda yace saki uku ya cika amma wannan ba karamin matsiyaci bane,Gwaggo tace wallahi tunda ya sako min ‘ya itama matar  tasa sai ya saketa wallahi bata Isa ta zauna a gidan ba,Gaji tace gwara haka itama a saketa ta rasa gidan ai sai ta fini damuwa tunda ita tana da yara,Mairo dai bata Fadi an lalatata ba shuru tayi tace ai kawai da suka sace ta gajiya Suka Yi da ita Suka saketa da kansu

     Bayan sati daya da sakin Gaji Dagaci malamai ya fada sai kace mace haka yake nemowa yaransa magani,Gaji tana kwance tana Jin haushin abinda Danbinni ya Mata sakin wulakanci ga mutanen Kauye sai gulmar tsiya sabo da rashin yawa kowa ya san kowa,gaba daya Gaji bata iya fita sosai,yau suna tsakar gida gaba dayansu suna hira Gaji tayi Shuru tana tunanin aurenta ana wata hirar daban sai ji akayi Gaji ta furta dama tun daga kallon gidan Danbinni kowa yasan baza a tsinci abin kirki ba,tun daga unguwar ma cewar Mairo daga nan aka dasa zancenka Danbirni da Zayya.

    Damuwa ce ke cina kwarai rashin kusantata da nawwar yaki yi,a dakina ya sameni na zuba tagumi tare da lulawa duniyar tunani, har ya zauna a gefena ban sani ba,hannuna ya cire yace Mene ne? murmushin yake naji kunya ma ta rufe ni sabo da irin kallon da yake min,Yace Miracle dina,kallonsa nayi da sauri Ina Jin Dadi yace miracle dinsa,Murmushi ya saki yace meke damar min matata,hawayene ya zubo min kunyarsa nake ji na rufe idona da tafukan hannayena nace Kaine kaki ka Shiga Oven dina,ya kamata kasa min memory ka Sha kida Amma kaki karka kace bani da kunya gaskiya na fada maka ni bana jin Dadi idan baka so na me yasa ka aureni,Nawwar yace tofa kiyi hakuri yau Inshaallah da dare zanyi,nace ni yanzu nake so,a raina burina Kawai ya shige ni yaji sabuwa ce ni kuma ni ban San zafin abin ba ga yanda su Star suke yabon dadinsa,Ina magana Ina kallon gefe Wai kunya Kar mu hada ido,a hankali yasa hannayensa ya juyo dani Muna kallon juna yana min wani kallo me wuyar fassarawa a hankali cikin muryarsa me rikitarwa ya furta I love you,Ina sonki ki cire komai a ranki bana so ne naji haushinki shi yasa na kasa kusantarki bana so naji abinda bana so Ina sonki kaunarki tasa nake gudun abinda zai bata Mana zama,hawaye ne ya zubo min da zargin da yake min,kuka wiwi na Fara yana kallona,fuskata ya tallafe da hannayensa biyu tare da hade bakinmu waje daya ya Fara min wata irin sumbatar da ban san da zamanta ba,Ina hawaye Yana aika min da sako,a hankali na zare Masa rigarsa jalllabiya fara na cillarta gefe,a haka Naga Antaina a cikin boxers ta Gama sankamewa nayi kasa da dan guntun wandon Ina shafa Antaina Ina sarrafata,Nawwar nishi yake ya gigice bai sanda ya rabani da kayan jikina ba har pant ya zare min,naji dadi yanda yake sarrafani Yana tsotsar Boobs dina Kamar karamin yaro,Ina kara tura Masa a baki Ina furta …shshhhh….shi kuwa sake zaucewa yayi ya susuce jikinsa har rawa yake Kamar wani mayunwaci,Kamar yaci babu yanda yake min cikin zafi zafi jikinsa yana sarrafani sai dana firgita da yanda yake min,Baki ya saka a Oven dina ya Fara min wani tsotsa duk na jike da niima,ihu na Shiga Yi na dadi Ina wayyo Star….Seraline…….Ashe ba banza ba Gwaggo suke cewa Dagaci zai kashe su nima zaka kasheni…..Zan mutu….Nawwar sai wani Jin dadi yake yasa Ina Jin sweet sai da na Kai kololuwa sannan ya fara kokarin shigata Ina ji naji Antaina taki shiga,har na Fara Jin zafi,Nawwar mamaki ya kamashi ya kashe shi,a Haka dakyar ya fara sa karfi zai shigeni na fara ihu na tashi zan gudu nace ashe da zafi wayyo Allah wlh ban San Namiji ba ban taba sex da wani ba zafi,fisgoni yayi ya jawo ni Ina wutsil Ina ihu tare da furta yanzu Yamma tayi la’asar ta wuce lokacin yanzu bala’u me sauka dan Allah ka bari sai dare,Sabreen ta fito taji ihu na Muna ta kokawa da Nawwar kasa tafiya tayi ta lallaba ta shigo bangarena ta labe a kofar bedroom dina tana Jin irin kokawar da muke Ina kuka da rokonsa

    Tana ji nace wayyo na mike tsaye na tsaya a saman bed yace Wai mene haka bana son irin wannan ki bani hakkina ya fisgoni na kwala kara Ina rokonsa dan Allah kayi hakuri wlh na fasa bana so,ai wani haukacewa da yayi ya jawoni ya rirrekeni yana tsuma da makyarkyata ina ihu nace na Shiga Uku yau na mutu,Sabreen baki ta toshe tana Jin Nawwar Yana magiya nayi hakuri na amince,danne Ni yayi sosai ko motsi kasa yi nayi na fashe da kuka wiwi ba ruwansa baya cikin hayyacinsa haka ya shigeni da karfi sabo da ya gwada ya lallabani abin yaki shiga, wani ihu na saki Ina kuka,ai shi ba ruwansa tunda yaji dadi Kawai daura min sirdi yayi kamar ya hau doki Yana sukuwa,Ihun kuka nake Ina tureshi Ina dukansa,ga cizo da yakushi,shi kuwa Yana jina yasan Virgin ce da nake ashe har da Yin kabbara Kawai Allahu Akbar yake furtawa Ina zunduma kuka,shi kuwa sai yabona yake Yana zuba min kalaman soyayya da kauna,ban taba son kowa ba sai ke,Ina sonki,kece zuciyata, bazan rayu babu ke ba idan ba ke wayyo kin hadu Baby…..washhhhh……ahhhhhhh…..kin hadu….ashe virgin ce ke na dauki hakkinki ki yafe min….I love you…ko me kike so Zan Miki…..bani da kamarki…..Ni Kuwa kuka nake wiwi gashi yau Kamar yasha maganin maza yaki ya kawo bare na huta na sake kecewa da kuka,gaba daya jini yayi kaca kaca da wajen,naci bakar azaba ranar sai yaji zai kawo sai ya zare Antaina sabo da dadin da yake ji bama ya so ya daina yi,Sai da yayi min kaca kaca Dan harka ya kwasa ta Allah tsine uwar me karya da zai kawo Kuwa harda hawaye yayi, Sabreen hawaye ya wanke mata Fuska gaba daya

   Abin ya bata mamaki ita nata ko quarter din wannan bai Mata ba yanda taji Yana ihu da sambatu ita Kuwa baya yi Mata Kamar ba mace ba haka yake Mata,a maganganunsu ta fuskanci Lallai Rabi virgin ce ko wani magani ne nasu na yan duniya ya Zama dole itama ta nemi maganin Mata ko ta samu Nawwar ya Mata ko da Rabin wannan ihun ne,bakin ciki kamar ya kashe Sabreen lokacin tasan ita lallai ba mace bace tana kuka ta fada dakinta tana cewa labena ya ja min na jiwa kaina masifa ta dinga kuka wiwi.
Ni kuwa kuka nake har muryata ta Fara dashewa  Yana ta lallashina Yana wani farin ciki yana godewa Allah sai Alhmdllh yake furtawa yana cewa Allah ya Miki Albarka ai ban sani ba,haba no wonder na iya rikeki a gidana bakya Neman kowanne Namiji haba ni fa Ina ta mamaki ace Yar bariki guda Kamar bata San Sex ba bakya kula maza ko daya na dade Ina mamaki,da murna ya furta Rabita tare da fadowa kaina ya rungumeni,nace duba min ka gani cinyata tana nan Kuwa tana jikina? Dariya yake yace tana nan mana Ina zata je, nace tunda tana nan da sauki nace shike nan Oven ya dagargaje a Kira min su Sera Yan Uwana,Yana ta murna ya Kira Wayar Star tana dagawa ya Mika min wayar,Kuka na saki nace ku taho Yar uwarku zata mutu,ko Gama ji bata Yi ba ta kashe wayar tace ku taho da yamman Nan za a kashe Mana Miracle gashi can ana dukanta,Santana yace ehehe yau akwai bantan bala’i ku bari na dakko Atamfar sallata,ku Fara yin gaba sai na Gama soya Miya ta gani Nan,Sera,Wise,Star da Yar Zabil su hudu Suka taho gidana, Nawwar kuwa daukana yayi zuwa toilet Ina kawarara kuka wayyo cinyoyina ka saukeni zafi Zan mutu,ya hada ruwan zafi da gishiri ya gasani sama sama shi ba iyawa yayi ba,yamin wanka har na tsarkin ma,dawo dani yayi saman kujerar mudubi yaga yanda bedsheet yayi kaca kaca harda ciro bedsheet din ya dinga zuba Masa kiss Yana furta wannan bedsheet din matsayinsa ya karu dan Albarka jinin Virgin wife Dina akai ai ya shiga tarihi,da Kansa ya wanke a washing machine ya shanya ya canja wani ya sake gyara min dakina yace bedsheet Yana bushewa Zan dauke abina na boye shi tarihi ne ya Zama na tarihi,ko kulashi banyi ba Ina daure da towel a kirjina ga wani ya nade min gashina jikakke,sai da yayi wanka shima tare da tsarkakewa sannan yazo yasa hair drier ya busar min da gashi Ina ta kuka na kasa magana ma Haka ya gyara min gashina ya sa ribbon ya Kama sannan ya sa min Riga doguwa marar nauyi  ya sake kwaso bra da pant yace na manta ba a sa wannan ba,da muryar kuka nace bana so ni wajen bai warke ba Zan saka na kumeshi cikin pant a barshi ya Sha iskaaaaaa…..na karasa da kuka sosai,dariya ta Kama Nawwar yace yanzu duk duniyancin nan Ina yake ne Wai Rabi da kuka akan Sex, zan maka Allah ya Isa ka daina kulani bana sonka,Ido ya zaro Yana dariya sabo da shi a cikin nishadi da farin ciki yake ya rasa inda zai sa Kansa.

   Hayaniya yaji a kasa ya leka ya dawo yace Wai dama Kawayen naki zuwa Suka Yi na gansu su hudu gasu can da Sabreen suna zaginta,fita yayi ya sauko Yana kallon Sabreen zaune a Palo tana sharbar uban kuka ya zaci ma zagin da Star ke Mata ya sata kuka,Star tana furta annamimiya me kisan kai gantalalliya Yar me kukan burar….ta karasa da ashar, Wise tace Allah yasa muji kece yau mu nada miki duka,Nawwar ne yace me ta muku ne haka Yana washe baki kamar gonar auduga su kansu basu San Yana da fara’a haka ba sai yau,Star tace mu matarka ce ta kiramu tana kuka ai mun zaci dukanta akayi,dariya Nawwar yayi yace tana dakinta kuje ku lallasar min ita Kar zuyata ta buga ,ya manta da Sabreen,su kuwa su Sera dariya ya basu harda shewa ahayyeeee Rabia gaskiya ta gama da zuciyarka waye ya Isa ya Kama kafarta a gidan nan Muna yinka ogan Rabia,Nawwar harda murmushin Jin dadi ance ogan Rabia,Sabreen bakin ciki ya Kama Sabreen ta mike ta fara danno musu ashariya iri iri tana cewa dadin abin mu yayan sunna ne ba yayan na surnaneki sunna bane yawwa da ubana da uwata auren sunna Suka Yi aka sameni,Nawwar ya gaji da magana Kawai cewa yayi kuje sama dakinta,Sabreen tace baku Isa ku hau Mana sama ku gane Mana sirri ba ai nan ba gidan ubanku bane,Wata mahaukaciyar shewa suka yi a tare heeeeeyyyyyyy hehehe suka Yi sama,Nawwar tuni Ya fice a mota ma,ya tafi samo Mata kayan makulashe.

   Suna shiga Suka iskeni zaune a saman kujerar mudubi na Kifa Kai Ina kuka,Wise tace ke Kuwa lafiya Oga ya fita cike da nishadi ke kina nan kina kuka ko sai an karanta Miki Suratul bakara ne,Yar Zabil tace kai ku bamu carbi dan Allah idan mijin bai sonki ko Suratul Yusuf ai ma karanta miki yanzu kafa goma goma ko Kya samu tabarakin farin jini,Ina kuka na dago idona jajir nace bana son Iskanci fa idan baku da addini kuyi Shuru ya fiye muku ni bani da lafiya,Sera ce tasa Hannu tana kokarin dagani tace taso ihu na saki Ina cewa zafiiiiii….Wise ta taimaka da Yarzabil Suka dagani jini Suka gani ya bata min Bayan farin towel din kadan, ai Star da Sauri ta kurma ihu ta dora Hannu akai taja baya tare da mannewa da bango tana furta mamiwoooooo ewooooo chaiii…….karuwa kamar virgin jini fa ke kasheki zaiyi Dan jakar ubansa,Wise tace shi yasa yake ta yaye dan baki Kamar kurtun majinar liman din kauyen mu dame cikin masallaci ashe aika aika yayi ke Kuwa wanne magani kika Sha ya matseki haka,Ina kuka nace Ni vurgince fa wallahi na basu labarin yanda akayi ni ban taba sex ba,Star tace ke dalla mu mun sani kyaleki Kawai mukayi ai mu ba mahaukata bane Kawai binki muke Yi da haka mun San ba uwar da Kika sani na Namiji,ke karuwanci fa ba karya bane,muma muna kyamar harkar Kawai dai mun tsumu a cikine,daukana Suka yi zasu gasani nace wlh Baku Isa ba baza kuga tsaraicina ba,inda Nawwar din yaje zaku gani ku Raina shi,dariya Suka yi Sera ta dura min ashar tace kina dashi Muna da shi fa abinda kike dashi shine damu Kuma mu ba Yan lesbian bane ki bari mu taimaka Miki wallahi idan ta ciyo shi haka zai sake Miki kaca kaca gwara ma ki taimaki kanki mu gasaki,nace wlh mugune Ina kuka,Sera tace to munji aure ne dai dake karki fada Mana sirrinku ba kyau ko ba haka akace ba mu dai zamu Fadi na yan bariki,Suka daukeni ta karfi Ina musu mafisa Basu kulani ba Suka Yi sama dani zuwa toilet,harda bugawa Mandula waya ta kawo musu magungunan gyaran jiki sai kace Iyayen mata haka suka dinga gana min azaba da ruwa me bala’in zafi ba irin wahalar da ban sha ba,Sera tace sai mun Miki ruwa biyar nace da zafi wlh baku da hankali harda cizon Star a hannu ta zuba min rankwashi Dan uwarki ki tsaya, sai dariya suke min wai na fiye kwailo,Sera tace baza ki Bude kafofin ba ke da naki ma yake fari gwanin dadin kallo,na samu Sera na kwala mata Body shower gel a Kai ta saki Kara ta ja baya Ina ta zaginsu da kyar aka min ruwa hudu naki yarda su ganar min alaurata,haka Suka bani towel na daura sannan na mike dama da bra ta a jikina na saka amma sun jikata,Ina fitowa na cire Suka shanyata Suka sake gyara min dakina harda toilet ma sannan Suka hado min tea na sha abincin ya Kare ma su kuwa Cornflakes Suka dinga hadawa da Madara suna Sha sai da Suka koshi Suka wanke kwanikan,Suna Jin motar Nawwar Suka ce to sai mun dawo gashi nace wlh baku Isa ba Kar shegiyar data dawo gidan nan, ficewa sukayi a compound suka yiwa Nawwar sallama Suka tafi suna ta dariya.

    Suna komawa Suka iske Santana Ya fito sanye da doguwar rigar leshi an Mata Kalar dinkin jallabiya ya fito Yana karairaya yaga sun dawo Yana duba fuskarsa a mudubi yace ban gane ba anyi Yamma da kare ya na ganku Kuma iceko Yar uwar tana lafiya? Sera tace disvirgin dinta akayi fa,Dandaudu ya dafe kirji tare da furta na shiga Uku kardai zancen Nan ya tabbata miracle bata taba sex ba,ai Kuwa ya tabbata cewar Sera,Santana yace ahayeee Ashe yau za a cashe wa yace bariki ba a samun virgin dan ubansa ya fito yayi magana ko waye yaga luguden bala’i Yana bankaro kirji gaba ya Shiga kwalawa karuwai Kira Ina Mandula dake Shirin zuwa tana hada magani zata kai fito,ke Manduwa,Pretty,charity tsohuwar alagongon fito,ke Honey tsohuwar karuwa,Ina big breast kilaki ku fito kowa yazo yaji mun Kai yarmu a virgin abin murna ya samemu abin magana yazo kuzo Karuwa virgin a gidan nan, wuuuuu wacece haka ni ‘yasu cewar dayan dan daudun Santana yace Miracle Allah ya nusa Yarinyar nan dai ashe a cikin Leda take a ledar ma a kwali yanzu Yan Uwa suka dawo daga gashi,heeeey sabadan inji dayan dandaudun harda zuwa ya rungume Mandula yace Karuwa virgin hhhhhh suka fashe da dariya dole ayi chasu yau,Nan take suka hada party suna ta gayyatar mutane Suka siyo drinks da kayan makulashe da za a ci ga kida da uban Dj,Santana ya Fara rawa Yana girgiza Yana furta munkai Yar mu virgin ya saki guda,Star Suka Shige rawa su Sera kamar bakin uwa.

  Nawwar Yana shigowa nayi sauri na rufe idona na Fara baccin karya,haushinsa naji ga wahalar gashi da na Sha ga azabar da nake ji,mafarkin karya na fara Jin yana tattaba min wuya na fara cewa Nawwar kaji tausayin marainiya wajen nan ba a binsa ta karfi Kalar wajen daban Allah ya yi shi baya son wahala,zaka kashe ni da wahala,yau ka bada min yaji wayyo zafin wahala,ba a irin wannan a rayuwa ka Kama baiwar Allah ba sani ba sabo ka barbadeni da yaji,Nawwar Ashe kai baka San na gida ba,ka zauna Kato dakai ka samu marainiya ka dinga gana min azaba haba amana bata ce haka ba,dariya ta kamashi yace idan ma Zaki tashi ki tashi yarinya ni Kam naga waje wlh ba daga kafa gwara ma ki Saba,yanzu zan karbe karuwancin naki zai dawo wajena, cikakken Dan duniya ne ni ya furta ban San sanda ya bani dariya ba amma ba halin nayi a zuciya nayi Wai sabo da Kar ma ya Kara kawo min wargi, yau ko Palo yaki fita Muna tare ya manne min ya hanani sakat,sabo da rashin tausayi haka Muka kwana Yana tattabe min jiki Ina jinsa naki yin mitsi Kar ma a samu matsala ya zauce min,haka Muka kwana.

Nawwar washe gari Sabreen ta dawo hayyacinta ta gama kukan takaicina gashi a sanda ya kamata ba abinda ta iya tunawa Wanda za a ace ta tuna sanda Nawwar ya kamata tana shaye shaye,tana zaune a palonta ta baje Nawwar ya shigo ya sameta kallonta yayi yaga ko a jikinta tabbacin bata San ma ya ganta ba,takarda ya mika yace gashi ki tafi gidanku na sakeki saki daya idan aka hada da Wanda na fara miki ya cika saki biyu dai dai,Sabreen wata mahaukaciyar dariya ta saki tace wallahi ba inda zanje Ina nan Ina nan Zama daram a nan zanyi Idda,Nawwar ransa ya baci ya daga waya nan take ya Kira Papa direct bayan sun gaisa yace ka fadawa Sabreen ta tattara nata ya nata ta bar min gida na sake sakinta tace baza ta tafi ba wallahi idan na illatata ita ta jawa kanta ya kashe wayarsa.
Sabreen tana kallonsa ya fice ta fashe da kuka Kamar zata kashe kanta

    Ko minti Sha biyar ba ayi ba Baffa ya Kira Nawwar,Iyamami,Mami,Mama,Amarya Ummin Haidar sai papa Suka sa Nawwar a gaba Kan lallai sai ya dawo da Sabreen yace wlh bazan dawo da ita ba,bai taba musu taurin Kai irin wannan ba,sunyi sunyi yace wlh bazan iya Zama da me shaye shaye ba har Coccaine Watarana zata iya kashe mu,Baffa ya dinga bala’i dama baka da mutunci yanzu tunda ka auri wannan cikakkiyar Karuwar ta zugaka ka bijire Mana mu iyayenka,to Aljannarka tana kafar mu sai ka bi mu zaka ga dai dai,Iyamami tace ato kaji da Kai mutumin banza Kai ai me rufawa Sabreen asiri ne shi yasa aka hadaku aure sabo da ka rufawa Yar uwarka asiri ashe Kaine me kwaye Mata baya,Nawwar magana zaiyi Mami ta tace ya Isa Nawwar bana son tashin hankali ka maida ta kawai,Baffa ya kalli Mami yace munafuka algunguma dama kece kike haddasa komai to wallahi bari kiji Matukar Nawwar bai dawo da ita ba kema igiyarki tana tangal tangal ka dawo da ita ko na saki uwarka,Mami ranta ya baci ta gaji tace karka dawo ita nawwar bani takardata,Nawwar yace no Mami Zan dawo ita,ko ka dawo da ita sai ya sake ni,Mami igiyarki Saura daya bari naje na dawo da ita,Mami tace idan ka dawo da Sabreen ban yafe maka ba ta mikawa Baffa hannu tace bani takarda ta,ba kunya ba tunani yace na karashe igiyata kije na sakeki saki daya ya Zama uku,Mami tace rubuta min ya rubuta Kuwa ta karba,Iyamami tace kinwa kanki kin shiga uku Kuwa babu ke ba samun Kamar dana,Nawwar harda hawaye,Papa yace ka jawowa kanku bacin rai haka kawai,Mami hannun Nawwar ta rike muje ta furta.

     Mami kayanta ta hada tana hawaye Iyamami ta biyota tana masifa ba inda Zaki je Mana da yara,Su Sultana kuka suke kawai Mami igiya ta Kare shike nan,Last born ne ya shigo ya samu abinda ke faruwa yace igiyar dake lilo ta karasa? Sultana tana kuka tace ae yace to mene abin kuka Kuma da damun kanku so what dan haka ta faru sai mu koma inda Mami take,Nasira tana kuka tace ai Baffa sun ce sai dai a barmu a nan mu kadai,Auta Ido ya zaro yace oh God shi yasa nace tun wuri nace ayi min aure aka ki ji da yanzu Ina gidan matata,dariya ya bawa kowa,ya sake cewa su Iyamami sun shiga Uku sunga ta kansu unguwar nan kaf sai tasan bani da uwa a gidan nan sai na Zama musu tsiya za a gani,Nawwar yace Kai dalla karka dame mu stupid ya ja tsaki,Auta yayi mukus yace tunda an saki bakar kadara yanzu kullum Ina gidanka yaya Allah ko sallama bazan dinga yi ba idan Zan shigo,Rankwashinsa Mami tayi sune Suka tayata ta hada kayanta na sawa sannan ta musu nasiha tace zata dinga zuwa Suma zasu na zuwa gidan da take,Yar aikinta tabawa ta dauka Nawwar ya kaita Daya daga cikin gidajensa da take so,komai na abinci sai da ya tabbatar komai ya zuba bata da matsala ya bar Mata kudin cefane sannan ya bar gidan ya dawo gidansa.

    Mama ya samu da Sabreen sun tattara kayan sawarta suna lodawa a mota Sabreen tana kuka tace wallahi Zan dawo sai nayi maganin Karuwar nan bari naje gida na huta,Mama tace ke dalla muje marar zuciya ko Dan gwal ne kin hakura da shi ai ba shine autan maza ba ko shine dan autan Mata yaje can ya karata dama ni ba son hada jinina nake da uwarsa ba,suna ta zage zage,Nawwar haushin an saki uwarsa ya karawa Sabreen saki yace Nima na cike uku ba aure tsakanina daje Suka bar gidan Kuwa suna ashariya,Nawwar ko ta kansu bai bi ba ya shigo ciki Kansa ya dau zafi.
Tunda na ganshi a yanayin kunci nayi zaton yanayinsa ne tunda dama bai fiye dariya ba,shi yasa na share Kuma ga tsoron abinda ya min ni yanzu tsoronsa nake Kamar masifa tunda nace Sannu da zuwa ya amsa ciki ciki ya haura sama banyi gigin binsa ba Kamar yanda na saba, Shuru yagani ban shigo ba har yayi wanka ya canja cikin Jallabiya ya fito bana main Palo Ina part dina na koma can,a ransa yace yau sauratar ce ta motsa ko abinci baza ace naci ba ta wani
shareni wato ko naci ko na barshi,yanzu Kuma bana girki a kitchen din kasa Kamar yanda Star ta bani shawara,Ina kallon Korean drama naji ya murda handle ya shigo sallama dauke a bakinsa,amsawa nayi naci gaba da uzurina,kwafa ya ja a ransa Kawai ya wuce kitchen din da Kansa ya ebo abinci a plate fried rice nayi da kaza,Fitowa yayi ya dawo gefena ya zauna dake a saman doguwar kujera nake,har ya Fara cin abincinsa bance Masa ta tafasa a sauke ba har ya gaji ya kalleni,Naga yana satar kallona sai na sake zumburo dan bakina karami,sai da ya kusa cinye abincinsa yace dakko min ruwa,na gaji ni na furta Kai tsaye,kallona yayi da sauri na dauke kai zuwa wasu lokaci na tashi dai Ina tafiyar agwagwa sabo da raunin Da ya ja min harda  sangarta irin an dameni naje na dakko da glass cup na kawo na ajiye masa naci gaba da kallona,bai ce min komai ba sai da ya gama cinye abincinsa ya sha ruwa sannan ya kalle ni yace ke Kuma me aka miki? Please do not add to my problems, what’s going on? nace ba komai nace,na gaji bacci nake ji da wuri zan kwanta karki  bata min lokaci ya furta, hawaye ya zubo min nace na Shiga Uku a raina a fili nace da wai da bani da wa kake kwana? Yace da Sabreen mana,wani kishi ne ya cika min zuciya,kamar zanyi kuka nayi shuru na mike nace muje,yace da wannan jean din Zaki kwana? Menene amfanin cire shi,ya kalleni yace me aka Miki yau ne? kayan wuta na kashe na wuce shi a hanya Ina sauri na riga shi zuwa dakin nasa a haka da jean Dina na wando da riga na haura saman gadon tare da kwanciya.

    Kyaleni yayi shima ya kwanta a jikina tare da sa hannu ya rungumeni a jikinsa,kasa bacci nayi sabo da uban kayan dake jikina ban Saba kwana da Kaya masu nauyi ba haka ba ga tsoronsa,sai mutsu mutsu nake Yi a jikinsa,duk motsi sai naji yace menene cikin muryar baccinsa duk farkawa sai ya lugwigwice min breast,duk a akwai bra,gajiya yayi ya shiga cire min kayan jikina Yana cewa sai kace yaki ya cire su ya jefo su kasa,hakan yasa ya kasa bacci ya fara murzani cikin salonsa,  yana Jin haushin kunyar nan tawa ta yanzu yafi Sona a Yar Duniyata a wajensa shi daya,wanj Kara kaunata yake a ransa,da kyar na saki Masa kuka ya kyaleni Muka samu bacci.

    Washe gari ba inda ya fita yana gida duk inda nasa kafa Yana wajen Kamar jela muna kallo yayi matashi da cinyata Seraline da wise Suka Yi knocking tare da shugowa,nace shegun duniya ba sallama? Wise tace la mun manta af ke fa na tuna tun kina gida baki manta sallama ba,Murmushi na saki tare da furta Allah ya shirye ku,ameen ai kilo meter nawa ce kike ji tsakanin mu da masallaci cewar Sera nace gaskiya da nisa Suka ce mu fa ko radio kin san bama ji sabo da Kar ma a saka wa’azi muji,nace rannan kunga na yini Ina kallon tashar wa’azi haba ku kalleni baku ga na kara kwarjini ba wai duk dan na samu suma su dawo kan hanya? Seraline ta Kare min kallo tace hasken musulunci ya shigeki gaskiya ai rabona da wa’azi yafi shekara biyu amma har yanzu bai bar jikina ba kwarjini nake karawa ,Dariya nayi Nawwar inda yake birgeni baya nuna musu kyama in sun zo,yace yau dai zaku bani labarinku naji kuma, Star tace kaiiiiii tab abin ba kyau.
Har ga Allah ban San Sabreen bata gidan ba sabo da ta Saba bacci shi yasa ban tambaya ba.

Sai hakuri yau ba editing na baku

Yau page daya Zan baku Ina da Uzuri kuyi hakuri haka pls.

AsmaBaffa
08061929616
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

                 81-85

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Mamu Galadima
Gimbiya Diyar Katibi
Mom Khalisat
Ummul Ayyan
Mmn Nasrin
Haleemat
Hajjora
Oum Abrar
Shertuh
DeeDee
Hafsat A Shehu
Maman Ammar
Oum Darajat
Zainab Usman
Salamatu Oniyanga

Gaisuwa ga
AIDA MAMAN TASNIM

       Star ce ta fara bamu tarihinta Wanda ko ni ban sani ba tace Sunana Aisha Usman ni Yar asalin Yobe ce Baba na Malam Usman dake dan gajere ne ni tsayin Mamana nayi sabo da Banana inda kasan Inuwar Battery haka yake guntu ne sosai,Mamata ita kadai ya aura tunda suke dama suna da rufin asari daga ni sai Kanwata Saima Allah yayiwa Baban mu rasuwa ,dama sai rufin asiri sana’ar kayan Miya yake,tunda ya rasu bamu da karfi,Mamanmu ta tsufa da yawa sabo da Basu samu haihuwa da wuri ba,na kusa gama secondary Saima Kuma tana primary tsakanin mu akwai tazara,duk layinmu babu Wanda ya iya taimaka Mana,Dan cikin mu uku amma sabo da lalacewar wasu Musulman yanzu ana kallonmu muna Fadi tashi kowa ya kasa taimaka Mana,Watarana sai mu kwana uku bamu dora tukunya ba sai yawon mu zamu fita gidajen da ake mutunci ko zamu samu kalaci,makarantar gomnati muke Yi amma sai da ta gagare mu uniform dinmu ya yayyage kudin makaranta Dan kadan littafa da sauransu bamu da yanda zamuyi mu biya Muna ji Muna gani Muka hakura Kuma a layinmu ko Yan uwanmu daga na uwa har na uba babu Wanda ke bamu sisinsa kulamu ma ba ayi sabo da bamu da abin duniya.

    Mu Yara matane Muna bukatar sutura da kayan kwalliya sabo da rayuwarmu ta inganta har mu samu masu auren mu amma wannan ya gagara kayanmu gaba Daya sai maho muyi kuka mu godewa Allah Muka Fara sana’ar wankau shima dai baya isarmu,an kasa tallafa mana,mutanen layinmu makwafta nayi Imanin sai Allah ya tambaye su hakkin makfataka domin basu sauke ba,akwai wani me hali a unguwarmu ganin bamu da gata Muna zuwa Neman taimako wajensa sai yace na dinga zuwa Ni kadai ma ba sai kowa yazo ba sannan na dinga Taya matarsa aiki zai taimaka Mana ya dinga bani albashi,Muna murna na Fara zuwa Yi Mata wanke wanke da shara tana fita wajen aiki to,Watarana sai ya shigo da lemuka a ciki ya dauki daya ya bani yace na Sha ban sani ba ban kawo komai a raina ba lokacin yaran suna makaranta ita matar ta tafi wajen aiki Ina Shan lemon hankalina ya gushe ya kaini daki ya mini fyade ya min kaca kaca sai da ya gama da awanni maganin ya bar jikina na dinga kuka,Kudi ya bani ya Kai dubu dari,ganin ma idan ban karba ba cuta ya rigada ya cuceni haka na karba na fito Ina dingishi Ina kuka har gidanmu,Mama na fadawa komai, yafi karfinmu baza mu iya ja da shi ba Yana da kudi sai kuka muke har Kanwata Saima,bayan na warke sai na daina zuwa gidansa matarsa ko tazo ta nemi mene dalili ko a jikinta sai daga baya wasu da yawa sabo da na tasa Suka Fara nemana da Iskanci gashi bamu da kudi wahala ta ishemu haka na koma gidan da aiki wannan mutumin shike bani dubu goma dubu biyar lokaci zuwa lokaci har dai ya fara hure min kunne rashin wayo na kuruciya ya bawa Yaronsa wani lemon,to yaran sun Saba dani an musu Shirin school yaron ya dawo da gudu yace aunty ga lemo Kisha ashe shi ya yiwa yaron wayo har ya kawo min lemon ni Kuma ganin yaron ne ban San shi bane na sake Shan lemo naci gaba da aikina sai sha’awa ta kamani Kamar zanyi hauka Yana zuwa ya Fara taba ni sai na yarda bai Sha wahala ba ya sake sex dani,bayan na dawo hankalina na dinga kuka daga ranar ban sake zuwa gidan ba,sai daga baya maza Suka Fara kawo min hari manya da matasa Allah ya sa min farin jini haba ganin idan na basu kaina Ina samun kudi Muna fita daga kunci, Kawai sai na biye na fara bin maza Ina samo Mana abinda zamu ci na maida Kanwata school Mamana tana tunanin na Fara bin maza itama ganin budi yazo Mana sai dai tayi ta min Nasiha har sai dai Allah ya hadani da wani me kudi Ina biya Masa bukatarsa shima Yana biya min tawa har gidanmu ya gyara Mana ya dawo me kyau abinci sai mun zaba,Kanwata na maidata makarantar kudi,ganin mun samu rufin asiri sai Dangin Baba Suka min caaaaa Dole sai nayi aure,bayan sun kasa taimaka mana sai da Maganar aure Suka iya zuwa Kawai,su lallai sai nayi aure Suka samu a gaba Kawai ni Kuwa dama Ina da kawaye lokacin na hadu da Wise a hotel mun kulla kawance Kawai saina Mata waya na tattara nawa ya Nawa na koma wajenta Abuja,Muka tsunduma cikin karuwanci sosai har Muka gagari su Abuja sai dai Kudu Muka sake nutsawa duk kudin da nake samu a bariki uwata da Kanwata nake turawa nasu kason,kudin da na tara naje na Gina Mana gida a wata unguwar ta musamman gida me kyau Suka koma can domin na tsani unguwar mu basa amfani da hakkin makwafta har yanzu abinda nake kenan ba a so na nake karuwanci ba Ina so na daina amma Ina tunanin halin da zamu Koma na talauci ta karasa Mana da kuka sosai tace Alhaji Dan lami a cuceni makwafcinka a rayuwar Nan shi zai iya lalata maka rayuwar da maimakon shine ace idan yaga wani abu marar kyau sai inda karfinsa ya Kare amma yanzu ba haka bane.

   Dukkanmu Shuru mukayi muna tausayin Star ita Wise harda hawaye sabo da sun shaku da Star,Nawwar yace tab amma Allah ya sawwakewa wasu musulmin Kuwa Ina hakkin makwafci yake mene amfanin makwafta.
Wise tace ni kuwa labarina iyayena suna da hali Yan asalin Jigawa ne mu Fulani ne asalin sunana Hauwa’u,babana hamshakin dan boko ne tunda na taso nake da karfin sha’awa bana iya jurewa ga babana yace bazai min aure ba sai nayi degree da masters nayi nayi na samu saurayina na gari Yana so na Ina sonsa tun kafin na gama secondary amma Baba yace bazai min aure ba sai na Gama degree da masters Ina Gama primary da saurayina Muka Fara sex sabo da Muna son juna amma Baba yace bazai min aure ba,har Yan Uwansa na samu Suka Zo Suka Masa nasiha yaki,bayan mun Fara amfani da juna nida saurayina Sam bana son karatu aure nake so,Muna ta muamularmu da saurayina har na Gama secondary aka sani a university,Karshe Saurayin da ya lalatani yace bazai aureni ba yanzu baya Sona,illar mace ta yarda da Namiji ta bashi kanta tun waje kenan.

     Duk da mun rabu naci gaba da bin maza abina a university har na Gama degree,Nan ma na samu wani Ina sonsa bamu taba lalata da shi ba shima Baba yace sai nayi masters na gaji da hakuri gashi na Saba da maza Kawai sai shima wannan Saurayin Muka fara lalata da shi daga haka sai gashi na samu ciki ban sani ba na Fara laulayi,abin ya bawa Umman mu mamaki ta kaini asibiti akace Ina da ciki,naci duka a gida ranar Baba Kamar zai kashe ni Ina da kanne Mata uku maza buyu,Baba ya fusata yace bazai ga ciki a gidansa ba ya koreni yace sai dai na fada duniya ba shi ba ni Ina kuka Ina garari har kwana nakeyi a tasha da kango sabo da bani da wajen zuwa,Abuja na tafi na dinga kwana a kasan gada Ina Fitowa Ina bara a titi na samu na cin abinci har na hadu da Hajiya Mazarkwaila ta nuna min gata ita ta kaini aka zubar min da ciki ta dauki nauyina na zauna a gidanta daga nan ta Fara hadani da maza manyan masu kudi har na hadu da Star Muka Koma kudu.

   Seraline tace Ni dama ga miracle tasan komai nawa na bata labari Kuma Kun sani Kanin Babana shi yayi min fyade Yana min barazana da rayuwata a haka ya dinga amfani dani har na samu ciki Inna ta turani Lagos wajen yar uwarta ashe itama bariki takeyi nima itace ta zubar min da cikin dake Nurse ce itace ta dinga hadani da maza har na goge nafi karfinta na dawo nan garin Ina cin gashin kaina domin a can 50-50 Muke yi.

   Yar Zabil tace Ni Kuwa bani da uwa sai uba,Yar asalin Kano ce dawakin kudu Babana tunda Mama ta rasu ya Karo aure matar uba ta dinga wahalar Dani ba karamin wahala na Sha ba ta dukeni ta zageni ta zuga Babana har dai ma ta zuga shi tun Ina 15yrs Wai a aurar dani na gandame a gida Kar na jawo Masa abin kunya,to gaskiya dama Babana irin masu saurin tsinuwa ne akwai iyaye masu saurin tsinewa yaransu Abu kadan yaro yayi sai a dinga tsine Masa ana Masa baki, tun Ina karama ko ya nayi wani Abu ba daidai ba tun Mahaifiyata tana raye zai ta cewa shegiya, Yar iska,banza,dabba,tambadaddiya ke dai baza ki samu albarkata ba,wannan anyi Yar iska tsinanniya haka yake zaginsa shi,zuga shi matarsa tayi akan ya aurar dani ya samo min abokinsa tsoho dashi wani marar Imani in Banda wari ba abinda mutumin nan keyi Wai shi zan aura Ni Kuwa naki yarda na dinga kuka nace wallahi ko an daura sai na gudu,kullum sai naci zagi da tsinuwan Babana har ma na saba,Ina iya maida Masa martani,Dattijon da aka bani Zan aura yazo zance wajena na dauki dutse na fasa Masa Kai akan wannan matar Baba ta zuga shi ya koreni yace na bar Masa gida ya dinga tsine min Albarka a haka na fita na bar gidan akan na auri wannan mutumin me doyin baki gwara na fada yawon duniya ga kuruciya,Haka nima na nufi Tasha sai Lagos ni bani da uwar daki ma da kaina na dinga siyar da jikina Ina samun kudi,Yar Zabil taci gaba kaga nayi karuwanci a tafa,na dawo suleja,na koma kwanar Dangora nice nayi reverse na dawo daka tsalle a can ma Ina da daki,kwanar gafan da dakina,na sake dawowa Abuja,na juya Gadar gayan,na fada Ilori,nice gujungu na dawo Abuja again na fada Lagos na koma Jos na kwaje a Nan Anambra nayi yawon duniya sosai fa Kuma nasan tsinuwa ce take bina Yar Zabil tace nayi missing Babana tana hawaye,wasu matan uban basuyi ba a rayuwa nayi rashin uwata.

   Mandula Kuwa a yawon talla maza Suka lalatata itace talla Tasha Tasha Kuma da iyayenta da komai tsabar son abin duniya yasa suna Dora Mata talla su Kawai kudi ba ilimin addini babu na boko sai talla tace a garinsu Adamawa haka ake ce Mata degree faranti sabo da masifar talla,suna haka Mandula ta shigo palona tace wacce munafukar ce take fadar asalina Muka Yi dariya Wise tace sorry nayi shuru Amma sunanki na gaskiya Zainab,Mandula tace Zainabu abu me tagwayen suna Degreenki a faranti,Ni a gaskiya Baba ta ce ta cuceni ita ko me zanyi a duniya Matukar zan kawo Mata kudi to an gama,Ni dama Allah ya gani banyi Kama da ita ba bata da da wuya da wuyanta da kirjinta a hade suke,Muka Yi dariya nace ku godewa Allah ni ko uba me Kama da Inuwar Battery tsabar gajarta bani da shi.
Mandula tace cab da zamuje kiji masifar Babarmu ita kadai huci take,nace cab ai zamuje dukkanku Dan ubanku sai mun kaiku gida Kun nemi gafara amma ko wacce ta fito da miji,Mandula ta rike baki tace kin taba ganin an tuba farar daya ku bimu a hankali a haka Kawai zamu tuba,Star tace gaya Mata dai
Manduwa kuwa aikatau aka kaita acan yaran me gidan suka Yi amfani da kudi Suka lalatata ta Saba da Iskanci aka ce ta koma gida za a mata aure taki yarda ta gudu barikinta cewar Stat

    Muna gama ji harda kuka na Nima na basu labarina kaf,Star tace Yasin kin fimu shiga masifa sabo da rashin iyaye baki San waye danginki ba sorry ga Nawwar nan kin samu ke Kam ai kin fimu sa’a nace Ina wata sa’a mutum mugu da shi,dariya Nawwar yayi yasan dalili.
Yace to yanzu duk ku manta da abinda ya faru yanzu kuyi hakuri da wannan karuwancin bashi da amfani yanzu mene ribarsa,da sauri Star tace ahhhh karka zagi sana’armu mu munci moriyarta uwata tana Jin dadin kudin,yace Amma nufinki zata ji dadin zamanki haka yanzu tafi so ta ganki a dakin miji ki Haifa Mata jikoki,sannan wannan babban zunubi ne fa a wajen Allah dan Allah kuyiwa kanku fada da girmanku bakwa sha’awar Mata na gari,Ni nayi Alkawari gaba dayanku Zan baku aikin Yi har Santana Dan daudu Zan bashi aiki a kamfanina burina ku daina dan Allah,Nawwar ya zauna ya dinga musu Nasiha Yana musu wa’azi,Nima nace wlh bana Jin dadin ganinku a haka,Wise tace ku tayani Addua Inshaallah sai na auri Papa sai naje nayi kishi da uwar Sabreen badai su basa son bare ba sai jininsu to na daura Niyyar shiga gidan tun Sanda Naga abinda Sabreen take nace sai na auri ubanta,Nawwar ya dinga dariya yace Ina fata ko a samu a ruguzar da akidar gidanmu so nake a cikin manyan wani ya auro bare shike Nan,Wise tace ai Kuma nasan kyakyawa ne ko? Nawwar yace Muna Kama dashi inda kisan shi ya haifeni,Wise tace ya shiga Uku ku bani address din office dinsa Nawwar ya bata address yace sunansa Yusuf,Wise tace Yusf Wai da gayanci ta fada Muka sheke da dariya,Star tace mu kuwa Shiriya ba yanzu ba sai na Kara ko da na shekara uku ne, Nawwar yace bana son shirme Indai Akan gidanku kike Yi ni Zan kula da ku Kuma kema Zaki karatun harda Sera duk ku hakura ku zubar da makaman,Haka cikin kawayenku Wanda Basu Zo ba Naga Kuna da yawa Dole sai na kawo muku babban malami ya muku wa’azi idan wasu sunji suzo na dauki nauyinsu wacce baza ta hakura ba Kuma to Allah Yana nan duniya zata bi da ita.

   Muna haka sai ga Santana rataye da jaka Yana rangwada ya shigo da shewa,Nawwar yace Kai bana son Iskanci kana Namiji ka watsa kanka ka maida kanka banza lusari,ahayye me ya kawo wannan magana ai irin wannan sai ku fada min kuce wa’azi ake yau a gidan Kar na shugo,Nawwar yace gidan matar tawa kana Namiji zaka dinga shigo min Kai tsaye,Kai rufa min asiri ka daina shigar Dani cikin jinsin Yan maza Allah sittira,Ni da zaka Kara ta biyu Dani ma ai da na huta inzo inyi kishi da Miracle,Nawwar ya kalleshi yace Allah ya shiryeka, amin ita muke fata ya kalleni yace oh Kinga miracle Kamar ba ita ba anbi Allah an likira Kai duniya, shegiya taji sabon memory,su Nawwar an Sha rawar  Kuma disco Bob merly ka taka ko kuwa Michael Jackson,ko ta Burna boy ce? Star suna dariya sukace ta michiel ce harda tafawa da Santana ,Mikewa nayi nace Allah ya shiryeku kwayi da wata ba Ni ba na tafi dingus dingus Ina tafiyar Yan kaciya,Santana Ido ya zaro yace yau naga Tolo Tolo ahhhh an Sha sabadan kai ku tashi mu tafi Kun damu Amarya ya tattara su Star yace wlh sai mun tafi ku tashi mu basu waje wlh karka daga kafa ka koma tasharka ta disco Suka mike Suka ebo lemuka a kitchen Suka tafi,suna tafiya Nawwar yace Allah ya shirye ku,ya na iya na auro kawar su na kore su taji haushina,nayi magana tace bana son kawayenta dole nayi shuru,tashi yayi ya biyoni bedroom dina nayi sauri na kwanta na rufe idona bana fata ya taba ni ma, dariya yayi yace gwara ma ki tashi yarinya idona a rufe nace zazzabi fa nake yi.

Sannu Yar baiwa ya kwanta a bayana tare da rungumeni tsoro ya kamani Jin ya Fara taba min Boobs yana min magana a kunne please Zan Kara kuka na fashe dashi nace jiya jiyan nan fa gaba Daya wajen a kayi Masa ragadada da shi ya tararrabe Kuma yanzu kace zaka koma sabo da baka tausayina a’a ke ni bazan iya hakuri bafa wlh Ni bazan iya ba,Ina zuba kuka yace ni yanzu bazan iya hakura ba a baya nayi hakuri yanzu bazan iya ba wlh, kukuna na karawa karfi nace wlh Nawwar baka da tausayi kana kallon a halin da nake ciki ni dai na Shiga Uku na rushe masa da kuka,amma Nawwar ko a jikinsa abinda ke gabansa yake nan Muka fara kokawa sosai har na samu sa’a na dirgo daga saman gado na fita da gudu na fada dakin Sabreen Ina cewa Gwaggo Sabreen ki taimakeni,Iya…Iya Sabreen dama haka mijinki yake na kulle dakin da key na juyo Ina cewa Gwaggota Sabreen sai Naga wayam ba kowa a dakin ba kayanta na duba ko Ina bata nan a dakin nace Gwaggo Sabreen ko an sake daka yajin ne oho,Wai sabo da sa’ar Nawwar ce na koma ce Mata Gwaggo,Nawwar kuwa haushi yaji yazo har kofar dakin yace Zaki fito ne ai ba a dakin Zaki kwana ba ya koma bedroom dinsa ya kwanta ya rasa inda zai sa Kansa sabo da jaraba yace Wai dama haka nake da jaraba ne ko kuwa Zumar Yarinyar nan ce ta jefani a haka pillow ya jawo tare da rungume shi ya matse shi Kamar ya sameni Yana furta Ina sonki matata,Ni Kuwa saman bed din Sabreen na kwanta sai bacci.

     Mairo tana dakinsu a kwance tare da Gaji tace Gaji Namiji nake sha’awa ba abinda nake bukata a yanzu sai Namiji Gaji tace yau na Shiga Uku ni Gaji ashe Muna daya nima wlh na Saba da mijina bazan iya rike zawarcina ba gaskiya Kuma kinga nafa samu ciki da Danbinni ya sani Kuma Amma ya sakeni,Mairo tace ki samu saurayi mu dinga Yi a boye Mana,Gaji tace ai dole ni sai na haihu ga idda a kaina na Shiga Uku ya zanyi,Mairo tace kiyi hakuri ke Ni Kuwa Ina da saurayi,Gaji tace ke da kike budurwa Dan Allah karki watsa kanki Mairo ki bari Allah ya kawo Miki miji kiyi aure ya sameki a budurwa Kinga Zaki Kara daraja a wajensa,Mairo ko a jikinta washe gari Najib Wanda ya taba Kidnapping dinta yazo ai da wuri taje motarsa me tint baki wuluk ba a hango kowa yaja motar suka je karshen gari inda ba kowa bayan motar Suka koma a ciki suka sheka ayarsu,aikin Mairo kenan da Najib Katsam sai Mairo ta Fara laulayin ciki, Gaji ma tana laulayi ciki ya fara fitowa,Gwaggo ta Fara mamakin Mairo yanda take amai kullum ga zubar da yawu,Aunty Amarya tace ni kin San Allah gani nake fa Kamar Mairo ciki gareta Gwaggo tace na shiga uku Amarya Ina Zan Sa kaina ga yarinya ta an sako min ita da ciki ga Mairo budurwa da ciki Nima Ina zargin hakan,Suka ja Mairo ita da Aunty Amarya wajen likitan da sukaje ya rubutawa Rabi cikin karya shi Suka koma ya musu gwaji ciki gaskiya ne har ya Kai wata biyu,Gwaggo Suka dawo da takarda suna kuka Aunty Amarya tana lallashi,Dagaci Yana zuwa ta sanar dashi,ya samu Mairo Kamar Allah ya Aiko shi ya dinga dukanta gashi Yana sonta,yace kin cuceni Mairo duk kaunarki da nake Mairo abinda Zaki min kenan,Mairo tana kuka sosai,Gwaggo tace sai muje a birge cikin nan tun kafin ya girma,Aunty Amarya ma tace gwara a zubar,Mairo tunawa tayi Najib dan daba yace idan aka zubar Masa da ciki sai ya karar dasu kaf sai Taki yarda a zubar aka buga aka buga taki yarda,Dagaci yace sai dai ta bar Masa gida Gwaggo tace ba inda yarta zata je,Gaji ce ta fito ta Gaji da Jin cece kuce tace Yar uwata ba inda zata je,Dagaci ya kalleta ya furta iyyeee Sannu gwana ke Kika Gina min gidan Gaji tana gatsine da fari da Ido cike da fitsara tace baza ta je ba a kanta aka Fara cikin Shege ba inda zata je uban kuturu yayi kadan wallahi ko waye ba uba ba Mairo ba inda zata je,Dagaci ya zaro Ido bakin ciki Kamar ya kashe shi Yana ji Yana gani Mairo taci gaba da laulayinta.

   Yau kwance yake a saman tabarma a jikin dakinsa ya daga Kai ya kalli sararin samaniya ya tsurawa sama Ido yana kallon tsuntsaye na gilmawa su Gwaggo duk suna tsakar gida abin duniya ya damu kowa Babu me yiwa daya magana Aunty Amarya da sauki tunda ba ita ta haife su ba,Muryar Dagaci Suka tsinta yace Ina ma nine tsuntsun nan da wallahi bazan zauna a Najeriya ba kasar waje Zan tafi,amma banzaye tsuntsaye gashi su ba man fetir zasu Sha ba Babu daya amma sun wani zauna a kasar nan wallahi da nine idan na tashi sama wajejen Sudan zanyi baza a sake ganina ba,Gwaggo tace Kar dai bacin rai yasa ka zauce,ya juyo da masifa yace karki dameni shegiya munafuka da duk bada arzikina ba arzikina baifi haka yawa ba me farar kafa,Aunty Amarya tace kaji da shi ka dai Riga ka auremu,Allah ya tsinewa uwar data haifoki Yar iska tunda na Kara aurenki bana Jin dadin duniya ance idan kana talauci ka Kara aure zaka samu budi za a bude maka kofofin samu amma ni dana Kara sai aka kulle min kofofin,Kardai kayi sabo ai dama Kai ka ka jawo gashi nan anwa yarka, karara mun San gaskiya kana lallabawa dakin Yarinyar nan Rabi zaka Mata fyade Amma kace karya ne Muka yarda munafuki algungumi Allah ya Isa cewar Gwaggo,Dagaci tashi yayi ya zaro Sanda ya mukawa Gwaggo da Aunty Amarya ya dinga shinfida musu Sanda Suka yo waje da gudu ya kifo su Kamar sun haukace,Aunty Amarya akan kishiya ce ta dinga Tara musu jama’a da ihu ku fito bayin Allah zai kashe mu akan yarsa tayi cikin Shege,Mairo ce tayi cikin Shege gata can kuje ku gani ya fara fitowa,Gwaggo Takaici tace dama duk inda kishiya take to har abada bata kaunarka shegiya Suka Fara fada suna tonawa juna asiri.
Amarya Takaici yasa tace Dagaci ne ya yiwa Rabi asiri wallahi tabi duniya shine yaje gidan Malam Wai lallai sai ta Zama karuwa suna bakin ciki Allah ya bata farin jinin masu kudi yaransu Basu da samari sunyi kwantai,ai Danbinni ashe talaka ne karya yayi ya auri Gaji taje taci ubanta a gidan miji aka sakota,Gaji ce ta fito ta zabgawa Aunty Amarya mari,Amarya ta samu Gaji tayi Mata barin makauniya ta Fadi a kasa sai jini malala ta kasan Gaji,Dagaci yabi Aunty Amarya yana duka Suka fada cikin gidan ya kulleta a daki sai da ya farfasa Mata jiki har kasa tashi tayi sannan ya fito ya iske Gwaggo tuni ta Kira me Napep ansa Gaji a ciki zuwa asibiti,Mairo tana ta kuka gashi gaba Daya zance ya baza gari wannan bacin ran yasa Mairo ta tattara kayanta Dagaci ya bisu asibiti Shim, Mairo ta gudu ta bar gari.

   Baffa tunda ya saki Mami ya rasa sukuni ranar ko bacci bai iya ba,ita kanta Ummun Haidar ta rasa Kansa ta rasa gane Masa,Ranar tsakiyar dare ya mike tare da zama a gefen bed dinsa ya zuba tagumi kamar zaiyi kuka,tunawa yayi da saki uku kenan hankalinsa ne ya tashi Yana tunanin me yasa ma ya furta sakin,ya rasa dalilin sakin da yayiwa Mami bai San Sanda hawaye ke diga a Idonsa ba,Ummun haidar ce ta mike zaune ta rungume shi ta baya tare da tambaya lafiya my love? Badai akan sakin Mamin Nawwar bane kake kuka,Baffa kwallarsa ya goge yace ba komai ba haka bane,jikinta ta jawo shi ta Fara faranta masa rai har ya saki ransa.
Bangaren Mami kuwa kuka take yi ita daya a boye tana son mijinta auren saurayi da budurwa kuka dai baya Kare mata meyasa ma tace ya saketa tana danasani gwara ko kullum zai daketa tana gidan.

   Sabreen kuwa Jamcy ce tazo suna ta jaje Jamcy tace ke Kika fito haka me yasa baki sumar da shegiya ba,Ido Sabreen ta zaro tace ke Kinga Kuwa kungiyar Yan Iska su Rabi wlh Kika taba Daya a cikinsu sai kin yabawa aya zakinta,Jamcy bata taba ganin su Sera ba shi yasa tace da kaina zanje ba sako ba sai na dauki fansa ke nifa bana tsoron uban kowa Kuma idan Naga dama sai na auri Nawwar din Naga tsiya, Sabreen dariya tayi tace Allah ya bada sa’a kije dan Allah ki gwada Marin Rabia ki gani ita kadai ma ta isheki shegen karfi gare ta ga naci in da kisan talauci fada da ita baya mutuwa sai sun hanaki Shan ruwa,ke dalla matsoraciya tsorata kika Yi cewar Jamcy suna hirar su, Sabreen tace sai kin dawo ga hanya.

    Wise yau da sassafe tayi wanka ta dakko sabon hijab dinta har kasa na Yan gayu tayi kyau matuka gata dama fara,Fitowa tayi ta iske Star suna game da su Seraline tace na tafi Neman Auren Baban Sabreen, dariya Suka dinga yi ta fice,tiryan tiryan har Office din Papa taje da takardunta Kamar ta kirki,tana zuwa Sakatariya ta kalleta tace wajen wa Kika zo, tace Alhaji Yusuf,Iso aka Mata  ta Shiga bayan an sanar da shi Yana da bakuwa yace ta shiga ya zaci wani serious abu ne,Sallama tayi tare da shigewa Office ya amsa tana shiga ta tsaya a jikin kofar ta hau yiwa Papa tafi da hannaye ,yace ke kalau kuwa ki shigo Kawai ki Fara min tafi raf raf ubanki na miki,Wise tace sai dai ubanka ta sake zaro Masa harshe harda daga Masa takardunta tace ka gani degree ne Dani bazan maka aiki ba Allah ya kiyaye na zauna a karkashinka,Dariya ta bawa Papa yace ni dama nace Zan baki aiki ne,ta Masa gatsine tace ko ka bani bana so marar mutunci ta Harare shi,tunawa tayi so take fa ta aureshi taji sirrinsa dan su yan bariki suyi aure su fito ba komai bane, nutsuwa tayi tace yeeee na maka Wasa dama Wasa nake,Papa ya firgita ya kwalawa security Kira yace yi waje da ita mahaukaciya ce,Su Wise Karuwanci yabi jiki an Manta ma da soyayya ita Wai a haka zata ja ra’ayinsa ya sota, tace sai na tona ma asiri nasan abinda ka aikata munana a shekarun baya sai na fadawa Dan uwanka komai an maka daurin rai da rai,tsoro ne ya Kama Papa ya zaci ta sani Kuma har ga Allah Wise ba abinda ta sani, Security yayiwa magana kyaleta karka tabata jeka Kawai,Wise kujera taja ta zauna ita ba son auren Papa take ba sai dan kawai ta San sirrinsa ayi maganinsa,tace kaji tsoron Allah wallahi akan abin duniya idonka ya rufe,mecece duniyar ,baka tsoron Allah duniyar nawa  take,Papa baki ya bude Kawai tazo tana Masa wa’azi ba gaira ba dalili Kamar tasan sirrinsa, Ido Suka hada Wise tace wallahi kayiwa kanka fada kaji tsoron duniya tun kafin tayi maka atishawar tsakin masara, Allah baya barin zalunci, ko baka da haddar Chemistry a kanka eyee, Wise ta rufe bakinta da sauri tace kaji Karuwa na wa’azi shiriya tazo ahhhhhh Wise harda wa’azi ashe yau da labari a gidanmu akwai show iyyeeee…. Wise ai wayarta ta dauka ta dungurewa Papa Kai kamar danta tace Dan banza ta wuce da sauri sai gida,Papa baki bude ya bita da kallo, tana zuwa ta fado cikin su Seraline tace ehooo na shiryu yau nayi wa’azi billahillazi Saura kadan na jawo Aya har na dauki Hanya zance zance Ijaza’a na rufe bakina Kar nayi sabo, Star tace to ba sai ki karasa ba Mene ne a ciki kina da Nawwar zai bamu kudi mu ja jari ke da kina da takardu aiki zai baki,Santana yana gyara gashinsa da ya maida shi pink yace yesssssss ya wani lashe baki Yana make murya Nawwar dai Allah ya Masa me Nice ahayye caasuuuuus inji barmani choge Wai zai kawo Mana malami musha wa’azi ranar da guda Yana tafi da hannu harda taro nonuwansa Yana furta chassss damu Suka saki shewa Ahayyeeee yasa hannaye ya taro dukiyar Fulanin Yar zabil ta zabga masa Mari ya saki ihu ya mike dafe da kumatu ya hau zaga wajen yana ihu Yana yarfe hanu dama gashi kamar tsinke

    Ina dakin Sabreen nayi bacci har na godewa Allah har dare sannan na fito na shige dakina nayi wanka na fito na zaci Nawwar ya fita sai na ganshi ya fito daga kitchen Yana min wani mayen kallo,Ido muka hada nace Allah nidai bana so ka daina kallona na turo dan bakina na Koma na sako hijab har kasa na fito Yana ta dariya yace Wai na taba Jin Yar Bariki da tsoron Namiji kallo ma a hanani Yi nida idona Kuma yau dai bazan hakura ba,Hawaye ya Fara antayo min a kumatuna,kofa ya bude Mami ta shigo da sauri na goge hawayena na koma part dina da sauri na wanke fuskata na dan shafa powder sannan na fito, a gabanta na tsuguna na gaisheta ban San Aurenta ya mutu ba nace Mami dama kwana Kika Yi yau a nan,Murmushi tayi tace a’a nace to ki tafi dani dan Allah harara Nawwar ya watsa min nayi shuru Ina so nayi kuka,Mami ita tunda taga haka Ina tafiya Kamar Yar kaciya ta mike tace dama biyowa nayi mu gaisa nayi nayi ta zauna taki ta tafi,nace to a turo min Nawaf Auta tace akwai school idan yazo damunku zaiyi Ina kallo Nawwar ya rakata kafin ta dawo na leka kitchen yana dafa indomie karasa dafawa nayi na juye na cinye tas,ya tsaya suna hira da Mami sai dawowa yayi yaga Ina Ina ajiye plate,ya leka kitchen ya dawo yace abincin Nawa Kika cinye? yace ai kuwa kin ciyowa kanki,na kalle shi na furta kayi hakuri zan biyaka indomie dinka yace ai sai indomie ta jikinki, nace wlh bani da indomie a jikina sai dai kankana sabo da ba irin Sabreen bace ni bare nace lemon tsami gareni yafi karfin lemon tsami sai dai kankana,dariya ta kamashi yace ai Masha Allah ita ake so,Zama nayi na dinga magiya Ina hada shi da Allah dan girman Allah,dan darajar Allah dan Allah naci albarkacin Mami ka kyaleni yau uhm mene abin sauri Kai ba kwace maka za ayi ba naka ne fa Oven dinnan wlh ya gasu da yawa ka bari na samu sauki ya huce zan yarda yace ni bazan yarda ba,nace to Indai iya romance ne Zan yarda na maka ka gamsu kayi hakuri da kyar da kyar na lallabashi yace ya yarda zuwa gobe.

   Da wuri a gurguje yaje sallar Isha ya dawo,Yana dawowa dauke da take away na kayan makulashe dama yace Kar na wahalar da kaina wajen girki, shi Muka ci na zama Yar lele a baki ya dinga ciyar dani shima yana ci sai da  Muka koshi muka Yi Shirin bacci a tsorace nake da shi sai faman zare Ido nake, kallona yayi yace dan Allah ki saki jikinki nace na hakura ba zanyi ba duk kin firgice haka,nace naji maza wallahi gwara da ake bawa maza gado yafi na Mata sune manyan mu gwara da ake bamu mu Mata rabin nasu na tabbatar sune shugabanni sune manyanmu Allah ya Kara girma mazaje,Nawwar rungumeni yayi sosai a jikinsa yana dariya yace ki nutsu ba abinda Zan miki,nace ai kune baku da amana akan abin nan yanzu sai ku birkice kace ka fasa hakurin,yace ki yarda dani My Heart ya sumbaci goshina a hankali har gumi ne ke tsatsafowa tsabar tsoro,a hankali ya maida bakinsa cikin nawa ban San na fara hawaye ba,yace kiss dinma Wai kin manta Sanda kike cacumata nace ban San dawar garin bane nidai Allah ya Kara girma,yace to zo mu kwanta,kafada na makale nace uhm uhm barni a nan ban yarda da kwanciyar nan ba,jiya naga disadvantage na kwanciya ,Nawwar yayi dariya Kamar me,ya dorani saman cinyarsa nace wallahi bana son Antainar nan taku shu’uma jiya kamar zata halakani, yace ai shanyeta zaki anjima nace uhm Ina Sosa kai,kwantar dani yayi nace tawa ta kare Kuma shike nan Rabi,lafiyar jikina yabi ya haye min jiki Yana min wani irin tsotsa da murza min Boobs Wanda jiya duk sun gaji,a hankali ya dinga bina amma na sa firgici a zuciyata haka ya sa antaintar nan a marararbar Boobs dina a nan ya samu nutsuwa ya kawo,naji Dadi sai lokacin na saki raina na kalli antainar nace Sannu Saliha yau ustazanci ake ji,yace wlh Zaki jawa kanki gwara ma ki Mata shuru kin wani kwanta kin kyaleni Ina kidana Ina rawata ni daya akan dan banzan tsoronki,mukus nidai nayi Masa,Ina kallonsa ya dauke ni cak ya kaini toilet tare muka Yi wanka na sake gasa kaina na shiga cikin ruwan zafi Ina ta ihu Yana kallona yace karfa ki kone min kayan aiki ato, Hannu na Mika Masa ya dagoni daga cikin bahon Yana bin kirjina da kallo,jawoni yayi da karfi na Fada kirjinsa kirjinmu ya manne dana juna ya rungumeni sosai tare da furta min I love you a kunne na, uhum uhum na furta tare da yin kasa da kaina kamar munafuka,kaina ya dago da yatsansa ya shiga kissing dina a baki kamar ba gobe,Jin zai zarme nace muje bacci nake ji.

    Washe gari naji karfi ba laifi duk aikina nayi shi har girki da komai tafiyata ta dan fara dawowa normal Nawwar Manniru ba inda yaje Ina girki Yana wajen in na dawo Palo ya dawo in na koma daki ya bini can,duk inda nasa kafa Yana wajen shi Kuma ba aiki yake tayani ba,Mandula ce ta danna Door bell na bude Mata ta shigo dauke da Leda tace basai na karaso ba ungo sakonki na karba na Bude Naga magungunan Mata iri iri nace wannan kayan bala’in fa da kuka kawo min salon na sha ayi min warka warka bada ni ba,Nawwar ne ya karaso tare da dora habarsa akan kafadata yace Muna so Mun gode nima Ina so a kawo min na maza,Madula tace ai kuwa akwai hadaddun man power yace a kawo min da gaske nake,nace karki kawo in Kika kawo na daina kulaki bani ba ke,Mandula tana dariya tace yo sai me dan kin daina kulani sai na kawo wlh anjima zan kawo maka ka ajiye kudi,yace sai kinzo,tana tafiya ya rungumeni ta baya yace Yan bariki akwai dadin rayuwa ba ruwansu komai normal,na fashe da kuka nace wlh in ka Sha bani ba Kai kawai so kake ka kasheni duk wannan karfin bai isheka ba sai ka kara,na dinga shagwaba yace to naji sai kin saba na Sha amma a kawo na ajiye abina Kinga bani da lokacin nemowa Watarana fa da kanki zaki dinga siyo min fa,hmmm Kawai na iya cewa bana son ma zancen.

      Muna cin abinci Muka Yi Sallah ko masallaci fafur yaki zuwa a gida ya jamu jam’i muna idarwa ya jawoni jikinsa a hankali cikin salon kwarewa ya fara lashe min baki yana tsotsewa ya hanani sakat biye Masa nayi Kawai sabo da na samu sauki shi bai San Wasa ba ai Yana Jin Ina tayashi yace bai san zance,bakina ya Kama kamar zai cinye min shi hannayensa suna dukiyar fulani na Yana Wasa dasu kayan jikina ya rabani dasu na Fara zare Ido nace Ni Wasa nake bada gaske nake murza ka ba Wasa nake maka,Idonsa tuni ya canja kala ya zauce min gaba daya sai rawa jikinsa yake ya fara rokona please Baby Zan iya mutuwa idan Kika hanani a hankali Zan Miki baza kiji zafi ba tsabar jaraba kalamansa da kyar suke fita,tsoro Antaina ta bani yanda ya cire kayansa ko kunya nace Kai Nawwar ko kunyata baka ji jibi aba dan Allah a gabana,yace Sanda kike min karuwancinki na hanaki ne abinda Kika dama kike min sabo da Haka yanzu Nima nawa nake Yi ki kyaleni mutum da abubuwansa duk kin hanani Ni wlh gwara ki dawo Yar barikinki yafi min dadi ni bana son wannan kunyar ki saki jiki muji dadi so nake na dinkeki tsab da ciki,kunya ce ta kamani na yunkura Zan gudu ya rikoni da sauri cikin zafin nama jikinsa Yana rawa har tsoro ya bani ihu na tsala da karfi na Fara burburawa na Zama Kamar me aljanu kuka wiwi Ina furta ni ka sakeni, ka sakeni na shiga Uku zan mutu, ka sakeni wayyo Allah,na shiga Uku na lalace wayyo Allah rayuwata zai kasheni,kuka hawaye wiwi Ina ihu tsakani da Allah babu me cetona,cizonsa nayi a hannu nace mugu zan maka Allah ya Isa,Nawwar baya ji baya gani,nace akan sadakinka dubu dari biyu zaka kasheni,kamar ana zare min rai Muna ta kokawa,ya furta kyaleki fa nakeyi ke ganinki karfinki ne yasa har kike iya motsi ko? ya sunkuceni kamar tsinke ya dorani Saman bed,Ina sheka kuka nace Zan zageka…Zan zageka ka ja mutuncinka Nawwar,Nawwar yace ai haka nake so ki zageni ki gani,ka ja mutuncinka Nawwar,karshen mutunci ai ya Kare bani da shi Indai a wajenki ne ai Jan girma da mutunci babu shi,Nayi masifar amma yaki hakura sai na Fara lallashinsa nace haba uban gidana Babyna, Kyakyawan mijina ga kudi ga kirki ga kyauta ga addini ga Kuma aji da Isa da izza yace ke ni ban yarda ba babu ya Kare yaci gaba da abinda yake yana tatattabe min na shanu na,Nasan Kawai bazai hakura ba sai naci gaba da kuka kamar an tashi injin markade ba tsayawa ba shakar numfashi shi kuma Sam bazai fasa ba.
Boobs dina ya cafka da bakinsa yana bude min kafafu Ina makale kayana,kirjinsa na shiga duka Ina ture shi Ina turje turje nace Nawwar kaja girmanka bani da mutunci Zan maka rashin hankali ko a jikinsa..

 

Ina godiya masu Sharhi Allah ya biya
Na koma posting da Yamma yanzu sabo da Uzurin da ya taso min

 

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

              86-90

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naki ne
Mrs Chief

Gaisuwa ga
AIDA MAMAN TASNIM

Duk masifar da nake yi Nawwar ko a jikinsa yakushi yake Sha kawai,a hankali ya fara lallashina yace ki tsaya fa ya fi miki Baby Zaki jawo na baki wahala bana son irin wannan sai kace Yar 13yrs haba Honey yana lashe min hawaye cikin shesheka nace yanzu fuskar ma baza ka kyaleta ba, kin fiso muyi ta kokawa dake zaki ji zafi fa ki tsaya ki ji dadi,nace nifa bazan taba yarda ba Allah ya gani Ina ajiyar zuciyar wahala, Alright ya furta yaji haushi ya mike Yana duba inda ya Sha yakushi da cizo,Ina kallonsa Yana ta fushi ni dai bance komai ba har bacci ya kwasheni,shi Kam bacci gagararsa yayi sabo da sha’awata Yana so yayi nafeela abin bazai yuwu ba Kawai kwanciya yayi ya jawo wayarsa ya duba online,hasken Wayar ne yasa na bude idona a hankali Ina kallonsa wayarsa nasa hannu na karbe nace me kake Yi da Daren nan,bani wayata me zan miki kije kiyi baccinki amma ki bani wayata,jikinsa na dawo na kwanta Ina Masa dariya nace sorry Sweety I love you, yau ya Fara ji a bakina ya kalleni kadan yace Allah? uhum Ina sonka na dade Ina sonka tunda Muka hadu sonka ya kamani, I love you so much bani da kamarka duk duniya, kaga bani da kowa sai Kai dan Allah karka juya min baya ka rikeni amana karka koma wajen Sabreen ka manta da ni,wacce Sabreen din ya tambayeni cikin rada,matarka mana Wai unguwa ta tafi ne? Kwanciyarsa ya gyara tare da makaleni a jikinsa ya furta na saketa ai saki uku ma,Amma Kuma Baffa ya saki Mami itama igiyarta ta Kare ta Sabreen ta Kare itama,Raina nane ya baci nace Maminka Innalillahi ai gwara ka kyale Sabreen din akan a saki Maminka,Nawwar yace naji takaici da ace nasan Baffa zai saki Mami wallahi da bazan saki Sabreen ba amma kaddara Allah yayi zaman ya kare,to tayi auren kisan wuta Mana hmm ai ba kyau sai in tayi aure tsakani da Allah idan waccan ya saketa shine fa,Amma shine baka fada min ba,amma ai Mami tana bukatar mutane a kusa da ita ka dawo da ita gidan nan dan Allah mu zauna tare,nayi nayi tace baza ta dawo nan ba,gobe ka kaini can na yini Dan Allah yace no Ina amarcin Zaki tafi unguwa ni bana so gaskiya, Yanzu Kai nawa ne ni kada? Gwaggo Sabreen anyi gida na faurta

   Murmushi ya saki yace ae Mana kafin na Karo wata tunda naga baza ki iya daukan lalurata ba ya Zama dole na nemo wata na aureta,da sauri na rufe Masa baki nace haba zan iya da Kai Mana Kai ka kiyayeni fa na tsumu a bariki,dariya ya saki yace to a bani Mana in haka ne,nace ai yanzu bana so ne ka dinga tsotse dadin so nake ka dinga Yi kadan kadan yanda zaka Kara kiba amma mu a gaya Mana duniyanci munyi degree da masters a nan,murna nakeyi an saki Sabreen duk na rude sabo da murna gemunsa na shiga shafawa nace ka hadu kana da Dadi,kalleki kukan da Kika min ya Isa yanzu sabo da karya Wai Ina da dadi, dariya nayi tare da tura fuskata a kirjinsa nace Allah farin ciki nake ka saki Iya Sabreen yanzu sabo da murna Zan yarda kazo ka bani zafinka tunda dai Zafin masifa ne da kai zo ka sake badeni da yaji in ta kuka akan Sabreen Zan iya shanye wahala ko wacce iri ce ai dole gobe su Sera suji labari,Zo mu tafi fadama nayi sauri na cika maka gida da yara yanda zanja kilo na gado idan ka rigani tafiya can,dariya mukayi yace au har gado ma kike jira kici,Hausawa ba haka suke Yi ba kaga mijinsu ba cin yau bare na gobe amma suyi ta zubo Yara a gida su a wahale yaran a wahale a kasa daukan nauyinsu yaro karami sai dai ya nemi sabulun wanki da kansa,bare azo Maganar school,Zo na biya Miki karatu kyale masu yaran nan.

    Yanzu cikin murna nake shi yasa na Fara kissing dinsa na shigar da bakina cikin nasa Ina tsotsa yanda naga dama  Yana sarrafa abinda yafi so na shanuna Yana sarrafasu Yana sakin ajiyar zuciya abinda zaka Yi a dubu yanzu gashi a Sadaka washsh…Baby kin zama amarya…nace dama itace ai dan mijina kyakyawa,sunnar ma’aiki zamu raya  ga dadi ga lada,duk cikin murnar sakin Sabreen na zauce Ina sarrafa shi shima Ni yake Sarrafawa yana lashe min kunne yana hura min Iska a hankali,nipples dinsa na shiga sarrafa Ina Sha Masa yana ta shidewa Yana nishin dadi, a hankali ya bajeni Yana min sucking a Oven Ina Jin dadi,Niima luntsum abina rabajajan yana ta lasheta shammata yayi kawai ya nemi hanya a hankali ya samu ya shigeni daga nan Kuma labari ya canja sai kuka kamar ana yankani, jikina har wani karkarwar azaba yake Ina tsumar masifa, nayi nayi na ture shi na kasa Ina ta dukan kirjinsa Ina ture shi amma Kawai sukuwa yake Yana sambatu da kukan dadi Yana wani irin gurnani da numfashi Mai wuyar furtawa,zafafan kalaman soyayya yake furta min masu Sanya masoyi nishadi amma ni Kam kuka nake, nace nikam gwara nakuda sau goma da wannan abin, ga boobs dina ya rike su da hannayensa bala’in yayi yawa naci kuka na gode Allah har ya samu gamsuwa yau ma Sanda zai kawo har da hawaye sharrrr a fuskarsa,nace yo Kai ka dorawa kanka wannan kuma,Sai da ya samu nutsuwa sannan jikinsa ya saki ya kwanta a jikina ya kankameni Yana shafa dogon gashina da ya hargitse Yana rada min kalamai masu dadin saurare,Shuru nayi Ina jinsa ba tare da ya zare Antainar daga jikina ba yace dama mu dawwama a haka,dukansa nayi a gadon bayansa na rungume shi sosai ina ajiyar zuciya,Ina sonki Ina kaunarki my wife Allah ya Miki baiwa ta musamman,nace Nima Ina sonka sai dai muguntarka tayi yawa ka fita a jikina,ai sake gasuwa nakeyi so nake na zarce second round ban koshi ba,tureshi nayi sannan ya fita a jikina Yana cewa fatan mahaifa ta karbi sakona,da kyar fa nayi adduar saduwa na kusa mantawa,yau ma na Sha wahalar gashinsa sai tsakiyar dare sannan Muka samu bacci Ina makale a jikinsa.

    Washe gari ba zuwa Office wai ya tafi Hutu,Khalil ya kirashi zaizo yace Kar kazo min gida hutu nake sai na gama, Khalil yace lallai soyayya tayi dadi Amma da nazo naji Karuwa Virgin da kace,dariya sukayi fafur ya hanashi zuwa,Ina jinsa ya kira Wise tana dagawa yace Kar ku soma zuwa min gida sai na gama hutu,Hutu nake sai na gama ki fadawa sauran ku kyale mu mu sarara,dariya tayi tace kace karatu kake biya Mata? Kwarai ma kuwa ya datse wayarsa.
Sera na Kira nace anyiwa Sabreen saki uku Amma fa an saki Mami itama uku ta cika,Sera tace tab to ai Mami tsohuwa ce me take nema taje mu dai tunda an saki Sabreen shike nan yau akwai chasu dariya mukayi Muka Sha hirar mu,Muna gamawa naje na Kara Shan maganina na Mata a boye,harda siyo min maganin asibiti sabo da na warke da wuri, duk zafin da nake Sha baya kyale ni kwata kwata kullum ne ba fashi sai yayi sau biyu sau uku,yau Tuesday zaune nake a doguwar kujewa na mike fafuna suna saman cinyarsa na dora su yana min Wasa da yatsun Muna kallon film Wanda Ni ba film nake kallo ba shi na zauna na zubawa Ido Ina kallon kyau inda yake,sanye yake cikin riga karama t-shirt purple da 3qtr shima arsh,Ni Kuma sanye nake da Riga me hannun vest purple da wandona Jean tight light arsh hadadde, kafafuna na dauke tare da ajiye su a kasa na sakalo hannayena ta wuyansa ya juyo Muna kallon juna,a hankali ya furta mene ne da kulawa,yatsuna na Dora a saman hancinsa Ina goge masa Ina tabawa nace Ina sonka, Ido ya lumshe ya maida kaina saman cinyarsa nayi matashi da ita yanzu Kuma shi ya koma kallona kamar zai cinyeni.

    Nace muje yawo dan Allah mu dan zaga ko a kafa ne a layin nan,gwara da Kika ce layin nan domin iya nan zan iya barinki,sai da mukayi Sallar magriba sannan ya dawo Muka shirya shi Kam Jallabiya ya Sanya wata blue me kyau dai dai shi me tsada,ni Kuwa
Material marar nauyi white and blue na saka dinkin buba abina nayi kyau na yafa dan mayafina Kamar Yar budurwa Yar 16yrs haka Muka fito a kafa hannuna cikin nasa,layin ba kowa dake unguwar manya ce,Muna tafiya muna hira  na wuce shi Ina gaba,ta baya ya saka hannayensa a kuguna ya dawo dani baya Muna dariya yace haka akeyin tafiyar Yan gayun  kin wuce mijin naki, dariya nayi na fyalle da gudu sai da nayi nisa na tsaya na juyo Ina tafiya da baya baya harda Yi Masa girgiza,dariya yayi yace karfa wani munafukin yana na Nan a labe Yana kalle min mata, Dake garin arna ne ko ina kaji kida Yana tashi Ina tsaye inda nake ya kusa iske ni tahowa nayi na fada kirjinsa na kusa fadar da shi sabo na shamma ce shi,dariya mukeyi Ina gaba Muka ci gaba da tafiya,hannaye ya Dora a kafaduna muna tafiya a Haka muna hira abinmu, Dan dukawa nayi na dawo baya mazaunaina na jikin Antaina harda murgudawa,yace Zaki kunna ni fa,ki bari ko wani munafukin Yana gefe Yana kalle min matata bana so a kallar min matata, dagani yayi sama Ina dariya ya ajiyeni muka ci gaba da tafiya har Muka zo wajen wani dan joint ice cream Kawai ake siyarwa na cikin biscuits, a wajen Muka tsaya aka zuba mana muna tafiya Muna sha nawa chocolate nasa white vanilla,horn muka ji ana Danna Mana Muka kalli motar da tayi slow a gefen mu,glass aka sauke kasa Sai ga Star tana driving,nace Dan ubanki motar waye wannan? tace kin tuna Alhajin nan da Muka hadu a Kano ya biya min Makkah Alhaji Sani,ohh me Jan Ido?na tambaya,tace ke lokacin masifa ce ta sashi a gaba ai Idonsa fari ne,Wai aurena zaiyi idan zan yarda ni Kuma bana son dan duniya,nace ke tafi zancen bana tsaye bane sai kinzo gidan,da sauri Nawwar yace bafa yanzu ba sai nan da wata guda sai ki zo,Star tace to Sannu sai mun Zo Allah gobe ma kuwa,ta ja motarta tayi gaba.
Murmushi nayi nace Allah sarki masoyana, tafiya Muka ci gaba sai da Muka Sha tafiya sannan ya goya ni a bayansa har gida,muna komawa ya fara cire min Kaya Yana bin jikina da murza da tsotsa,har yanzu ba sabawa nayi ba sai wahala nake ji, Boobs dina manya masu kyau ya tasa a gaba yana shafa su yana tsotsa,a hankali ya gangaro kasana Yana min wani irin tsotsa a Oven, Ina Jin dadi na sa yatsansa na tsakiya cikin bakina Ina tsotse sai da ya shigeni sannan na fara kukan zafi amma ko a jikinsa haka yake sukuwa a kaina, naci wahala yau har round biyu yayi ba tausayi ba komai.

    Bayan sati daya Wise ta ci wanka na kirki wankan manyan yara kace wata Yar shugaba ce a Nigeria direct Office din Papa ta nufa a dalleliyar motarta tana zuwa Yana parking shima driver ya kawo shi ta bude mota ta fito Suka hada Ido da Papa gaban Papa ya Fadi ya ganeta yace ko dai Yar wani ce tazo Rannan ta gwadani Allah yasa naci jarabawa shike nan Ni Kam arziki yazo min har gida,Office ya nufa da sauri a hankali Yana furta zata biyoni na sani zata zo…ya juyo ya kalleni Ina bin bayansa waya a kunnena Ina Wayar karya,Papa cewa yake zata zo zata Zo zata Zo gata nan, da sauri ya fada Office dinsa Nima na shiga Ina wayar karyata Ina furta haba Daddy 15million yayi kadan gaskiya,Papa yaji kudi a ransa ya furta Yar me kudi ce wayyo,Wayar ta gama ta zauna a kujera kenan wani Kiran ya shigo wayarta ta daga cikin tsawa da fada tace haba 5million kaje dakina ka ajiyeta a saman bed, Wata Wayar ta daga tace hello Daddy kayan nan sun shugo amma ance na Belgium basu Zo ba suna saman ruwa,kace me eh Ina jinka okay,na turkysh sun Zo tuni,to Inshaallah zanje tunda kana so ya zanyi gaskiya bana son China amma ya zanyi to ba matsala Allah ya kaimu,Papa yace a ransa gaskiya Yar me kudi ce,sorry na furta na ci gaba da wayar karya na gama nace Kai mutane suna damuna wlh bai san duk da Santana muke waya ba dama mun tsara da shi.

    Juyowa nayi nace Sannu ko,wani Murmushi Papa ya saki suna bala’in Kama da Nawwar,nace wata kwangila dama Zan baka jiya abinda ya kawo Ni kenan Ina son hada harkalla da company dinka, Star ce ta Kira a waya na sata a handsfree nace sister ya akayi ta Wayar tace Zan wuce Uk ne nan da 2hrs kudin da Kika manta a dakina Zan kawo Miki ni nayi shiri na,address na Bata na kashe Wayar,Papa a ransa yace wato har kudi ake iya mantawa a dakin wata lallai kudi ya musu yawa inama Ina da yaro na sa ya nemi Aurenta mu ai min huta,Amma ko ni ai da kuruciyata na aureta mana kawai yanda nake din nan ai dai dai nake da  Nawwar, Papa Murmushi ya sakarwa Wise tare da furta me za a kawo Miki to ki sha?nace ba komai,yace a’a Yan Mata ko makoshinki ai kya jika,tace just water ta furta,da Kansa ya tashi ya kawo Mata ruwa Eva,ba a dade ba sai ga Star taci wanka na kirki kamar zata je chasu cikin kana nan Kaya tazo har Office din Papa me kyau,Papa Yana washe baki ko gaisar da shi Star Bata Yi ba tace Eesha ban son shirme me yasa Baki da tarbiyya ne shi yasa nake son Sarah ta fiki hankali ki gaida shi Mana first,Star tana turo baki sis Daddy fa jirana yake ta karasa da shagwaba ga Mummy yau zata wuce Kaduna itama for God sake ki karba na wuce ohh fuck,bani bani please,Papa yayi zuru yace lallai gata ya musu yawa yayan gata ne an tabarasu da kudi,hand bag star ta bude Papa yaga dollars da Bundles na Yan dubu dubu cikin jakar a ransa yace ke dan Allah Ina sonki kai ji kudi,Kawai Wise ta karbi kudade ta maida Jakarta tace wait bari na rakaki airport,Star harda doka kafafu na shagwaba,Wise ta mike tace kayi hakuri yarinya ce please bari naje Zan dawo next tomorrow, Alright… Alright cewar Papa duk ya rude,yace please can i have your number? Wise tace yeah why not ta karanta Masa ya shigar ya Kira tayi saving tasa sannan Suka fice,Suna barin layin a mota Suka tafa Star tace kinga yanda ya rude Kuwa Suka sake tafawa,Sabreen Ina zuwa kwanan nan Zan zama Mamanki.

    Kwana biyu Baffa ya hau Kiran Wayar Mami amma tana kallo taki dagawa,gashi bai San Ina zai sameta ba,Sultana da Nasrin sune Suka Zama Iyayen sune suke komai a part dinsu,Baffa ne ya shiga part din,Suka gaida shi yace Ina Mamin ku take? Bamu sani ba bata fada Mana ba munyi munyi da ita taki fada Mana sai dai ka tambayi Yaya Nawwar,kunyar Nawwar yake ji bazai iya tambayarsa ba,Kawayen Mami ya fara bi Daya bayan daya Yana tambaya ko sun San inda take Suka ce basu sani ba,ya dinga bin gidajen Nawwar da ya sani amma ba inda ya ganta,ya dinga nemanta amma bai ganta ba,rasa sukuni yayi ya rasa inda zai sa kansa,Iyamami ya samu a part dinta ya sata a gaba ya dinga rusa kuka shi fa matarsa a dawo Masa da ita dake komai girman da a gaban iyayensa to yaro ne,Iyamami tace Kai baka ji kunya ba dan Allah to ka sani aurenku ya Kare bata da sauran igiya taka ,sai tayi aure ta fito,Ni bana so kowa ya aurar min matata,ai sai kayi Kuma cewar Iyamami,yace ai dama nasan bakya kaunata da Yusuf ne ai da kin saurare shi Amma Ni bakya kaunata,Iyamami baki ta bude tace Sulaiman yaro kake so ka dawo ne hala? Nidai bakya so na wlh a dawo min da matata ko na talauce na daina Neman kudi ai kunfi kowa Jin dadin kudin idan ban daina zuwa Aiki ba Allah ya tsine min,dariya ta Kama Iyamami,ya kalleta idonsa jajir yace Indai matata bata dawo ba in Zama talaka ya mike a fusace ya bar part din,Iya Mami tace ikon Allah lallai shegiyar ta mako Masa asiri tab zata ci ubanta kuwa,baza ta taba dawo Mana gida ba Indai Ina raye ayi mace Kamar ba jinin mu ba.

    Mairo Kuwa tana Isa Tasha sai Kaduna a can ta sauka tana tafiya a tashar gab da fita wata matashiya tazo ta bangajeta ta wuce,Mairo ta fisgo rigar Yarinyar nan,tana juyowa ta kantsame Mairo da Mari,Mairo baki ta bude tana zaro idanunawa tace na shiga Uku Rabi kece haka ta ya Kika dawo talaka haka Ina mijin naki ke da Kika goge Kika waye,Budurwar Mai Kama da Rabi sak ba babanci sai dai wannan da alama ba a cikin daula take ba,tace ke uwar wace Rabi din kina lalata min suna Ina Rufaida ki dinga ce min Rabi shegen hancinki Kamar Alkaki ta ja tsaki tace ke wallahi bana Jin magana takadariya ce ni naci ubanki yanzu Yar Kauye chus dake bigi bagiro,wani tsoho ne ya karaso wajen me Kama da Rabi sak yace Cele a kasko kin San tafiyar nan ance Saura wata uku,Budurwar tace ai Kamar yaune Kaka Haba ka isheni ni Ina zuwa kasar Sai siyar da awarata acan ma Sai na Zama Cele a kasko sana’ar da zanyi kenan a kasar, mu tara kudi maganin bala’in duniya,kudi maganin uban kowa,kudi maganin jarabar duniya,Kudi maganin duk wani matsiyaci da matsiyaciya burina Kaka na siyi Skoota Vespa na dinga ja a kasar dama tawa ta tsufa,Mairo tayi galala tana kallo lallai ba Rabi bace,tana kallo Yarinyar ta nufi wata tsohuwar Skoota Vespa ta tsufa tukuf ta haye dogon wandonta ya bayyana na cikin doguwar rigar atamfarta kadaddiya,tsohon ya haye bayanta ta Mata key ta haye abarta tayo Kan Mairo tana Danna Mata ashar tace matsa Dan burar….goyon kaka ce ni ba hankali gareni ba yanzu nayi ciki dake,Mairo ta matsa da sauri ta ja baya,suna wucewa tabi bayansu taga sun hau main road Yarinyar nan da tace sunanta Rufaida harda ihu a titi tana ta zagin masu motoci,mayafinta ya Fadi iskar babbar mota ta dauke shi ta dinga zagin motar nan Kamar Allah ya Aiko ta,tsohon yace tsaya ki dakko mayafin mana kyale banza Kaka ai ya Fadi kenan yaje,Babu fa dankwali a kanki Cele,duk fadan da nake Miki bakya ji taki kulashi a Haka Suka bacewa Mairo,Mairo ta dafe kirji tace kaga Yar guguwa Anya wannan ba yar uwar Rabi ce ba Kuwa cab.

    Gaji kwance take a gadon asibiti cikin nata ya zube,tunda aka saketa Danbinni yasan tana da cikinsa Amma ko leke bai Zo ya ganta ba,Gaji harda kuka tana son Danta tana kuka tace shike nan Danbini ya ci banza, yo ai kusan Daya nake da Karuwar Ni kasar nan Zan bari,Dagaci suna ta lallashinta Amma cewa take sai naci ubanki Zayya zanzo wlh Ina warkewa zaku ga tsiya zanzo ne sai na dauki fansa, Gwaggo tace ki kyale mu da bala’in da ya tunkaro mu a wajen  Mairo,Dagaci yace Inama na Mairo ne ya zube to cikin Shege taurin Rai gare shi sai na sunna ya tangale amma na shege daram da shi,kwana Daya aka sallamesu bayan anwa Gaji wankin ciki,suna dawowa gida suka iske ba Mairo ba kayanta, Aunty Amarya tace ta tattara kayanta ta bar gari harda dariya,Dagaci yace wayyo na shiga Uku, ku haka rami ku binne Ni Kawai na huta,ku binne ni Dan Allah duk ya zauce Bai San ma me yake fada ba,Gaji tana kuka tace yanzu Ina zamu ga Mairo Innalillahi,Gwaggo Kuwa ta Zama kurma Kawai.

     Mairo Kuwa tunawa tayi da gidan wata kawarsu da Suka Yi school tare a nan Kaduna take,sai ta kunna wayarta ta kirata tana ta murna kawar tata Sadiya ta Mata kwatancen gidan su,Mairo can ta nufa tare da kashe wayarta again,tana zuwa sai Murna suke Sadiya bata da uba Yar macece Babanta tun suna kanana ya rasu sai Babarsu Yar tuwo tuwo ce har ta fara yiwa mutane hanyar zuwa Takarci kasar Saudiya da sauran kasashe,Sadiya ma tana ta shirye shirye zata tafi Neman kudi Saudiya,Mairo bayan ta huta zuwa dare ta bawa Sadiya da babarta labarin abinda ya faru da ita,Hajiya Ladi tace Allah sarki to kema na Miki Hanya mana ku tafi da Sadiya in yaso sai ayi Miki dan dabara tunda babu me ganewa kina da ciki duk wata almundahana mu zamu San yanda za ayi ki tafi da cikinki ba tare da an gane ba,sai ki Fara sana’a kina biyan kudin da kadan da kadan har ki Gama biya,Zan wuce Miki gaba a kaiki a bashi tunda Muna yin jaka in kinje can Zaki biya da ribarki ta aikinki,Mairo Farin ciki Kamar ba gobe tana godewa Allah tazo a sa’a.

    Nawwar bai koma aiki ba har yau sati biyu kenan kullum sai ya gurjeni tas Ina Jin azaba,Nawwar kullum sai yayi ta rokon su Sera dukkansu wajen mu ashirin akan su shiryu sun ki,har malaman sunna ya samo aka tara su aka musu wa’azi amma Wanda Suka yarda zasu zubar da makamansu sai Sera,Star, Wise,Yar zabil, Mandula da Santana sauran kuwa duk sunki yarda har da Manduwa taki yarda,ana haka wani me kudi attajiri Wanda su kansu basu san waye ba arne ne dai gagarimin club aka gayyaci  karuwan, lokacin Star,Sera,wise,Yar Zabil da Mandula suna gidana baza su je ba,anyi anyi suje Nawwar ya hana Muka dinga rokon su Kar suje ai Kuwa da kyar Suka yarda,Santana Yana can da shi aka tafi club din da dare kusan dai dai ku ne karuwan da basu je ba,ana ta rawa masu shaye shaye suna Yi ana cashewa a club din,wani VIP aka ja su gaba daya can cikin Underground ne a cikin club din,suna ta shaye shaye sai ga manyan police sunzo da bindigu,Santana Yana ganin haka dabara ta fado Masa shi dake Namiji ne ranar ba daudu Kawai ya dauki katuwar kwalabar giya ya bugawa wani police a kai ya fice da gudun tsiya Yana ta gudu har ya bar club din yana uban gudu cikin duhun dare ko birki bai ci ba bai saurara ba Kuma sannan bai hau abin Hawa ba gudu yake surfawa Kawai,Su Kuwa karuwan a nan gaba police din nan duk Suka harbe su basu bar ko Daya ba babu Wanda ya rayu ko mutum daya,dama da sanin gomnatin jahar aka yi hakan sakamakon karuwan sun addabe su suna ta watsa musu gari an rasa ya za ayi da su sabo da mugunta shine Suka kashe kowa Kawai Suka Yi tafiyar su.

     Santana Kuwa har gidan Nawwar yazo a kafa Yana uban gudu Yana ihu Kamar mace a gudun ma Yana wani watsal watsal da hannaye,Yana zuwa ya fado Mana palo Muna tare da su Star cikin dare Kawai sai ya sume a wajen,gaba daya mikewa Muka Yi Muna tambayar lafiya,Nawwar na shiga kwalawa Kira Baby….Baby…. Honey hoho…honey ho….Fitowa yayi nace kayi sauri Santana zai mutu,kwasarsa Muka Yi sai asibiti sai da ya Sha ruwa Leda uku ya farfado  Yana kallonmu Daya bayan daya duk mun tsaya a kansa,yace na tuba nabi Allah bani ba bariki su Manduwa suna club police duk sun harbe su dama ana sani aka gayyace mu dan a kashe mu,ai duk kusan Yan barikin mu sun mutu,hawaye muka fara nace wayyo Manduwa ta pretty,charity, yace ai duk suna barzahu yanzu,Star da su Wise dukkan su a kasa Suka zube sai kuka sabo da shakuwa kowa yasan kowa Muna son junan mu,Nawwar ya kalli Sera harda burbuwa tana cewa Manduwa ta wayyo Allah,Nawwar ya kalle su yace kunga abinda ake taso ku gane yanzu mene ne amfanin wannan rayuwar gashi sun mutu a banza basu tsaya sun bautawa Allah ba,mene ne a cikin kwalta,mene amfanin rayuwar street,wannan ya isheku ishara,duk dan bariki a banza yake mutuwa ba kowa Allah ke nufa da shiriya ba kafin ya mutu,wasu ma cuta suke haduwa da ita su mutu a wahale ko a kashe su a banza,ko wasu su hadu da marasa Imani Yan fashi suna karuwanci karshe sune ajalinsu gashi nan dai mutuwa ta wulakanci,ana fada muku gaskiya amma bakwa ji,Yar Zabil tace Ashahadu Allah ila ha illlah wa Ashhadu Anna muhammadurrasulillah na musulunta tana hawaye,Nima kuka nake Ina tuna bikina yanda gaba daya suka je min Suka rufa min baya,kuka na saki me karfi,Nawwar ya rungume ni Yana lallashina,yace muje can muje mu karbo iya Musulman mu gashi kusan duk ba Wanda yasan inda sauran Suka fito sabo da bariki ba a fadar asali kazo nazo ne.

    Nawwar dake akwai kudi Santana ya kaimu har can har an kwashe gawarwakin an kai can asibiti mutuware acan da police Muka samu aka bamu gawar su Manduwa da sauran Musulman duk Muka taho dasu Nawwar ya tattaro abokansa da wasu manyan aka musu wanka da sutura aka kaisu makabarta aka binne su Muna zaune a Palo na Muna zaman makoki,Santana Kuwa da su Sera duk sun koma sun kwaso kayansu tas sun dawo gidana an basu part guda Wanda sai anyi tafiya me Dan nisa sannan azo part Dina da Nawwar, Santana dakinsa daban bangaren masu aikin gida aka bashi dakinsa,Muna Palo mun zuba tagumi duk mun saka hijab rike da carbi a hannunmu ,Santana ma ya shigo Yana zaune a kasa da carbi duk da cewa sai a hankali zai dawo normal Namiji ya Saba da abin mata,Mandula ana Shan majina tace min gode Rabi da mijinki kuka hanamu zuwa da yanzu muma muna can ana loda Mana gudumar walakiri,Allah ka yafewa su Manduwa Allah ka gafarta musu,sai da Muka Yi kwana bakwai Muna jimami amma duk da haka Nawwar bai fasa dagargazata ba shi Kam amarcinsa yake yi.

   Bayan mun gama jimami ya samo Mana malamin addini zai Kai 40yrs mutum kyakyawa wankan tarwada kamili gashi wani Dan gayu,Sai mace malama me koya Mana turanci banda Wise ita tana da ilimin boko na addinin ma duniyanci yasa ta manta wani abin,gashi Sun fara yin Sallah har Santana.
Malam yau yazo Fara Mana karatu dukkanmu mun fita harda note book dinmu Daya Daya da biro zamu dinga jotting Abu me ma’ana,Muna zaune a jere saman wasu kujeru na Yan gayu cikin garden,Malam yasha Jallabiya fara kal Yana kamshi,Sallama yayi Mana da kalkala,nan take Muka kalli juna gaba dayan mu,muma da kalkala Muka hada baki Muka amsa sai da ya murmusa,yace sunana Sheikh Abul khair dan Mazarawi,kallon juna muka sake a tare,Sera tace sunan larabawa,yace Mashaallah Alhmdllh, farko Nasiha ya dinga zuba Mana akan karuwanci da Kuma falalar aure kafin a tsunduma a karatu dama Nawwar ya sanar masa Yan bariki ne shi yasa ya Fara da haka,ana zuwa ana magana akan muhimmancin aure Star ta daga Hannu sama tace Ya sheikh Ina da tambaya,yace Na’am tace mene hukuncin Saduwa da style na goho? Kunya ta Kama Malam daga zuwa zancen aure sai tambaya akan saduwa ya furta a ransa,a fili yace idan da aure ba damuwa,Star ta dauki biro da sauri tana rubutawa harda karantawa a fili ya halalta Saduwa ta hanyar goho sai ta rufe littafin, Sera tace to saduwar kaikaice fa? Yace itama ba laifi Matukar da aure itama tayi sauri ta rubuta,ta zaune fa? wise ta jefo tata itama,Yar Zabil tace akaramakalla ni kaga Kamar ni nafi son na kwanta na bararraje a dinga sambada min antaina haba nakanji mandon dadi,ya kace idan nayi aure ba laifi ko? malami ya bude baki yace ku saurara nifa karatu nazo Yi muku ba fitsara ba,Nace yo ai kaji shi yasa Muka ce a kyale mu a jahilanmu amma daga tambaya sai kayi fushi,Dalla Malam in zaka amsa Mana ka amsa balagaggu ne mu fa cewar Star, tunawa yayi Karuwai ne fa tuba ake so suyi ya Fara lallaba mu Kawai ya bar karatun falalar aure ya koma Mana Qur’ani,yazo akadari babin wanka,tafi su Star suka Fara harda cewa a tafawa Malam yeeeee Santana yace anzo wajen billahillazi zamu ji wace bata iya wankan tsarki ba.

Na gaji.

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

              91-95

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Mum Amatullah
Pharteema Muhammed
Hajiya Hauwa
Ummu Shureim
Hassana Habeeb
Zainab ashiru Adamu
Saudatu Abdullahi
Ammin Airah

 

       Malam kunya ta Kama shi bai taba ganin irin wannan rashin kunya ba,Wise ce ta mikawa Santana Hannu Suka kawo zasu tafa sai Suka janye tare da hada Baki suka furta ba kyau kowa ya maida hannunsa, ana Mana babin wanka Mandula tace ai ni bana wani gaggautawa da cuccudawa ai kawai Malam na kwara da roba na wuce wajen to Yar degree faranti ce ni, Santana da su Star harda shewa,Star tace ashe a ruwan ma akwai me tsarki da tsarkakewa to idan Mata da miji suna wanka fa amma dai shi ba matsala,Malam dai yace ai Yana da kyau sunna ce wanka da matarka,Wise ta rufe baki tana kunshe dariya tace Malam to kaima kana Yi wai,yace ae Alhmdllh Muna dan tabawa,Ido Muka zaro ai mun zaci banda ustazai yo Ustaz yayi ma bare tubabbun karuwai Papa kaga ta kanka cewar Wise ,Star ta kalli Malam tace Abul khairi Mazarawi? Yace naam dariya tayi tare da kifa kanta a saman cinyoyinta tace ya amsa wlh gaskiya Ina sonka ni Kaine ka birgeni da gani dai dai dani kake tana karewa wandon Malam kallo tace amma Malam daga wajejen Isra’ila kake ko, Malam ya Sha kunu Kawai irin ba Wasa, nidai Nace Malam ni Ina da aure ya  mazaunin mace yake idan tana yiwa miji kukan shagwaba,Malam yace ba laifi wannan Abu ne me kyau duk cikin kara dankon kauna ne,nace tab Nawwar ka shiga Uku Malam yace da kyau,ya daina Wasa yaci gaba da biya mana Muna ta iya shege ya gama da sauri ya sake Mana nasiha sosai sannan yace gobe cikin darasi harda tarihin annabawa,Star tace toooo an kusa zuwa Suratul Yusuf suna ta murna Ina jinsu Dan ni na fisu ilimin addini da Wise ma tana da nata ba laifi,Malam ya tafi da yamma Me English tazo,tace banda hausa a nan ta Mana darasi Muna ji,tana ta Mana iyayin turanci,tace zamu Fara da Noun,nace now ta yanzu yanzu ko kuwa wata Hajiya Now din ce daban,Wise ta dinga dariya da malamar ma haka,munyi nisa da karatu Nawwar ya shigo a mota yayi parking cikin jerin motocinsa,a fili nace Excuse Zan karasa Ilimina a can tare da dafe kirjina nace My life ya dawo,Malama tace karatu muke fa,baki na bude nace Man of the world fa ake ce miki,My Hero,My Star haba malama ko daga birtaniya kika zo ai kya saurara min,tashi nayi na wuce abina,fitowarsa kenan na taho da gudu na fada kirjinsa nace I wanna be in your life,dariya ya saki yace ko karatun ne ya Fara aiki,dariya nayi nace a street na tsinta, daukana yayi kamar Baby a haka Muka wuce part dinmu

     Bedroom na tayashi ya cire kayansa ya fada toilet,lekowa yayi yace Miko min key din can,daukowa nayi na Mika Masa ya damko Hannu na tare da jawoni cikin toilet din,nace yanzu fa nayi wanka,ai tayani zakiyi Yana min rada a kunne haka na hakura Muka yi wankan tare yana Wasa da sassan jikina haka Muka Gama muka fito tare da shiryawa,ya sa Kaya marasa nauyi sea blue ni kuwa guntuwar gown na saka peach and green me kyau sannan na fita kitchen na kawo Masa abinci,nice na ciyar da shi Yana danna waya har ya gama ci Muna hirar masoya, yace jibi zanje Abuja,murna nayi sabo da dama na gaji da irin yanda baya barina na huta,nace ai kuwa sai muyi ta karatunmu Allah ya dawo da Kai lafiya,Kallona yayi ganin Ina ta Jin dadi,kwafa ya ja wato murna ma kike yi to na fasa kuma ma Zan iya tafiya dake ai kina da ilimin addini, wani dukul naji yace ki hada Mana kayanmu sati zamuyi amarci sabo,tagumi na zuba haka na kumbura baki tare da cewa to,Murmushi ya shiga yi,Ashe tsokanata yayi dama ban sani ba haka na shiga hada mana kaya yace Wasa nake Miki,nace Allah ba matsala muje ko da gaske ne ai kana so Ina son abinda kake so,tsokanarki nayi tsakanin kafafunsa na dawo na zauna tare da maida kaina da gadon bayana saman kirjinsa, Wayar dake hannunsa ya ajiye gefe ya shiga Wasa da jikina sai da ya murzani son ransa sannan ya kyaleni lokacin malama ta gama darasinta har ta tafi ma,suna part dinsu sun saki kida sai cashewa suke yi Kamar basu ji Nasihar Malam ba Santana Yana can Yana ta faman murguda duwunsa Kamar na dan tsako.

   Baffa kwana biyu ya rasa inda zai ga Mami Kawai sai ganinsa nayi a gidan yayi knocking Ina Budewa na ganshi na kalle shi Muka hada Ido kallon palon yayi ko Ina Kal Kal Yana zuba kamshi yace Yana nan Kuwa? Nace ae,shigo Mana,ya shigo ya zauna na durkusa na gaida shi sai kunyata yake ji ya tuna sanda ya kaini hotel,nace Baffa ya kawata Kuwa Star, har gumi yake yace dan Allah ki rufa min asiri karku fadawa iyalina da yarana ki rokar min kawar taki ta rufa min asiri,nace wlh ya wuce har abada baza mu fada ba amma idan ka daina fa,da sauri yace wallahi daga Sanda nasan kina tare da dana ban sake ba Kuma na tuba sahihin tuba bazan sake ba har abada Inshaallah,nace to ka dauka komai bai faru ba dan Allah ya wuce har abada Allah ya Kara kiyayewa ya Kare mu ya shirya mu,yace ameen Yar Albarka sai yanzu nasan Zina bata da amfani,ga zunubi,ga zubar da mutunci dama Indai sana’ar mutum kenan to Watarana sai yaji kunya zai iya Neman yarsa ma bai sani ba,nace wlh ai mu Kam Allah ya Kare mu yanzu ma duk su Star sun dauki hanyar tuba Nawwar ma ya samo Mana malami Yana koya Mana yaki da jahilci,Baffa yace madalla kaji Dan Albarka Allah yasa wannan ya Zama shine silar shigarsa Aljanna,nace Ameen Ameen Baffa Inshaallah damu daku a Aljannar ma a GRA muke,yayi dariy tare da furta ameen ameen,nace da anyi mashahuriyar Yar giya a aljanna,Baffa ya dinga dariya yace kin San inda Mamin Nawwar take kuwa? Nace Baffa ya akayi haka ta faru har saki uku kayi ganganci wlh uwar yaranka guda,Baffa yace to ba a kaunata a gidanmu shi yasa aka kyale ni babu me fada min gaskiya gashi nan yanzu kullum ‘yata sai nayi kuka,dariyar Baffa ta kamani Kamar ba surukarsa ba sabo da a bariki Muka hadu shi yasa,nace kaga ko ni ban San inda take ba wlh Amma Watarana tana zuwa nan,Baffa yace kiyi amfani da damarki a wajen dana ki samo min inda take dan Allah Hakuri Zan bata Kawai ta yafe min tun kafin hakkinta ya kamani Allah yasa dai tayi aure da wuri mijin Kuma ya saketa ta dawo wajena,Nace Baffa ai ko ba’a saketa ba sai mun kaddamarwa mijin dole ya sako maka matarka,Baffa yace da kuwa bani da kamarki a duniya Allah ya Miki Albarka bana so ma ta fito ta hanyar da ba daidai ba Indai Allah yayi za’a saketa ne again Kinga dama kuskurena nake so na gyara,cikin magana kasa kasa nace an gama Inshaallah zata dawo muyi ta Addua Kuma zan tsaya maka iyakar iyawata Baffa ai Kai namu ne tun a baya,Baffa Yace daina tuna min na tuba wlh, Nawwar ne ya sakko daga sama ya iske mu Ina zaune Baffa ma Yana kujera a zaune Muna ta hira, yaji dadi a ransa sosai ya rasa alakarmu da Baffa da muke hira sosai, Yana zuwa na mike na kawo Baffa kayan ci da sha,Kuma ya zage yaci ya koshi,Nawwar sai mamamaki yake Suka gaisa da Baffa,yace yau ziyara na kawo muku,shi dai Nawwar yasan ko Sabreen bai taba zuwa gidan ba sai Rabiah da baya son auren.
Haka shima ya zauna Muka dinga ta hira,ya Dade a gidan sannan ya tafi,Yana tafiya Auta Nawaf yazo tsabar tsaurin Ido na yaron nan mota ya dakko ba a sani ba da kyar yake kallon gabansa haka yazo har gidanmu na fito zanje part din su Star na ganshi harda jakar kayansa, Nawwar ya fito zai fito shima ya ganshi yace Kai motar ubanwa ka dakko motar Baffa fa yaushe ma ka iya ganin gabanka? Auta yace Yaya Ina kallon gabana Mana idan naje fitsari,dariya ta kamani Nawwar harda min dakuwa ya min ambola Yana dariya,Jakar Auta na karba nace wata daya zanyi Aunty,Nace oyoyo muje ciki muka koma na Kai Masa jakarsa part din Sabreen data bari ya Sha gyara,yana zuwa harda cire agogo ya ajiye a saman gado yace kawo min shinkafa ni idan banci shinkafa ba bana Jin dadin duniya,kawo Masa nayi da ruwa da lemo wai yace ki kawo min fresh milk nace wannan Kuma baka Isa ba sai dai kaje da kanka,Zan fita yace Ina kawayenki ne Aunty? nace ai suna gidan nan an basu part guda amma wasu duk sun mutu na bawa Auta labari yace Allah sarki Allah yaji kansu fatan dai ba wannan Wise din ni kin San ita nake so,Kai Amma da tsaurin Ido kake Nawaf tafi karfinka ai nawa kake,yace wallahi da za a aura min ita Zan iya Zama Kuma na riketa tsaf nifa a SS2 nake fa ai na Isa aure,to girman aji ne aure,ke dai ba ruwanki ki hadani da ita, nace Indai itace gata gaka ba ruwana idan ka Sha mari.

   Part din su Wise na Shiga Ina dariya na basu labarin Nawaf,Wise tace kaji shegen yaro sai dai ubansa,nace ke karki zagar min uba wallahi uban miji uba ne,to Allah ya baki hakuri Mrs Nawwar nace Ameen Ina masifa,Wise tace wannan Ina zai iya dani, Wai ba yaron nan da yazo da biki ba? Nace ae Suka Yi dariya Sera tace karki kawo shi wallahi yaro haka Kawai a koya Masa fitsara nace hauka nake Nawwar yace mun lalata Masa kani domin bakin nan naku da babu sakata,shi kuwa Auta Yana Gama cin abinci sai ganinsa mukayi a part din ya shigo yayi sallama yana wani iyayi,su Star sai kunshe dariya suke,Wise tace Dana yau kazo,Auta yaji haushi yace a ransa wannan ta Isa ta haifi kamata ita din wa,a fili kuwa ya basar ya zauna a gefe,Santana ya fita baya gida ya tafi kasuwa Wai girki zai musu a part dinsu na musamman su Star duk zaman da suke kenan su ci girkin Santana ya kware da girki.

    Wise tace Nawaf Naga kana hamma,yace bacci nake ji Yana ta kallonta ta dakko zanin Atamfa tare da furta zo dan ubanka na goyaka na jijjiga ai Kai a wajenmu jariri ne,Nawaf harda harara ance za a goya shi da zani ana maida shi yaro tashi yayi ya fice ya tafi kallon ball wai yayi fushi,Mandula tace yau Naga balagaggen yaro,wlh Yana Isa aure suyi Masa Kar ya lalace cewar Seraline.

    Dagaci kullum ramewa yake Yana tumburewa sai dan ciki kwajaja a gaba wuya Kamar Sandar kiwo,Gwaggo ma duk sun rasa sukuni,suna haka manyan garin kowa yaji asirin Dagaci ya tonu an gama gane gaskiya yanzu,su Star da shigigi har kotu Suka je a kano,ni naji suna yawan tafiya kano ashe Kara suka shigar akan abinda Dagaci yayi min ni Rabiah,aka Nemo hukumar gidan reno da su ake zuwa kotu har garin Suka je Suka ji gaskiyar labari abinda ya faru da yarsu nan da nan aka fara kawo labarin karar a gidajen Radio,sakayya ni ban San me akeyi ba sai ji nayi kotu na nemana a Kano lokacin Suka bani labarin komai suna cewa wlh baza su kyale ba, da Nawwar Muka je sai da Muka halacci kotu sau biyu sannan aka samu sarki da Kansa yasa aka tugewa Dagaci rawani aka sauke shi daga sarautarsa tare da cinsa tara ta kudade masu yawan gaske,Haka ya siyar da gonakinsa kusan gaba daya gonarsa ta gado ce kawai ta rage,ya bani kudi ni Kuma ba mutunci na karbe na Kai tallafi gidan marayu gaba daya kudin, Dagaci harda cewa Rabi babu tausayi? Ki tausaya min,nace Ni Sanda kuka min mugunta tun Ina yarinya Kun tausaya min ne,abinda Zan iya muku Kawai yafiya ce amma ni bani da hadi da ku bani ba ku kuje Kuma abinda kuka min kanku kuka yiwa,gashi ban fasa ci gaba ba na juya Muka tafi ,Gwaggo tayi tsumu tsumu itama, da kotu cewa Suka yi za a kaita prison nice na nemar musu Alfarma aka kyale su a haka.
Dagaci fa duniyar ta Masa zafi Aunty Amarya Kuma sun daura gaba da Gwaggo kullum basa zaman lafiya,Dagaci ya Gaji ya saki Aunty Amarya, da Gaji da Gwaggo Suka nada Mata dukan tsiya ta fito zata tafi Suka bita da duka ko kunya basa ji har gefen babban titi suna kokawa mota tazo wacce birkinta yaki tsayawa Kawai ta banke su gaba daya har Gaji.

   Mutane Suka cika wajen aka kwashe su zuwa asibiti,Dagaci ya tafi asibitin Yana kuka abubuwa sun Masa yawa Yana zuwa ya samu Aunty Amarya tayi karaya wajen biyar itama Gwaggo karaya ta Kai hudu,Gaji Kuwa Allah yasa motar kadan ta shafeta bata karye ba.
Me chemist din kuwa da Gaji Suka je Suka sashi ya min sharrin ciki gaba daya yanzu bashi da kasuwa duk da ba a San me yayi min ba babu Wanda ke saurar chemist dinsa sabo da an bude sababbin chemist,Ni Kuwa Nawwar nasa ya bawa Bala Babban jari ya tura Masa dubu dari uku ya ja jari sai godiya yake min kamar ba gobe.

     Tsabar son abin duniya na Papa kullum sai ya Kira Wise tun Yana Kira yace ya Kira ne ya gaisheta har ya saba da hira,Yau da dare cikin dare suna kwance da Maman Sabreen ya lallaba ya tashi ya barta ya fito Palo ya Kira Wise bugu Daya ta dauka da muryar bacci,yace Sorry na tashe ki ko kiyi hakuri na riga na Saba da ke nifa Ina ganin kamar mun wuce matakin da muke na gaisawa ni gaskiya sonki nake Yi Kuma aurenki zanyi idan kin amince, Wise tayi Murmushi a hankali tace gaskiya anya Kuwa to ka bani dai lokaci nayi tunani yace na baki farin cikina,kece ruhina,Wise tana jinsa tace ji mutumin banza Yar cikinka a fili tace na gode yace dan Allah ki soni karki ce a’a na Riga na baki Amanar zuciya….Amanar zuciyaaaaaaa yaji Mama ta fito tana tambaya uban wa ka bawa amanar zuciyarka? Dama abinda kake kenan kullum tsakar dare sai waya waya haba Yusuf Ashe amanata zaka ci kace baza ka min kishiya ba ka tuna Alkawari fa kayi min,Papa yace na karya shi yau shike nan bazan Kara aure ba ance idan ka Kara aure kofofin budi zasu Kara bude maka shike nan so kike nayi asara tsaki yaja yaci gaba da wayar,Wise tace Uwargida ce ne? Yace itace take min ihu,tace kyaleta kishi ne ni gaskiya Zan fasa auren naka yace kiyi Hakuri Dan Allah kyale wannan tsohuwar hakorinta fa sun Fara cirewa,nace Allah sarki bata da hakora yace ai duk na gaba sun zube tsufa ya kamata da gaske, Wise tace gaskiya kana bukatar sabuwar zuma,dariya ya saki Hahahahaha shi yasa kike birgeni,Mama tayi sororo tana ji yace kiyi mafarki na sannan ki gaishe min da kudadenki, Wise Ido ta zaro tace amma wannan ya cika mayen kudi har kudin Nawa ma na gaishe Masa da su,Yana Gama wayar Mama tace yanzu Yusuf ni zaka cewa hakorana sun zube kayi min sharri,Tsaki ya ja ya mike Mama ta cakumo shi ta kafa Masa hakoran a gadon baya tana cizonsa Yana ihu,tace wannan mene kace sun zube,ranar sabo da bala’in Mama basu yi bacci ba.

     Jamcy ce taci kwalliya ta shigo gidan Nawwar a motarta tana parking ta fito ita ga tsagera tana tauna chewgum tana taku,taci sa’a su Star suna palona gaba dayanmu ta shigo ko sallama,Yar zabil tsawa ta Mata ke koma kiyi sallama,ubanki ma yayi kadan bare ke cewar Jamcy,Ina shegiyar da akace ta gagari kowa ba wacce ta Isa ta auri mijinta gani ni na zo Kuma sai na auri mijinki Nawwar na dade Ina sonsa,Star basu ce Mata kala ba Suka maidata banza ta gama zage zagenta Shuru,Wise ce ta dakko sabuwar hira ya dinkunan Kuwa kin karbo? Nace sai gobe Inshaallah,Jamcy bata hakura ba tace ana magana Kun maida mutum mahaukaci nan ma Shuru basu ce kala ba sai hirarmu muke ta zubawa Muna tafawa,taci gaba da cewa idan Kun hana Sabreen Zama ni nafi karfinku baku Isa ba,Nan ma shewa mukayi muka tafa Muna hirar mu,Jamcy ta kule Kamar ta hadiyu zuciya tayi tsokanar tayi Shuru sabo da bata da abin fada,Tsaki ta ja tace karuwan banza karuwan wofi Yan Iska duk Wanda yake ba dan sunna bane ai dole yayi haka,idan Kun haifu kuyi magana banzaye karuwai,Ni dariya ta bani Kawai kizo ba gaira ba dalili ki dinga tsokana,ba Wanda ya kulata duk magana intayi sai mun saki shewa wannan yafi Mata ciwo ta juya ta fice tana Jan Tsaki,ko da ta tafi ko zancenta bamuyi ba hirar mu Muka ci gaba,Wise tace Allah yasa ta dawo yanzu mun Mata abinda yafi komai ciwo to nan gaba jini da majina zamu hada mata.

    Baffa kwance yake a dakin Iyamami saman gadonta ya sata gaba ya hanata sukuni,yace gaskiya ni a san yanda za ayi dani dan ni gaskiya ku Nemo min matata ai da zugarku yasa na sake ta kune kuka dinga zugani,Iyamami ta juyo da masifa tace kai kaci ubanka yau naga marar mutuncin yaro abinda kake ko Auta bazai Yi ba,Nema kake ka susuce ta ja tsaki,Baffa yaki tafiya yace Allah sai Kun Nemo min matata ba inda zanje ai da Yusuf ne da tuni kuna tausayinsa Ni shike nan kamar bare an ware ni ba a so na ya karasa da muryar tausayi,Nawwar ne ya shigo bayan sun gaisa Baffa yace Nawwar wato baza ka fada min inda uwarka take ba ko? to ai kafin a sameka ni ta sani ita na sani yanzu kazo sabo da uwarka ce ka fini zakewa,Nawwar shi kunya ma yake ji abinda Baffa ke yi, Ya hana kowa sukuni tashi yayi zai bar dakin Baffa yace sai na talauce tukun zakuyi bayani tunda so kuke ku ganni na zama abin Allah sarki a gari,Nawwar tafiyarsa yayi ya bar Baffa da Iyamami suna ta fama.

   Satin Mairo biyu a Kaduna rannan sunje kasuwa da Sadiya kawarta ta sake ganin Rufaida Cele a kasko tana ta yiwa me shago masifa wannan waken suyar kace wani naira dari ta karu akai sabo da tsadar rayuwa ni a awarar tawa nawa ce ribata eyyeee Zan daina zuwa siyayya wajenka Dan Allah jibeka gaba Daya kamannin Yan Tanzania ne da kai,Haka tana mita me shago Yana dariya yace Cele tsiyarki yawa gareta,sai da ya gama zubawa ta dakko biscuits Kato me tsada tace alakoro na Sha shayi da shi,ta dauki kayanta tana juyawa taga Mairo a bayanta ta kafeta da Ido,tace baiwar Allah wai lafiya da wata fuskarki Kamar anyi kilishi da biri, Nuna Mairo tayi da yatsa ke dai da gani koko da miyar kuka sunyi saukar ungulu a fuskarki,Sadiya ta kalli Cele sanye take cikin tsohon leshi riga da zani tace ke wai ke bakya Shan kokon ne aikin banza,Cele tace Kutmar….ta duro ashar ta ajiye ledar wake taci kwalar Sadiya tace wa ya fada Miki Cele tana magana ana maida Mata da martani,karki ganni a Haka kina ganina Kinga Kalar shayi jikina duk shayi ne kwakwaran juyi nayi sai dai kiga Lipton da citta da kaninfari suna zuba kasa shegiya me kunnen bera ta sake jijjiga Sadiya,Sadiya ta shaku sosai sai kakari take,Mairo tace dan Allah kiyi hakuri ta raba fadan da kyar,Cele ta sake kallon Sadiya tace ke dai wlh ko bilget ne ya aureki karewar kudi baza ki taba gyaruwa ba baza ki kyau ba,juyawa tayi Kan Mairo ta nunata da yatsa tace ke Kuma wallahi duk ranar da Muka sake haduwa dake a hanya Kika kirani da Rabi sai….sai…ta zaro slifas dinta ta kwalawa Mairo a goshi tace sai naci uwarki,suna kallo ta dauki Wakenta ta Kara gaba a shegiyar tsohuwar Vespa dinta tana cewa kowa ya matsa ba mutunci,baki bude Mairo Suka bita da kallo.

   Cele wata unguwa ta shiga ta talakawa futuk,gidansu wani mugun tsohon gida ne me dauke da daki biyu sai bandaki a tsakar gida sai kitchen,da alama gidan babu matar aure daga Ita sai tsoho Kakanta,Zuwa Yamma likis ta fito da awarar da ta rigada ta dafa ta yanyankata a kofar gidansu ta kunna wuta tare da dasa kasko ga dankalin hausa shima a yanke a wanke ana soyawa,tun kafin ta Fara suyar ana ta kawo kudi wajen ya cika da samari matasa babu digon Rahama a fuskarta,tana fara suya tace Kai Safiyanu zo dalla ka karba tana cika tana batsewa,Safiyanu ya matso Yana cewa ai sai Cele,bata ko kulashi ba ya tafi,tana soya wata tace Nasuru matso kusa shegen baki Kamar damusa na hamma aka sheke da dariya,su matasa sabo da kyawun Rufaida gata budurwa yasa samari ke dandazo duk bala’inta,tanayi ta kwala Kira Bashariiiiii…ta dari uku ko? Kuma du zaka cinye? Yace ae tayi min kadan ma wlh manage zanyi,tana suya ba tare data kalle shi ba tace amma salka ce a cikinka ko kake tarawa?in ba haka ba Ina tunbinka zai dauke sai dai ko Allah ya maka wata jaka daban ma’adanar abinci ungo ni karbi,ta soya wata ta zuba a Leda tace Hamisu ta hamsin ko yace ae tace uhmm sarkin tsumulmula wannan matarka ta shiga uku kullum ta hamsim Anya Kuwa kana bawa budurwarka kyauta ungo gayyar tsiyarka karbi jeka karka isheni,dankali ta soya na dari biyu tace Usyyyy.. yazo ya karba tace amma Kai kadai kake kwana a daki ko yau akwai banka tusa ungo basir salamu Alaykum dinka,a haka ta sallami matasa da yara ta juyo Kan wani yaro yasha kwalkwabo tace zo Kai ya mato yaro karami tace Miko min shegen kan nan naka duk kwal uku,ya miko kuwa tasa hannu ta zuba Masa rankwashi tace jeka naci ladan aska,yaro ya fara hawaye tace zan karyaka na tatsile ma wuya bar nan dan uwarka asabe me Miya Kamar yawun kaza ta Mika Masa tasa ya tafi sum sum tace Yan banza Wanda iyayenku basu iya gayu ba basu San wanka ba su samu yaro a salle Masa Kai sai kace Shedan,Kaka ne ya dawo da kekensa tace Sannu da zuwa Kaka yace yawwa Jikalle ta a zubo min awarar Nima na lasa,ta soya ta Mika Masa a Leda tace Kaka ka Mana jullof din taliya,in Banda abin Rufaida wannan tsoho Haka shi zai iya wani Jollof cewar wani saurayi da zuwansa kenan,tace Masa’udu Ina ganin mutuncinka kasan hali na tam Kaka ba girkin da bai iya ba Rannan ma cewa nayi wallahi sai yayi Mana fried rice na siyo kayan yi a kasuwa sai da na koya Masa, Kuma watarana Indai nace yayi ya kasa sai nayi sati guda Ina gaba da shi,Masa’udu ya kwashe da dariya yace Cele na gode jiya naje wajen kawarki da Kika hadani da ita,tace Allah ya kuka Kare? Yace mun Sha love,Rufaida tana kallonsa tace kace har abin nan ta maka me Kama da tsaki,yace me? tace kamarsu daya da tsaki dai ,yace oh wai kiss? tace ae mana shi,yace bata min ba ai sai an saba,to Indai tayi maka shi na daina kula Hajara bani ba ita wannan ai Iskanci ne soyayyar Shan minti ku dama samarin yanzu halinku kenan daga Fara soyayya sai tabe tabe da matse matse bada ni ba shi yasa ba ruwana da soyayya idan ka min Zan aureka to ba wani zance go Straight to the point Kawai a daura aure amma wannan Iskanci bada ni ba,Rannan Sailuba tace tayi saurayi kirjinta karmar zai cire,to ba ruwana ni harda dukan cinya taci gaba da suya.

    Zuwa dare bayan ta gama tana zaune tana irga kudi tace Kaka gobe geron yin Rufaida yogourt zai Kare sai naje kasuwa gobe,Dattijon yace Allah ya kaimu ta dakko jullof din taliyarta da Kaka ya girka gata nan a cabalbale tana ci aka yi Sallama ta amsa

    Wani yaro yace wai ance Cele a kasko tazo,zanyi masifa Kaka ta furta yace dan Allah jikalle kije ko alheri ne,dan Kawai kasa baki ne wlh ko wanka fa banyi ba,Haka ta fita tana zuwa ta samu wani Alhaji yazo da motarsa katuwa dama ga haske a kofar gidan ya kasa magana sai kallonta yake Yana kallon kirjinta duk kuwa da cewa Hijab ne a jikinta,ta kalli Alhajin taga ya zura Mata Ido tace Kai idan kirjin kazo kallo dan Allah fisge ka tafi da shi gidanka ka dinga matashi da shi Kawai,wannan da ganinka gwauro ne kai Allah ya kaimu watan azumi sai nasa an maka kidan gwauro, tana Gama fada tayi juyawarta gida ta bar shi nan tana balbalin bala’i,Kaka Yana kwance a saman tabarma a tsakar gida to wa ya taba min ke ne haka? Yo Kaka kirjina yazo kallo ashe shine dalilin Kiran shi yasa na dawo,Kaka ya dinga masifa zai lalata min jika da Ido tambadadde ya tashi ya dakko Sanda ya fito Yana tambaya Ina munafukin yake algungumi lokacin mutumin ya tafi ma tuni,sai da ya gaji da masifa sannan ya dawo gida.
Washe gari da sassafe Rufaida ta dama kokonta na siyarwa cikin bitikin painti uku ta fita kofar gida da shi,kokon da take damawa ta siyar shine samari Suka sa masa Rufaida Yogour din Cele

   SAUDIYA

    Hamshakin balarabe ne Kyakyawan gaske Wanda ko a larabawan ba karamin Handsome bane haifaffen dan Makkah ne amma a birnin Riyad yake da matarsa,balaraben matashi ne bazai wuce sa’an Nawwar ba zai Kai 30 zuwa 32yrs,sanye yake cikin kayan likitoci Mai kudi ne Kuma gashi likita ne da Shirin fita ya fito Yana sauri ,matarsa Balarabiya ce itama usul me Yar kiba kyakyawa da ita Mashaallah itama ta fito sanye da kayan likitoci domin itama kwarariyar likita ce ta bangaren Mata,Dining Suka nufa Wanda yake shake da kayan abinci irin nasu na larabawa Wanda me aikinsu wata Yar kasar Bangladesh ta gama shirya musu,suna cin abinci suna magana akan matsalar dake damunsu ta rashin haihuwa gashi shi zai iya haihuwa amma matarsa mahaifarta baza ta dauki ciki ba, an auna su akan hakan matarsa Kuma Zafin kishi gareta baza ta yarda ya auri wata ba,Kiran Sunansa tayi tace Ahsan cikin harshen larabci tace bazan iya sharing miji da kowa ba Kawai mu samu wata a Mata dashen ciki ta haihu tunda maniyyinmu zai iya bada yaro Kawai mahaifata ce baza ta iya daukan ciki ba, mu samu a masu zuwa aiki kasar nan a samu wata,cikin larabci yace haba Maheerah ni bazan zalunci kowa ba wannan zalunci ne ko da Zan iya yarda sai mace wacce ta haifi Kamar Yara uku ta Saba da wahalar ciki da dawainiyarsa sannan sai da yardarta Kuma biyanta zanyi kudi me yawan gaske,Maheerah Kuwa tana daga cikin larabawa marasa tausayi da imani sannan akwai nuna kabilanci,a fili tace ba matsala hakan yayi a ranta Kuma tace ta karfi ma zan samo wata ba ruwana wala budurwa wala bazawara Kawai dai ni na samu yaro jinina jinin mijina,suna Gama cin abinci shi da Kansa yayi driving matarsa wurin aiki asibiti sannan sabo da wahala shi kuma ya Kira driver ya kaishi nasa kamar yanda yawancin larabawa ke yi matarsu da kansu zasu kaita unguwa,ga Wanda kudinsu ya kai driver Kawai shi zai tuka.

    Wise Wasa Wasa sosai alakarsu tayi nisa da Papa har Nawwar ya shirya ranar da zasu je garin su Wise a daidaita da iyayenta ta koma gida kafin biki, kullum Kuma suna karatu Wanda Watarana malamin ji yake kamar ya ajiye koyar dasu idan Suka kwabo Masa tambaya,ga Star ta sa Malam gaba kullum yazo karatu sai tayi ta zana Masa hoton love ta dinga nuna Masa a littafi,tun Yana sharewa har ya Fara basarwa.
Yau Muna zaune Yana Mana Karatu Star suna hada Ido da Malam sai ta kashe Masa Ido tana Masa wani kallon kauna,shi kuwa Malam wannan kallon na Star shi yake tafiya da imaninsa sai Yana cikin karatu sai aji yayi duf ya shagala da kallon Star,yanzu ma yana biya Mana Tafsir na Qur’ani dake daga kasa ya fara yana cewa Suratul Iklasi…surar Khadaituwar  ubangiji,a maka aka saukar da ita,tana da ayoyi hudu,kalmomi goma Sha biyar harufai arba’in da arba’in da bakwa…da ba…daaaaaaaaaaa Yana can suna ta signa da Star  shi da ita,su Muka zubawa Ido muna kallon ikon Allah,Wise ce tayi gyaran murya tace Malam Abulkhari Kalli gabanka da sauri ya dawo hayyacinsa ya fuske Yana basarwa Antaina har ta mike a wando ana gani kuru kuru dake wani yadi ya saka me karamin dinki,Muna ta dariya kasa kasa a boye,ya bata rai ya cukule yana mazewa.

     Kwana uku tsakani Star kafin ta fito karatu sai ta zauna tana ta faman tsala gayu duk Muna can anyi nisa a karatu Muna ta bada hadda,Malam wajen zamanta yake ta kalla Yana so ya tambaya Yana Jin kunya can dai ya gagara daurewa yace Wai Ina nutsatsiyar Yarinyar nan ne? Muka Fara kalle kalle Muka hada baki har Santana Muka ce Malam ai duk cikinmu ba Nutsatse mu,yace akwai Mana wacce tafi kowa nutsuwa wannan me hankalin me sunan tauraro,dariya Muka kece dama mun San Star yake nema matar da tafi kowa Iskanci zai ce nutsatsiyar cikinmu,Yar Zabil tace mugun ciwo ya Kama Malam,Mandula tace ahayeeee Muka saki guda ayyiriririri ganin Star ta fito cikin gayu,Sera tace Malam ga wankan ka nan,Malam harda sosa keya,nace yau Nawwar sai yaji labarin nan Mun rinjayi Malam,Ina karyar malinta a guji sharrin mata,Wise harda waka karuwa tayi rana…karuwa tayi rana….Malam ya daure Fuska Kawai yaci gaba da karatunsa irin ba raini.

Masu Shari wlh Kuna birgeni

 

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

96-100

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naku ne

Asmeen
Maman Anwar
Pharry
Halima Abubakar
Shafa’atu Barde
Layuza Yusuf Adamu
Mom Ihsan
Aishadangile974
His Queen
Health care
Ummul Khalil

 

       Sai da Muka gama karatu me turanci tazo itama muka yi, Wasa wasa Muna karatunmu sai gashi har mun kai kusan wata biyu,kamar bama Ji iyashegen mu Yana nan sabo da Sabo sai a hankali,Kamar kullum yau Malam Abulkhair yazo sai gashi da abu a wata ledar shopping me kyau,Star tana zuwa ya mika Mata yace gashi kyauta ce akan kinfi kowa kokari,inji karyar malam Star in banda iya shege me ta iya duk mun fita kokari amma dake Yana so Kawai ya Mata kyauta sai yace tafi kowa kokari,Nawwar yana dawowa na mike,Malam yace ke koma ki zauna ana karatu zaki tafi,nace Antaina ta karasa min ni kam,Star tace muma Allah ya nuna Mana mijin mu sai mu dora da harka,Malam harda cewa Ameen sabo da Star ce tayi magana, Star ce tayi rubutu a takarda ta cillawa Malam a kafarsa yayi sauri ya take da kafa ya wani Fuske yaci gaba da karatu sai da akayi nisa sannan ya tsuguna ya dauke takarda ya karanta a tsayen da yake tayi rubutu Kamar haka

    My Abul ka dinga sauri da karatun ka gama kaga Mata suna kallemin Kai,idan kana so na ka tabbatar zaka iya kula Dani da kayan gyaran skin dina? bana so ayi aure ka dinga kawo min ayoyi kullum,a’a akwai lokacin karatu daban sauran Antaina ta dinga biya min darasin,ya kace zaka iya daukan nauyi na ko a’a Kai sai wa’azi?
Dariya ce ta Kama Malam Wai mene Antaina da suke ta zancenta ne oho,biro ya dauka yayi rubunsa, sai ya fara zagasu Yana karatu duk cikin karatu ne ya zagaya su yafi sau biyar sannan yana zagayowa yazo ta saitin Star sai ya jefa Mata takardar,dauka tayi ta bude ta karanta Kamar haka
Haba Mai zai hana ba abinda zai gagara Inshaallah,Ina da babban aikin yina ko Mene za a miki,dama matata ta rasu da ciki a jikinta tun daga lokacin ban sake aure ba Allah ya hada mu dake nikam kin mini Ina kaunarki fatan Zaki zama uwar ‘ya’ya na,bani da yaro ko daya matata Bata haihu da wuri ba Kuma da cikin ma ta rasu
Yours Malam
Star takardar ta mikawa Wise ta karanta itama ta mikawa Sera ta karanta ta mikawa Yar Zabil ta karanta aka mikawa Mandula ta gani itama ta mikawa Santana Yana karantawa ya saki shewa Ahayeee Suka hada baki matarsa ta rasu ba kishiya ba kishiya ba Kishiya ahahayyeee chasss,Malam sabo da kunya nasa ya nasa ya tattara yace sai jibi gobe bazan zo ba Ina da Uzuri ya tafi,Star da shagwaba tace Malam zanyi kuka,Santana yace Banga laifinki ba Malam ai ya hadu hanci Kamar karas haka Malam Yana jikin motarsa zai shiga Santana yace nidai in biki ya tashi Malam Ina saida Man Power,Malam dai motarsa ya shiga ya tafi Yana ta Jin dadi ya Fadi abinda ke ransa shike Nan Star ta Zama tawa harda karanta doguwar surah sabo da nishadi shi a dole Malam ba kida.

    Ina bedroom ban San me suke ba Nawwar yayi wanka yaci abinci Yana kwance a jikina Yana murza boobs dina duk ya taso min sha’awa sabo da yanzu Ina dan Jin dadin harkar,Labari yake bani Mami zata Zo anjima ta Mana Sallama zata tafi Saudiyya Kuma zata dade acan sai ta kusa shekara Wai ibada zata tafi can zata zauna a hotel har iya tsayin lokacin da zata dawo Kuma a Madina zata zauna ba a garin Makkah ba,nace Allah ya kaimu Amma za a kashe kudi yace ya za ayi to taje tayi Ibadar yafi tunda ita har yanzu Baffa Yana ranta,nace Allah ya daidaita su yace ameen, Wayata na dakko Kamar Ina game Baffa na turawa text Mami zata Zo yau gidanmu da Yamma.
Ina turawa na ajiye Wayar nace nima muyi ibadarmu garin shegen Shan maganinmu yanzu kullum a sha’awa nake kadan nake jira,Nawwar yace ai a ko Ina in kayi ibada tana karbuwa shi Bai ma gane ibadar da nake nufi ba,nace nifa ibadar Antaina nace, baki ya rike Yana mamaki yace yau Kuma da kanki? ashe an Fara sabawa ke Kuwa wata biyu kullum ana aiki ai ya dace dama ki Saba tunda ke ba karamar yarinya bace,nace jiya baka Yi ba shekaran jiya ma baka Yi ba Allah yasa dai lafiya kake? Yace kalau nake barinki nayi ki huta naga kamar Ina takura miki,da sauri nace a’a wlh a’a sam kullum kazo ko yaushe ko round nawa ne , karfa azo ki fara wannan kukan kamar Zaki zageni nace Allah ya tsareni da zaginka da nayi asara kuwa,amma to kamin hankali ina wata shagwaba,yace ai ba sai kince ba zanzo da kaina ma, bakina na jefa cikin nasa na Fara Masa wani irin sha kayana ya cire min muka Fara kashe kanmu da Dadi,Allah yayi Ni macece ni me shegen ihu idan Ina Jin dadin abin gashi yanzu nayi feshin ruwa ba jira,Nawwar Yana shan karadi da maganganu harda na hauka ma,shima haka yake shi yasa bama son wani yazo part dinmu Kar ma yaji wani dan abu, sarrafa juna muke Muna Jin Dadi tunda ya shigeni Ina Jin Dadi Ina ihun sweet abu yayi zurfi Yana yi sosai na Fara Jin zafi zafi kadan haka na daure Kar yace na fiye raki,yau ganin haka ya canja min style nasha wahala ba kadan ba amma na daure Ina ta uhun wahala na nuna Kamar na dadi nake ji,Yana canja wani style din na fashe da kuka nace wlh wannan zafi ko kulani baiyi ba duk maganin da su Mandula Suka bashi ne sai ya dade yana abu daya baya tunanin ni ban Saba ba,nace Dan Allah ka dawo Style na walgargajiyatu da gargajiyatu dan Allah wayyo Allah Zan mutu,a hankali ya maidani na gargajiya nace haba koda naji salama,yaci gaba nai dade ba Allah yasa ya gamsu ya bani madararsa, hanci ya lakace min Yace Baki da dauriya ko kadan da kina Jin dadinki kina min sambatu wai ni zaki wa wayo kina Jin zafi kina min kuka sabo da nace na dadi ne to na Dadi ai ba ya buya,da farko nasan na dadi kikeyi Ina canja style Kika fara Jin wahala Kuma wlh shima a haka zaki saba kullum yanzu sabo za ayi,mukus nayi Ina zare ido,dariya ya dinga min tare da rungumeni Yana cewa I love you,kece Kika jawo ni,nace dan ba Kara ai Ina manne a jikinsa.

    Yamma nayi Mami tazo Muna tsaka da labari sai ga Baffa Kamar an jefo shi,Muna amsa sallamarsa ya wuce gaban Mami suna wani kallon juna Kamar zasu lashe juna,tashi Muka yi ni da Nawwar Muka haura sama Baffa zube gwiwoyinsa yayi a kasa Yana dan Allah Salamatu ki yafe min dan Allah ki dubi girman Allah ki yafe min sai hawaye sharrrrrrr Kamar yaro,Mami ma tana kallonsa ta fashe da kuka tana ta shesheka sun dade a haka kowanne Yana kuka a cikinsu,nayi kuskuren da bazan yafewa kaina baaaaaa ya sake sakin kuka irin na manya Yana durkushe a gabanta ya rike kafafunta ki yafe min dan Allah,Mami tana goge hawaye tace ba komai na yafe maka ya wuce na yafe,Baffa ya manta Idonsa ya rufe ya rungume ta,Mami tace zaka shiga fushin ubangiji ni ba muharramarka bace yanzu,Baffa ya saketa yace yace na cuci kaina na yiwa kaina na biyewa son zuciya,yanzu da me Ummin Haidar ta fiki ni me ya rufe min ido ne,Mami tace Kai ka sani kuma,akan na zauna da Ummun Haidar gwara na dawwama a gwauro duk azumi azo a kada min ganga harda karasawa da tausayi,duk zuga ce tayi tasiri a kaina ,Iyamami,Yusuf,Ummin Haidar sune ke zugani gashi yanzu sun jawo min sun barni a ruwa,Mami tace oho maka kuma, Yana ta kame kame dai Mami sabo da takaici ta mike tayi tafiyarta ta bar gidan,tana komawa gida sai kuka take Kamar ba gobe,washe gari Nawwar ya kaita Airport ta shiga jirgi tana ta uban kuka tana tuna tsohon mijinta.
Baffa kuwa Yana komawa gida cikin fushi ya saki Ummin Haidar saki daya yace gwara na zauna a tuzuruna munafuka algunguma kina kallo na dauki hanyar jahannama ashe Kara danna ni ciki kike bakar algunguma kwashe kayanki ki tafi Kuma ki barmin yarana,Ummin Haidar za a bar gidan daula sai kuka taje wajen Iyamami ta fada mata,Iyamami tasa aka Nemo Baffa tayi tayi ya maida Ummin Haidar yace wlh Kuna takura min Zan karasa sauran igiyoyin gaba daya itama gwara ku kyale ni,Iyamami tace au au to Kinga jeki gida idan ya huce zai dawo dake da Kansa,Baffa ya kalli Ummin Haidar yace ke Kar a doraki a keken bera ki sani bazan dawo dake ba tunda ke ba matar arziki bace Kawai ke kanki Kika sani,kina kallo Ina kwana a dakinki na Hana Mami kwananta Kika kasa tunatar dani akwai Allah,kina kallo Ina cin mutuncin wata Kika kasa fada min gaskiya sai dai ki zugani to baza ki jani jahannama ba wallahi sai dai ki tafi ke kadai bar min gida ya daka Mata tsawa,Yaje ya kwashe yaransa biyu ya kaiwa Nasira da Sultana yace gashi nan ku kular min dasu.
Daga ranar Suka dawo Jin dadin babansu kullum sai yazo cikinsu ko ya kirasu part dinsa suyi ta hira tare,akwai maza masu daukan zugar matansu ko iyayensu ko da kuwa ba akan gaskiya ake Dora su ba,irinsu idan mace ta gari Suka samu to za a ji dadinsu zasu amfani alumma sabo da matar zata basu shawara su dauka,Mata a guji dora mazaje akan hanyar da ba dai dai ba,wani zaiwa Yan Uwansa kyauta kibi ki kankane sai naki Yan uwan,zaiyi wani aikin Allah na lada ki hana,Kuma da yawa maza suna daukan Maganar matansu.

    Yau Sunday a jirki Muka tafi Jagawa state ni,Nawwar,wise,Star,Yar Zabil,Mandula harda Santana zamu je gidan su Wise ayi sulhu ita ce ta Mana Iso har gidansu Muna zuwa Muka hango wani Dattijo me Kama da Wise a kofar gidansa a zaune kujera da farin glass dinsa da wani katon littafi na tattalin arzikin duniya da gani kaga tsohon dan boko wasu  suna tabarma da sauran dattijai irinsa ana hira,Wise a mota har zufa take sabo da tsoro tasan babansu,Muna Fitowa a motocin guda biyu taxi Wise ce ta Fara fitowa harda sa hijab mu Kuwa duk mun Sha gayu,farin glass dinsa ya cire a hankali yace Hauwa’u kece abin mamaki sai ya tashi ya rungumeta irin dan boko nan wayayye, Yana murna yace ki yafe min Hauwa nayi kuskure dana takura Miki sai kinyi karatu bayan ke aure kike bukata karshe na kore ki banyi tunanin Ina Zaki je ba,ki yafe min Hauwa daga kanki ban sake takurawa kowa sai yayi karatu ba a gidana,Wise tana kuka tace ya wuce Daddy nima ka yafe min nayi kuskure,Dattijan suna ta taya shi murna Muka shiga ciki gaba dayan mu,kannena Suka fito da uban gudu suna murna,Maman mu duk ta rame sabo da bakin cikin Ina na shiga mijinta ya korar Mata ‘yarta,itama muka fashe da kuka ta rungumeni Muna ta murna,gaba daya muka zauna har su Nawwar, bayan an kawo Mana kayan motsa baki sannan Mama ta Dora Mana girki gidanmu me kyau Kato da gani kasan akwai rufin asiri,labarin komai na zauna na bawa Daddy da Mama suka dinga ta kuka suna Kuma godewa Allah da yasa na shiryu,Daddy yace ai bayan tafiyarki kadan nayi ritaya Hauwa duk wannan kudin Nawa yanzu babu sai rufin asiri gidan ne kawai,da Nawwar Suka dinga hira Yana magana Daddy Yana jefo turanci shi ga dan boko daga nan ya Fara bawa Nawwar labarin yanda tattalin arzikin Russia ya karu,yace kasan Bellarus da Azarbajan tare da Ukraine Russia ai ita ke juya wasu manyan state nasu masu karfin tattalin arzikin,wannan yakin da akeyi ai ita Ukraine itace bata da Gaskiya,baka karanta Littafin yarjejiniya tsakanin Russia da Ukraine ba kafin ta amince Mata ta shiga yankin Europe,kasan ai da duk a Soviet Union suke under Russia,Nawwar dai yana haka ne,uhmm,ae haka ne kam ,nace Wise ma ta samu miji ma zasu kawo kudi kwana nan,Daddy yace mashaallah,sai Yamma su Nawwar Suka ce zasu tafi,Wise tace nima binku zanyi ni bazan iya rayuwar nan ba yanzu kwata kwata idan an tashi biki zamu taho nan,Mama tace ai Kuwa baki Isa ba ki zauna Mana muma muji duminki,da kyar Wise ta yarda tana Fushi Muka taho Muka barta a can harda kuka,nace ke da an kusa biki zaki dawo Mana mayi waya tace to video call zamu na yi Muna dariya Muka tafi.

    Sai da Soyayyar Star da Malam tayi karfi yace zai turo manya sannan itama Star muka shirya Dan bala’i ana gobe zamu tafi sai ganin Wise Muka Yi tazo Wai da ita za a Kai kowa,Washe gari Sai Yobe state,nan ma gidan su Star dama daga babarta sai Saima Yar uwarta Star tace ta samu Miji amma sai bikinta zata zo Saima an girma an Zama Yan Mata itama da Saurayinta a nan Yoben Nawwar yace sai a hada ayi bikin,Star wato Aisha ta hakura a nan gida aka barta tare da kanwarta da Mamanta.
Tunda Muka dawo Wise ta koma gida ita da Star,Rannan Sabeer abokin Nawwar Wanda da shi aka je bikina yazo wajen Nawwar yaga Seraline ya nace shi ita yake so,Reraline sai Murna take matashi haka hadadde me kudi da shi itam me zata ce da Allah sai godiya,zance ya Fara zuwa,Sera anci gayu anje tace ni gaskiya Allah ka canja suna sabo da Naga me irin sunanka marar mutunci sam halinta bai da kyau,Sabeer yace to fa Yana wani nishadi ana Masa shagwaba,yace wacece? Sera an goge da bariki harda gyara Masa kwalar riga tana cewa Sabreen mana wacce Nawwar ya Fara aure, Kai Sabeer ita Sabreen gaskiya ka canja please My Man tana wani narkewa,Sabeer gani yake duk duniya ba Wanda ya kaishi dace yace Eyya sorry su Daddy sun riga sun yanka min rago a haka, Sera ana wani dire diren kafafu ni Allah…Allah….uhum..uhm….farin ciki ya cika Sabeer ta gama tafiya da shi a rayuwa,Sabeer shi mamansa da Kannensa suna can asalin state dinsu Katsina,Amaryar babansu Hajiya Sumayya tana nan a wajenta Sabeer yake sun shaku,Baban Sabeer a nan ya kawo Amaryarsa tunda anan yake kasuwanci idan Kuma yayi wata Daya ko biyu sai ya koma Katsina wajen Uwar gida,Hajiya Sumayya yaranta biyar Yan Mata dasu duk suna University,Hajiya Sumayya da Yaranta kaf basa son Sabeer ya auri Sera su basa son talaka,tunda Suka je kauyen su Sera Kai kudi Suka ga garin da gidan Suka Fara sukan auren amma Maman Sabeer da Babansa duk suna so sabo da haka ma aka sa ranar aure,duk kuwa da sunbi didigi sunji da a baya ance karuwa ce,shi aure haka yake da tone tone.

    Yar Zabil da Mandula Suka ce to mu ko wa zamu samu oho Kinga munyi kwantai mu duk shegen degree faranti na cewar Mandula,ana haka Katsam tsohon saurayin Mandula wani Igbo kyakyawa ne sosai fari gashi da rufin asirinsa matashi da tana zuwa tayashi kwana,bashi da Iyaye baida kowa sai dangi shi kadai iyayensa Suka Haifa Yana kaunar Yar Zabil a duniya shikam bai bin ko wacce mace sai ita,shine yazo Wai Yana sonta suyi aure tace a’a bai halatta mace ta auri Wanda ba musulmi ba,kayi min komai naka yayi na yarda da Kai amma mu a addininmu bai yuwuwa mace ta auri Wanda ba musulmi ba,Saurayin Yar Zabil Michiel ya damu Nawwar Kamar me shi Yana sonta Nawwar yace a’a sai dai ya musulunta idan Yana so,ya tafi ya dade bai dawo ba an zaci ma ya fasa aurenta sai gashi ya dawo dauke da carbi a hannunsa cikin Jallabiya fara da Yar hularsa tashi ka fiye naci,Nawwar ya dinga dariya a ransa yace kaga sabon tuba,Ashe tafiya yayi ya musulunta ba tare da ya fadawa kowa ba,Nawwar yace karfa ka aureta muji ka koma addininka na baya wlh sai ka sakar Mana ita,yace ai nayi niyya dama ni musulunci ya dade Yana birgeni Kuma ko Bata aure Ni ba bazan fita daga musulunci ba na musulunta sabo da Allah,Nace wlh idan ka aureta Muka ji matsala wallahi sai ka gwammace kida da karatu sai mun kaika Sambisa forest yace Inshaallah Inshaallah,Nawwar yace ya sunanka yanzu? Yace Ahmad Kuma Ina zuwa wajen malami Yana min karatu yace okay idan kunyi aure sai kuci gaba da zuwa tare da ita itama ta Kara ilimi yace to.

    Yar Zabil harda rawa Nima na shiga na shiga nayi kasuwa eh eh eh ya Kika ce ta sanadiyata an musulunta nazo duniya a sa’a ni San Sanda za a haifeni kukana ma haka nake cewa Allah Allah Allah,Mandula tayi dariya,ana haka Nawwar yace Wai zai hada Mandula da Santana aure tace kwarankwatsa dubu bana sonsa,yace Santana yace yarinya kinwa kanki santalelen yaro son kowa kin Wanda ya rasa, ni dama me zanyi dake, Mandula tace baki kamar kana hura algaita bada ni ba,ka gama tambadewa dan Iska ta duma Masa dundu a baya,Nawwar Muna ta dariya Santana yace ni Ina da budurwata ma su nanta Karima tana can a garinmu Adamawa ance bata Yi aure ba har yanzu tuni ma na samo number dinta mun daidaita kije can Mandula Karuwar banza.

   Mandula tace Yaya Nawwar ni dama da Baffa ka hadani,yace Allah ya kiyaye min wlh baki Isa ba ki Zama uwata bada ni ba,Muna ta dariya su Mandula dai ba a samu Miji ba har Baffa yaje ya kai kudin auren Wise wajen iyayenta na Papa,aka sa biki cikin sati biyu sabo da Papa ya matsu Kuma a shirye yake,Wise cokali basu siya ba,Test din aure anyi lafiya Wise take Papa ma Haka.
Munyi Shirin biki Papa harda hada dinner bayan an kawo Amarya,Mama da Sabreen sun hada kansu sai wulakanci sukewa Papa basu San ma an kusa biki,sai ana gobe daurin aure sannan ya sanarwa Mama gobe daurin aure na,Mama tace wallahi sai na tona maka asiri Matukar ka Kara aure,yace ai Kuwa sai dai ki tona in Kinga dama ki Zama kaza sabo da tone tone,Wise anci gyaran jiki ciki da waje ko Ina an matse gam,ana gobe Muka tafi can Jigawa washe gari su Nawwar Papa da Baffa da sauran dangi sunzo 11:am aka daura auren Yusuf da Amaryarsa Hauwa’u,shi dai Papa tun daga kallon gidan su Wise yasan kudin da suka dinga nuna masa babu shi,Kawai suna da rufin asiri,mukus yayi yace ko ba kudin dai na more da sabuwar Amarya matashiya,gaba Daya da Yamma da Dangin Wise Muka taho ranar Yamma likis aka wuce Dinner, Papa an dauki wanka Kamar matashin saurayi haka ya hade ga amaryarsa,Wise ta dinga fitsara tana Masa kiss,Papa Kawai yabi yarima shima aka Sha kida,ya lika kudi na hauka agaban su Nawwar,Auta Nawaf Kuwa tunda ya tabbar budurwarsa Papa ya aure shike Nan yace ba shi ba Papa ya daina kulashi ko ya ganshi baya gaishe shi,Papa ya rasa dalili,daga wajen Dinner aka wuce da Amarya gidan angonta,bangaren Iyamami Muka fara kaita tayi nasiha sannan aka kaita bangarenta.

   Papa sai rawar kafa akeyi da wuri ya wuce bangaren Amarya Wanda Nawwar ya kashe Mata kudi ya zuba Mata komai,Papa Yana Shiga ya iske Amarya a lullube,ya ajiye ledar kayan makulashensa ya rungumeta a haka cikin mayafi Yana shakar kamshinta yace duk wannan nawa ne ni kadai wayyo Allah Dadi kashe Yusufa ya sake kankame Wise itama tana shakar kamshinsa,wise harda pretending irin budurwar Nan,harda rawar jiki ana kame kame kamar zata Yi kuka,Papa yace sorry Naga baki Saba ba a Sannu Zaki Saba,to uhum Wise ta furta kamar munafuka,ya jawo ledar kayan dadi yace Bude min mayafin mana Naga sanyin idaniyata ya cire mayafin,Wise harda boye Fuska Wai kunya take ji,ya Fara ciyar da ita tana kalmashe kaza tana cewa ni bana son ci ma kunyarka nake ji,yace ya za ayi nabar matata cikin yunwa daure,ki maze ki cije dan Allah ki ci ungo karbi,ta sake kalmashe kaza yace yawwa good girl,Wise dariya ta kamata ta kunshe a ranta sai da Suka koshi sannan tayi wanka ta Sanya wata matsiyaciyar rigar bacci komai ana gani a waje,Papa shima yayi wanka ya canja kayan bacci marasa nauyi Riga da wando.

   Yana shiryawa duk ya rude a gigice ya rungumeta yace wayyo Maman Sabreen yau ke dai zaki kwana na tausaya miki shekara da shekaru ana Jin dumin miji kullum, Wise kadan dama take jira macece me sha’awa Kuma gashi an saba,Papa Yana sakin Nishi Yana gurnani ya Fara Sarrafa Wise Yana shafa Boobs dinta yace sak na sweet 16 basa zubewa ke ba irin na Maman Sabreen ba inda kisan mota ta taka kwado a kwalta,dariya ta Kama Wise ta dinga dariya yace Allah Amaryata abu kamar slifas din yara,gashi karami gashi a tatsile Kai na dade Ina cin kwal ubana,tunda ta haihu nake fama,ki dinga min style ita sai dai ta kwanta inda kisan tsohuwar motar a gareji tayi damkam a Kan gado ni zanyi ta wahala sama da shekara talatin a haka nake,Wise dariya yau kamar cikinta zaiyi ciwo ya Fara kissing din bakinta yace haba yanzu naji baiwar Allah a nan amma ita idan ta wage min baki nawa sai ya kule a cikin nata gaba daya da lips din har wajen haba abin ba kanta kaji naki kamar lollipop.
Wise ta daure tayi Kamar bata San Kan komai ba tana kukan zafi zafi,haka Papa ya shigeta da kyar anji magani masu tsada sai kace budurwa irin yanda Yan matan yanzu keyi, a zahiri dadi take ji sabo da ta Saba amma ta fake da kuka tana zafi ka kaini karshe ka kure ni,har sai data Yi loosing control ta Fara Zan mutu,Papa bai gane ba ya zaci zafi ne yasa, Wise anyi dace irin Wanda take so a dade ana aiki dai dai ita ne,ranar farin ciki Kamar me sabo da an tuba an Dade ba a hadu ba sai ranar,a fili Kuma Papa wawa ya dawo ya zauce Yana cewa ta tabbata Mata suna Suka tara,Ashe da wuya nake ci a hannun Maman Sabreen wai wai Sailuba kenan Salam da ita,Ina kaunarki matata karki rabu dani wlh ko me kike so zanyi,Wise ta dinga zunduma kukan karya Wai ya Mata da zafi,Papa ya rasa inda zai sa Kansa taki Shuru,wayata ya kira da sasaafe,bayan mun gaisa yace Yar uwarki ce bata da lafiya tana ta kuka tun jiya kuzo dan Allah,Dariya ta kamani Nawwar Yana ji yace bana son wulakanci Kun samu Babana Kuna ta Raina Masa hankali Kun caka Masa tubabbiyar karuwa a budurwa,Dariya muke,Papa yaga Shuru ban Zo ba ya Kira Star,Star harda Lallaba Papa tace Zan kirata,tana kashe waya ta Kira Wise ta dinga danna Mata ashar lokacin Papa ya fita Wise dariya take Kamar me, Star tace shegiya kin bani darasi Nima Malam haka Zan Masa,wise tace ai ke yasan tuba Kika Yi,zanci uwarki munafuka cewar Star suna ta dariya suna waya,Papa Yana turo kofar Wise waya a kunnena ta barke da kuka tace zafi wayyo Allah azaba dan Allah ku kaini asibiti wayyo Oven wayyo local government,Star taja Tsaki ta kashe wayarta,Papa ya hauro saman bed Yana haba mazarkwailata,Wise tana shesheka tace sunan wata ne fa yiiiiiiiiii zafi tana yarfe hannu.

    Papa anji zuma an gigice shi ya Mata wanka yayi Mata komai tana wani hawaye.
Akan Amarya Papa ko sauraren Su Mama bai Yi,kwanansa uku  ya samu Sabreen a palonsu yace Sabreen ki je ki gaida Mamanki ta biyu,Sabreen bata San ma Wise aka auro ba bata so ma taga komai na auren,baki ta turo ni wlh bazani ba,Mari taji Papa ya zabga Mata ke Ni kike cewa baza kije ba direct sabo da baki da mutunci,tana kuka ta tashi da sauri ta tafi Part din Wise tana zuwa Palo wise tana zaune an harde kafa daya Kan daya an matse cikin kana nan kaya,ko kallon Amarya bata Yi ba tace Ina kwana ta dago zata juya gabanta ya Fadi ganin Wise,da yatsa ta nuna ta tace ke? Wise a nutse tace ei nice Wise ‘yata zo ki zauna mana Lokacin Papa ya shigo Yana Jin Dadi Wise tana tarairayar yarsa Kawai Sabreen ta Kai hannu zata Mari Wise, Wise ta rike Hannu tasa nata ta tsinke Sabreen da mari tas tace Ina matar ubanki ni ba uwarki bace yanzu,ki hankali da kanki,Papa ne yasa baki yace kinyi dai dai good ko gobe ta Miki ki dakata na baki okay,ai ke ba sa’arta bace uwarki Sabreen itace sa’ar yin Amaryata fita ki bani waje shashasha Yar kwaya ya hankada keyar Sabreen tayi waje tana uban kuka sai wajen Mama tana mun Shiga Uku kawar Miracle ya auro wlh karuwa ce,Wise sunanta Karuwa ce yanzu ta mareni Papa ya goyamata baya harda hankada min keya,Mama tace iyyeeee ta mike tsaye ta fice sai part din Amarya,Suna tsaka da soyewa Papa yana uban kiss kamar ba gobe, Wise tana cinyarsa suna love Mama ta fado palon,ya juya kenan Wise tasa hannaye ta tallafo fuskar Papa tana wani shafa gemunsa tana cewa Allah ya Kara ma tsawon rai mijina Nawa na kaina Ni kadai ungo abinka Shata zuge zip din Riga ko a jikinta abinka da Yar duniya tana kokarin ciro nono waje,Mama ihu ta saki ta juya da gudu tana yau na shiga Uku bala’i ya fado min gida, Papa Kuwa ya manta ma da wata mama ya Kama Abu Kamar karamin jariri Yana faman zuka harda lumshe ido Wise ana shafe Masa Suma.

   Iyamami tana part dinta Mama taje ta sanarwa dan hauka Kawai ta taho tace sabo da na barshi ya auri bare shine shima ya dakko min karuwa ta tako har part din Wise da kafafunta tana idan ita Yar iska ce ni Yar guguwa ce ta shigo da bala’i idonta ne ya kyallo danta Yufuf ya koma jariri Yana ta tsotsar dukiyar fulani ana shafa Masa kai Yana Wasa da Daya,Iyamami salati ta rafka Papa zai mike Wise ta rike shi tace please Dadi nake ji ci gaba Sha abinka Allah ne ya baka ko na Iyamami hala baka Sha da yawa ka koshi ba da alama da wuri aka yayeka,Papa yace watana bakwai aka yayeni,Iyamami ta rafka salati ta juya baza ta iya gani ba,har zata tafi ta dawo tace Yusufa ko dai asiri aka maka na shiga uku ni Iyamami Baffa ya haukace kaima kabi sahu  ,Wise tace muje daki Antainarka dadi muje na ja Kaya,Sai da Suka mike sannan Wise tace Laaaa Iyamami Sannu da zuwa ai ban kula ba kiyi hakuri shigo Dan Allah irin wannan ai Knocking ake kin riske mu mun lula duniyar zuma,Iyamami da masifa tace ubanki nace shegiya fitsararriya oh karshen duniya yazo ta fashe da kuka ta juya,Papa yace Iyamami kiyi hakuri wlh bana hankalina ban San kinzo ba kema ai bai dace ki shigo Mana bakatatan ba ai ya kamata ki ja girmanki,dama rufata kuka Yi Kai da Dan uwanka kuka auro karuwa,Papa yace gaskiya Iyamami ba karuwa bace matata ce dan Allah ki daina kiranta da karuwa ni ko Karuwar ce Ina son abata haka,Iyamami ta saki sabon kuka ta fice tana na shiga Uku ku kasheni ku huta,Wise tace ai uwa uwa ce jeka ka lallasheta,Papa yace hankalinki Yana haukata ni,kina da tunani Yar Aljannata tace Ameen ya fice zuwa wajen Iyamami,Sabreen kuwa da Mama hada Kai Suka Yi lallai sai sun kori Wise daga gidan.
Iyamami wajen Baffa ta nufa da kuka ta Shige dakinsa ta sameshi yayi tagumi Yana tunanin Maminsa,Iyamami tana kuka tace Sulaiman naga abinda ya isheni ashe baki kuka hada kuka auro Mana Karuwa,Baffa yace Karuwa Kuma tace uwarka nace dan banza marar mutunci duk ba da Kai aka hada bakin ba kasa ya auri kawar Yarinyar nan fitsararriya Rabi matar Nawwar, abinka da tsofaffi ba kunya tace gashi can a gabana ta bashi Mamanta Yana tsotsa Kamar jariri sai wani Mamul mamul yake yau naga bariki a gabana to wlh ku San yanda zakuyi ko ni ko Karuwar ta juya tana kuka.

     Bikin Star da Malam Abulkhair Yana motsowa yayin da Wise da Papa suke zuba love basa ji basa gani,Santana Kuwa Iyayen tsohuwar budurwarsa sun ce baza su bashi yarsu ba ya Gama barikinsa yazo su bashi yarsu su baza su bawa Dan daudu ba,Muna zaune Yana bamu labari Yana karairaya yace no wahala Shaa ta yiwa kanta sun cuci yarsu,wallahi yarsu Suka cuta wuuu su Karima anji jiki,Mandula tace kaga Santana kaje ka nemi auren Jamcy kawar Sabreen Kawai shegiya,nace abu yayi wlh Santana yace na San fa Baban Yarinyar Muna mutunci ba laifi Yana da hali Kuma sai da na samu shiriya sannan ya sanni,Sanda Nawwar ya aikeni na Kai wani sako to office din Wanda naje a nan muka hadu baku ganshi ba kamilin mutum wlh sai kayan muni ga kirki har number sa ya bani,yayi tafi yace Allah na tuba da Jamcy shi ta yo ai baza ta ganu ba amma dake uwarta tayo gata nan mashaallah ni har Kun sa ma naji Ina sonta,Kuma yanzu Babanta zan samu na shige jikinsa,nace ka nutsu fa sosai,yo mu a gaya mana nutsuwa Allah na tuba.
Haka Santana ya dinga gaishe da Baban Jamcy a awa har ya Fara zuwa gidansa ko Office dinsa suna gaisawa sai da suka Saba sannan ya bullo da cewar yaga yarsa Jamila rannan Yana sonta idan ya amince,Kamar ba Santana ba yanda ya nutsu ya koma namijinsa ga Nawwar ya bashi aiki a kamfaninsa albashinsa me tsoka,a Yar unguwa ta masu rangwamen kudi ya siya Masa gida karami 3bedroom flat da Palo sai kitchen da toilet,Har garinsu ya koma ya kawo Yan Uwansa suka ga gidansa suna ta murna,Shi dai Baban Jamcy ya cika da farin ciki yarsa ta samu masoyi dama ya gaji da iskancin shaye shaye da take a gari,Kawai kiranta yayi yace ya Mata miji Kuma aure ba fashi,bata Isa ta iya Masa musu ba,itama Maman Jamcy ta gaji da halin yarta shi yasa taji Dadi ta marawa mijinta baya,Jamcy anci kuka an gode Allah,Babanta yace ki shirya cikin shiri Wanda na bawa ke a shirye yake sabo da haka aure ba dadewa,sannan zai zo zance yau ko gobe,Jamcy ta fashe da kuka ta Kira Sabreen a waya tana bata labari Sabreen harda bata shawara karki sake yazo wajenki wani zance in an kaishi kya ganshi Kawai ki gudu shine zai tabbatar bakya sonsa sai a fasa auren cikin sauki mu ai da tamu Karuwar muke fama wlh Wai wata Wise kawar Rabi itama Karuwa ce wlh tafi Rabi duniyanci ta hanamu sakewa Kar kiga yanda suke zuba love da Papa a gaban kowa take kiransa da Baby,Wai Papa ne Baby Kuma wlh amsawa yake Wai naam Sweety a gabana fa ai ba tsari,Jamcy tace kice nazo na Sha kallo,Sabreen tace kizo wallahi kiga bariki ai muna kallo a gidan nan.

     Jamcy a ranar da Yamma ta tafi gidan su Sabreen gulma,tana zuwa ko hutawa bata Yi ba suka tafi part din Wise  a palonta Wanda yaji gyara sai kamshi Kawai ke tashi sai da Suka dade sannan Wise ta fito sanye da rigar papa ta wani yadi me kyau,da fara’a tace au kune sannunku kuyi hakuri wlh Babyna nake wa wanka ku zauna,Jamcy tace dama kin haihu ne? ke Yar Kauye mijina uban kawarki ko baki da labari ana cewa masoyi Baby Yar Kauye,Jamcy tace wannan zagin ya shige ni ahhhh ya shige ni,Papa ne ya kwalawa Wise Kira Sweety… Sweetheart….naam Babyna Ina zuwa ta amsa sannan ta kalli su Jamcy tace bari naje Mai Zan shafa Masa ban Gama shirya shi ba kuka zo,Jamcy baki bude take kallon Wise tace Kun Shiga Uku Sabreen taku ta Kare,Sabreen harda kwalla tace bata da kunya tashi mu tafi wallahi a gabanmu zata iya ciro boobs dinta ta bashi tace ya Sha bata da kunya muje Suka bar part din.
Santana an Sha shadda anje zance Jamcy tana gidan su Sabreen,maman Jamcy ta fito da kanta tace Kayi hakuri tana sani ta gudu karka sake zuwa zance haka za’a kawo ma ita gidanka ba dai Iskanci take ji ba Bari a daura auren dai,yanzu kaje kayi test na aure ka kawo Mana itama Zan kaita da kaina ayi Mata yace to Mama ba damuwa na gode Allah ya Kara girma,Mama a ranta tace kalle shi yaro Nutsatse da shi na samu suruki na kirki hhhhhh bata san Santana ba.

    Gaji anji sauki an warke Aunty Amarya Yan uwanta sun dauketa sun maidata wani asibitin Kashi a can suke jinyarta,Itama Gwaggo Gaji ce take jinyarta a wani asibitin Kashi na kudi anyi musu aiki ko wacce Dagaci shi ke dawainiyar komai na Gwaggo Banda Amarya tunda an saketa sai Yan Uwa da suke tallafa masa,Dagaci wahala tasa yayi nadamar halayensa yana tuna abubuwan da ya aikata a rayuwa shi kadai sai ya fashe da kuka yace Allah yasa Rabi tace ta yafe Mana amma dole na sake Neman gafarar Rabi Allah na tuba,tashi yayi yaje har gidan Inna ya samo Sabuwar Number ta,Ina yankewa Nawwar farce Kira ya shigo na daga tare da yin Sallama,Nawwar jikinsa ya maida ni yana taba Boobs dina,Dagaci yace Rabi Baban Mairo ne,nace Oh Ina yini ya gida ya yara yace lafiya Alhmdllh,yace Rabi Kira nayi dan Allah ki yafe min ki yafe Mana dan girman Allah,Murmushi nayi nace wlh ni kam na yafe muku bana rike kowa a raina na yafe a gaida su Gwaggo,Dagaci yace ai mota ta bige Gwaggo ta karye gida hudu Amarya Kuma gida biyar ta karye Gaji ma ita take Jinyar Gwaggo,Nace Subhannallahi Allah ya sawwake ubangiji ya Basu lafiya yace Ameen Ameen,nace an musu aikin ne? Yace ae wallahi na karasa siyar da gonata sai Yan Uwa da Suka taimaka min duk da haka dubu dari asibiti suke nema shima Kuma na Kai musu,Nace Allah sarki Allah ya sawwake zanzo dubiya yace Allah ya kaimu na gode.

    Bayan mun gama waya nace Honey yace Na’am yana shafa gashina nace Dagaci ne yace naji ai,dan Allah Honey….bazan bayar bama Indai wannan mutumin ne mugaye azzalumai Kuma ba inda Zaki je,Na yafe musu ko ba komai uwata ta jefar dani tayi amma a haka matarsa tace tana sona ta min wanka Ina jaririya cikin jini,ka tuna ko karasa yanke min cibi ba a Yi ba,Kuma yanzu wlh ya gane kuskurensa Kuma duk da shi dama bai so aka Raine Ni a gidansa ba ka tuna matar data karairaye itace tace tana so na,taci Kashi na da fitsarina ko ba komai wallahi tayi kokari,kokarin banza matar data kulla Miki sharri Suka koreki daga gidansu,ban san Dagaci ne ya min asiri na fada bariki ba shi yasa na zake nace to ba gashi ta wuce ba, da basu koreni ba ta Ina zamu hadu kaddarata ce,kaddarar haduwa da kaine,tunda kin yafe musu ba shikenan ba sai kin bashi wani kudi,ko ba komai ai suci arzikin Rabin da suke ganin bata ma da amfani a duniya gashi Allah ya min baiwa ni na tallafa musu,Allah Yana son me hakuri da yafiya,shi Kansa Muna masa laifi ya yafe Mana,bazan bayar ba ki nemi naki ki bashi,haka kace yace ae,Fushi nayi na jefar da Nail cutter di. Yace Dole ma Zaki dawo ki yanke kin San ba me yankewa sai ke,tafiyata nayi na koma dakina na kwanta nace lallai ma mutumin nan wato na nemi nawa na bashi,wato gori zai min akan kudi,shigowa yayi bedroom dina na fashe da kukan shagwaba,yace ya Miki kyau da me zanji ne ance Miki hako kudi nake yi ne,kawayenki wace ban dauki nauyinta ba ki duba irin kudin da nake kashewa,Mami ta tafi Saudiya ni ke daukan nauyi sannan yanzu ki kawo min wasu mutanen banza har kina kuka akansu,Shashasha wacce bata kanta ba,nace nice shashshar ko? Yana hararata yace da mecece to,nace wlh sai na fadawa Baffa,Kuma zaka San ka ce min shashasha zaka sani na mike Zan sake ficewa rungumoni yayi yace Sorry ba shashasha bace Yi hakuri please,Nawwar tsoro yake ji ko Zan hanashi hakkinsa,fisgewa nayi na bar Masa dakin,Zuwa dare nayi Shirin baccina na nufi dakinsa cikin rigar baccina hadaddiya maroon,ya zaci bazan zo ba,Yana ta aiki a System dinsa na gaji da Zama nace kazo mu kwanta,Me Kika ce ya juyo da sauri,Murmushi nayi nace kazo mu kwanta nace,yace ai banyi zaton Zaki zo ba,akan me? Yace sabo da munyi fada,nace Kuma akan munyi fada shike nan sai na kauracewa mijina bada ni ba,System din ya rufe yace Allah ya Miki Albarka ya hauro saman bed Muka kwanta yana Kara Jin kaunata a ransa,yace Nawa za a Baki? a Raina nace kaji aikin hakuri duk abinda hakuri bai baka ba to tsiya ma baza ta baka shi ba,gashi a banza yace Nawa nake so gaskiya wasu matan Muna cutar kanmu wajen Fushi da miji a kaurace masa.
A fili nace a’a ka barshi Allah abin ai zai maka yawa sai yanzu naga ma bai dace nace ka bani kudi ba kayi hakuri,su Dagaci basu cancanci na basu komai ba,no za a basu ai ko banza sun raineki amma abinda nake so ki fahimta a sake barinsu suji jiki tukun,nace to ba damuwa,wlh kwanan nan Ina yawan Jin tashin zuciya anya Kuwa ba ciki ka min ba ko fa period 1month kenan banyi ba,Murmushi yayi yace Allah yasa,ubangiji yasa cikin ne da naji dadi,gobe muje asibiti ko,nace to,yau ma kwana Muka Yi Muna raya sunna.
Washe gari da wuri ya kaini asibiti duk wasu gwaji an min bani da cikin komai Wai Ulcer ce ta kamani sannan rashin period ma stress Yana kawowa zai canja time din zuwa ne,ya rubuta min magunguna Muka dawo Ina ta Jin haushi Nawwar Yana min dariya sai tsokanata yake.
Me aiki ya samo min wata dattijuwa me kwari a gidan Baffa take aiki bangaren Mami akwaita da kwazo ga hankali Laure kenan.
Ana gobe daurin auren Wise muka dunguma sai Yobe Papa da kyar ya bar Wise sai da tayi Masa kuka,Star a gidan Malam fa.

Mairo duk wasu takardu an musu da visa sai tafiya kawai,washe gari suka Yi shiri sai Airport a can Suka Iske maza matasa Suma wani kamfani ne zai kaisu,su Mairo bata kamfani bane,Cele a Kasko da Kakanta Su Kuma ta mota Suka tafi zasu bi ta Sudan sannan su tsallaka Saudiya ta ruwa,akwai masu tafiya Kuma ta Hanya gurbatacciya Wanda Basu da takardun komai zuwa kasashe daban daban ba sai lallai Saudiyya ba.

Masu Sharhi na gode

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*
_Jama’a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau’i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number…… 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k’iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da ‘yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!…ga masu bukatar sari ko sayan d’aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi…….*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya ‘kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu ‘batawa kai lokaci🙏🏻_

_nfection_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu’amula mussaman ga ma’aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za’a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_

_Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

AsmaBaffa
🌼’YAR AIKIN KARUWAI🌼
LITTAFIN KYAUTA NE

               101-105

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA DUKKAN YARAN TSUNTUWA

Page naki ne
ALHUSNA

 

        Bikin Star muna can ana warwasawa Nawwar sai gobe daurin aure zaizo sai waya muke su Wise suna ta zirga zirga,in kaga Star sai kace ba ita bace irin gyaran data sha,Ustaz sai wani bugo waya yake,dare yayi Muna kwance dukkanmu  Wanda Suka rage,Yan Uwa suna ta hada hada,Star tana waya da shi tace karfa gobe na ganka da rawani sai kace wani liman ato wannan shaddar da na zabo maka aka dinka ita zaka sako dama itace ta daurin aure ai,Malam yace dama yaushe ni na Isa ranki ya dade ai sai abinda kike so,kayan ke Kika sa na dinka set goma Sha biyar ai sabo da angwanci sai kace na hadawa kaina lefe takalma ma gasu nan kin zaba min na siya,sai nake ganin Kamar lefen da na hada Miki akwati biyar sunyi kadan,Star tace a’a sunyi gaskiya ba makusa Kaya fa ka zuba masu tsada,yace wato ainihin Yayata ce ta hado kayan suna son ki,Star tace na gode musu,sun dade suna waya harda cewa gobe i yanzu muna tare,Star tana ji ta daki Mandula kasa kasa yanda bazai ji ba tace kinji Malam abar kaikayi take Masa,dariya Muka yi tayi sauri ta datse Wayar tana cewa aikin banza sai ya ji ku Kuma ku fa ba a sirri daku.
Washe gari 2pm aka daura Auren Aisha Star da Angonta Abulkhair akan Sadaki dubu dari,Sai Kanwarta Saima da Angonta itama Sadaki dubu dari, Star tana Jin labari an daura taci gayu cikin wani dakakken leshi pink, Fitowa tayi cikin danginsu da take Jin haushin su basu taimaka musu ba a rayuwa sai da biki yazo sun zo sun dame su suna murna Kamar wani kaunar su suke yi, tace Dan bakin ciki sai dai ya sheka lahira ban balbalce ba bamu shiga wani hali ba,Kuma cutar da ake ce min zata kashe ni HIV Allah ya tsare baiwarsa gashi na auri malami Ustaz ma kuwa Kuma me hankali,Kanwata ta samu Ilimi Kuma uwata taci me kyau ta Sha me kyau Allah bai bamu kunya b…Maman Star ce tazo tace wallahi ranki zai baci idan baki bar Maganar nan ba,Star Allah yayita da biyayyar iyaye bata musu ko kadan Shuru tayi ta dinga chasa uban rawa a kidan da su Saima Suka kunna da kawayenta speaker suna bin wakar Auta mg boy kin Zama amarya.

    Saima ma shigowa tayi ta rungume Star suna rawar su a haka suna bin wakar ana ta kallonsu,wata tsohuwa tace Yara man kaza Indai Namiji ne ba dan goyo bane,su fa gani suke Yi Babu Kamar su yanzu a dacen miji zaku ci ubanku ku tambaye mu halin maza mu baku labari,Taron abokan Ango gaba daya sunzo Yan Izala sun Sha shaddoji sai kamshi sukeyi,Saima kunya taji ta daina rawar amma Banda Star a gaban abokansa manyan malamai na sunna harda shugabannin Izala sun zo amma Star Hannun Malam biyu ta riko suna facing juna,mu Kuwa da su Wise sai hotuna muke musu da videos tunda yace ba party shi dan Izala ne,Malam kunya ta kamasu,Mandula tace Malam anzo hannu,sai da maza Suka Yi dariya ganin yanda Muka Raina Malam,kidan aka kashe nazo nace video nake Malam,Star tace Abukhair gyara Wai ba wani Malam yanzu ita Kam yanzu ba Malam,daga baya Kuma sai ga Nawwar ya shigo cikin arniyar shaddarsa arsh Kamar shine angon Yan Mata da dukkan Mata sai kallonsa suke,wata na maida Kansa Ina Masa video Ido Muka hada ya harareni Yana Murmushi Wai na saka karamin mayafi,ya wuce Suka gaisa da Maman Star da danginta suna ta Masa godiya,ana cewa Baban Star ne shine ya dauki nauyin komai,Ni Kuwa Ina ta Masa video duk abinda yake Ina dauka,Ina ji Maman Star tana cewa ai shine waliyyin Aisha shine ya daura Mata aure,a Raina nace iyye su Nawwar an girma harda walicci,angwaye Kuwa ana yin pics a gurguje Suka tafi,Nawwar ya fito dukkan mu Muka tattara har su Yar Zabil aka mana pics sannan yace min tafiya zanyi sauri nake Ina da meeting 4pm ,ku taho fa yau yau naji ana cewa sai gobe za a kawo Amarya ba wannan zancen,Nace Maman Star tace ita ba Wanda zai zauna ayi biki biyu daga yau an gama yanzu zamu taho da Amarya,yace okay danginta mutum nawa? Nace ai har Mamanta sai wata a Dangin uba shike Nan Wai,yace to shike nan hakan ma yayi muje ki rakani,Ina zuwa a motar Airport aka kawo shi ya Shiga ya koma ni Kuma na koma muka ci gaba da bidiri,Ashe Papa ma yazo sai ji Muka yi ya Kira Wise a waya Wai Yana kofar gida,can Muka je Muka gaisa,bai dade ba ya tafi shima.

    5pm muka Fara Kai Saima dake a garin take Mama harda kuka,nace yanzu wa za a barwa Mama su zauna tare? Star tace Yar uwarta ce daga Kauye Haule ta dawo wajenta tunda itama Dattijuwar ce tare zasu zauna,nace okay Muna dawowa muka bi jirgi Muka koma,Wise mijinta ya dauki nauyinta,Sera Kuwa Sabeer ya biya,Yar Zabil Ahmad tubabben Saurayinta ne, sai Santana shi ya biya Kansa yazo daurin aure ya koma abinsa,sai Mandula da ni Nawwar ya dauki nauyin mu.
A cikin tawagar Angwaye wani yaro Wanda bai fi 26yrs ba matashi ya makale Wai Mandula yake so,Muka ta Mata dariya tace Allah ya kiyaye min,wani ma a yobe Yana sonta yace ita baza ta bar kudu ba ta Saba da can Indai ba a kudu ba baza tayi aure ba,Haka wani Dan Kano shima yace Yana so wlh mutumin arziki da shi tace Sam bata so.

   Amma yaron nan sabo da ta ganshi kyakyawa dashi handsome Dan fari Wai shi ya mata Indai Yana da aikin yi shike nan yaron da bashi da bashi da komai yanzu ma ya gama University shima Dan yanzu ana karatu da wuri ne shi yasa har ya gama.
Mun taho da Amarya a jirgi,jirgin cike yake da mutane Star tace haka ake dakko Amarya ba guda wa yasan Amarya ce da Allah ku girgiza Mana mutanen jirgin nan,Yar Zabil da su Mandula,Sera suka saki guda Suka dinga sharara guda suna tafi dukkan mutanen jirgi kallo ya dawo kanmu,hausawa suna cewa Amarya Suka dakko,Ni dai Ina ta video suna guda da tafi mun dakko Amaryar Ustaz,Mama ce ta gaji tace Kai dalla kuyi Mana shuru muna sararin samaniya rayuwar mu tana hatsari amma ku guda ma kuke,Muna zuwa Muka ce anzo anzo yeeeeeeee   sai sabuwar guda ana ta dariya.

Muna sauka Malam tuni an turo motoci uku Muka shige sai gidan Star bamu da wani nisa da ita,Gidane me bene Hawa Daya dan cif cif Kyakyawan gida,gate me cin mota biyu Masha Allah gidan yayi ya hadu kayan daki na kirki itama Nawwar ya zuba Mata ko Ina an tsara mata,mun Kai dukkan kayanta da lefe can,Mama harda kuka taga gidan yarta tayi ta Mata nasiha sannan a ranar Suka juya a jirgi Nawwar yasa Santana ya rakasu har gida ya dawo sabo da tsofaffi ne basu taba Hawa jirgi ba.
Star ana gadonta a zaune mun Kara gyara ko Ina mun turare ko Ina da kamshi,9pm sai Malam muka gani ya canja wankan yadi me kyau yayi kyau sosai dama gashi dan Kyakyawan Ustaz, Wise tace to nifa Sweety yazo daukana ta fice wajen Papa yazo daukanta da kansa yau kwananta ne, tana shiga mota yace ko girki baki min ba tace na gaji yau gaskiya mu wuce mu ci a restaurant,yace to Suka wuce hadadden wajen cin abinci a can Suka ci Suka koshi harda take away na kayan makulashe Suka dawo gida.
Mandula da Yar Zabil ma sun tafi gidana tare da Sera,Star tace Miracle Dan Allah ki kawo Mana abinci da safe ko me aiki ki aiko nace gwara da Kika ce na Aiko da me aiki kin san yanda Nawwar yake da zalama Jiya bana gida yau sai ta Allah,dariya tayi tace to mayu kice ni su Sera masu zaman banza su dafa su kawo min,nace to an gama,Malam Kamar zai koreni haka yake ji,nace Malam sai kayi hakuri fa mijina nake jira,dariya yayi yace nace Miki wani Abu ni ya cire hularsa,Malam da tara uban Suma ta Sha gyara,Ina zaune ni dai Malam harda fara yiwa Amarya addoi yana Mata nasiha,dariya nake a raina nace Malam to ai ka bri na tafi,yace ai rage Hanya nake Kinga na gama da wannan babin sai na gaba,Star ta mintsineni kadan ta cikin mayafi Wai gulmar Malam take,Nawwar ne ya kirani na mike nace Zan tafi,ta jawoni na kawo Mata kunnena ta min rada tace Yasin bana gane Nasiharsa dama Antaina ya bari ai tayi min nata yafi shiga,dariya nayi nace Malam sai da safe harda bin bayana ya rufe kofarsa Kamar zai datse min hannu.

    Gaban motar Nawwar na shiga ya ja motar Muka tafi,nace Walliyin Star dariya yayi yace wlh danginta ne Suka ce sai na karba,tun a mota ya Fara min adumbule ya hanani sakewa,Muna komawa nace bari naje wajen Sera na fada musu sakon Star,Rakani yayi har can na fada musu suyi Mata girki da safe wata taje ta Kai,Suka ce to,Nawwar daukana yayi harda sabani a kafada Muna shiga Palo muka samu Nawaf Autan Mami da sauri Nawwar ya ajiyeni ya Fara Masa masifa sai ka dinga zuwa gidan mutane baza ka fada ba dazu na fita sabo da kasan code din kofar ko,Auta ya kalleni yace wallahi Aunty baki kyauta min ba shine kuka bawa Papa Budurwa ta ya aure sabo da shi Yana da kudi,ai sa’a kuka ci nazo ma da nace na daina kula kowa, dariya nayi nace to kayi hakuri Auta Zan samo maka dai dai kai,bana so ya furta,Nawwar yace Wai Kai Kuwa kalau kake Wise din katuwa da ita ta ya zaka iya da ita Dan yaro da Kai sai balagar zuci,Auta yace to da ku aura min Mana kaga yanda zanyi da ita wallahi wata tara ta haihu,Amma Papa sai ta shekara biyar bata Yi ko Bari ba,Nawwar ne yaje zai mammake shi ya tashi da gudu ya fice ya bar gidan yana fushi yana masifa yace duk gashi nan Yaya Yana da kudi sai samowa mutane aiki yake Yana aurar da wasu Yana kyauta da kudi amma Dake dan tsako ne samu kaki dangi ni ya hanani aiki sai karatu kullum a takura min da makaranta kudi ma baza a bani ba,Baffa ma yayi ta min fada ni an tsane ni,gida ya koma Yana zuwa gida yaga Papa da Wise sun dawo ya dinga hararar Papa,Wise ita tasan zancen tace Auta ba magana,yaro tsakani da Allah Kamar zaiyi kuka ya juya yayi tafiyarsa,Papa yace na rasa me na yiwa yaron nan yanzu ya tsaneni sai harara tsakanina da shi,Wise tace kuruciya ce kowa da tasa zai daina ne.

     Ni kuwa na gaji yau amma Nawwar sai da ya sake tara min gajiya duk da yanzu na Saba Ina Jin dadin Sex din sosai.
Star Kuwa Malam da ledarsa ya dawo bayan ya rufe kofar,mayafin ma Star ta cire abinta tuni ita, ko da ya bude kayan dadi shi ya bata a baki Wai kunya take ji,Malam harda Jin Dadi ya zaci Nasihar ce tayi aiki,bai san pretending bane kawai,bayan sunci sun koshi shi ya Fara wanka ya fito sannan ta Shiga tana Jin kunya Wai kallon surar Malam akwai kunya,Malam harda dariya shi a dole namiji, wanka tayi ta fito ta gudu dakinta ya bita da kallo harda dan gudunta,shiri tayi ko Ina lungu da sako kamshi yake ta saka rigar bacci ba marabarta da tsirara,tana shugowa ta tsaya a bakin kofa tana wani bobboye jiki Malam an hamkimce a saman gadonsa Yana Shan kallo yace Alhmdllh mashaallah Allah ya albarkace ni da samu mace sankakaceciya,tasowa yayi yana kallonta yayin da Antaina tuni ta sankame,ta bayanta ya zaga Yana kallon mazaunanta yace Alhmdllh tabarakallah ya rungumota ta baya wato Allah ya Miki baiwar mama Wanda batureh ke Kira da mango shape harda wani Kara h shi ga Malam,yace irin wannan ko haihuwa goma zakiyi basa zubewa za a dade ana cin duniya da su sai mu dage wajen kula dasu,Star tana ta dariya a ranta tace kaji Malam ashe shima dan duniya ne,Maganar ce ta fada a fili bata sani ba sai ji tayi Malam ya bata amsa yace in banda abinki me sunan tauraro ai ba a lahira Malam yake ba a duniya nake Kuma ni ba waliyyi bane Malam ne kawai,mu Kuwa malamai baza a gaya Mana babin kwanciyar aure ba sai dai mu koyar da mutum ma bare ma Kinga na taba aure, na dade Ina fama da sha’awa babu Mata yanzu Allah ya azurtani da samunki Kinga sai bushasha,Star tace Sannu Alhaji bushasha,Malam yace yawwa irin wannan shu’unin lamari ba’a Wasa dashi,Malam ya Fara murza Star yana shidewa sai Alhmdllh yake cewa Yana murza Boobs ya furta Masha Allah mu karasa kan Sarir mu kwanta, lokacin Star tace au Bed da larabci Sarir? Yace Na’am yana shafa dukiyar fulaninta,Saman bed ya jata Suka fada saman bed,ya cire Mata kayan jikinta shima ya cire nasa,Wise taga Antainar Malam katuwa tace mashaallah Allah ya azurtani da anifin azzakar gungumemeh tayi yanda Malam yake da murya,Malam Yana dariya yace duk wasu sunnoni munyi har Sallah yanzu tambayoyin da kike min su zan fara amsa miki a zahiri, kina tambaya Malam ya halalta kwanciya ta hanyar goho yau duk zan amsa miki su, Abhulkhair a nutse yake Sarrafa Star suna murza juna,tun tana nuna kunya har tayi watsi da kunya suna kashe juna da love, Malam ya Fara harka,Star ta Fara haukata shi da salonsa sai sambatu yake Mata ya zauce,Malam dan hannu harda sucking Star ta Sha yanda iya sarrafa mace ka rantse bai hada Hanya da malinta ba,Yana shigarta a nutse ya haukace tare da furta na tsunduma a tafki….Yana ta ihu da Nishin dadi Yana sakin zance wani abin ma Sai an toshe kunne, malam…Malam..Malam…Star take iya furtawa tana ihu ai Kuwa Malam yace laa Malam Sahibi ne,Habiby dinki,Malam ana Jin dadi Yana Kiran Star da Noorita Noor….yau Malam an sha zuma,Star tasha kiss da sambatu sai Albarka yake sa mata,Star taji Dadi yau na musamman Malam ya hadu,tace aure da dadi yake,Malam Kuwa ya zama wani surkududu,sai Albarka yake sawa Star ya rasa inda zai tsoma ransa sabo da farin cikin da ya tsinci Kansa a ciki.

    Seraline Kuwa Sabeer yace shi zai Mata komai gidanta ya zuba Mata komai cokali bai bukata,Mandula da yaronta Omar sai love suke yaro ya siye zuciyarta gashi baza a barshi yayi aure yanzu ba,a tawagar Yan Uwan Malam Abulkhair yazo bikin haka Suka hadu da Mandula,Nawwar Gajiya yayi da zuwan yaron zance kusan kullum sai yazo,aka nemi mijin Star Malam shi ya Fadi komai na yaro family ne na kirki Kawai baida aiki ne,Iyayen mutanen kirki ne,Nawwar yaje ya fada musu komai Baban yaron yace gaskiya Omar baida Sana’a ya Gama karatu dai cikin gidajena guda biyu da Suka rage dama na bashi daya,nasa ne guda Daya sabo da halin rayuwa,yayyensa ma basu Yi aure ba tukun,amma idan ya samu aiki bani da matsala zai iya aurensa,Kuma muma a bamu dama muyi bincike,Nawwar yace idan Kun amince babana zai bashi aiki a kamfaninsa,sai Murna da farin ciki Suka ce ba matsala,ko da Suka je bincikensu Suka ji ai Mandula Yar asalin dangi ce Amma a Nan kudu take Zama gidan Yan uwansu sabo da tunda Mandula ta bar gida sai babarta sabo da gudun abin kunya tace ta kaita wajen Yar uwarta,Kuma watarana suna ganin Mandula tana zuwa a shigar Kamala tunaninsu ma wayewa tayi a can,shi yasa basu San tayi bariki ba,shi dama Omar tunda yaji ance Alhmdllh Yarinyar kirki ce ya dinga murna shi yasan Mandula bata da kunya Kuma ta fada masa ta danyi duniyanci idan Yana sonta a haka to,so Hana ganin laifi ba ruwansa yace ko ta haifi yara goma a duniya shi Yana so bare bata da ko daya,Haka ake so ko wanne haline ko cuta a daina rufar maza a fadawa mutum gaskiya idan Yana so a Haka ya aura amma idan aka boyewa mutum abu yazo yaga ba yanda ya zata ba to fa baza a zauna lafiya ba.
Wajen Baffa Nawwar yakai takardun yaro aka bashi aiki babba,iyayensa Suka Dan hada Masa kudi ya sake gyara gidansa me kyau 3bedroom flat da Palo sai harda toilet ta tsakar gida bayan ta dakuna,Yar Zabil da Sera ba abinda Nawwar yayi komai mazajensu sun dauka Rana Daya aka daura aure,munyi munyi a raba auren Anki,Ni Ina wajen Sera a can garinmu,Star tana wajen Yar Zabil,Wise tana wajen Mandula,ko wacce aka daura aure aka tattaro aka taho da amare sai da Muka je gidan ko waccen su,Mandula ce kadai Nawwar ya Mata komai sabo da iyayenta Basu da karfi babarta sai kuka take tana nadamar halayenta na dorawa yarta talla komai ita a Bata kudi,haka na Yar Zabil Babanta ya Dade da sakin matarsa wacce take zugawa Yana tsine Mata ya yafe Mata ya nemi gafararta.

   Dukkan Amaren ba Wanda ya Kai Mandula Shan soyayya Dake yaro ne bashi da matsala itace tayi disvirgin dinsa,sai abinda tace sai yanda tayi da shi yaro duk ya susuce yaji dadi gashi da jini a jika ta koya Masa jaraba,Sabeer ma Shuru kake ji ko aiki an daina zuwa an wani kashe waya Seraline tana kashe shi da dadinta,
Yar Zabil me tubabbe ma ba a barsu a baya ba.
Bayan wata daya Wise ta kwace Papa sai abinda tace,Yau Sabreen bata da kudi taje har part din Wise dake yau a dakin Wise yake ba na Mama ba ta samu Papa a dining an shirya Masa better Yana iba,tana zuwa tace Papa dan dubu hamsim din da ka min Alkawari,Wise tana cin abinci itama tace baza a baki ba baki da aiki sai shaye shaye kudin a banza ake baki marar tarbiyya,kullum kice kudi kudi sai shaye shayen banza,Papa yace to kinji dama na gaji da baki kudi gaba Daya ke kike talauta ni kece Kika jefa Ni a halaka sabo da na biya Miki bukatunki tashi ki bani waje,Sabreen ta mike cike da takaici,Wise race idan bai wuce dubu daya ba a bak, ko kula Wise bata Yi ba itaje ta fadawa Mamanta,Mama ta fito a fusace tace wallahi na gaji yau sai na tona Masa asiri bangaren Iyamami taje cike da bala’i tace ke tsohuwa wacce bata iya tarbiyya ba ki sani danki Yusuf shi ya kashe Dan Uwansa na Jini Sunusi guba ya sa Masa a hankali ya Fara rashin lafiya ya mutu sabo da hassada da son kudi na gaji da rufa Masa asiri,shine ya tura Yan fashi Suka yiwa Baffa fashin milliyoyin kudi sabo da ya dauki nauyin yarsa,yanzu Haka shine ya siyar da wasu kadarori na Baffa ba tare da shi Baffan ya sani ba,na gaji da rufa Masa asiri,gwara ayi uwar watsi,Papa ya taho wajen Iyamami yaji abinda Mama ke fada jikinsa ya hau tsuma,lokacin tare suke da Wise,ta rufe baki tace cab di,Iyamami ta kwashe Mama da Mari tace Yar sharri,Papa ne ya shiga yace gaskiya ta fada ya zube gwiwoyinsa a kasa hawaye Yana zuba a idanuwansa yace wannan abin da nayi shine mafi Muni a rayuwata na rasa yanda zanyi na iya fada amma abin Yana damuna bana samun sukuni idan na tuna nine sanadin dan Uwana,Ki Kira Sulaiman ya kaini kotu a yanke min hukuncin kisa ko naji sanyi a raina,ya kalli Mama yace kema a yau dole na Fadi naki kece Kika Hana faccalarki zaman lafiya kece munafuka.

  Labari ya Fara bayarwa yace Sanda taga faccalarta Mamin Nawwar tana zaune lafiya da mijinta gashi mijinta yafini kudi shine ta hada baki da wani mutum a matsayin babban malami ne yake zuwa Yana fadawa Baffa Mami tana Neman ransa tana Masa asiri nan gaba idan bai gujeta ya kaurace Mata ba zata iya kashe shi,kullum malamin nan Yana zuga Baffan Nawwar Yana fada Masa karairayi tun baya yarda har ya yarda ya Fara wulakanta Mami da yaranta Kuma da sa hannunki kema Iyamami ko Baki San da zancen ba? Iyamami tayi mukus yaci gaba yace sabo da kin tsani Mami kina ganin ta mallake Miki danki kuka hada Baki,sannan ke Kika jawo har na iya kashe Dan uwana kullum sai ki dinga cewa nine abin tausayi bani da komai sai dai na zauna a karkashin Yan Uwana Kika dinga cewa Mami ce tasa Baffa Bai maidani me kudin gaske ba duk kuwa da kokarin da yake ke ba kya gani ai wani baya yiwa wani arziki Kuma gidajen da na siyar na Baffa kece Kika zugani Kika ce na siyar ai bazai gane ba,duk kece Kika dinga hada Yan Uwa fada dama irin wannan wasu Iyayen suke raba Kan yaynsu ya karasa Yana kuka,Iyamami tana kuka wiwi tace ai bance ka kashe Sunusi ba,ke Kika zugani Kika ce sun hada Kai sun ware Ni sun fini arziki kece wallahi ko me ya faru kece kika dinga zugani, Baffa da ya Riga ya shugo tare da Nawwar kafarsa kasa daukansa tayi ya zube saman kujera sabo da bacin rai, Maman Sabreen asirinta ya tonu Sai kuka, Iyamami kuka Papa ma kuka,Nawwar mamaki yake abin kamar a mafarki,Iyamami faduwa tayi ta sume aka kwasheta zuwa asibiti gaba daya Kuma aka tattara har Wise zuwa asibitin,an Dade kafin Iyamami ta farfado,Baffa da Papa sune a kanta a hankali ta Bude idonta tana magana a hankali tace ku yafe min dan Allah,Hannun Baffa ta kamo ta kamo na Papa tace ku yafe min dan Allah ku hada kanki ku yafi juna,Yusuf kayi kuskure Amma da hannuna a ciki ban San abin zai Kai ga kisa ba,tunda ka Gane gaskiya ka tuba ga Allah kabi Allah ka gyara kuskurenka yanzu a Zamanin nan ko an kaika kotu ba lallai ma a yanke maka hukunci dai dai da laifinka ba,Abu ya faru sama da shekara talatin me za ayi,Papa yace za a iya yanke min hukunci Mana Sulaiman ya kaini kotu ko naji sanyi a raina ya sake fashewa da kuka yace wlh tun daga ranar da Sunusi ya mutu na rasa kwanciyar hankali in na tuna nakan kasa bacci ya zanyi da hakkinsa,Baffa bai iya magana ba ma bare Nawwar,Mama tana gida tana tattara nata ya nata ta gudu gida garinsu itama tana ta kuka,Sabreen ce tazo da gudu tace Papa Mama ta tafi,Papa yace tafi ruwa gudu na saketa saki daya Zan rubuta Mata takardarta,Sulaiman yace shashasha mutumin banza mene amfanin sakin nata,Papa Wise ya ruko ta fisge hannunta tace yo Ni ai ban San laifin naka yakai haka ba wlh bazan zauna da makashi ba,Nawwar yace ai Kuwa kinyi karya,wani yace kice kina sonsa ba inda zaije Kuma Zama a gidansa ba fashi idan Kuma kece kike da kanki sai ki tafi gida na gani,Wise tace gidanka Zan koma ai,yace badai gidana ba,tace idan banzo gidanka ba gidan wa zanzo wallahi nan Zan dawo dole ne na taho ta fice daga Asibitin hankalin Papa ya sake tashi shi Kam a baya Dan kudi auri Wise amma tunda tazo gidansa ya fada kaunarta da gaske son da bai taba yin irinsa ba,Nawwar yace Papa kayi kuskure da badan abin nan ya Dade ba wlh da kaina Zan Kai kararka,yanzu ma zaka iya Nawwar mene amfanina,Baffa ne ya harari Nawwar yace Wai Ina ruwanka ne bana son rashin kunya,Nawwar yace ai gashi nan garin son malamanku masu kudinmu sai a samu wani banza kazamin malami ya dinga zugaku tunaninku yasan gaibu,Kuma karya ce sannan ma malamin ma kaji fake ne wani katon banza ne ya shiga rigar Yan tsubu yace Yana hango maka Mami tana Neman ranka wannan daga ji kasan ba gaskiya bane,Mami kafi kowa sanin wacece,Zanci ubanka idan baka min Shuru ba Saura naji zancen a wajen matarka,Nawwar yace ita da take kawarka baka suruka da ita sai kawance kuyi ta hirarku bakwa so ma naji zancenku dan taji Mene.

    Iyamami duk ta cika dakin da kuka tana kaicona nayi asara gwara na mutu na huta,Papa yace ba inda Zaki tafi Dake zamuyi nadama muna nan Allah ya Kara tsawon rai.
Wise ma kayanta ta iba sai gidan Nawwar,ta shigo min tana kuka nace lafiya tace Sweety ne,nace sakinki yayi? tace a’a,nace to mene ke da bakya sonsa Kika ce asirinsa Zaki tono,wlh Ina sonsa yanzu ni na kamu da son mijina,to Mene Wise taki fada wai an iya boye laifin miji ba a so a tonawa miji asiri,Nayi nayi ta fada min taki fada,nace ke Kika jiyo kuma,sai da ta gaji sannan ta bani labarin komai mamaki ya kamani nace tab aiki ja,Kuma sai ki taho tunda dai Yana nan Abu ya faru shekara aru aru mene amfanin tahowar,Wise ta zumburo baki tace bazan koma ba idan Zaki koreni Kuma to,nace a’a me yayi zafi idan Nawwar yazo dai kin san sai ya koraki.
Nawwar Kuwa Yana dawowa ya dauki wise ya maidata da kansa,ana mayar da ita ta daina kula Papa.
Sabreen sai ita kadai tace gwara ma na samu mijina nayi aure na huta da wannan bala’in na gidanmu,shaye shayen ma yaushe rabo tunda aka kawo wannan shegiyar Papa ya daina bani kudi ta hana shi.

      Cele Kuwa motarsu sai da Suka je tsakiyar Sahara ta lalace sunfi su ashirin a motar Mata duk sunfi yawa sai maza,Yan matan ciki kwata kwata mutum hudu ne,Cele,Sameera,lawisa,murja sai maza matasa su Uku,Abdul,Mustapha,Awwalu,sai irin su Kakan cele mutum biyu,sauran Kuma duk matane manya dasu.
Dake su Mairo a jirgi Suka tafi su har sun Isa kasa me tsarki,sai Wanda mazane matasa Kamfani ya kaisu ciki akwai Bashir,Bello,Aminu,Danlitu da sauransu,sai masu zuwa wasu kasashen daban daban.

       KARSHEN YAR AIKIN KARUWAI KENAN

    SAI BOOOK 2 ME TAKEN MATAFIYA DA ZAMU SHIGA BAYAN NA HUTA NA SATI BIYU ZAMU DAWO MU DORA DAGA INDA MUKA TSAYA.

WANNAN BOOK2 MATAFIYA, DARASINSA DABAN NE DA NA BOOK1,SANNAN WANNAN KARON STAR DINMU ITACE CELE A KASKO ME KAMA DA RABI SAK WATO RUFAIDA ,ZAMU DINGA TABO MUKU BANGAREN SU RABI SUMA TUNDA LABARIN YA SHAFE SU SUNA DA DANGANTA DA SHI SANNAN A BOOK1 KARKU MANTA BA A GAMA BA FA AKWAI SAURA DAN KO RABI BATA SAMU CIKI BA TUKUN,GASHI ZAMU JI YANDA ZAMAN AUREN WISE ZAI KAYA,SAI NA SU STAR SUMA,SAI MAKOMAR MAMI DA BAFFA,DAGACI SHIMA DUK SAI A BOOK2 MATAFIYA.
INSHAALLAH INA FATA LABARIN DAKE CIKIN BOOK2 MATAFIYA ZAI FADAR YA ILIMANTAR KUMA YA NISHADANTAR DOMIN AKWAI NISHADI SOSAI A GABA.
FANS INSHAALLAH ZAKU DARA A BOOK2 MATAFIYA.

  LABARI NE AKAN MUTANEN MU YANZU WANDA SUKE TAFIYA NEMAN KUDI KASASHEN DUNIYA,WASU KASASHEN MUSAMMAN YANKIN LARABAWA,WASU IN SUNJE SUNA DACEWA SU SAMU ABINDA SUKA JE NEMA SHIMA ABU NE ME KYAU,SAI MASU AKASIN HAKA IDAN KA FADA HANNUN NA BANZA,KO KAJE DAGA NEMAN KUDI MATAN MU SUNA LALACEWA ACAN,WASU SU KOMA BARIKI,WASU SU FADA LESBIAN,WASU KUMA A SAMU WANDA YAN KASA NE SU BAUTAR DA MUTUM TA HANYA DA DAMA,GA MATAYENMU MUSAMMAN NA KAUYUKA DA AURENSU MACE TA BAR YARANTA TA TAFI TAKARCI WATA KASA,WATA TAJE A BASHI,WASU DA KUDINSU DA DUK WASU TAKARDU,WASU TA BARAUNIYAR HANYA KO GURBATACCIYAR HANYA SUKE TSALLAKAWA KASASHE,WASU SU TSIRA DA RAYUKANSU,WASU KUMA A HANYA MA SUKE MUTUWA WAHALA   TASA SU RASA RANSU.
WASU WAJEN TAFIYAR MA SU FADA HANNUN YAN DAMFARA,SAI AN KIYAYE AN KULA SOSAI WANNAN BA KARAMIN ZUBAR MANA DA MUTUNCI YAKE BA A IDON DUNIYA.

   INSHAALLAH BOOK2 SAI YA BAKU MAMAKI,KUMA A CIKI ZA A KARASA MUKU BANGAREN SU RABI

KARKU MANTA STAR DINMU CELE ME KAMA DA RABI SAK.

 

ASMABAFFA

Leave a Reply

Back to top button